Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

tana buga game da sauri ta mik'e a lokacin data ga Alhaji Bala ya fad'o d'akin kamar Wanda aka hankad'o




Alhaji Bala wani irin ajiyar zuciya ya sauke tare da dafe zuciyarsa a lokacin daya ga Naila


Naila a tsorace tace "Daddy Lafiya kuwa"?


Alhaji Bala girgiza mata kai kawai yayi ya juya yayi waje


A tsakiyar d'akinsa ya tsaya tare da d'ora hannunsa aka yana tunanin mafita dan Na Maliya yafi k'arfinsa ahaka ya raba dare yana tunani sai da wani tunani ya fad'o mishi ya saki wani murmushi cike da farinciki dan gani yake idan yayi haka shikenan Babu yanda za'ayi Na Maliya ya d'auke mishi Naila da wanan tunanin ya samu bacci yayi awon gaba dashi rabon da yayi bacci cikin dadin rai irin wanan har ya manta



Bashi ya farka ba sai wajen Tara da rabi na safe yana kuwa tashi ko sallah bai yi ba ya fice daga gidan dan yaje ya sama musu Visa shi da Naila dan barin k'asan shi zai fiye mishi Alheri



Bai dawo gidan ba sai wajen k'arfe hud'u yana zuwa yacewa Hajiya Lubna ta fara had'awa Naila kayanta zasu bar k'asan goben nan


Mamaki ne ya rufe Hajiya Lubna da Naila zasu yi magana Alhaji Bala ya dakatar dasu ta hanyar d'aga musu hannu yace " bana San tambayoyi ki had'a mata kayanta kawai gobe zamu tafi Dubai ke kuma zaki iya tafiya garinku idan na dawo zan biyo na d'auke ki"



Hajiya Lubna wani mamakin ne ya k'ara rufeta tace "mai Naila zata je tayi a Dubai Al halin basuyi hutun makaranta ba wai nikam Alhaji mai ke faruwane da kake b'oye min wlh idan baka fad'amin ba babu inda za'a kai min 'ya dan Sam bana gane maka kwana biyu idan wani abun ne zai samu Naila ka fad'amin mana"


Wani mugun tsaki Alhaji Bala yaja yace "kindai San bazan cutar da 'yata ba ko ko ke baki isa ki had'a kanki dani ba awajen kaunar Naila gobe zan kai ta Dubai idan an kwana biyu zan dawo da ita idan kinga dama ki had'a mata kayanta idan baki ga dama ba ki barshi idan munje can na siya mata sababi"



Daga haka Alhaji Bala ya shige d'akinsa


Hajiya Lubna zaman dirshan tayi akan kujera tana tunanin mai Alhaji Bala ke nufi da kai Naila Dubai definately akwai abinda ke faruwa da yake b'oye musu"



Naila kuwa tsoron Alhaji bala ne yafara rufeta dan bai tab'a cewa zai kai ta waje ita kad'ai batare da mahaifiyarta ba

A takaice haka su ukun sukayi jungum jungum ko abincin dare babu Wanda ya ci acikinsu

*2:am*


Alhaji Bala kwance akan gadonsa shi kad'ai sai sakin munshari yake alamar yana jin dadin baccin da yake yi



Hajiya Lubna kuwa tana kwance ita da Naila dan tare suke kwana


Kamar a Mafarki Hajiya Lubna taji ana ja mata k'afa bud'e idon da zata yi sai tayi tozali da wani dirkakken mutum a tsaye hannunsa rik'e da wani dogon bindiga sallati tayi cikin fad'uwar gaba ta bud'e idonta sosai anan taga su wajen shidda ne duk sun d'ora k'afa akan gadon da suke a kwance kai ko baka fad'a ba kana ganinsu kasan Arna ne dan dukansu wuyansu sanye yake da cross gasu murtuka murtuka



Naila itama juyawa tayi da zumar ta gyara kwanciyarta kamar cewa akayi ta b'ude idonta tayi tozali da samudawan da suka zagaye gadon da suke kwance babu alamar imani Sam a tattare dasu dan bama su San shi ba tunda arna ne




Jikin Hajiya Lubna rawa kawai yake bakinta ma haka


Da hannu d'aya murjejen dake gabanta ya damk'ota daga kan gadon ya wurgar da ita k'asa d'ayan ma ya cakumo Naila da hannu d'aya sukayi waje


A babban palon gidan suka zubar dasu


Anan ma wasu hud'un ne a zaune akan kujera sun ma fi wayanda suka shiga d'akin Girma da tsayi


Tuni hantar cikin Hajiya Lubna ya kad'a Naila kuwa tafara shivering



Cikin Command Wanda ke zaune akan One seater yace "go and fetch me the boss"


Da sauri biyu a cikinsu suka nufi b'angaren Alhaji Bala



Alhaji Bala kuwa hancinsa a sake sai sharara munshari yake bai ma San abinda ke faruwa ba



Wani wawan duka John ya sakarwa Alhaji Bala a cinya


Alhaji Bala ya mik'e a firgice

Hantar cikinsa ne ya kad'a a lokacin da yayi tozali da wayanda ke tsaye akansa kafin ya kai ga tunanin wani Abu


John ya capko hannunsa yaja shi daga kan gadon


Alhaji Bala ji yayi kamar da rodi John ya rik'eshi ahaka suka hankad'a keyar Alhaji Bala sai gasu agaban Steven ogansu gabad'aya



Steven kuwa kalle kalle kawai yake yana pito sai wasa yake da bindigar hannunsa

Alhaji Bala kuwa tuni ya jike da gumi cikinsa na murd'a mishi dan wadanan sun fi k'arfinsa nesa ba kusa ba addu'a kawai yake aransa Allah yasa iya kud'i suka zo d'auka



Steven cikin kakausar murya yace "Mr man you know wetin bring us so no waste our time if u mess up I go scatter your head"


Alhaji Bala jiki na rawa yace "okey sir if it is money u would have it but pls don't harm us"


Wani Mahaukacin Dariya suka kwashe dashi gabad'aya Steven yace "go bring money jare na only money we go chop and this girl we get tiny tiny breast"


Steven yace yana kai hannu kirjin Naila dake rawar Dari


Alhaji Bala cikin tashin hankali da kad'uwa ya daka tsalle yaje ya tsaya agaban Steven gabansa na mugun fad'uwa..........



Dan dan dashhhhhhhh anzo wajen 馃弮馃徎鈥嶁檧馃弮馃徎鈥嶁檧馃弮馃徎鈥嶁檧馃弮馃徎鈥嶁檧馃弮馃徎鈥嶁檧
[2:39PM, 4/7/2018] 鈥�+234 806 462 6766鈥�: 馃寫 馃寫 *B馃叞K'IN D馃叞RE*馃寫馃寫馃寫馃寫馃寫馃寫馃寫馃寫馃寫


*Written by*
馃拝馃拝 *Sadnaf*馃拝馃拝


*A heart touching story*



庐 *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
_莎蓻 蓶啤艐'脓 啤艐俪醿� 蓻艐脓蓻艡脓膮谋艐 艐蓶 蓻蓶懦膯膮脓蓻, 醿撑� 莎蓻 膮俪艦啤 脓啤懦膯骚 蓶 骚蓻膮艡脓 啤蕜 艡蓻膮蓶蓻'艦_


#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
*#IG PML WRITERS*
#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
#http://maryamsbello.blogspot.com




*Follow me on Wattpad@Sadnaf*




*Wanan shafin naku ne*


*Billy shantali*
*Meenah parrot*
*Meela Adeel*
*Biebie Isa*
*Sholingaye*
*Ummu arfat kanwata*
*Da duk wacce take cikin grps d'in Sadnaf Hausa novels*

*page 12*




Steven wani irin Kallo yayi wa Alhaji Bala dake Neman sakin fitsari a wando yace "ehe wetin shock you like this go inside bring money Jo u dey waste our time"


"Alhaji Bala zubewa yayi agaban Steven yana "Sir I beg u in the name of God make u no harm my pikin she is the onIy one I have I go give you plenty money and oll my cars we dey outside"


Steven Dariya ya kwashe dashi yace " u beg me with who"?

Cikin rawar murya Alhaji Bala yace "God and Jesus"


Kyalkyalewa sukayi da dariya gabad'aya har Ogansu Steven na fad'owa daga kan kujera da k'yar ya tsayar da dariyarsa yace "me I no even know God before you go waste your time beg me with am I beg go bring money make I chop food dey go"



Fad'ar tashin hankalin da Alhaji Bala ya tsinci kansa a ciki b'ata bakine banda lugude babu abinda kirjinsa ke yi


Mugun tsawan da Chucks ya mishi ne ya sa fitsarin da yake rik'ewa ya k'wace mishi "Go bring money my friend u think say na play bring us here"


Aguje Alhaji Bala ya nufi d'akinsa Obi da Emmanuel suka bishi a baya


Duk kud'ad'en dake cikin gidan sai Da Alhaji Bala ya fito musu dashi jikinsa sai rawa yake addu'a kawai yake Allah yasa kar su tab'a mishi Naila



Sai da su Emma suka tabbatar da duka kud'in dake cikin gidan ya fito musu dashi sanan suka koma palon


Ghana must go d'in suka ajiye agaban Steven


Steven ya saki wani murmushi ta gefen baki ya janyo Ghana must go d'in ya zura Hanun shi a ciki ya d'ebo 'yan dari biyar biyar ya kai hancinsa yana shinshinawa tare da Lumshe ido


A hankli ya bud'e idonsa ya Kalli Obi yace "Money good ooo today we go enjoy now mak una separate una self mak una choose food wen una go eat me na dis rat I go eat bcos na fresh blood she be"


Da Sauri suka raba Kansu gida biyu Obi Emma John Chuku Destiny sukayi wajen da Hajiya Lubna ke durk'ushe jikinta na mugun rawa suka tsaya agefenta suna wani Lashe lebb'e


Steven kuwa wani irin murmushi kawai yake yana kad'a k'afa yabi su Daniel Uche Ikenna Andy da kallo da suka tsaya a kusa da Naila ce musu yayi "una sure say only me no go fit kill this rat we dey my front because even me na she I go eat"


Naila a guje ta nufi wajen Alhaji Bala ta kankameshi jikinta na mugun rawa Dan ta d'auka su biyar d'in harbeta zasu yi cikin matsanacin kuka tace "Daddy ka taimakeni kar ka bari suyi min komai sunce harbeni zasu yi Daddy karka bari su Kasheni"



Alhaji Bala zuba mata ido kawai yayi take ya fara ganin fuskar sa'arta da yayi raping a lokacin da suka je fashi wani gida yarinyar haka taje ta kankame Mahaifinta tana kukan ya taimaketa amma me fincikota yayi ya yage kayan jikinta Mahaifinta babu kalan rok'on da bai mishi ba kuka sosai Mahaifinta ya ringa yi yana rik'e mishi k'afa da yaga ya takura mishi ya buga mishi gindin bindiga akai take ya suma awajen shi kuwa ya Danne yarinyar ya mata fyad'e tun kan aje ko ina yarinyar ta daina numfashi har ya gama bidirinsa Lion ya hau ya sauka Killer shima ya hau duk da yarinyar bata numfashi ahaka suka baro gidan basu sani ba ko ta mutu ko tana rayye wai sai gashi abun ya juyo kansa 'yarsa da yake tattallawa wasu na Neman keta mata had'i


Ihun Naila ne ya dawo dashi daga tunanin daya tafi a lokacin da Steven yazo ya janyeta daga gabansa babu ko kaya a jikinsa



Alhaji Bala shima ihun ya saka dan hallitar Steven ya tsorata shi babu shaka idan ya kusanci Naila zai iya kasheta




A guje yaje ya durk'usa agaban Steven ya rik'e mishi k'afa hawaye na gudu a kuncinsa mantawa ma yayi Steven baya jin Hausa ya fara rok'onsa yana "Dan Girman Allah karkayi Mata komai yarinya ce bazata iya d'aukarka ba idan ka kusanceta kasheta zaka yi ka taimaka min zan baka duk dukiyata ita kad'ai gareni Dan Allah"



Steven bai ma San mai Alhaji Bala yake cewa ba yafara k'ok'arin Danne Naila



Naila kuwa sai Ihu take da iya k'arfinta tana "Daddy karka bari ya kasheni Daddy kazo ka taimakeni"


Alhaji Bala duka ya fara kaiwa Steven cikin tashin hankali yana kuka



Steven kuwa ko gezau bai yi ba dan kamar ba dukan shi ake ba




A fusace Emmanuel ya janyo Alhaji Bala ya zuba mishi naushi a fuska a take jini ya b'alle a hancinsa yaji gidan na juya mishi Dan kamar da guduma ya buga mishi hanci ahankali ya sulale k'asa tare da Rik'e kansa da hannu Biyu Dan jiyake kamar ba a duniya yake ba


Hajiya Lubna kuwa Steven kawai ta zubawa ido a lokacin da ya danne Naila da ko motsi bata iya yi sai ihu sabida mugun Nauyi da kib'ar Steven Jikinta rawa kawai yake tana wani tsuma ita kadai



Mugun Ihun da Naila ta fasa ne yasa Alhaji Bala ya d'an dawo Hayyacinsa Hajiya Lubna kuwa ta Kira Sunan Naila da K'arfi




Alhaji Bala wani gigitacen ihu ya fasa a lokacin da yaga Steven ya rufe Naila ruf baka hango komai nata in ba tafin k'afa ba rose flower dake kan center table Ya raruma yayi kan Steven a guje Kafin ya k'arasa wajensa chuku ya tare shi ya zuba mishi naushi biyu a fuska a take Alhaji Bala ya baje a k'asa



Steven wani mugun dariya ya kwashe dashi a lokacin da yake d'aga Nailan dake kwance ko numfashi bata yi cewa yayi "this girl no strong at all she just be like toy I no even do anything she dey faint I beg mak we no kill person pikin Daniel na only u go ride am mak d rest leave am go chop d Mama may b she go strong pass in pikin mak una do fast make we dey go"


Daniel da Sauri ya cire kayansa yana wani lashe lebb'e yayi kan Naila


Emmanuel kuwa ya nufi wajen Hajiya Lubna shima yana zare belt d'in dake kugunsa




Wani irin zabura Hajiya Lubna tayi ta mik'e suka fara k'ok'awa da Emmanuel aikuwa ya zuba mata lafiyayyun mari biyu daya sa taga stars tadiyeta yayi ya hau ruwan cikinta tsabar azaba Hajiya Lubna k'asa ma ihu tayi Dan ji take kamar itace yake tura mata agabanta ga wani mugun wari dake fita a jikinsa ga masifar nauyi ahaka ya gama bidirinsa ya sauka John shima ya zo ya hau ruwan cikinta tun Hajiya Lubna najin radadi da zugi da azaba a hankali ta fara k'ok'awa da numfashinta sai da suka sadu da ita dukansu duk da itama ta daina numfashin


Alhaji Bala kuwa yana daga kwance yana kallon duk abinda suke yi take ya fara tuna lokacin da ya ketawa wata mata haddi da duka da cizo da yak'ushi haka ya danneta mijinta da yaranta nata ihu ko sauraransu bai yi ba sai gashi shima agaban idonsa wajen maza bakwai sun sadu da matarsa ya kasa yin komai


A hankali suka fara sulalewa daga palon bayan sun d'auki kud'in Steven ne kusan na k'arshe k'afa yasa ya hambareshi yana "Stand up my friend mak u carry them go hospital may be dem still dey alive d next time I go come na u I go chop cos me I dey do boys and girls" daga haka ya yasaka kai ya bar palon


Alhaji Bala kuka ya fashe dashi ya yunkura dak'yar Dan kansa kamar ba a jikinsa ba da rarrafe ya k'arasa wajen Nailan da bata numfashi ko kad'an


Jijigata ya fara yi da k'arfi yana kiran sunanta yana ta taimaka mishi karta mutu ta bar shi

da sauri ya kinkimeta yayi waje da ita ya saka ta a mota ya koma ya kinkimi Hajiya Lubna ya saka ta a mota itama sai kuka yake kamar k'aramin yaro aguje ya ja motar ya bar gidan ba tare da yabi ta kan mai gadi dake d'aure ba



Emergency akayi dasu Naila dan tun a bakin gate aka taro shi dan ya musu waya



Alhaji Bala kuwa ana shigewa dasu Naila ya zube a k'asa yana wani irin kuka



Bayan minti goma da aka shiga dasu sai ga likita yafito daga d'akin yana sharce gumi


A guje Alhaji Bala yaje ya tare shi yana "Ya 'yata ta farfad'o"?

Doctor ahankali ya sauke ajiyar zuciya cikin tausayawa yace " Am sorry sir we lost her but your wife is alive"



Wani irin razanannan ihu Alhaji Bala ya saki ya zube a k'asa a sume


Nurses sukayi kan shi a guje dan su bashi taimakon gaggawa



Da k'yar Alhaji Bala ya farfad'o ahankali ya bud'e idonsa yana karewa Likitocin dake kansa a tsaye kallo ahankali maganar doctor ya fara dawo mishi "Am sorry we lost her but your wife is alive"


Wani mugun ihu ya sa yana kiran Sunan Naila ya mik'e cikin zafin Nama duk ruk'on da likitocin suka mishi sai da ya zubar dasu yayi waje aguje ya nufi d'akin da aka kwantar da su Naila



Kan Naila yayi da sauri da aka rufe mata fuska ya bud'e zanin da aka rufe ta dashi ya zubawa Naila ido yana kallonta tamkar bacci take


Rungumeta yayi gam ya fashe da wani irin kuka yana "Naila mai yasa kika tafi kika barni bayan kinsan banida sama dake Naila dan Allah ki dawo zan baki Raina"


Kuka Alhaji Bala yake sosai yana kankame da Naila


Likitoci kuwa suka ringa k'ok'arin banbare shi daga jikin Naila da k'yar suka iya janye shi suka yi waje dashi


Alhaji Bala kuwa ya kwanta a k'asa ya ringa ihu yana kururuwa yana a taso masa Naila ita kad'ai gare shi


Zumbur ya mik'e yayi waje da sauri yana bazai yarda ba sai ya kashe su Steven............
[2:39PM, 4/7/2018] 鈥�+234 806 462 6766鈥�: 馃寫 馃寫 *B馃叞K'IN D馃叞RE*馃寫馃寫馃寫馃寫馃寫馃寫馃寫馃寫馃寫


*Written by*
馃拝馃拝 *Sadnaf*馃拝馃拝


*A heart touching story*



庐 *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
_莎蓻 蓶啤艐'脓 啤艐俪醿� 蓻艐脓蓻艡脓膮谋艐 艐蓶 蓻蓶懦膯膮脓蓻, 醿撑� 莎蓻 膮俪艦啤 脓啤懦膯骚 蓶 骚蓻膮艡脓 啤蕜 艡蓻膮蓶蓻'艦_


#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
*#IG PML WRITERS*
#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
#http://maryamsbello.blogspot.com




*Follow me on Wattpad@Sadnaf*


*Page 13*




Dak'yar aka kamo Alhaji Bala Dan sam ba a hayyacinsa yake ba



Hajiya Lubna kuwa tunda ta farka ta zubawa gawan Naila ido tana ta zubar da hawaye dan gani take kamar a mafarki wai Naila ta rasu kuka ta fashe dashi sosai tana kiran sunan Naila a lokacin da taje ta yaye mayafin Da aka rufe Naila dashi ta kankameta tana kuka


Dak'yar Nurses suka janyeta



Alhaji Bala kamar ya haukace a lokacin da aka saka gawan Naila a ambulance aka nufi gidansa Dan ayi mata sutura akai ta gidanta na gaskiya



Sai ririk'eshi ake yi yana tirjewa


Hajiya Lubna kuwa wani irin d'auriya ne yazo mata ta ringa addu'oi aranta


Kafin kace me mutane sunji Labarin mutuwar Naila 'ya d'aya tilo ga Alhaji Bala kasancewarsa sananne mai taimakawa talakawa kowane gidan radio da television labarin kawai ake yi


Akram da ogansa Abdullahi na zaune a lokacin da suke kallon labaran a tashar NTA

Akram kabbara yayi a lokacin da yaji sanadin mutuwar Naila Dan Alhaji Bala tamkar mahaukaci duk wanda ya gani sai yace mishi agaban idonsa akayiwa 'yarsa fyad'e har ta mutu dan haka bazai yarda ba sai inda k'arfinsa ya kare


Akram girgiza kansa yayi yacewa Ogansa "Allahu Akbar Allah da girma yake abinda Alhaji Bala yakewa yaran mutane da matan mutane gashi ya juyo kansa tun ba'aje ko ina wlh baka ga yanda yake ji da yarinya nan ba idan kana so kaga fara'arsa da dariyarsa ka kira shi da Daddyn Naila wlh naji tausayin yarinyar laifin mahaifinta ya shafeta"


"Eee da tausayi dan tausayi kam dan batayi saan uba ba Sam to yanzu da aka mishi mutuwa zai yiwu muyi arresting d'inshi a gobe kuwa"?


Abdullahi yace yana kallon Akram


Akram shiru yayi na 'yan mintuna kafin yace " ina ganin mu k'ara gwada Alhaji Bala mugani ko ya dan rusuna sabida abinda akayi wa 'yarsa mu bashi zuwa nan da sati biyu mugani ko ya kira ko bai kira ba zamuje muyi arresting d'inshi kawai abinda zamuyi a k'ara tsare yaransa sosai sabida kar ya gano shirin da ake akansa"


Da haka sukayi ta tattaunawa ta hanyoyi da zasu b'ullowa Alhaji Bala



Alhaji Bala kuwa rik'eshi akayi tayi lokacin da aka zo fita da gawan Naila sai ihu yake yana kiran sunanta


Hajiya Lubna kuwa d'aurewa tayi sosai tayiwa 'yarta addu'ar rahamar Allah har aka tafi kaita gidanta na gaskiya



A haka idan kaga Alhaji Bala sai ya masifar baka tausayi dan mutane sun San irin San da yake wa Naila sai surutu yake shi kad'ai yana sai ya nemo barayin da suka kashe mishi 'ya wasu ma sun d'auka ko tab'in hankali ya samu


Manyan mutane ne suka ringa zuwa mishi gaisuwa sabida sun San yanda yake hidimantawa talakawa ciki kuwa har da wasu 'yan siyasa


A cikin masu zuwa kalilan d'in mutane ne kawai Alhaji Bala bai yiwa fashi ba wani Alhaji Ghali hamshakin mai kudi dake tashen Naira shima ya biyo wani abokinsa dan suyi wa Alhaji Bala gaisuwa



Duk da Alhaji Bala baya iya amsa gaisuwar da ake mishi amma yana sane da duk wayanda suke zuwan mishi gaisuwa tunda Alhaji Ghali ya zauna Alhaji Bala ke satar kallonsa dan ko iya suturar dake jikinsa da agogon dake sak'ale a hannun shi idan ka kalla kasan ba k'aramin kud'i aka kashe wajen siyansu ba


Su kuwa tattaunawa kawai suke akan yanda b'arayi suka addabi Mutane bayan sun maka sata ma bazasu barka haka ba ko suyi kissan kai ko suyi raping d'in iyalanka mata Alhaji Ghali kuwa shima sai tofa albarkacin bakinsa yake yana cewa A Nigeria babu matakan tsaro sosai shi yasa barayi ke abinda suka ga dama dan babu kasar da ake yin haka sama da Nigeria dan haka yana gama ginin gidansa a Cairo zai kwashe iyalinsa su koma can dan duka yaransa ma can suke karatu Hutu kawai ke kawo su nan shima yana kasuwancinsa acan sosai



Duk hirar da suke Alhaji Bala ya baje kunnuwansa yana jinsu a zuciyarsa yana tunanin Alhaji Ghali shine next target d'insa dan abinda su Steven suka mishi yasa ya k'ara jin babu ko digon imani azuciyarsa


A cikin hirar da suke yi Alhaji Bala ya ringa samun information akan Alhaji Ghali da irin sana'ar da yake yi kansa a sunkuye yana wani Jan carbi kamar bai San hirar da suke ba mik'ewa sukayi suna k'ara yiwa Alhaji Bala gaisuwa tare da bashi shawaran ya saka yan sanda su binciko wayanda suka mishi wanan aika aika



Alhaji Bala godiya kawai yake musu yana share hawayen dake zubo mishi su kuwa tausayin Alhaji Bala ya ringa rufesu dan sun San irin kaunar da yakewa tilon 'yarsa


Har bakin mota Alhaji Bala ya rakasu yana k'ara nazarin Alhaji Ghali inda har ya rike lambar motar Alhaji Ghali har sai da suka tafi ya juya ya koma yana sak'e sak'e aransa


Bayan kwana bakwai da rasuwar Naila Alhaji Bala yana zaune a d'akinsa shi kad'ai ya saka hoton Naila a gaba yana kallo sai hawaye ke zuba a idonsa da ace zai iya ganinsu Steven da babu abinda zai hana ya kashesu ya yankasu ya k'ona su


Hajiya Lubna kuwa tafi Alhaji Bala tawakalli dan tasan Allah da ya basu Naila yafi su San ta har mamakin rashin tawakkalin Alhaji Bala take



A yanzu ma zuwa tayi ta tarar da shi yasa ka hoton Naila agaban yana kuka


girgiza kanta tayi ta nufi inda yake ta zauna a gefensa tare da d'ora hannunta akan kafad'arsa


Wani irin zabura Alhaji Bala yayi kamar an d'ora mishi wuta yabi Hajiya lubna da wani mugun kallo




Hajiya Lubna sakin baki tayi tana kallon shi cikin tsananin mamaki


d'aurewa tayi tace "Alhaji Lafiya mai yafaru"?


Wani Mugun kallon ya k'ara binta dashi yace " ki fitar min daga d'aki bana San ganinki babu matar dana tsana sama dake wlh naso ace ke kika mutu ba Naila ba yar iska kawai mara mutunci"


Jikin Hajiya Lubna ne ya hau rawa sabida girgiza da tayi da maganarsa hawaye kuwa suka hau wanke mata fuska cikin in ina tace "Mai na maka haka Alhaji"?



" dalla ki b'ace min da gani har ni zaki ringa tambaya mai kika min sabida ke tantiriyar 'yar iska ce agaban idona maza bakwai sukayi layi akanki suna saduwa dake tsabagen kina jin dadin abinda suke miki ko tari bakiyi ba ballantana naji ihunki ballantana akai ga kiyi k'ok'awa dasu akan kar su sadu dake lumshe idonki kawai kikayi kina jin dadi Lubna Ashe ke yar iska ce bansani ba wlh na masifar tsanarki bazan iya cigaba da zama dake ba kyankyaminki ma nakeyi"


Hajiya Lubna zubewa tayi a k'asa kirjinta uwa ya fad'o k'asa ta ringa nanata "Innalillahi wa inna ilaihi rajiun" kallon Alhaji Bala kawai take dayake binta da wani irin kallon tsana cikin matsanacin kukan da ta fashe dashi tace "Bala nice yar iskar a zo har cikin gida ayi mana fyad'e nida 'yata bakayi wani yunkuri dan ka hanasu keta mana haddi ba har na rasa 'yata amma ka ce min 'yar iska kai da kake namiji ma sunfi k'arfinka sai ni danake mace zanyi k'ok'awa dasu"


Wani mugun tsawa Alhaji Bala ya daka mata yana "dalla rufe min baki yar iska sa'oinki da ake zuwa yi musu fashi a nemi a keta musu haddin kinsan irin k'ok'awar da muke yi dasu dan kawai kar a keta musu haddi akwai matar ma da sai da ta gwammace ta rasa ranta da a keta mata haddi Dana 'ya'yanta amma tsabagen ke 'yar iska ce kwanciyarki kawai kikayi suka ringa hawanki suna sauka"


Alhaji Bala Sam bai San ya saki layi ba


Hajiya Lubna kuwa kalmarsa kawai ke amsa kuwaaa a kunenta "


_Kinsan irin k'ok'awar da mukeyi dasu dan kawai kar a keta musu haddi_


Kanta taji ya mata nauyi a hankali ta mik'e ta fara ja da baya tana nuna Alhaji Bala cikin rawar murya da jiki tana "Bala Bala dama kai dan

Please Login or Register in order to submit comment