Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

"Daddy yana tsaye fa aka kashe""""

Da Sauri Alhaji Nazifi ya katse ta yana "Sau nawa kukeso na ringa fad'a muku kwanan mahaifiyarku ya Riga da ya kare ko ya hana shi ko bai hana shi ba sai ta amsa kiran mahallici and j told u guys this young guy is doing his job bansan wane irin kunne ne daku maza ki koma ki d'auko musu ruwan sha kafin na sasab'a miki"


Da Sauri Saheeba tayi waje a tsorace Dan wani irin tsoron Akram takeji


Tana ficewa Alhaji Nazifi yace "am so sorry for what happen kasan yarinta ke damunsu tun ranar da asirin Alhaji Bala ya tonu suke ta surutai sun k'asa ganewa akan aikinka kake aikinku ya gaji haka in banda yarinta idan Ajali ya kira ai sai kaje"


Akram jiki a sanyaye ya d'ago yace "Alhaji nasan hakan zai faru Dole yaranka su tsane ni zakayi mamakin abubuwan danayi undergoing kafin nasamu nassarar capke Alhaji Bala wlh I left my family I live a miserable life just to reveal his secret pls tell your children to forgive me wlh ba laifina bane sai kayi pretending you are one of them zaka iya gano irin su Alhaji Bala"


Alhaji Nazifi murmushi yayi yace "haba Akram karka wani damu aikin Alheri kayi Dan ba dan kai d'in ba babu Wanda zai San true colour d'in Alhaji Bala da yana nan yana tapka b'arna a d'oron k'asa karka wani damu yarana basu tsaneka ba kawai wanan bak'in Daren da suka rasa Mahaifiyarsu ne bazasu iya mantawa ba"


Yazeed godiya ya fara yiwa Alhaji Nazifi shi kuwa Akram gabad'aya jikinsa ya k'ara sanyi ya rasa mai ke mishi dadi dan yasan watak'ila haka Samha ta tsane shi idan taganshi zata tsorata kamar yanda Saheeba ta tsorata


Yazeed fad'awa Alhaji Nazifi yayi na abinda ke tafe dasu na Akram yaga d'aya daga cikin 'ya'yansa yana so kuma ba wasa ya kawo shi ba Aurenta yake so yayi

Akram d'agowa yayi ya kalli Alhaji Nazifi dan yaga yanda ya k'arbi zancen aikuwa ya hango tsantsar farinciki a fuskar Alhaji Nazifi dan murmushi kawai yake yi hakan ne yasa yaji sanyi aransa dan yasan koda Samha zata bashi matsala Alhaji Nazifi zai iya shawo kanta


Alhaji Nazifi duk da yaji dadin maganar da suka zo dashi dan babu Wanda zai k'i bawa Akram 'yarsa ya Aura sai da yadan jinjina lamarin aransa duk da baisan wa yake so a cikinsu ba yasan sai an kai ruwa rana koma wacece a cikinsu zata amince ta Aure shi sabida kiyayyar da suke mishi


Alhaji Nazifi ce musu yayi babu Matsala indai ta b'angarensa ne addu'a zai raka su dashi Allah ya musu zabin da yafi Alheri amma Abu d'aya ne zai sa bazai bashi Auren 'yarsa ba idan dai ta nuna bata sansa dan gaskiya babu wacce zai yiwa Auren dole a cikinsu ballantana ya tursasa wacce yake so duk da bai San wa yake so a cikin yaran nasa ba


Sai a lokacin Alhaji Nazifi ya tambayeshi wa yake so a cikin 'ya'yansa


Akram da jikinsa ya gama mutuwa gabad'aya da maganar Alhaji Nazifi dak'yar ya bud'e baki yace k'aramar cikinsu yake so"


Ajiyar zuciya Alhaji Nazifi ya sauke yace babu damuwa bari ya fita ya turo musu ita Allah yasa su dai-daita


Godiya suka had'a baki suna mishi har ya fice daga palon


Yana fita Yazeed ya daki kafad'arsa yana mik'ewa tare da tsallen murna yana "Abokina wlh na samu irin matar danake so na Aura gaskiya 'yar nan tasa data fita ta had'u"


Akram tsaki yayi ya buga tagumi yana kallon bakin k'ofa fargaba duk tabi ta cika shi

Yazeed kuwa sai santin kyaun Saheeba yake yana shima ana kwana biyu zai zo ya samu Alhaji Nazifi akan yana Santa



Alhaji Nazifi kuwa a lokacin da ya isa b'angarensu a Palo ya tarar dasu a zaune sunyi jungum jungum kamar wayanda akayi wa rasuwa


Yana shiga palon Suhaima tayi Sauri ta tare shi tana tambayarshi dagaske Akram ne yazo gidansu?


Suhaima kuwa tana rakub'e a gefe kirjinta kamar ya fad'o k'asa tunda Saheeba ta gaya musu Akram yazo taji jikinta na rawa tama rasa wane irin tunani zatayi


Alhaji Nazifi kuwa waje ya samu ya zauna ya kirasu d'aya bayan d'aya suna Amsawa

A hankali ya fara musu Nasiha mai ratsa jiki yana nuna musu su ajiye kiyayyar da suke yiwa Akram bashi da laifi a mutuwar Hajiya Nafeesa akan aikinsa yake koda ma basu zo ba a ranar kwanan Hajiya Nafeesa yariga da ya kare nasiha ya musu sosai sai da ya tabbatar da jikinsu yayi sanyi ya maida kallonsa kan Samha da ta had'a gumin babu gaira babu dalili yace mata sabida ita Akram yazo wajensa yana Santa da Aure



Wani irin mik'ewa Samha tayi hankali a tashe ta nuna kanta tana " Daddy ni yake so da Aure kuma ka amince wlh ni bana sansa na tsane shi bana so na bud'i ido na ganshi bazan iya Aurensa ba"


Tana gama fad'ar haka tayi d'akinsu da gudu Tana kuka


Alhaji Nazifi bayanta yabi da kallo har ta shige dan yasan dama za'a Rina bazata yi accepting Akram cikin Sauki ba


Mik'ewa yayi ya koma palon b'aki ya bawa Akram hakuri akan su dawo wani lokacin insha Allahu zai yi k'ok'arin ya shawo kan Samha idan kuma ta d'age bata San shi sai dai yayi hakuri dan bazai iya tilasta mata ba


Akram ji yayi kamar guduma Alhaji Nazifi ke kwad'a mishi aka sabida yanda yaji nauyin maganar take hankalinsa ya tashi dan agaskiya bazai iya hakura da Samha ba yanda yake jin mugun Santa a zuciyarsa


Alhaji Nazifi kuwa ganin yanda Hankalin Akram ya tashi yasa yafara kwantar masa da hankali yana kar ya damu zai yi k'ok'ari ya shawo kanta


Ahaka suka mishi sallama suna mishi godiya Akram kuwa kamar ya kife sabida tashin hankali.......

🌑 🌑 *B🅰K'IN D🅰RE*🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑


*Written by*
💅💅 *Sadnaf*💅💅


*A heart touching story*



® *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
_ɯɛ ɖơŋ'ŧ ơŋٳყ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛ'Ş_


#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
*#IG PML WRITERS*
#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
#http://maryamsbello.blogspot.com




*Follow me on Wattpad@Sadnaf*


*Am speechless a hak'ik'anin gaskiya banida bakin da zan yiwa dukanin masoyana godiya sai dai nayi muku fatan Alheri Affan na godiya da adduo'in da kuka mishi Allah ya saka da Alheri ya biya muku bukatunku na Alheri*

*Wanan shafin nakune muna mugun tare*

*Nafeesa I shehu*
*yar Baiwa*
*Bilkisu ya'u BK*


*Page 19*


Alhaji Bala kuwa tuni aka jingine case d'insa a gefe guda sabida shi da matacce babu maraba Dan kamar ma ba mutum ba in banda wari da rok'on mutuwa babu abinda yake yi dan Na Maliya bai fasa zuwa ya watsa mishi ruwan kaikai ba duk da yanzu babu fata a jikinsa sabida cizgeshi da yake yi da kansa


Akram kuwa bashida wani Matsala arayuwarsa sai na rashin shawo kan Samha dan zuwansa gidan uku bata yarda ta fito last zuwansu ne ma sukayi kicibus da ita ta dawo daga Islamiyya a lokacin da yayi tozali da ita ji yayi kamar k'ara kwarara mishi wutan Santa ake Ashe kallon tsoro yayi mata daddare Samha ba k'aramar kyakyawa bace

Samha kuwa jikinta ne ya d'au rawa gabanta na Balain fad'uwa ita kad'ai tasan abinda ya ringa mata yawo a kowane sassa na jikinta a lokacin da ta had'a ido dashi amma dan k'arfin hali irin nata da taurin zuciya d'aure fuska tayi ta ratsa ta gefensu ta wuce duk da kiranta da yake yi da husky voice d'insa dake k'ara narkar mata da zuciya a lokacin Alhaji Nazifi baya nan haka su Akram suka zauna a mota suna jiran dawowarsa dan Akram k'asa tafiya yayi dan gani yake idan bai Shawo kan Samha ta aminta dashi ba komai zai iya faruwa dashi dan duk fitar numfashinsa kaunar Samha linkuwa yake aransa fuskatar kawai yake gani a idonsa da sexy eyes d'inta dake sa shi kasala


Samha kuwa aguje ta k'arasa d'akinta sabida bugun da zuciyarta keyi a k'asa ta zub'e tana maida numfashi tare da dafe saitin zuciyarta sabida harbawa dayake dan Kaunar Akram ayau data gan shi wani San sa ne yak'ara bin ko ina na jikinta babu abinda ke amsa kuwaa a kunnenta sama da muryarsa mai dadin gaske sigar ma da ya kira sunanta ya bambamta da yanda ake kiranta babu Wanda ya kai shi iya kiran sunanta

Lumshe idonta tayi ta na jin muryarsa a kunnenta still tana dafe da kirjinta a hankali ta mik'e taje bakin window ta d'aga labule dan ta k'ara kallon sa


Kirjinta ne ya hau bugawa da Sauri a lokacin da ta hango shi a saman motar shi a zaune ya dafe kwantacen suman Kansa daya sha gyara bak'in agogon dake sak'ale a hannunsa sai kyalli yake shigar white and black yayi na kananan kaya fad'ar kyaun da yayi ma b'ata bakine

Samha ko kifta idonta batayi sabida kallonsa da take wani irin Kaunarsa na ratsa ilharin jikinta


Motsin da taji a bakin k'ofa ne yasa tayi sauri ta saki labulen tare da nufar kan gadonta dan bata so 'ya'yyenta su gane halin da take ciki sabida har dasu ake rarrashinta akan ta saurari Akram


Alhaji Nazifi sai da Magriba ya iso gida bai shiga da motarsa ciki ba ya sauko sabida hango su Akram da yayi haka kawai yake tausayin Akram dan yasan yana balain San Samha sai dai har yanzu Samha tak'i ta karbeshi a matsayin mai sonta duk da ban baki da Nasihar da yake mata


Su Akram kuwa suna hango shi suka tareshi tare da zubewa agabansa suna kwasar gaisuwa bayan gaishe gaishe da tambaye tambaye Alhaji Nazifi yace musu su shiga suyi Alwala suyi sallah tunda Magriba tayi inyaso idan sun idar sayi magana


Shiru su Akram sukayi suna Sauraren Alhaji Nazifi dake cewa Akram ya hakura da Samha ya zabi a cikin Suhaima da Saheeba tunda Samha tak'i ta aminta dashi yasan Suhaima da Saheeba bazasu bashi Matsala ba sun d'an fi Samha saukin Kai duk da itama Samhar ba fin k'arfinsa tayi ba zai iya tilasta mata amma baya so ya tilasta mata d'in dan yiwa yaro Aure dole baya cikin tsarinsa baya kuma so ya takura mata dan yarinya ce sosai kuma shi har ga Allah yana so ya had'a zuria dashi sabida nagartattun halayenshi dafatan zai amshi tayinsa ya zabi Suhaima ko Saheeba tunda duk d'aya suke da Samha


Tunda ya fara magana Akram ya jike da Gumi yaji kamar guduma yake kwad'a mishi dan San da yake yiwa Samha bayajin zai iya hakura da ita sai dai idan Aure aka d'aura mata da wani batun su Suhiama kuwa bai ma San kamaninsu ba ballantana har d'aya daga cikinsu ta kwanta mishi aransa gashi yana jin nauyin Alhaji Nazifi baya jin zai iya duba tsabar idonsa ya watsa mishi k'asa a ido



Yazeed shima tuni hankalinsa ya tashi daya ji abinda Alhaji Nazifi yace dan ya kamu da San Saheeba yana tsoron Akram yace Saheeba yakeso


Alhaji Nazifi kuwa kamar yasan tunanin da Akram yake yace mishi kar ya damu yaje yayi tunani bazai mishi dole ba idan dai babu wacce ta mishi a cikinsu kar yaji nauyinsa ya fad'a mishi



Wani d'an ajiyar zuciya Akram ya saki dayaji abinda yace dan hanya kawai yake nema da zai zille


Godiya ya hau yiwa Alhaji Nazifi

Alhaji Nazifi yayi murmushi yace ba komai su tsaya suci abinci sai su tafi


A tare suka mik'e suna ce mishi sun koshi sun gode


Babu yanda Alhaji bai yi da su ba akan su tsaya a kawo musu abinci dan so yake yayi amfani da wanan damar yasa su Suhaima su kawo musu abinci daga nan yaga wacce ta kwanta mishi amma fir suka k'i ahaka suka mishi Sallama suka tafi suna mishi godiya.





Suna fita waje Yazeed ya cakumi wuyan rigar Akram yana kar ya sake ya zabi Saheeba dan ita yake so

Akram doke hannunsa yayi ya buga tsaki tare da shigewa cikin mota dan shi ya ma manta kamanin Saheeba ai baya jin ko sarauniyar Indiya za'a mishi tallarta zai so ta kamar yanda yake San Samha

Yazeed ne ya ringa surutansa shi kad'ai yana ya hakura kawai da Samha tunda bata San shi ya zabi d'aya yar uwarta ta kawai tunda yaga alamar dukansu kyawawa ne Akram shi dai bai ce uffan ba har suka isa gida yana tunanin hanyar da zai bi ya shawo kan Samha ta so shi gashi bashida lambar wayarta ballantana ya ringa communicating da ita ko ya samu ta saurare shi

Aranar Akram kwana yayi yana addu'ar Allah ya mallaka mishi Samha amatsayin matar Aurensa indai Alheri ce agare shi idan kuma ba Alheri bace a gare shi Allah ya cire mishi Santa a zuciyarsa


B'angarensu Samha kuwa bayan sallar ishai Suhaima ta zubo musu abinci a faranti suna ci har da Alhaji Nazifi dan tunda Hajiya Nafeesa ta rasu ya maye gurbinta suke cin abinci tare


Alhaji Nazifi kallon Samha yayi dake ta juya cokali tana cakalar abincin haka ta koma shiru shiru tunda Akram yace yana Santa tunani yayi watak'ila sabida K'in da takewa Akram ta koma haka

Murmushi yayi yace "Baby meyesa bakya cin abincin?

Samha d'agowa tayi tana murmushin yak'e tace " Babu komai daddy"

Girgiza kai Alhaji Nazifi yayi still da murmushi a fuskarsa yace "Baby kenan ai nasan meye yake damunki tunda yaron nan yace yana sanki kika bi kika takura kanki kina tunanin zan tilasta miki ki so shi to ki kwantar da hankalinki bazan miki dole ba yau yaron yazo ya sameni nace ya hakura dake zan bashi Suhaima ko Saheeba dan nasan su bazasu k'i shi ba"

Alhaji Nazifi da zai lura da ya hango tsantsar tashin hankalin dake kwance a saman fuskar Samha da ya jiyo irin bugu da tsallen da zuciyarta yake yi kamar ya fad'o k'asa


Alhaji Nazifi kuwa bai lura da halin da take ciki ba ya maida kallonsa kan su Suhaima dake cin abincin su hankalinsu kwance da alama basu damu ma da maganar da Alhaji Nazifi ya fad'a ba hasali ma kowace a cikinsu fata take ace Akram ita ya zab'a dan duk wace ta amsa sunanta mace mai aji da kyau bata da burin da ya wuce ace Akram ya zamo mallakinta


Alhaji Nazifi cewa yayi "Suhaima Saheeba nagayawa Akram ya zabi d'aya a cikinku tunda 'yar uwarku bata San shi kunga kuma babu yanda za'ayi na tilasta mata dafatan duk wacce ya zab'a a cikinku bazata watsa min k'asa a ido ba"

Murmushi kawai sukayi suka sunkuyar da kai alamar dukansu sun amince

Alhaji Nazifi kuwa murmushin jin dadi yayi dan yasan mai murmushinsu ke nufi

Samha kuwa wani irin jiri ta ringa ji yana Neman kayar da ita sabida tashin hankali murmushin data hango kwance a saman fuskar su Suhaima ba k'aramin d'aga mata hankali yayi ba


Babu Wanda ya lura da halin da take ciki har suka kamalla cin abincinsu suka mik'e dan dama idan suna cin abinci itace take tashi a karshe

A daddafe ta mik'e ta kai farantin kitchen ta wuce d'aki tana zuwa ta zube a k'asa wani zazzafan zazzabi ya rufeta atakaice aranar da mugun zazzabi ta kwana da mafarkan Akram


Suhaima da Saheeba ganin Asuba tayi bata tashi dan tayi sallahr asuba ba yasa suka nufi kan gadonta dan su tasheta

Sallati sukayi gabad'aya da suka ga halin da take ciki a rude suka d'agata suna tab'a jikinta dake tururin zafi

atakaice sai da Samha tayi kwana uku a asibiti kafin a sallameta tabi ta rame sabida tunanin Akram haka kawai take jin haushinsu Suhaima


Alhaji Nazifi kuwa sai lallab'ata yake yi shi da su Suhaima abunka da yar Auta


Bayan kwana biyu da aka sallamota daddare wajen k'arfe biyu tana kwance tana tunanin Akram sai juyi take sirarran hawayen nadama na bin kuncinta sai yanzu take data sani k'in amincewa Akram sai yanzu take data sani data d'orawa kanta girman kai tak'i k'arbar soyayyar Akram yanzu gashi Akram ya hakura da ita zai zabi d'aya daga cikin 'ya'yyenta ya Aura


Juyawa tayi ta kalli su Suhaima dake baccinsu peacefully duk abinda take yi Saheeba na kallonta dan juyawa tayi da zumar gyara kwanciyarta ta hango samha na Jan majina tana sharar k'walla mamaki ne ya rufeta tayi kamar bacci take yi

Samha kuwa durowa tayi daga kan gadon ta nufi Palo dan ta sha kukanta ta gode Allah


Tana ficewa Saheeba tayi sadaf sadaf tabi bayanta

A 3 seater Samha ta kwanta ta bud'e wayarta ta shiga Zgallery ta bud'o hotunan Akram tana kallo tana shafa kan wayarta hawaye sai zubowa suke a idonta


Saheeba dake jikin labule ta d'an bud'e dan ta ringa hango abinda Samha ke yi mamakine ya k'ara rufeta data hango tana kuka tana shafa hotunan Akram

Samha kuwa magana ta fara yi ahankali Saheeba ta k'asa kunnenta dan ta jiyo ta

"Ina San ka Akram ina Kaunarka Girman kai da taurin zuciya zai sa na rasa ka bansan yanda zanyi rayuwa babu kai ba ina kunyar na koma wajen Daddy ince inasanka yanzu ya zanyi Akram"?


Kuka take sosai har da sheshek'a


Saheeba kuwa ahankali tayi baya ta koma d'akinsu jikinta a sanyaye bata tsaya b'ata lokaci ba ta tashi Suhaima ta rik'e hannyenta sukayi wajen palon suka kuma lab'ewa

Samha kuwa surutanta take ita kad'ai tana shafa screen d'in wayarta sai da suka ji duk abinda take cewa a k'arshe ta rungume wayarta a kirjinta tana sauke ajiyar zuciya


Suhaima tsaki tayi lokacin da suka koma ciki tacewa Saheeba "Kece fa baki sani ba wlh na dade da sanin tana San sa tsabar munafirce da taurin zuciya yasa ta Dage bata San shi aikuwa sai na wanata na wajigata zan gayawa Daddy gaskiyar tana San shi ni gobe ma hirarsa zan tayi zance ina sansa sai zuciyarta ta kusa bindiga zan kyalleta"


Murmushi Saheeba tayi tace "kai Aunty Suhaima Auta ce fa"


Tsaki Suhaima ta k'arayi tace "Autar fa dalla jekiyi kwanciyarki Ashe shiyasa ta ringa ma rashin lafiya takaicina ma Daddy yaringa lallab'ata akan ta so Akram Ashe ta dade tana sansa"

Takun da suka jiyo ne ya sa suka hau gadonsu da sauri suka rufe ido kamar masu bacci

Samha kuwa sai da ta lelek'a fuskarsu taga bacci suke ta hau kan gadonta ta kwanta ta na sauke ajiyar zuciya sabida kukan da tayi........
[8:15PM, 4/22/2018] ‪+234 813 272 6929‬: 🌑 🌑 *B🅰K'IN D🅰RE*🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑


*Written by*
💅💅 *Sadnaf*💅💅


*A heart touching story*



® *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
_ɯɛ ɖơŋ'ŧ ơŋٳყ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛ'Ş_


#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
*#IG PML WRITERS*
#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
#http://maryamsbello.blogspot.com




*Follow me on Wattpad@Sadnaf*






*Page 20*
*FINALE*


B'angaren Akram kuwa yana ta tunanin yanda zai fuskanci Alhaji Nazifi yace mishi babu wacce tayi mishi a cikinsu so d'aya tak Samha yake yiwa Yazeed babu yanda bai yi dashi ba akan ya hakura da Samha yace Sam idan ba Aure ko mutuwa tayi ba babu abinda zai sa ya hakura da ita dan duk addu'oi da istahara da yake yi akan Allah ya mishi zabin da yafi Alheri Samha yake gani a matsayin matarsa kuma yana ji a jikinsa Samha matarsa ce ahaka dai ya d'aure akan zaije ya samu Alhaji Nazifi ya gaya mishi halin da yake ciki Dan kar yaji shi shiru




B'angaren su Samha kuwa washegari Alhaji Nazifi na fita Suhaima ta hau tambayar Samhar da ta tasa breakfast d'inta agaba ta kasa ci sabida tunanin Akram akan me yake damunta haka take tunani kwana biyu bata gane mata


Samha d'aurewa tayi ta saisaita kanta Dan kar su d'agota tace musu babu komai kawai Mummy ce ta fad'o mata abunka da Wanda yake jiran kiris take hawaye ya hau zubo mata


Saheeba ta guntsa dariyar da ta taho mata dan tasan karya Samha take yi San Akram ke dawainiya da ita


Suhaima kuwa tab'e baki tayi tace ta dai fad'i gaskiya ba abinda ke damunta ba kenan akwai dai wani Abu da take b'oyewa yake nukurkusarta a zuciyarta


Samha kuka ta fashe dashi tana ita babu abinda take b'oyewa daga haka ta mik'e da gudu tabar palon ta nufi d'akinsu


Suhaima harara ta bita dashi tana ce mata munafika Saheeba kuwa sai Dariya take dan tasan zallar yarinta ke damun Samha

Aranar hawan jini ne kawai basu sawa Samha ba Dan har d'aki suka bita suna hirar Akram kowace na cewa Allah yasa ya zab'eta har suna fad'ar irin San da suke mishi Samha kuwa duk inda ta kai ga San ta d'aure sai da ta fashe da kuka Dan ji tayi gwara su rufeta da duka akan maganganun da Sukeyi su kuwa sai dariya suke aransu


Bayan kwana biyu Akram ya shirya shi da Yazeed suka nufi gidansu Samha Dan ya gayawa Alhaji Nazifi gaskiyar abinda ke ransa daga nan kuma ya shigar da maganar yazeed akan San da yake yiwa Saheeba

Har palon Saukan bak'i aka sauke su Akram dan Alhaji Nazifi yasan da zuwansu sai da ya lek'a d'akinsu Suhaima yace su shirya bak'onsu ya zo duk wacce ya zab'a a cikinsu ta k'arbeshi da hannu bibiyu


Samha da bata da aikin Da ya wuce kwanciya da tunani tabi ta rame tayi zuru zuru sabida tunani wani irin mik'ewa tayi kirjinta kamar ya fad'o k'asa dataji abinda Alhaji Nazifi yace


Su Suhaima kuwa da gangan suka nuna farincikinsu a fili Dan so suke Samha tayi admiting tana San Akram da kanta


Alhaji Nazifi halin da yaga Samha a ciki ne yasa ya zuba mata ido yana "Baby Lafiya kuwa mai ya sameki"?

Samha kuka ta fashe dashi Alhaji Nazifi yayi Sallati yana nufar inda take hannyenta ya ruk'o yana tambayarta abinda yake damunta kamar k'ara zugata yayi ta kara volume d'in kukanta Dan agaskiya bata jin zata iya shiru ta cutu gwara ta gayawa Alhaji Nazifi halin da take ciki


Su Suhaima kuwa ido suka zuba mata suna jiran suji mai zatace


Aikuwa Hakan da ta gani yasa ta sadda kanta k'asa tana tunanin yanda zata fito ta gaya musu halin da take ciki


Alhaji Nazifi kuwa ganin tak'i magana ne yasa ya mik'e ya kalli Suhaima yace tazo ta tambayeta abinda yake damunta zaije wajen su Akram kar ya b'ata musu lokaci



Samha tuni hankalinta ya tashi Dan tasan idan ba fitowa tayi ta ajiye kunya da jin nauyinsu a gefe ba zata kwari kanta Akram yayi mata Nisa



Da Sauri ta tsayar da Alhaji Nazifi dake dab da ficewa daga d'akin tace " Daddy"


Alhaji Nazifi juyowa yayi yana kallonta

Samha kuwa tayi sauri ta sunkuyar dakanta haka kawai kuma taji wani irin kunya da nauyinsa ya rufeta

"Ya akayi Baby"?

A hankali ta d'aga kanta ta kalli su Suhaima da suka kura mata ido tayi sauri ta maida kanta ta sunkuyar gabanta na fad'uwa


Alhaji Nazifi kuwa ganin tana b'ata mishi lokaci yasa yayi tunanin shagwabar ta ne ya motsa tsaki yayi ya juya zai bar d'akin yaji siririn muryar Samha na cewa " Daddy wlh ina Sansa ina kaunarsa"?


A mamakince ya juyo Dan ya gaskata abinda tace yana juyawa yaga ta mik'e dagudu ta shige band'aki ta kulle


Suhaima da Saheeba kuwa dariya suka kyalkyale dashi suna tsokanar Samha akan da ta tsaya girman kai taga ikon Allah

Alhaji Nazifi kuwa maida kallonsa kan su Saheeba yayi Dan su mishi Karin bayani aikuwa suka hau bashi labarin irin San da Samha keyi wa Akram

Hamdala Alhaji Nazifi ya runga yi a zuciyarsa Dan Yasan Akram zaiji dadi idan yagaya mishi Samha ta amince girgiza kansa yayi cikin farinciki ya d'aga muryarsa yanda Samha zata jiyo shi yace "ai da kin tsaya girman kai kiga yanda kwad'o zai miki k'afa"





Samha kuwa dafe k'irjinta tayi tana mamakin yanda akayi Kalmar ta fito daga bakinta wani irin kunya da nauyin Alhaji Nazifi da su Saheeba ne ya rufeta ita da ta gama cika baki bata San sa sai gashi babu kunya babu tsoron Allah ta bud'e baki tace tana San sa ahaka ta mak'ale a band'aki ta kasa fitowa

Su Suhaima kuwa sai

Please Login or Register in order to submit comment