Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

shirya hajiya ta kaisu asibiti

Bayan an duba TASLEEM harda Karin ruwa NUR ta zauna kusa da ita hajiya ko na tsaye

NUR tace"hajiya nagode Allah ya saka da alhairi"

Murmushi tayi tace"babu komai amma yaya sunan ki ne?"

NUR tace"NURUL HUDAH"

Hajiya tace"OK NUR amma ya kamata kuyi ta kula da ita saboda wanan ciwon da kike gani ba abin wasa bane ba wuya ya halaka mutum kun dai ji abinda likita ya fad'a tana bukatar kulawa kuma tayi ta yawo da inhailer ta"

NUR tace"wallahi hajiya ina kokari jiya nan ne ya kare kuma babu kudi hannu na shiyasa ban siya ba har biyu nike siya in ajiye saboda emergency "

Hajiya tace"toh a dai kula domin in gaya miki matar d'an na Afan tayi fama da wanan ciwon shiyasa da na gan TASLEEM sai na tuna ta domin suna d'an yanayi"

NUR tace"Allah sarki,Allah ya bata lafiya"

Hajiya zata yi magana sai ga zakiya ta shigo da sallama da kular abinci hanunta"

Hajiya tace"har kin dawo?"

Zakiya tace"eh na dawo"

NUR ta kalli zakiya tace"ina kika samu kudi kika daho abinci?"

Susa keya zakiya tayi tana murmushi tace"ki ci nasan tun safe baki karya ba"

Hajiya tace"wai NUR in tambaye ki ina mijin ki"

NUR tace"ai ban taba aure ba"

Tace"toh yariyar waye wanan?"

Tace"ya'ta ce"

Hajiya tace"toh tayaya kika samo ta in baki taba aure ba"

Hawaye ne ya fara bin kumatun NUR,ganin NUR na kuka ga zakiya tayi suru-suru da idanu yasa hajiya cewa"it OK in baki son ki sanar dani amma ina zaki har na bige ki?"

Zakiya a ranta tace"wanan matar akwai bin didigi"

NUR tace"aiki naje nima amma ban samu ba"

Hajiya tace"wani qualification kike dashi"

NUR tace"degree "
Hajiya tace"wani course?"

Tace"urban and regional planing"

Hajiya tace"wani grade?

Tace"second class upper"

Tace"good,kefa zakiya"

Zakiya tace"degree,account and auditing first class lower ".

Hajiya tace" gobe Ku same ni a AFSAMAN building company karfe 7:30

NUR zata yi magana zakiya ta katseta da inshaallah zamu zo

Hajiya tace"in ruwan ya kare za a sallame Ku ni zan tafi"kudi ta mikawa NUR sanan suka yi sallama

Tana fita NUR tace"miyasa kika hana in fada mata nan nike aiki da aka koreni"

Zakiya tace"ina ruwan ki da yan iskan nan da alamu ita ke da company in ta dauke ki babu Wanda ya isa ya Kore ki"

NUR tace"Allah yasa"

Misalin karfe 6:12pm aka sallame su"

NUR ta kalli TASLEEM tace"baby me zaki ci?"

TASLEEM tace".......



Maman
Noorul
Hudah✍✍
Luv u my fans
Pls share
[07/06, 14:54] Maman noorul huda marubuciya: πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„
RAYUWAR NUR
πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹
By maman noorul
Hudah

🌟GORGEOUS WRITERS FORUM🌟

🌟G.W.F.🌟

Home of gorgeous,interllingent,and expert writers, we are the best among the rest.

dedicated to iya latifa
πŸ…Ώ1⃣9⃣&2⃣0⃣

Bismillahir Rahmanir Rahim

TASLEEM tace"ni naman kaza zan ci"

NUR tace"toh muje hanya in siya miki"

Zakiya tace"har dani zan ci"

Murmushi NUR tayi tace"sannu hajiya wanan kudin da kike gani gobe zan je in biyawa TASLEEM kudin makaranta da takardu ga islamiya"

Zakiya tace"dubu talatin ne ba zai hana mu cin kaji ba"

NUR tace"naji zan siya muku"

Zakiya tace"har da kema in baki ci ba bazan ci ba"

NUR tayi murmushi tace"toh naji madam"a hanyar su ta komawa gida suka siyi gasashiyar kaza

Suna kaiwa gida suka sa a tare suna ci

Zakiya tace"Allah yayi wa hajiyar nan albarka gashi sanadiyarta muci kaza"

NUR tace"amin"

Hira suke suna cin Kazan har suka gama

Da misallin karfe 9:00 na dare zakiya ta shirya cikin riga da wando jeans ya bala'in kamata dama yawanci irin kayan take yawan sawa

Kwaliya tayi sanan tasa takalmi a hankali ta tako zuwa inda NUR ke kwace hanun ta kai dai-dai fuskarta dan tabbatarwa ko tayi barci

Ajiyar zuciya ta sauke tace"Allah nagode ma da kasa tayi barci da yanzu sai ta rufe ni da wa'azi ta hana ni zuwa club"

A hankali take tafiya har ta fita daga dakin ta ja musu kofa

NUR dake kwance tana jin duk motsin zakiya har ta bar gidan girgiza kai tayi tace"Allah ya shirya ki"

A club ko zakiya sai rawa take amma babu wanda ya zo manna mata kudi kamar inda aka saba

Gajiya tayi da rawa ta koma gefe ta zauna

Wani gaye ne ya zo ya taba ta yace"babe muje mana mu huta ko nawa kike so zan biya ki"

Hararanshi tayi tace"ni ba irin matan nan bane"

Dariya raini hankali yayi yace"kar ki raina min hankali mana ai duk wata mace arziki ba a ganinta a irin wurin nan"

Tsaki tayi ta bar wajen wasu yan mata biyu dake kallonsu suka kece da dariya

D'aya tace"jibeta fa yar rainin hankali wai ita kamilla"

Ta biyu tace"ke dai bari ga ta da farin jinin bala'i kowa ya ganta sai ya kyasa jiya ma ba inda cash mony beyi da ita ba akan su je su huta zai bada dubu dari amma taki"

Zee tace"ai ta bani haushi wallahi"

Zakiya na barin wajen suka yi karo da wani gaye,fadiwa yayi har kasa da alamun ya sha giya ya bugu

Cikin masifa tace"kai baka gani ne?"

Tashi gayen yayi ya fara magana cikin maye sai rufe ido yake yana cewa"yi hakuri masoyiyata zo muje muyi rawa"

Kwace hanunta tayi tace"karka kara taba ni mashayi kawai"

Ai sai ya rike kunni shi yace"yi hakuri madam"

Inda yayi magana cikin maye sai abin ya bata dariya

Zuwa yayi yana rawa in ya fadi ya tashi sai dariya take

Girgiza kai tayi tace"kai giya baiyi ba wallahi"

Shiko cigaba yayi da rawa an taru ana mai dariya domin kwata-kwata baya hayyaci shi

Murmushi tayi tace"bari in ciro waya ta inyi video in naje gida in nunawa my NUR na San zata sha dariya"

Waya ta ciro ta shiga video ta fara kwashe shi tana dariya

Cikin rawa ya cire wando jikin shi ya rage shi da boxers ai sai aka fara ihu dan wajen su abin burgewa ne

In ka cire zakiya dake dariya tana kwasheshi a waya

Da ya gaji sai ya zube kasa yana kwarara amai har ya b'ata jikinshi har a wanan lokacin zakiya na kwashe shi

Barci ne yayi awon gaba dashi

Sai misallin 12:am

Zakiya tasa DJ sauketa a gida da shike sun saba dashi

Tana kaiwa gida tayi wanka ta dauro alwala ta tada sallah nafila a haka NUR ta farka daga barci ta gan ta

Tace"hmm fuska biyu"

Itama alwala tayi ta tada nata sallah

Washe gari da asuba suka farka suka yi sallah asuba harda TASLEEM dan duk asuba sai NUR ta tasheta tayi sallah

Da misallin karfe 7:00 suka bar gida sanda suka kai TASLEEM makaranta NUR ta biya mata kudi sanan suka tafi AFSAMAN building company
amma NUR taki magana da zakiya domin fushi take da ita

Zakiya tace"yi hakuri my NUR bazan kara ba na daina zuwa club din"

Shiru NUR tayi har suka shiga elevator din building

Wajen manager suka je yana ganinta yace"NUR meya kawo ki?"

Tace"wajen hajiya hafsat muka zo ita tace muzo"

Yace"OK kune ashe tace in kun zo a kai Ku office dinta,Ku biyoni"

Har office din hajiya ya kaisu


Bayan sun gaisa ta amshi takardu su

Tace"ke zakiya da sameer zaki yi aiki domin shine babba a audit department kuma abinda kika karanta kenan so kene p-a dinshi"

Zakiya tace"toh nagode hajiya"

Hajiya hafsat tace"kuyi ta kirana da ummi ko baku so in zama ummi Ku?

Murmushi suka yi cikin jin kunya suka ce muna so

Tace"NUR ke da Afan zaki yi aiki"gaban NUR ne ya fadi tace"ummi a canja min department"

Ummi tace"meyasa?"labarin abinda ya faru tsakanin ta da Afan ta bata

Ummi tace"muje in me magana be isa ya Kore ki ba yara kena sai bakin hali"

Sanda ummi ta nunawa zakiya office din ta da sameer sai dai be zo ba sakamakon ciwon kai da ya tashi dashi

Bajewa zakiya tayi a kujera bayan ta kunna a/c

Har office din Afan ummi ta kai NUR yana ganin NUR yace"ummi ina kika samo wanan mahaukaciyar?"

Rai b'ace ummi tace"lafiyar ka kuwa ka gan tayi kama da mahaukaciya ce?ka kiyaye ni"

Yace"yi hakuri"

Ummi tace"gata nan tare zaku yi ta aiki kuma ban amince ka walakantata ba"

Yace"toh"tashi ummi tayi tace"NUR a yi aiki lafiya"

Ummi na fita Afan ya kalli NUR daga sama har kasa yace"watoh na Kore ki shine kika je kika hada ni da mahaifiyata ko?"

Girgiza kai NUR tayi tace"wallahi ban....."buga tebur da yayi ne yasa tayi shiru

Yace"yi min shiru munafuka alguguma ni zaki maida yaro"

Hawaye ne ya fara fita a idanun NUR cikin kuka tace"yi hakuri"

Yace"sorry for yourself"

Kallonshi tayi tana hawaye

A fusace yace"bar kallo na"

Jiki a matukar sanyaye ta fita taje ta zauna

Sai karfe 10 sameer ya shigo office a inda p-a ke zama kafin ka shiga office dinshi ya tarar da zakiya ta kife kai tana barci dan zakiya akwai barci in tana barci sai ka sace ta bata sani ba

rai b'ace yace"what the hell"buga tebur din yayi,a firgice ta mike tana raba idanu

Yace"follow me"ba tare da ya kalleta ba dan ummi ta Riga da sanan dashi an samo me p-a

Office dinshi ta bishi zama yayi yana kallonta daga sama har kasa

Yace.......




Maman
Noorul
Huda
Luv u my fans
Pls share
[07/06, 17:47] Maman noorul huda marubuciya: πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„
RAYUWAR NUR
πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹
By maman noorul
Hudah

🌟GORGEOUS WRITERS FORUM🌟

🌟G.W.F.🌟

Home of gorgeous, interllingent,and expert writers,we are the best among the rest.

πŸ…Ώ2⃣1⃣&2⃣2⃣

Bismillahir Rahmanir Rahim

Sanda ya gama kallonta daga sama har kasa sanan yace"ke ya sunan ki?"

Share shi tayi kamar ba da ita yake ba

Buga tebur yayi yace"dake fa nike magana kin share ni,kina wani kallo na kamar kin sanni"

Murmushi tayi tace"yi hakuri malam kayi min kama da Wanda na sani ne,sunana Aisha idris amma ana kirana da zakiya"

Yace"watoh dan raini hankali shekaran jiya kika ce sunan ki NUR dan mu kore ki zaki wani dawo da wata sallo da sunan zakiya,toh bari in fada miki karki gan dan ummi ta kawoki ki ce zaki nimi ki kawo min iskanci da raini wallahi in kika raina ni korar ki zanyi,mayya kawai"

Ga mamakin sameer sai ya gan tayi murmushi tace"an gama oga amma kaima ka bi a hankali domin ni din nan da kake gani bana d'aukar raini,kuma ina dai-dai da ko wani d'an iska,kuma karka ce da kai nike"

a ranshi yace"watoh dan rainin hankali ta kirani da d'an iska kuma wai ba dani take ba"a fili
Yace"ni kike fad'awa maganar banza,toh ki koma gida na sallame ki"

Tace"ba ka da ikon yin hakan domin ba kai ka kawo ni ba,hajiya kadai ke da wanan ikon"ta karashe magana da murguda me baki"

A ranshi yace"ikon Allah ummi ta jawo mun raini da ta kawo min wanan yar iska"

Katse shi tayi da cewa akwai aikin da zanyi ne ko na koma na cigaba da barci?"

Yace"what?barci a wanan office din?"

Tace"toh in ba aiki me mutum zaiyi?ai sai hutu"

Murmushi yayi a ranshi yace"aiki ko yanzu za ki gan aiki"file ya dibo diyawa ya mika mata yace"gashi kije ki had'a figure din a zuba a computer so nike ki gama aikin nan yau"

Kallonshi tayi ta kalli file din tace"toh ba damuwa"kwashe file din tayi zata bar office din sai yace"zo nan"

Zuwa tayi ta tsaya a gabanshi rike da file din

Yace"ina son ki sani bana son shishigi da iyayi kuma duk lokacin da zaki shigo office dina kiyi sallama in kika ji shiru ki koma,bana son latti "

Tace"OK sir"ta juya zata wuce

Yace"ke wayace ki tafi?"

Tace"na dau ko ka gama ne ai oga"

Yace"zaki iya tafiya"

Tana fitowa ta zauna ta kunna computer ta fara aiki

Bangaren NUR ko bayan ta zauna Afan ya kwaso mata project yace"tayi planing din building"

Tace"sir kafin na fara aikin sai na gan filin da irin unguwar da za a yi gini saboda nasan inda zan fara"

Kallonta yayi a ranshi yace"ashe ta San abinda take yi"a fili
Yace"Ok,bari zamu meeting in muna dawowa zamu biya"

Tace"OK sir"

Yace"banson sir,kiyi tacewa sir Afan"

Tace "OK sir Afan" zama tayi tana treating file din dake gabanta cikin kankani lokaci ta gama"

Zakiya ko aiki take hankali kwance ga a/c ta bude tana jin dadi a fili tace"nayi missing A/c ai ko dan wanan A/c zanyi ta zuwa aiki,gashi my NUR na fushi dani"

Shiko sameer zama yayi yana zuke-zuken shi na sigari

Domin shi baya son yin aiki yanzu ma aikin shine ya kwashe ya bawa zakiya tayi kuma jira yake ta kawo ya duba ko tayi kuskure dan ya samu abinda zai rike ummi ta koreta

Zakiya tana cikin aiki sai wari sigari take ji,tun tana ji kad'an kad'an har abin yayi yawa tashi tayi taje dai-dai bakin office din shi tayi sallama
So biyu bai amsa ba

Sameer dake zaune yana busa sigari jin sallama yasa shi tashi da wuri ya fara fesa turare ya kwashe Wanda yasha a wani karamin plate ya buye

D'aga murya yayi yace"waye ne?"

Zakiya tace"nine"

Yace"lafiya?"

Rasa me zata ce tayi sai tayi shiru

Yace"nace me kike so?"

Ai sai tace"ummi ne ta aiko ni"

Jin ummi ya kara d'aga me hankali sweet ya Ciro a aljihu yasa a baki dan a zatan shi tare da ummi suke

Yace"shigo"Shiga office din zakiya tayi tana dube -dube har ta hango karamin plate din daya boye a karkashin kujera

Ganin bata da niya magana gashi sai kallo wuri take kamar me niman Abu yasa shi

cewa
Ke lafiya?ina ummi take?"

zakiya tace"sir kamar warin sigari ko?"

yace"a ina kika ji?"

tace"wallahi da nike aiki wari ya dame ni kuma nasan a nan department din ne shine nace bari in zo in ma magana saboda bai kamata ana shaye-shaye a cikin building din nan ba ya kamata ka dau mataki"

kallonta yayi yace"ke ban son iskanci tunda nike babu Wanda ya taba cewa yaji warin sigari a wanan company sai ke watoh kin fi kowa hanci kenan ko"

zakiya tace"........

gaskiya zan daina posting dan na lura baku shirya ba,saboda comment ma gagaran Ku yake sai turo min emojis da sticker ake instead of comment ko Sharhi,ai kamar wahalan banza nike kullum ina takura kaina dan in faranta muku amma comment ya gagare ku, gaskiya in ban gan canji yau ba zan ajiye labarin nima in huta,

Maman
Noorul
Hudah✍✍
Luv u my fans
Pls share
[08/06, 01:37] Maman noorul huda marubuciya: πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„
RAYUWAR NUR
πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹
By maman noorul
Hudah

🌟GORGEOUS WRITERS FORUM🌟

🌟G.W.F.🌟

Home of gorgeous,intelligent, and expert writers,we are the best among the rest.

πŸ…Ώ2⃣3⃣&2⃣4⃣

Bismillahir Rahmanir Rahim

Zakiya tace"oga ba haka bane ai be kamata bane, amma in kayi fushi kayi hakuri zan fad'awa ummi tasan abinyi tunda kai baza ka dauki mataki ba, kuma gaskiya bana son warin sigari na ma tsane me sha yana sa numfashi na yayi ta daukewa,kar a zo a cutar dani"tana gama magana ta juya zata wuce tana dariya kasa-kasa

Da Sauri yace"ina zaki?"

Tace"wajen ummi"

Yace"ba sai kin fad'a mata ba zan San abinda za ayi"

Murmushi tayi kasa-kasa a ranta tace"ashe zargin da nike ya tabbata bai son asan yana shaye-shaye" juyowa tayi ba tare da tayi magana ba ta fara tafiya

Yace"ke ina zaki ne?"

Tace"windo zan duba dan warin daga office din nan ya ke fitowa shine nike son in duba ko nan ake makalewa"

Jawota yayi yace"nace ki bari zanyi bincike"

Tace"OK"

Barin office din tayi tana murmushi kasa-kasa

Shiko sameer tana fita yace"na shiga uku an hado ni da mayya ,wallahi ni wani lokaci rikid'a take,wani lokaci tana min kama da ummi,wani lokaci kuma alhaji tsoho gashi farko dana fara ganinta a office din Afan fara ce Sol bata da kiba yau kuma ta d'anyi duhu ga kiba,nidai naga ta kaina tunda aka had'a ni da mayya tunda nike babu wanda ya taba zargina da shaye-shaye sai ita gashi ummi ta gargade ni akan bata son a koreta,Allah kadai yasan safi da tayiwa ummi

NUR ko aiki take tana duba agogo saboda lokacin tashin su TASLEEM ya kusa a makaranta

Shiko Afan sai kallonta yake da gefen ido

Tana ganin 2:30 yayi ta mike ta karasa gaban Afan tace"sir ina son in tafi gida d'auko ya'ta a makaranta"

Yace"koma ki zauna ai 4:pm ne lokacin tashi sai lokaci yayi zaki tafi"

NUR tace"please sir kayi hakuri wallahi zata ta jirana"

Afan yace"toh ki kira mahaifinta mana "

NUR tace"bata da kowa sai ni"

Yace"what kina nufin bata da uba?"

Eh NUR tace a takaice

yace" rasuwa yayi ne"

NUR tace"ah'ah"

Dariyar rainin hankali yayi yace"Ashe shegiya ce"

Cikin b'acin rai NUR tace"ni ya'ta ba shegiya bace"

Yace"oh rashin kunya zaki min kenan?"

Tace"yi hakuri sir amma bazan yarda kowa ya sheganta min ya'ba a gabana please"

Afan yace"ashe baki da kunya toh ki koma ki zauna,toh in ba shegiya ba wacece?"

Tace"sir in kana so ka tsira da mutuncin ka karka kara kiran ya'ta da shegiya dan ba zan d'auka ba,domin akan TASLEEM zan iya rabuwa da kowa banda zakiya "juyawa tayi ta je wajen zamanta ta dauki Jakarta har zata fita

Yace" in kika fita karki dawo"

Ba tare da ta juyowa ba tace"akan ya'ta zan iya barin aikin nan,saboda aikin nan zan bar ya'ta a bakin titi?toh ni ba zan iya ba,yama za ka San da haka tunda baka San darajar ya'ya ba,amma ina son ka sani wata rana yar ka ko kanwar ka zata iya fad'awa a halin da nike ciki,in aka masu haka ya za ka ji?"tana kaiwa nan ta yi tafiyar ta

Tana barin office din ya fad'a duniyar tunani,yace"wai ni yau akewa gorin haihuwa nan take ya tuna marigayiyar matan shi ga wani tsanan NUR na ratsa shi

yace"Allah sarki summaiya da kina raye da yanzu yar mu nada shekara 7

tunawa yayi da ranan da summaiya ta dawo daga asibiti ta fad'a me tayi scarning kuma ya Nuna ya'mace zata haifa.ba zai taba mantawa ba irin farin ciki da yayi ba a take yace mata sunan yar hauwa'u kasancewar sunan kanwar mahaifiyar shi ne"

Ko ta kan zakiya NUR bata bi ba ta bar building din cike da b'acin rai na kiran TASLEEM da yayi da shegiya

A gate suka yi karo da sameer ko kallonshi bata yi ba ta wuce shi

Shiko ya bi ta da kallon yace"ikon Allah Ashe zargina ta tabbata gaskiya mayya ce,tunda gata da wani kalar kaya jikinta"

Yana Shiga office kuma ya tarar da zakiya tayi bake-bake tana cin abinci da minerals a gabanta

Da gudu ya shige office har yana hade kafafu yace"yariyar nan aljanane yanzu kuma da take cin abinci da abbana take kama"

itako zakiya kallonshi ta cigaba da yi tana lashe hanun a ranta tace"kowa da kalar haukanshi shi kuma wanan me ya tsoratashi"


Wanene AFAN da SAMEER

UTHMAN SULEIMAN ADAMS (AFAN) shine asalin sunan shi d'an ne ga marigayi barrister SULEIMAN ADAMS
da mahaifiyarshi hajiya HAFSAT
su uku mahaifansu suka haifa shi da kanen shi mata biyu zainab da ihsan Wanda yanzu duk suna gidan miji

su asalin yan Cameroon ne AFAN ya taba aure shekaru takwas da suka wuce amma matar shi ta rasu Wanda ake zargin yan garkuwa (kidnaper)da mutane suka kasheta a lokacin tana da tsohon ciki a hanyarta ta zuwa minna daga kano kasancewar ita yar asalin minna ne,sai dai lokacin da aka ga gawanta baga ciki tare da ita ba wanda da dukan alamun an tabbatar da ta haihu amma babu jaririya a inda aka gan gawanta

AFAN na matukar son matar shi summaiya Wanda suka hadu a makaranta lodon ta hanyar wata cousin dinshi fatima watoh yariyar kanin mahafinshi domin Fatima kawar summaiya ce Wanda summaiya bata da wata kamarta

sai dai abin da summaiya bata sani ba shine Fatima ta dade tana son Afan tun tana yariya amma yana ganin ta tare da summaiya ya nuna yana sonta ita kuma ta amince,hakan ba karamin d'agawa Fatima hankali yayi ba amma sai ta daure a fili ta nuna tana farin cikin alakar summaiya da Afan amma a zahirin gaskiya ba haka bane
dama kawai take nima ta raba su koda hakan kuwa na nufin kashe summaiya ne

bayan sun kammala karatun su a London inda ita summaiya ta zama cikakiyar likita,ita kuma Fatima yar jarida shi kuma Afan Architect

kowa ya koma kasan shi ita summayya ta dawo gida Nigeria Fatima da Afan suka koma Cameroon

ba tare da b'ata lokaci ba s waliyan Afan suka zo Nigeria niman auren summaiya inda akayi komai cikin kankanin lokaci

bayan auren su summaiya da wata uku Allah ya bata ciki kafin ta fad'awa Afan sanda ta sanar da Fatima sai dai hakan da tayi ba karamin b'atawa Fatima rai yayi ba amma sai ta nuna tayi murna

cikin summaiya na shigan watan haihuwa ta nace zata gida ta haihu Wanda Afan bai so ba amma sai mahaifiyarshi tasa baki akan ya bari taje tunda ta nace

a ranan da zata dawo Nigeria Fatima ta fara kira ta sanar mata zata shigo Nigeria amma zata shigo kano su gan juna kafin ta wuce minna

kasancewar fatima a kano take aiki tana zama da yayar mahaifiyarta domin mahaifiyarta Nigeria ce,tun bayan gama makarantar ta ta dawo Nigeria

fatima na jin summaiya zata zo Nigeria kuma sai ta biyo kano zata je minna hakan yasa ta bada kwangila kashe summaiya wa su bullet

sanda summaiya tayi kwana biyu a kano sanan ta shiga motar minna

a nan su bullet suka samu nasarar sace ta da wata yar makaranta zuwa daji sai dai kafin su kasheta sun dawo sun tarar da ita a mace kuma basu gan cikin jikinta ba ga wanda ke gadin ta da ita yar makaranta sun gudu

bayan kwana uku



Maman
Noorul
Hudah✍✍
Luv u my fans
Pls share
[08/06, 02:07] Maman noorul huda marubuciya: πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„
RAYUWAR NUR
πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹
By maman noorul
Hudah

🌟GORGEOUS WRITERS FORUM🌟

🌟G.W.F.🌟

Home of gorgeous,interllingent,and expert writers,we are the best among the rest.

gaskiya naji dadin comment dinku jiya yanzu na yarda kuna matukar so RAYUWAR NUR
πŸ…Ώ2⃣5⃣&2⃣6⃣

Bismillahir Rahmanir Rahim

Bayan kwana uku police suka tarar da gawan summaiya a wani gida da ba gama ginawa ba

Mutuwa summaiya ya taba kowa da yara da manya domin summaiya macece mai kirki ga son talakawa da taimakon na kasa da ita

An danganta mutuwarta ne da yar garkuwa da mutane kasancewar ba a gan wani shaidan da zai nuna cewa kasheta akayi ba domin babu albin bindiga ko wani abu,sai dai abin da ya daurewa mutane kai ba a gan abinda ta haifa ba mahaifinta alhaji nasir ya fi kyautata zaton asthma ne ya kasheta

Hakan yasa ba ayi bincike ba sai dai police sunyi alkawarin zasu kamo duk wanda hanunshi ke ciki

Itako Fatima ba karamin dadi ta ji ba burinta ya cika na raba summaiya da Afan

Da ta tambayi su bullet yar da summaiya ta haifa sai suka mata karya cewa sun kashe ta sun wurgata cikin rafi hakan yasa ta kwantar da hankalinta

Sai dai ta dau alwashin kau da duk mace da ta had'a dangantaka da Afan

Bayan rasuwar summaiya da shekara biyu mahaifin fatima yace"ta fito da miji ya gaji da ganinta haka"

A shekara na uku mahaifinta yayi mata aure da d'an abokin shi domin taki fito da miji da ta tunkari Afan ya nuna mata baya sonta,son da yake mata na yan uwantaka ne ba na aure ba

shekara Fatima uku da yin aure ta kashe aurenta domin bata hakura da Afan ba

Sameer ko

SAMEER Mohammed Suleiman shine cikeken sunan shi d'an ne ga alhaji Mohammed Suleiman

mahaifinshi yaya ne ga mahaifiyar Afan sameer ya ba Afan shekara uku sai dai baka taba sani domin bashi da aboki da ya wuce Afan

sameer ya taba soyyaya da wata shuwa Arab mai suna safeena yana mutuwar sonta amma daga karshe ta yaudare shi ta hanyar auren babban abokin shi Bayan ta gama cime kudi wanda bayan aurene ya gane bakin su d'aya da abokin shi aliyu shi ya turo ta dan su samu kudi

tunda daga wanan lokacin ya daina yarda da abokai sai dai d'an uwanshi Afan

sanadiyar wanan yaudarar ne ya fad'a a harkan shaye-shaye kuma ya tsani mace

sameer karshen d'an duniya ne sai dai baya zina ga wulakanta d'an Adam halin shi d'aya da Afan sai dai Afan baya shan komai hasalima baisan sameer nayi ba

abinda ya kawo su Nigeria shine niman kanwar mahaifiyasu hauwa wanda kakarsu alhaji tsoho yasa a nimo ta domin ya yafe mata

sai dai suna zuwa Nigeria suka gan ana gwanjon wani company building a minna

hajiya hafsat ta siya suka canja sunan zuwa AFSAMAN wanda aka hada sunan Afan da sameer sai Suleiman

wanda Afan yana zama ne dan yana son yayi binciken mutuwar summaiya da kuma yar'sa shikuma sameer haka kawai yaji

Please Login or Register in order to submit comment