Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

sai ta mike tace ".......




Maman
Noorul
Hudah✍✍
Luv u my fan
Pls share
[05/06, 18:42] Maman noorul huda marubuciya: πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„
RAYUWAR NUR
πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹
By maman noorul
Hudah

🌟GORGEOUS WRITERS FORUM🌟

🌟G.W.F.🌟

Home of gorgeous,interlingent,and expert writers,we are the best among the rest.

Dedicated to my groups

πŸ…Ώ9⃣&1⃣0⃣

Bismillahir Rahmanir Rahim

Ai sai ta mike cikin fargaba tace"alhaji dole a canja wa zakiya makaranta karka manta saboda wanan dalili mu ka baro kano zuwa bauchi wallahir in asiri nan ta fito ban San ya zamu kare ba domin zakiya ce ta maye mana gurbin rashin haihuwar mu Wanda ba kowa ya San yar sintuwa bace"

Abba zakiya yace"karki damu domin na lura yaran basu dauki kamar tasu da wata manufa ba kuma san da na tambayi NUR din ta tabbatar min ita kadai iyayen ta suka haifa,kuma har wuyan ta na kalla babu wanan sarkar dake wuyan zakiya "

Hajiya balkisu tace"dole a raba zakiya da wanan sarka domin za a iya gane ta"

Murmushin takaici alhaji yayi yace"hajiya ki manta zakiya bata son rabuwa da wanan sarka ko kin manta daru da akayi tayi da ita akan an cire mata sarka"

Tace"hakane babu wanda ya isah ya raba ta da wanan sarka "

Washe gari alhaji ya kira zakiya akan cewa zai canja mata makaranta amma zakiya ta rikice me akan baza ta iya rabuwa da NUR ba,babu Inda ya iya haka ya hakura

Watani goma suka yi a makaranta sanan suka koma gida da k'yar suka rabu da juna harda kuka,

NUR na komawa gida ta koma gidan jiya har yafi ta da domin maimuna azabtar da ita take

Sati hudu sukayi result dinsu ya fito inda suka samu 200 level direct,NUR ko ta zabi course din urban and regional planing domin ta iya drawing da kera abubuwa, ita kuma zakiya account and auditing

Har zazzabi NUR tayi saboda kewar zakiya duk da kullum suna waya sai a mai take babu lafiya

A ranar da aka bude makaranta ranar NUR ta shirya domin ta gommace ta koma makaranta zakiya tayi jinyar ta domin ko ta zauna gida ba kulawa zata samu ba

A garaji Abbanta ya sauketa ta Shiga mota kasuwa inda ta tarar da wata kyakyawar mata mai tsohon ciki

Gaisheta tayi ta amsa da fara'a jinginawa NUR tayi jikinta,ai sai ta ji da zafi gashi tana numfashi a wahale

Matar tace"baiwar Allah kamar baki da lafiya ko?"

NUR tace"eh"

Tace"toh meyasa baki sha magani ba?"

Tace"nasha"

Matar tace"mu gan irinshi"bude hand bag NUR tayi ta Ciro panaldo"

Matar ta kalli driver tace"please ina zamu samu chemist a nan?"

Yace"ga chemist can bada kudi a anso miki"Biro ta ciro da takarda ta rubuta sunan magani ta bashi da kudi"

Bayan minti goma sha biyar ya dawo da maganin ta bawa NUR ta sha

Tace"sunana Dr summaiya kefa"

Nur tace"NURUL HUDAH"

Tace"ina zaki? gashi baki da lafiya"

NUR tace"makaranta "

Summaiya tace"amma be kamata a barki ki tafi ba bayan baki da lafiya"kallaon driver summaiya tayi tace"driver me Muke jira"

Yace"ai motar be cika ba"

Tace"muje cata zamu dauka"kallonta NUR tayi tace"bani da kudi"

Summaiya tace"karki damu zan biya"

Jaka ta jawo ta biya driver ta biya shi sanan ya ja Mota

A mota summaiya sai Jan NUR take da hira domin ta fuskance tana da damuwa tun NUR na nokewa har ta saki jiki da ita ta zayyana mata labarin ta

Sai dai abinda basu sani ba tun a kano wata bakar mota ke bin su gashi har sun kusa shigowa minna sai dai a daji suke


Kafin driver ya ankara motar tasha gaban shi ji kake kiiiiiiii karan Jan birki bayan motar suka bude suka Ciro summaiya

Fitowa NUR tayi ta kama kafar dayan dama su uku ne

Tuni driver ya gudu ya bar mota

D'aya daga cikin su yace"babawo in bata sake ka ba ka hado da ita mu huta

Ai ko daukar NUR yayi suka shiga daji wanda ba karamin tafiya sukayi ba kafin suka kai wani gidan da ba gama ginawa ba nan aka sauke su a ka daura NUR summaiya ko tuni numfashin ta ya fara sama da kasa domin tana da asthma

Waya bullet ya ciro ya kara a kunni a speaker yasa muryar mace naji tace"kun gama aikin?"

Bullet yace"eh"

jin muryar Wanda tayi magana yasa
Summaiya dangowa da k'yar ta tace"Fatima me nayi miki kika sa a sato ni"da k'yar take magana

Fatima ta kece da dariya tace"ke ko kika min laifi,bullet kashe min ita da abinda ke cikinta"

Yace"an gama"kallon d'aya daga cikin su yayi yace"babawo kai zaka yi gadin su zamu anso cocaine musha kafin mu aiwatar da aikin mu,wanan shine gwajin ka na farko kuma kai zaka kasheta"

Jiki na rawa yace"toh oga"da alamun sabon Shiga ne


Suna tafiya ba da dadewa ba summaiya ta fara nakuda,kokarin kwance kanta NUR ta fara yi ganin haka yasa babawo ya kwanceta yace"ki taimaka mata ina waje"

Tace"toh"

Da gudu ta karasa inda take tana mata sannu

Bayan minti 40 summaiya ta haiho kyakyawar yarta mace sai dai jini sai zuba yake ga numfashinta bai dawo dai-dai ba

Daukar yariyar tayi ta kalla sanan ta mikawa NUR tace"na baki ita kyauta ki rike ta amana sunanta hauwa suna ne da mahaifinta ke burin sa mata daga yau baza ki kara kukan rashin yan uwa ba domin a halin yanzu ke kadai na yarda da ita sunan mahaifinta
UTHMAN SULEIMAN ADAMS

Jin shiru yasa babawo shigowa yace kuyi sauri mu gudu tunda ta haihu NUR ko kuka take tana cewa"please karki mutu anty amma idonta ya fara kafewa

Babawo ko hawaye yake yace"ki yafe min kuma ki daure muje asibiti,wallahi ba laifina bane nayi karatu amma ba aikin yi ga mahaifiyata a asibiti ana niman dubu dari uku a yi mata aiki shiyasa na fara wanan sana'a,wallahi bazan yafewa kai na ba in wani Abu ya same ki"

Kallonshi tayi tace"na yafe maka duniya da lahira"sarka wuyanta ta Ciro da d'an kuni ta mika me

Tace"ka sayar zai isheka biyan kudin asibiti"

Kuka yake karasawa yayi zai taimaka mata ta girgiza kai tace"ka taimaka ka gudu da su karka bari komai ya same su"
Yace"toh"kama hanun NUR tayi tana murmushi har hanun ya sake


NUR ko


Maman
Noorul
Hudah✍✍
Luv u my fans
Pls share
[06/06, 01:13] Maman noorul huda marubuciya: πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„
RAYUWAR NUR
πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹
By maman noorul
Hudah

🌟GORGEOUS WRITERS FORUM🌟

🌟G.W.F.🌟

Home of gorgeous,interllingent,and expert writers,we are the best among the rest.

Dedicated to GORGEOUS WRITERS FORUM

πŸ…Ώ1⃣1⃣&1⃣2⃣

Bismillahir Rahmanir Rahim

Murmushi tayi tana shafa fuskar NUR har hanunta ya saki alamun rai yayi halinsa

NUR ko wani kuka ta saki da karfi da Sauri babawo ya toshe mata baki ga jaririyar ma kuka take

Babawo yace"ki tashi mu gudu kafin su cin mana a nan

Hijabin jikinta ta cire ta nade jaririyar,babawo ya rufe idon summaiya

NUR tace"a nan zamu barta?"

Yace"eh mana domin in mun tafi da gawar ta zamu shiga Matsala tashi muje"

Tashi tayi suna gudu a daji har suka fito titi

Cikin ikon Allah suka tarar da motar da direba ya gudu ya bari da makulli jikin shi

Bude mata gidan baya babawo yayi yace"shiga muje"

Tana shiga ya ta da mota sai hayan cikin gari

Motar su na barin wajen su bullet suka shigo

Direct gidan yar uwarshi ya kaita wanka akayiwa jaririya be boyewa yar uwar tashi komai ba ya sanar da ita, har kuka tayi saboda tausayi summaiya sanan ta ja wa babawo kunni akan bin abokan banza kaya kala uku ya suyo musu

A na gamawa yace"yanzu ina kikayi ne?"

NUR tace"FUTMIN"

Yace"muje domin zamar ki tare dani yana da hasari dana sauke ki zan San Inda zanyi da motan"

Tace"toh"har makaranta ya sauke ta,ta fito da kayar ta a booth har zata wuce

Babawo yace"ji mana ga sauran kayar ki"

Tace"ba kaya na bane kayan marigayiya ce"

Yace"kwashe wata rana zaiyi miki amfani tunda ga yarta a hanun ki"

Ba tare da tayi magana ba ta kwashi kayan

Tana shiga ta tarar da zakiya kwance

Zakiya na jin sallamarta ta mike tace"my NUR kin dade fa tun dazun nike jira kuma saboda ke na dawo yau"

Kafin NUR tayi magana jaririyar ta sala ihu

Zaro ido zakiya tayi tace"ina kika samo baby"

Ciro ta NUR tayi ta zauna sanan ta zayyana mata komai

Cikin kuka zakiya tace"lallai duniyar nan,amma muje station a nime yan uwanta domin su amshi jaririyar su"

Ai sai NUR ta zube kasa tana kuka tana rokon zakiya akan cewa karta fada kowa domin ta zama yar'ta kuma baza ta iya rabuwa da ita ba"

Zakiya tace"me zaki fada a gida?"

Tace"karki damu"

Zakiya tace"toh me za a bata kin gan tana kuka gashi sai tsoso hanun take alamun yunwa"

NUR tace"raka ni pharmacist in samo mata madara"

Haka fa rayuwa ta cigaba da tafiya inda NUR ke raino TASLEEM da taimakon madara kowa a makaranta yayi mamakin ganinta da baby masu gulma nayi amma ko a jikinta dama basa kula mutane"

Yanzu sun shekara da dawowa makaranta har TASLEEM tayi wayau tana d'an takawa sai dai bata yarda da kowa sai NUR da zakiya gashi kowa nasan d'auka ta domin tana da sha'awa gata bulbul dan ta fara cin abinci,

da akayi hutu NUR taki tafiya gida wai zata koyi computer gashi tana fargaba zuwa gida da tasleem hakan yasa zakiya ta sanar da abbanta zata tsaya ta koyi computer.

be hanata ba sai ma dadi da yaji domin baya son ta dawo ta tarar da bala'in umminta da take cewa a dole sai ya kore zakiya saboda ta samu ciki,babu inda baiyi da ita ba akan ta hakura zakiya ta cigaba da zama dasu kila ma sanadiyar ta ne Allah ya basu nasu"

amma tace"ba haka ba dama tana zama da ita ne saboda bata da haihuwa tunda Allah ya basu toh bata gan me zakiya zata musu ba ai sunyi kokari da yar suntuwa"

sanda suka shekara kuma babu wanda ya nimi NUR a gida,a yau driver ya zo ya kwashe su "

shima driver yayi mamakin ganin NUR da goyo,zakiya ta rungume NUR tace"sai muyi waya"wasa take tayi da TASLEEM a bayan NUR sai dariya take,kissing nata tayi sanan ta shige mota

kano

NUR ne zaune a kasa tiles gaban Abba ga TASLEEM gabanta

Abba yace"ke nike jira ki fada min ina kika samo yar nan"

NUR tace"ya'ta ce amma....."kafin ta karasa maimuna tayi tafi tace"cikin shage a gidan nan shiyasa da akayi hutu kika ki dawowa gida ashe kina can kina iskanci,nidai alhaji kasan Inda zakayi da ita kar a b'ata mana zuri'a"

cikin b'acin rai Abba yace"ke yar waye wanan?"

cikin kuka NUR tace"ya'ta ce amma ba ni....."saukar mari taji a kumatu

yace"kafin makotan su San wanan labari zan kai ta gidan marayu"

maimuna tace"ai alhaji babu shakka yar'ta ce ga kama nan Ashe shiyasa kwanaki da ta dawo hutu take ta amai"

Abba yace"toh amma shekara d'aya kenan da tafiyar ta makaranta kuma da gani yariyar nan ta shekara toh in ma ciki tayi kama ta ai a ce yar na wata uku ko biyu"

maimuna tace"kai alhaji raba kanka da d'an yau boye cikin tayi damun ina kyautata zato da tsohon ciki ta dawo"

Abba yace"na baki nan da kwana uku ki yanke shawara ko ki bari a kaita gidan marayu ko ki bar mu gida"yana kaiwa nan ya bar falon

rungume TASLEEM NUR tayi ta saki kuka tana cewa"bazan bari a raba ni da ya'ta ba"

washe gari maimuna ta Shiga makota ta fara raba zance akan cewa NUR tayi cikin shage,hakan yasa jama'a na nuna Abba in yana tafiya abin ba karamin b'ata me rai yayi ba yana dawowa gida ya fito da NUR akan sai ta ba da TASLEEM ya kai gidan marayu.kankameta NUR tayi taki badawa,cikin fushi yace"ta barme gidan shi

ai ko ta goya TASLEEM ta hada kayar ta sai garaji

bangaren zakiya ko ta tatar da tashin hankali da bata yi zato ba hajiya balkisu ta da bala'i akan sai alhaji ya kori zakiya da yaki sai tace"ai dama yar karuwan shi ya kawo mata gida"

itako zakiya kuka take kamar ranta zai fita jin cewa ita tar suntuwa ce bata da asali

har alhaji ya dauko Biro da takadda zai sake hajiya zakiya ta suguna ta roke shi

tace"bana son zama sila rabuwar ku Abba karka damu zan tafi amma dan alla ka sanar dani inda kuka since ni"

yace"yi hakuri ya'ta ban so ki san wanan sirri ta wanan hanyar ba,a bola bayan gidan mu a kano muka since ki,ina da tabbacin sarka wuyan ki zai taimaka miki wajen niman family ki domin dashi muka since ki"

tace"toh nagode Abba har abada kai ne mahaifina"karasawa tayi gaban hajiya tace"nagode ummina bazan mata da kulawar ki ba a gareni"

kiran NUR tayi a waya tace"gata nan dawowa minna dan dama ta fada mata abin da ta tarar a gida"

a makaranta suka hadu kowa sai kuka yake da yike ana hutu hakan yasa zakiya niman agent ya kama musu daki

bayan shekara biyar......

na gan comment akan rayuwar nur ya ba Ku tausayi wasu ma har kuka suka yi,abinda nike so shine a duk lokacin da ka ji labarin da ya taba ki,ba kuka ya kamata ki yi ba amma ki koyi darasi domin duniyar nan abin tsoro ne, muna dai rayuwa be amma bamu San wake son mu ba,Allah yasa mudace
[06/06, 13:24] Maman noorul huda marubuciya: πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„
RAYUWAR NUR
πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹
By maman noorul
Hudah

🌟GORGEOUS WRITERS FORUM🌟

🌟G.W.F.🌟

Home of gorgeous,interllingent,and expert writers,we are the best among the rest.

dedicated to my husband nagode da sopport dinka Allah ya bar mu tare,you always help me with my novels,kaine mai editing mistake I have nothing to say than to thank you my husband. u are the best
πŸ…Ώ1⃣3⃣&1⃣4⃣

Bismillahir Rahmanir Rahim

Bayan shekara biyar suka kammala karatun su da taimakon kudin dake account din zakiya sai dai tun a final year kudin ya kare ga TASLEEM ma na zuwa makaranta domin nursery 2 take,per time aiki NUR ta nima a inda suka koyi computer ana biyan ta dubu goma kafin result dinsu ya fito

Sai dai TASLEEM na da shekara biyar alamun asthma ya fara bayyana basa wata basu kwanta a asibiti ba da farko ce musu akayi nimonia ne

Result na fitowa NUR ta nimi aiki a wani building company da taimakon Allah ta samu ana biyan ta dubu arba'in da biyar domin degree take dashi

Zakiya ko ta nimi aiki amma bata dace ba

A haka rayuwa ta cigaba da tafiya inda mai gidan da suke haya ya koresu saboda basu biya

NUR ko ta nimi wani karamin gida domin daki d'aya ne Sai bayin garwa ko sillin babu ga gidan na laka,dubu goma a shekara da farko zakiya tace"baza ta zauna ba"

NUR tace"hakuri zakiyi muna cikin jarabawa ne kin gan ba kudi bane damu"

Da k'yar ta yarda gashi ta hana abbanta taimaka musu domin hajiya ta mata kashedi

A haka suke rayuwarsu uku sai dai kudin NUR akan TASLEEM yake karewa domin yanzu an gane asthma ne

NUR na matukan son TASLEEM infact ita ce rayuwarta domin zata iya yin komai dan farin cikin TASLEEM

A haka suke rayuwa inda yanzu TASLEEM nada shekara bakwai ko makaranta zata da inhailer ta a jaka

Halayen NUR da zakiya ya banbanta,domin NUR tana da sanyi bata son hayaniya,NUR fara ce Sol kyakyawa ce a jin farko tsayawa fadin kyaunta b'ata lokaci ne komai nasu iri d'aya ne da zakiya domin suna matukar kama sai dai NUR tafi zakiya haske da tsayi ita kuma zakiya ta fita kiba kadan amma ba kowa ke lura da haka ba domin suna matukar ruda jama'a

In kana son ka gan b'acin rai NUR ka taba TASLEEM domin TASLEEM ita ce weakness dinta NUR tana da addini sosai domin tun tana gun kakarta ta sauke,bata bacci kullum sai nafila

Zakiya ko irin yan Matan nan ne masu baki da masifa bata daukan raini a gun kowa ga raini bala'i

Itama akwai addini amma baza ka gane hakan ba sai kun zauna tare

Sai dai fa zakiya tana da wani hali na zuwa club da dare kuma duk randa taje toh da safe za a ganta da kudi

NUR tayi mata nasiha ta gaji amma ba canji

Zakiya na matukan kaunar NUR da TASLEEM amma kullum sai ta tunawa NUR akan karta manta a ko wani lokaci za a iya raba ta da TASLEEM domin dole wata rana siri zai fito

Itako NUR abin da ta tsana kenan a ce za a raba ta da TASLEEM

Har fushi take da zakiya in ta mata maganar,

TASLEEM ko babban burin ta shine ta gan daddy ta domin a makaranta kowa na bada labarin daddy shi ita sai dai tayi shiru

Yanzu da zakiya da NUR suna da shekara ashirin da biyar

Wanan kenan


Cigaban labari


masu bina PC akan bana zuba love a littafai na,toh ina so ko sani ni ba wanan ya dameni ba,ya kamata Ku gane abubuwa na faruwa a duniya mai yasa zamu b'ata lokacin mu akan rubuta soyayya,a film soyyaya komai soyayya is high time we know what we are doing and learn from mistakes of other people let not waist time writing and reading what is not important.ba wai ina nufin babu kyau karanta littafin soyayya bane but kowa ya San soyayya novel ba ya faruwa a zahiri sai ka gan ance mata da miji har suka kare rayuwar su basa fad'a kuma shi ke mata wanka(I laugh in Spanish)please marubuta ya kamata mu ajiye maganar soyayya a gefe mu fara rubuta abinda zai amfani al'uma,

in akwai Wanda na b'ata wa rai a magana na ya yi hakuri

Maman
Noorul
Hudah✍✍
Luv my fans
Pls share
[06/06, 20:38] Maman noorul huda marubuciya: πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„
RAYUWAR NUR
πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹
By maman noorul
Hudah

🌟GORGEOUS WRITERS FORUM🌟

🌟G.W.F🌟

Home of gorgeous,interllingent,and expert writers,we are the best among the rest.

πŸ…Ώ1⃣5⃣&1⃣6⃣

Bismillahir Rahmanir Rahim

Toshewa zakiya baki NUR tayi tace"inshaallah babu wanda zai raba ni da TASLEEM"

Zakiya tace"hmmm Allah ya sa"

Misalin 2:30pm NUR tace"zakiya bari inje in dauko TASLEEM a makaranta"

Zakiya tace"toh sai kin dawo"

Bayan minti 30 sai gasu sun shigo da sallama

TASLEEM ta gaida zakiya ta amsa

TASLEEM ta kalli NUR dake zuba mata taliya tace"mummy gobe ance mu kawo kudin makaranta in ba haka ba za a Kore mu"

NUR tace"toh allah ya kaimu,ga abinci yi sauri ki ci ki tafi islamiya"

Bayan TASLEEM ta ci abinci ta gama tayi sallah NUR tayi mata shiri zuwa islamiyya ta tafi

Tana barin gidan NUR tayi tagumi

Zakiya tace"lafiya kika yi tagumi?"

Ajiyar zuciya NUR ta sauke tace"zakiya babu ko sisi hanun na ga maganar kudin makaranta TASLEEM,ga maganin ta sun kare inhailer ma kadan ya rage,ban San ya zanyi ba in ta samu attack,gashi aikin dogara na dashi an Kore ni"

Zakiya tace"gaskiya ne akwai matsala musamman maganar magugunar TASLEEM domin ba zan manta attack dinta na karshe ba,babu Wanda ya San zata rayu,amma ya kike ganin zamuyi?"

NUR tace"gobe inshaallah zan fita niman aiki,kema dun Allah ki zo muje tare ki daina zuwa club da wanan barcin asara"

Murmushi zakiya tayi tace"toh ni wallahi raini ne ban so,in kaje niman aiki ayi ta raina ka ana baka doka"

NUR tace"ba dole ba tunda bake keda company ba"

Zakiya zata yi magana sai ga TASLEEM ta shigo da sallama

Da mamaki NUR ta kalleta tace"me ya dawo da ke a wanan lokacin?"

TASLEEM tace"korata akayi ban biya kudin makaranta ba"

Kafin NUR tayi magana zakiya ta mike tace"muje in gan Wanda ya kore ki,a ce saban son abin duniya islamiyya ma sai an biya abinda a da sadaka ake ba dawa ranan laraba amma yanzu sai a ce sai an biya nasu ma har dubu biyu,a haka ma bamu taba kin biya ba sai wanan wata amma saboda rashin kara da yiwa mutane uzuri shine zasu koro ki,muje in gan malamin"

NUR tace"kyalesu kawai in na samu zan biya"

Zakiya tace"wallahir sai naje"

hijabi tasa sanan ta saka TASLEEM gaba sai islamiyya

Suna kaiwa zakiya tace"baby kaini wajen malamin da ya koro ki"

Malami na aji yana koyarwa zakiya tace"kira shi"

Yana fitowa ya tarar da zakiya tsaye bayan sun gaisa

Zakiya tace"malam yanzu abinda kayi ka kyauta?"

Yace"me nayi baiwar Allah "

Tace"ka hana yariya karatu akan bata biya kudi ba sai a wani korota alhalin bawai an saba rike kudin bane ba a biya"

Malam yace"ai ba ita kadai aka kora ba"

Tace"malam wai in tambaye ka"

Yace"ina ji"

Zakiya tace"kasuwanci kake ko niman lada"

Yace"niman lada"

Tace"good ashe bai kamata kana amsa kudin wata ba goma ya kamata ana baka duk laraba in mutum yayi niya"

Yace"a goma ma sai anyi niya,ina fa da iyalai"

Tace"sai ka nimi aiki kana zuwa da safe bawai ka dogara da islamiyya ba,ai da bakin ka kace niman lada kake ba kasuwanci ba"

Ai shiru yayi domin ta gama daure shi

Kallon TASLEEM zakiya tayi tace"ina ne ajin Ku?

Tace"gashi can"tayi mata nuni da hanun"

Zakiya tace" yi sauri ki shige ki yi karatu"

Yana ganin shigan ta tace"malam sai anjima"tayi tafiyarta

Shiko sake baki yayi yana kallonta

Washe gari

Da sassafe NUR ta shirya zakiya tace"ina zuwa"

NUR tace"zan shiga bari ne niman aiki ko za a dace,ki kula da TASLEEM domin yau baza ta school ba,please karki barta ita kadai domin tun jiya numfashinta ke sama"

Zakiya tace"toh sai kin dawo Allah yasa a dace"

Tace"amin"

Yawo NUR tayi a cikin gari sai dai duk inda taje sai a ce ba vacancy

Gajiya tayi da yawo ta samu wani dakali ta zauna hana hutawa ga kishin ruwa

Zaman ta ba dadewa ba wayarta tayi kara zakiya ce

Da sauri ta d'aga

Zakiya tace"hello NUR TASLEEM ta samu attack gashi inhailer ya kare"

Ai a rude ta mike tace"gani nan zuwa "

Gudu ta farayi ba tare da ta kula a titi take ba

Ko duba hanya bata yi ba ta shige titi

Ji kake kiiiiii ai buge ta

Ta fadi kasa wata mata ce ta fito

Tana fitowa ta.....

Ku gyra zama cause the real fun has just begun

Maman
Noorul
Hudah✍✍
Luv u my fans
Pls share
[07/06, 02:13] Maman noorul huda marubuciya: πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„
RAYUWAR NUR
πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹
By maman noorul
Hudah

🌟GORGEOUS WRITERS FORUM🌟

🌟G.W.F.🌟

Home of gorgeous,interllingent,and expert writers,we are the best among the rest.


Dedicated to all my fans especially Wanda basa group di na,ina yi Ku sosai nagode da kaunar ku.


πŸ…Ώ1⃣7⃣&1⃣8⃣

Bismillahir Rahmanir Rahim

Wata dattijuwar mata ce ta fito

Tana fitowa ta karasa inda NUR ta fadi

Tace"sannu tashi muje asibiti yar nan"

NUR na tashiwa ta dauki jakarta tace"karki damu hajiya ba wani ciwo na ji ba"

Jin muryar NUR yasa matar juyowa ta kalleta,ai sai taji murya kamar na kanwata hauwa

Tace"no dear bari muje asibiti a duba ki ga jini na zuba a goshin ki"

Ai sai NUR ta fashe da kuka tana cewa sauri nike TASLEEM ba lafiya"

A rude tace"subhannallah wacece TASLEEM?"

NUR tace"ya'ta ce yanzu aka kirani asthma ta ya tashi kuma wallahi bani da ko sisi ki taimaka min hajiya kar ta mutu dan naga alamar kina da kudi,ki taimaki rayuwata"

Murmushi hajiya tayi tace"toh yi sauri ki shiga mota muje"da sauri ta shiga motar

Suna kaiwa gida suka tarar da zakiya zaune da TASLEEM kwance a jikinta tana numfashi sama-sama domin abin ya fara sakin ta

Da mamaki NUR ta kalli zakiya tace"ina kuka samo inhailer?"

Zakiya tace"da naji shiru baki dawo ba har idonta ya fara kafewa sai nayi tunanin ko kin dawo babu kudi hanun ki shine nayi gudu naje shagon uche nace ya bani inhailer ba tare da ya San babu kudi tare dani ba,yana mika min na gudu na dawo gida na bata"

Rungume zakiya NUR tayi tana kuka tace"nagode Allah ya bar mu tare"

Zakiya tace"miye haka ko kin manta nima TASLEEM ya'ta ce?"

Itako hajiya shiru tayi tana kallon su da yanayin gidan duk sai taji tausayin su ga wani abu da zuciyarta ke raya mata

Tace"Ku dauko ta muje asibiti duk ta wahala"San da tayi magana zakiya ta lura da ita.

Gaisawa suka yi da zakiya,hajiya sai kallonta take kamar ta taba saninta

NUR tace"zakiya shirya muje a duba ta"kafin zakiya ta mike sai ga uche ya fado dakin ko sallama babu yace"give me money"

Zakiya tace"I don't have money in na samu zan kawo maka"

Yace"that one na lie sai kin bani kudi na"ganin zai ta da hankalin jama'a yasa haji tambayar shi nawa kudin ta biya shi

Ya bar gidan


Cikin minti goma zakiya ta

Please Login or Register in order to submit comment