Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ina hawaye babu abinda ya fad'o min sai tunanin iyayena inama suna da rayuwa suma su dangwali albarkacin haihuwata. Duk sai jikinsu yai sanyi ganin ina kuka, da kyar na daure nace da ita.


''Inna duk yanda kuka yi hakan yayi amma dan Allah cikin wanda aka bani ina so acire rabi aje akai masallaci asai wani abin mai muhimmanci ko tabarmi ko butuci ko alkur'anai domin suma iyayena su sami ladan.''

''Allahu Akbar Allah yai miki albarka Ruma" Cewar baba.

Da yamma Baba yana zaune inda yake yin alwala yana yin asuwaki nikuma ina zaune cikin baranda ina had'a littatafan dana samu bakina har kunne tsabar farin ciki da jin dad'i, Inna na gefe tana ta gyaran kajin da ta siyo dama inna akwai son dad'i ita dai a rayuwarta ta sami jin dad'i ace yau itace hajiya Suwaiba, Shi yasa ko kujerar makkan dana samu tana cewa itace zataje ta yiwa iyayena addua' babu wanda ya musa domin ansan bama zata yarda ba.


Sallama aka yi har sau uku kafin baba ya mike da sauri yana nanata ana zuwa. Har ya fita sai kuma gashi da sauri yana fad'in.


''Suwaiba kawo tabarma alhaji Yahaya ne da kaninsa wanda ya yiwa Ruma kyautar kujerar makka.'' Da sauri kuwa ta mike har jikinta na rawa


''Laallah! Kace manyan baki ne damu to sannunsu.''


Kasa zama tayi sabida zullumin me kuma ya dawo dasu har wani lekawa take yi ko Allah zaisa taji wani abu. Niko ina gefe ina dariya domin lokuta da dama lamarinta kan bani dariya.

Gefena ta dawo tace. ''Ruma kaddafa malam ya gayama alhajinnan cewar ba kece me zuwa makkan nan ba dan nasan zai iya wallahi.''

"Kai haba inna ya za ai yace haka dama ai dole ke zaki ai babu wanda yafi cancanta da zuwa saike, nidai kin san tsarabata ta da bance ko inna?''

Cike dajin dad'i ta dafani tana cewa. "Ah kwarai ma kuwa, insha Allah d'iya ta shi yasa nake sonki wallahi.''


A can zaure kuwa, Alhaji Yahaya ne ya kalli malam Sule bayan sun gama gaisawa yace.


"Nasan kila zakai mamakin ganinmu anan, toh malam wannan dai sunansa Yusufa nasan ba sai nayi maka bayanin shi ba, kasan na gayyaceshi wajan walimar jiya kuma gashi ya samu ya halarta harda da gudummawarshi wacce ba'a zata ba, to kuma daga baya sai ya nuna sha'awar Rumana akan shigowa cikin iyalinshi ma'ana yana so ya nemawa yaronshi Haidar auranta idan ba ayi mata mijiba shi yasa yana gaya min nace ai duk gida ne bari kawai muzo da wuri, gashinan ayi komai agaban shi domin da tun safema zai tafi amma sabida wannan maganar sai ya dakata.

Cikin farin ciki malam yake furta. "Alhamdulillah lallai abu yayi kya, Allah ya taimaka kuma ya shige mana gaba sannan ya zab'a mafi alkhairi. Toh amman wani hanzari ba gudu ba, nasan dai kasan cewa yarinyar nan marainiya ce ba uwa babu uba ita mai d'akin nawa itace yayar mahaifinta kaga kenan akwai yiwuwar dole sai anyi shawara da iyayenta nacan kadda suga kamar munayi musu karan tsaye akanta, kuma wallahi kaga ansami sab'ani domin sai d'azu suka wuce can gida maska.''

"Toh ai babu komai ni sai muje dakai har can garin domin neman izini amma yanzu dai ka kiramana ita innar tata taji daga bakina kasan halin mata.'' Cewar alhaji Yahaya.


Tare suka dawo da ita cikin zauran jikinta duk yai sanyi musamman data hangi wata dalleliyar mota daga k'ofar gidan, ga manyan mutane zaune a cikin zauren wanda ya gama bud'ewa da kamshin Alhaji Yusuf domin tasan sai dai shi d'in domin alhaji Yahaya anriga an saba dashi.

Bayani sukai mata dalla-dallah yanda zata gane kafin shi Alhaji Yusuf d'in ya d'ora da fad'in.


"Kamar dai yanda yaya na yai miki bayani yarona yana kasar waje karatu amma ya kusa gamawa abinda yasa nai mishi sha'awar Rumana gaskiya na yaba da tarbiyyarta sannan nasan kowa zaiso ace ya had'a iri da ita, ina fatan zaku amince domin Haidar shi kad'ai ne yarona ina so ya samu mace ta gari.''


Wata zufar farin ciki ne ta zubowa Inna ta ko'ina daga jikinta kafin ta d'an muskuta ta kuma gyara mayafinta tace.


"Toh shikenan insha Allahu komai ba zai gagaraba tunda ba ayi mata mijina ba, sannan ga malam komai nene sai kuji daga gareshi.''


Cike da farin ciki Alhaji Yusuf yabar garin BAKORI bayan yayan shi yai mishi alkawarin cewar a cikin satin nan zaija malam Sulen suje maska domin nemowa Haidar auran Rumana din. (To ruma da auran mahaukaci🤭)


Sai dare ya shiga cikin katsina hankalinshi kwance bakinshi cike da adduar Allah yasa abinda yake son shiryawa ya zama alkhairi garesu baki d'aya.

Mudi yayi murnar ganin shi duk da cewa har sun kwanta bacci lokacin, sai da ya gama duba jikin Haidar d'in yaga babu matsala sannan ya wuce d'akin shi wanda aka gama fesheshi da asirirrika kala-kala.

Da bismillah ya jefa kafarshi tare da bi da ayatul kursiyyu da falaki da nassi domin haka kawai ya farajin fad'uwar gaba lokacin da ya dumfaro d'akin nasa.

Kwance take saman gadon shi tayi dai-dai tana kwasar baccinta, wankanshi ya wuce yayo ya gyara jikinshi sannan ya rab'a gefenta ya kwanta bayan ya gama tofe jikinshi da addu'a.


*******


"Oh gaskiya rikonki ya zame min alkhairi Ruma, Allah ya jikan iyayenki, zanzufa makka zanje sannan ga wannan alhaji da yake so ki auri d'anshi kinga shikenan muda talauci munyi hannun riga ko?''

Turo bakina gaba nai ce. ''Kai inna nidai wallahi bana sonshi kin dai san duk yaran da ake kaiwa kasar waje karatu a iskanci suke dawowa, kuma shikenan saiki aura min wanda bazai tab'a sanin darajata ba?''

"Innalillahi na bani ni Suwaiba, Ruma kina da hankali kuwa? Toh wallahi ahir d'inki da yimana bakin ciki, gobe idan Allah ya kaimu zamuje maska gaba d'ayan mu, saura idan an tambayeki ki musa Allah saina yankaki aikin san zan iya ko?''


Kuka na saka mata nace. ''Inna duk ga masu sona nan a garin nan ga Mansur ga K'asim ga malam Umar kullum nacin tambaya suke yi zasu turo kinaki sai wannan daga zuwa wama yasani ko d'an fillan kai ne.''


Dariya tayi kamin tace. ''Yaro man kaza, to kodai tukunyar tsafince shi gaba d'aya dole shi zaki aura garama kisawa zuciyarki salama, haba Rumana dama fa wallahi ke matar manya ce kinga ban tab'a haihuwa ba ya kamata ki sharemin hawaye na kinji ko? Yauwa Rumana Allah yai miki albarka ai insha Allahu nasan zai kasance nagari domin Allah baya wulakantar da bawan shi musamman ma kuma marainiyan Allah.''

Ina rungume a jikinta ina magana cikin zuciyata. 'Inna ai Allah ne yaga abinda ya gani har ya hanaki haihuwar, dan da yanzu kin tashi BAKORI da tashin hankalinki musamman na san sai kin addabi kowa, ji duk kalar wulakancin da kike min amma yanzu sai wani lallashina kikeyi sabida tsabar son duniya kai Allah ka rabamu da wannan kalar rayuwa.'

Dije ce tashigo gidan da sallama bayan ta gaida innan muka wuce d'akinta ita kuma ta sab'a hijabi tai gaba abinta, domin ita in dai zuwa unguwarta ya tashi toko baban sai dai yazo ya tarar bata nan, na sha nuna mata babu kyau amma inaa wani lokacin ma makemin baki take yi wai tunkafin a haifi uwata takejin wa'azi kai inna ko...!


Labarin walima muka dasa nida dije kafin in kuma matsawa jikinta nace. ''Ke dije kinsan meya faru kuwa?''

Hankalinta na kan kayan sawar dana samu tace.


''A'a sai kin gaya min.''


"Humm kin tuna mutumin da ya bani kyautar kudi da kujerar makka?''

Dariya tayi kafin tace. ''Ai dama na sanshi yana da kirki sosai a katsina yake mai kud'i ne sosai uwar su d'aya uban su d'aya da alhaji Yahaya ya aka yi?''

"Dije kindai san bani da k'awa garinnan saike kuma dake kawai na yadda dan Allah kibani shawara wallahi tun shekaranjiya nake cikin tashin hankali jiya ko baccin kirki banyi ba, kinji wai shine yazo yana nemawa yaron shi aurena kuma wai yaron nashi yana kasar waje karatu.''


Batare dana sani ba naji ta wani rungumeni tana murna kamin tace.


''Alhamdulillah! aiko maganar malam ta tabbata daya ce ked'in matar manya ce, Allah ya tabbatar da alkhairi Ruma wannan ai abin farin ciki ne domin kowa yasan alhaji Yusuf mutumin kirki ne yaron ne dai ban sani ba gaskiya domin sau d'aya na tab'a ganin wata mota tazo gidan Alhaji Yahaya ni kuma zan wuce naji wasu na cewa yaron alhaji Yusuf ne yazo gaida yayan mahaifinshi, kumafa shi kad'ai ne d'an shi, ai kinga dole ya hau manyan motoci, toh ni dai iyakar abinda na sani a kanshi kenan. Amma insha Allah babu wata matsala ki kwantar da hankalinki ki dage da addu'a shawarar da zan baki kenan.''

Ajiyar zuciya kawai na sauke amma sam bana cikin nutsuwata. Kayan da ta gama gani nace.


''Toh ki d'auki ko kala biyu ne dije.''

"Waaa! ni? a'a wallahi wancan hijab d'in dai zan d'auka sabida yayi min kyau shima dan naga kina da kalarshi ne amma da bazan d'auka ba.''


Sai yamma lis sannan muka rabu da ita sabida an bamu hutu na sati d'aya a islamiyya sabida kacaniyar da aka sha.


Washe gari... Kamar yadda aka tsara Alhaji Yusuf ya aiko da mota da direba wanda zai kaimu maska kuma ya dawo damu. Duk irin yanda nake jin jikina da zuciyata hakan be hanani sakayawa fuskata murmushi ba musamman dana lura baba yana ta kallona da alama wani sauyi yake son gani daga gareni, ba kamar inna ba wacce take ta harkar gabanta a cikin motar.


An tare mu sosai domin ansan da zuwan mu ranar, nidai ko hutawa ban yiba 'yan uwana wa'inda muke sa'anni suka dinga jana gidan dangi bamu nan bamu can sabida su koda yaushe kallon wata madaukakiya suke yi min tun iyayena na raye.

Bazance ga abinda iyayena suka tattauna akai ba domin ban sani ba sai dai muna dawowa aka ce baba da mazan su alhaji sun wuce saini da inna kawai aka bari.

Naso na kwana a gidan kakannina na wajan uwa amma iya tayi mirsisi tace a gadonta zan kwana. Humm komai suke nufi da hakan oho.

Dangin Mamana na sona sosai amma sam basu samu sakewa dani sabida wata irin zuciya da dangin mahaifina keda ita duk kusan halin su d'aya tunda basu da 'yan uba duk iya ce ta haifesu dama ance abbana ne kawai bai d'auko halinta ba kamar yadda naji labari shi yasa gashi nan Allah ya dauke shi ya barta da masu kalar halinta.


Hanani bacci suka yi iya da inna wai da sunan bani shawara nan kuwa duk maganar d'aya ce kadda na basu kunya gara na zauna inda zan huta har suma su dangwali arziki. Kai kud'i basu yi ba wani lokacin. Babu ruwan su da wane irin kalar mijin zan zauna ba ko wane hali zan shiga ba sudai kawai na auri mai kud'i kodan su samu kud'i suma.

Can sama-sama na fara bacci naji iya na tamabayar inna.


''Waike me yasa kika ce asa bikinnan wata biyu?''

"Babu komai iya haka dai nace sabida kadda aga kamar neman kai muke yi da ita nifa ta fara bani tausayima.''


Mittsww.. ''Dalla bani wuri, to uban waye yace baya jin tausayin ta? ai jin tausayinta da muke yi ne shi yasa muke so ta auri wanda zata huta a gidan shi, kinga alhajin nan yace kadda akaita da komai sai suturunta komai zai yi mata tunda marainiya ce memakon ayi komai cikin sati biyu ko d'aya kika wani zabi har wata biyu dan iskanci.''


Cewar kakata iya, gashi dai ta manyanta amma hankalinta gaba d'aya yana kan dukiya kome zata yi da dukiya alhalin yanzu tana kan hanya? Eh mana tunda yanzu ko ita ta san da wuya ta nanata koda kwatan shekarunta na baya.


Wasu hawaye masu d'umi suka zubo min ina mamakin halin rayuwar yanzu, bansan lokacin da bacci yayi gaba dani ba.


**** *****


''Alhaji wai lafiya kuwa naga kanata shirye-shirye kamar mai shirin yin wata hidima?''

Ba tare daya kalleta ba yace. ''Ai hidima zanyi hajiya domin kuwa yaronki zanyiwa aure insha Allah.''

Idanunta ta fito dasu tare da dafe kirji, ''Alhaji wani yaron nawa?''

Ganin kalar kallon da yake mata ya sata wayancewa da cewa.


''Amma dai da mamaki Alhaji mai zaisa kai mishi aure yana cikin wannan halin? ai sai naga kamar rashin adalci ne, to ma wani mahaukacin nee ko nace kwadayayyen ne zai bawa mahaukaci 'yarshi?''


Wayarshi ya zara tare da ficewa yabar mata d'akin.


Hannuwa tasa saman kanta tare da budce baki zata saki ihu komai ta tuna kuma sai tai gaggawar rufe bakinta tare da nanata.


''Kan bantan uba..a'a wallahi da sake.''












*MAMAN KHADY*🙇🏻‍♀
[4/2, 11:15 AM] Re@l💍 K@usy🌹: Rumana 12






Kwance nake ina
barci bayan gama sallar magriba domin lazumi nakeyi bansan barciv ya kwasheniba.
Jinai ana shafamin k'afafu kamar mage tsabar laushin da nakeji.
Tun inaji sama-sama harna bude idanuna,Manyan idanuna na kuma zarowa ganin haidar kusa dani kuma shine me shafar k'afafuna.
Kauda kanshi yayi gabarin kallona amma bedena shafar kafar ba.


Tashi nai zaune cikin mamaki domin betabamin hakaba,Yayana lafiya kuwa me kakeso?
K'aramin yatsanshi yacigaba da zirawa tsakanin yatsun kafana amma ko fuskata be kallaba.
"Ikon Allah.
Hannuwanshi nakama duka na rike ina kallon cikin idanunshi domin shima yanzu kallona yakeyi, Kamar zaice wani abu.
Sauke idanuna k'asa nayi Sabida yanda wani nauyinshi ya kamani musamman yanzu Dana ganshi kusa dani sannan dogon wandon wani yadine kawai jikinshi k'aton kirjinnan nashi awaje.


K'afata naso janyewa yakuma jawota yana lumshe idanunshi,Murmushi nayi kamin in tallaboshi jikina,Aiko nan da nan ya kwanta acinyata hadda sauke numfashi saidai hannunshi be tsawa waje gudaba saima lalubata dayafara hannunshi har zuwa kirjina.
Jin yatabo tudu akirjina yasashi tashi zaune yana lekawa cikin rigata da alama tudun dayajine yakeson leko ko menene.
Inajin duk abinda yake amma wallahi tsabar mamaki da tsoro yakasheni sainaji ko motsi na kasa.
Ahankali naji yafara matsamin kirji ahankali kamar mejin tsoron fashewarsu,Idanunshi alumshe harwani gyara kwanciyarshi yake.


Tsawon lokaci sannan yafara sauke numfashi alamar barci ya daukeshi.
Mamaki naitayi domin betabamin hakaba iyakacidai yakan yita kallona wani lokacin.
Fatana Allah yabashi lafiya.
Lallabashi nayi na kwantar gefe sannan naje na canzo alwala domin tuni jikina ya sauya Sabida jagulamin kirji da yayi.




Ina gama sallar isha'i. Natkofar wurin kenan naji ana kwankwasa kofar,Hijab dina danafara cirewa na maida da sauri na nufi kofar tunanina ko abbane yadawo.
Saidai ina bude kofar sainaga wannan abokin haidar dinne domin yana zuwa lokaci zuwa lokaci domin dubashi.
Hanya nabashi yashigo tare dayimishi sannu da zuwa musamman danaga yana kallona da alamun damuwa sosai afuskarshi.
Ruwa da lemo na kawomishi bayan ya zauna.
"Amarya ya kwana biyu ya dawainiya?
Da alamun kunya nace Alhamdulillahi yasu umma?
Dayake mahaifiyarshi tazo wajena harsau biyu.


Yajima yanamin hira sannan yaimin sallama bayan ya maida haidar saman gado domin da ak'asa yake barcin inda nai salla.
Haryakai bakin kofa ya sai kuma ya juyo Rumana har yanzu babu wani cigaba da kikeganin ansamu?


" Kallonshi nayi kamin ince gaskiya ana samu domin yanzu ciwon yadaina tashi kaga andaina bashi wa innan kwayoyin amma kaga yana barcinshi wannan bige-bigen duk ya daina bashi cikin hayyacinshi amma gaskiya da sauki koni yaushe rabon daya kai hannu jikina da sunan duka.


"To Alhamdulillahi bari inje zuwa jibi insha Allah zan kawo miki wa incan magungunan wa inda akace za ahada kedai ki daure kinji ko?


" To shikenan insha Allah nagode sosai saida safe.




Najima ina tunani kamin barci ya kwasheni musamman yau ko addua banyiba Sabida yanda barcin yakamani sosai.




Bude idanuna nayi saina tsinci kaina cikin wani guri me mummunan duhu zuciyata tai wani irin bugu nan da nan naji wani matsiyacin tsoro ya dirar min musamman danaga ko tafin hannuna zan banganiba.
Wata irin mummunan tsawa naji saman kaina wadda takuma firgitamin kwakwalwa.
Yake wannan figigiyar kaza sarkin tone tone to lallai munaso ki dakatar da duk wannan tone tonen naki kamin ki tone wukar yankaki.
Wata muguwar murya mara dadin sauraro taimin wannan maganar.
Addua nafara cikin zuciyata domin sam tsoron dake baibaye dani yahanani bude bakina balle inyi addua da karfi.
Wannan shine kashedi Wanda ya kasance akanki lallai kifita rayuwar wannan mahaukacin tunkamin ki koma irinshi kokuma mu kasheki kisa na har abada.
Wasu dogayen hannuwa naga sun shakemin wuya nanfa nafara kokarin kwacewa tare da kakari jin irin shakar da akaimin.


Afirgice na farka yayinda jikina ya jike da zufa haske na kunna nan naga haidar zaune ya zaiba fitsarinshi domin ga lemanan tunda daga inda yake kwance har kusa dani.
Ajiyar zuciya na sauke Dana gama tabbatarwa agado nake.
Tashi nai har lokacin jikina bedaina rawaba domin na masifar tsorata.


Gyaramishi jikinshi nayi tare da canzamishi kaya na yaye zanin gadon nasaka wani sannan na kwantar dashi na tofeshi da addu'a sannan na shiga toilet na wanke Wanda yabata nima na dauro alwala barcin daban komaba kenan domin kwana nayi raya wannan dare ina kuma kai kukana ga Allah.
[4/2, 11:15 AM] Re@l💍 K@usy🌹: Rumana 13








Da wani shegen
zazzabi da ciwon kai na wayi naso kwarai intabuka abun kwarai kamar, yadda nasaba amma ina wani nauyin jiki ya hanani ko motsin kirki.
Wayata taita ring amma inajinta nakasa tashi.


Sai wajan goma nasafe nakuma bude idanuna daga Dan barcin daya kwasheni,Abbane keta sallama Ashe yaji shirun tai yawa shiyasa ya shigo da makullin hannunshi dama Sabida haka ya rike wani ahannunshi.


"Dakyar na mike idanuna nakan haidar Wanda yaketa zare abin dardumar Sabida wata beza beza gareta.
Ina wucewa yabiyoni baya hadda daukar cup dadi ya kasheni to kodai hankalinshi yafara dawowane tunda gashi yanzu alamu sun nuna binda yakemin yunwa yakeji,Sabida nasaba kullun danatashi tea nake fara hadamishi kamin inyi abin kari.


" Da mamaki ya zubamana ido ganin yanda haidar din keta bina da cup ahannu ammadai kanshi akasa danbama hanya yake kalloba.


Zamanai ina sauke numfashi na gaida abban,Ya amsa da tambayata lafiya nake kuwa yau da alama har yanzuma baku karyaba ko?


Abba natashi yau da zazzabi da ciwon kai shiyasa nakasa tashi akan lokaci amma yanzu zan hada.


Wani mugun bacin raine ya tasomishi Sabida wani tausayina daya kamashi tunda nazo gidannan nake dawainiya Ashe kenan haka zata kasance idan banda lafiya babu Wanda zai kula da wani cikinmu kenan?
Amma Fatima bata kyautaba beyi tunanin zata barshi har hakaba musamman dayaji yadawo hayyacinshi yabata hakuri sannan yaba iyayenta hakuri amma da yake rikone dasu shine ta tsallake tatafi wata uwa duniya kuma da aurena akanta.
"Numfashi yakuma saukewa kamin yace kiyi hakuri dama saida nai tunanin haka wallahi Allah ya sawake to kodai me aiki za asamo miki?
A a Abba zan iya komai insha Allah naji saukima sosai.


" Eh koda kinji saukin ai zata temakamiki da wasu abubuwan kema kindan huta ko?


Shiru nai ina murzar hannuna,Kamin ince Abba ka barshi kawai hakan zai kasance kamar tonuwar asirin zaman da nakene kaga wasu daga dangina zasu iya zuwa kadda asami matsala su fahimci kalar zaman da nakeyi bazasuji dadiba gara ahaka kaga babu Wanda yasani.


"Ajiyar zuciya ya sauke kamin yace eh hakane kuma bari insamomuku abinda zaku karya saikisha magani dannaga wannan ogan ma da alama yunwa yakeji gashinan yana binki da Kofi,Wallahi sai yanzu na yadda ana samun cigaba ta bangaren maganin nan domin dacan idan zaiyi sati beci abinciba to bazai nuna yana bukataba Allah yaimuku albarka yabashi lafiya,Bari ina zuwa.


Tashi nai nima na hadomishi tea din Allah sarki bawan Allah da zafinshi yadinga kaiwa baki ina kokarin anshewa yana kawomin bugu da kyar yabari na shekamai shi,
Lokacinda Abba yadawo yana kwance jikina sai sakalamin hannu yakeyi cikin riga Allah yasama da hijab jikina.
Wani farinciki yaji lokacinda ya kalli kofin tea din da haidar din yasha sannan yaji dadi dayaga har inabari yahau jikina lallai dole ya gaggauta bin bayan Fatima har India din domin tadawo tunkamin haidar din yafara Neman hakkinshi to Abu gamara hankali yaje ya taushe yarinyar mutane babu matemaki ai akwai matsala garadai da babba tsakaninsu,Sannan bazai yiwu shine komaiba garama haidar din idan yakula dashi babu matsala ammadai gaskiya bazai yiwu ya zake irinhakaba wajan suruka.
Ganin yai nisa atunani yasani cewa Abba ka zauna mana kana tsaye,Lokacin nasamu na zare haidar da jikina na hadashi da filon kujera.


Abba na zaune saida naci waina da miya hadda nama wadda bansan inda yasamotaba sannan yabani maganin nasha.
Har ya yunkura zaitashi nace am Abba" na'am akwai wani abune?


"Uhum dama cewa nai yaushe zakaje bakori?


" murmurshi yayi kamin yace kedai kawai kice kina kewar gida,To Amma ai danginki basu jima da zuwaba ko akwai wata damuwa ne?


A a Abba babu damuwar komai damadai inaso inje maska ne domin kasan mahaifin mamana babban malamine inaso inganshi akan wasu matsaloli danafara fuskanta cikin kwanakinnan sannan sai ingayamishi matsalar yayan nasan zai fahimceni sannan bazai gayama kowaba nasani.


"Ajiyar zuciya ya sauke kamin yace eh hakane Ruma ni kaina nafarajin tsoron kadda lalaurar haidar ta shafeki Sabida abune na mutanen boye Sabida haka ki shirya gobe idan Allah ya kaimu zansa harun ya kaiki shine kawai Wanda zakutai tare insami nutsuwa inyaso ni sai in tsaya da haidar din kamin kidawo nagode sosai da kikai wannan tunanin Allah yaimiki albarka Ruma Allah yabaki ladar jinya.
" Kaina akasa na amsa da ameen.




Tunanin mafarkin danayi Sam yaki barina ko yaya na motsa yana makale cikin zuciyata.
Ga ya haidar yau rigima yakeji ta gaske domin zazzabin da yakeyi duk inda nake yananan nane dani yana hawaye Wanda koda abban yakuma shigowa wani dadine yakamashi domin Wanda keba ya haidar din magani ya tabbatar da cewa lallai duk lokacinda yafara kuka da idanunshi to alamune na amfara samun nasara.




Sai yamma sosai daf da magriba sannan Abba ya barmu akan lallai in shirya da wuri zamu wuce.
Araina inata murna domin kusan watana hudu kenan amma bantaba zuwa gidaba sonake mufara biyawa ta bakori idan naimata sallama saimu wuce maskan.

Nasaba yimishi wanka da alwala duk dare danhaka yauma saida nagama shirina sannan nahadamishi ruwan wanka na ajiye na alwala gefe.
Bra din Dana aje dazan shiga wanka ita na tadda ahannunshi yanata matsawa tare da Neman taushin dake jikinta.
Dariya ta kamani kamin ince ya haidar rigar nono ce ko kaima kanaso insamaka? Haka nakeyifa wani lokacin idan inamishi magana sai adauka nima na zare din domin sosai nake biyemishi.
Sam be magana nidai inba tari ba ban tunanin ko gyaran muryarshi natabaji.


Hannunshi nakama naje naimishi wankan tare da alwala sannan mukadawo daki ko mai banshafamishiba Sabida becikason shafaba wani lokacin.
Cikin bargo nashige ina addua shima yashigo tare da shigewa cikin jikina sosai,Mamaki ya kamani domin kullun ninake jawoshi in rungume amma yau yashigemin jiki harwani sauke numfashi yakemin awuya.


Addua na shafamana ina mitar wannan zazzabi har yanzu yaki barinka ya haidar kodai maganin zan kuma baka?
Mutsu-mutsu yafara tare da gogamin jikinshi ajikina yanawani Dan kuka-kuka abinda ya tasarmin hankali domin yatabayin haka Abba yacemin sha'awarshice

Please Login or Register in order to submit comment