Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

takan duniya.





** *** **




Irin gyaran da bangarena ya diba sai mutun yai mamaki kullun cikin gyare gyare yake yahana kanshi sakat tsabar zumudi duk da cewa yana zullumin haduwarmu tunda yasan cewa fishi nakeyi dashi,Ammadai ya k'udure komadai menene yasan zan huce indai nadawo din.


Ranar da zandawo kuwa ai hana Harun sakat yayi tun safe yadameshi da kira dayake shine Wanda zai daukomu.




Nagama shirina tsaf haka inna tagama kintsamin duk abinda tasan zan buk'ata duk da umma da Abba sun gargadeta akan kadda taimin wata wahala daban amma ina saida ta hadamin kayan da ake raka mejego dasu da yawa hadda dan akuyanta ta yanka aka soyeminshi.
Dijee na hadama kayana sosai da wasu danabarma inna din da atanfofi kozata dinka hakama baba nabashi kudi sosai dan tuni ansaimin fili da kudin danasamu wajan haihuwa gakuma ragowa da inna tace sai azuba kiwo.




Anshiryasu cikin kayan sanyi sabida iskar mota yaran sunyi wayau fiye da tunanin me karatu har wasa sunsani dan sunfara dariya sunyi wata irin kiba kamar sunyi watanni hudu ko biyar nan ko watansu biyu da yan kwanaki kawai.
Jinai kamar insaka ihu lokacinda harun ya iso,inna ta tarbeshi sosai saida ya huta sannan ya shirya kayanmu cikin motar har baya dole saidai wajan zamana ya kasance gaban motar dan sosai kayan sunyi yawa waifa damma narage sosai nace abawa mabukata.


Rungumar yaran yayi yanata murna da santin yanda suka koma ko wannensu idanunsu k'yar tsabar wayau sai dariya yakeyi dajin dadin ganin yaran balle dayaimusu wasa yaga sunyi dariya.
Kallona yayi yana dariya gaskiya madam haidar yaimiki wayau yo ai naga babu ta inda yarannan sukaimiki kara ta dauko wani kamanni naki kin lura da hakan kuwa?


Nidai murmushi kawai nayi,Dan ni kaina ina mamakin irin kamannin yaran da mahaifinsu.


Saida yaima inna kyauta ta girma sannan mukabar garin bakori munbar inna da sharar hawaye bata taba tunanin zanjawomata arziki irin hakaba,Saigashi dabata haihuba Allah yabatani kuma tanajin dadi.





****




Tafiya tayi nisa na sakasu cikin hijab sabida iska amma yarannan sukace ba hakaba saima uban ihun da suka sakamin lokacin guda gashi nasaba da inna na temakamin aduk lokacinda suka fara rikici.
Jinai kamar insakamusu kuka lokacin dole saidai ya faka motar ya rikemin daya sannan naba na hannuna nono saida ya barci sannan na lallaba na kwantar dashi ajikina na amshi na hannunshi,Kusan atare muka sauke ajiyar zuciya nida Harun din lokacinda yaran sukai barci kamin yacemin "Sannu da k'okari madam Allah yasa masu jin kammune!


Da murmushi na amsa da ameen ya Allah sannan yacigaba da tafiya jefi jefi muke fira kusanma duk firar matarshine datake fama dalaulayi yanzu.




Muje katsina
[4/2, 3:09 PM] Re@l💍 K@usy🌹: Rumana 54




Saida ya mula dan kanshi sannan ya furta"Amma umma dan Allah tun yanzu za'a fara batamusu cimarsu? Tunda tanada wadataccen nono jikinta abarsumana har zuwa ko watanni shiddane ko?


Wani kallon banza taimishi kamin tace sannu ubana' To bari kaji insha Allah nanda wata shida summa kama abincin gaske danhaka kaje ka tasota tazo ta sallamesu kaikuma ka fice nemo madara kamin ranka yabaci kaji ko?


Bakinshi ya turo gaba yana nanata kai umma.


Tarairayoni jikinshi yayi yana tashina,Idanuna da sukai ja kuma sun kankance na saukesu akanshi,Ina yamutsa fuska dan wallahi nagaji fiye da yanda za a hasaso wannan fitina dame tai kama dan Allah?


Wata muryar tausayi yayi tare da cewa"Ga ruwa can na hadamiki kikuma gasa jikinki kuka sukeyi duk yunwa sukeji.


Naji dadin jikina sabida ruwan zafin daya ratsa jikina sannan na nufi falo dan can nakejin sautinshi Dana umma kamar dai fada take mishi.


Cikin mutunci muka gaisa sannan tabani Abdurrahman dan dama yafi korafi,Kamin wani lokaci yai luf jikina yana shan nonan,Ganin fuskarshi cidin cidin yasani kallon umma sainaga Ashe harararshi taketayi,Jinai kamar insaki dariya wlh.


Shima abdurrahim saida yasha sannan nasamu nima nacika cikina.


"Wai zaman me kakeyi haidar? Kobakaji abinda nagayamakaba kai banfasan shirme wlh.
Fuuuuu yatashi yabar falon kuma har umma takoma da yaran be fitoba.Zamana nayi falon dan wani irin tsoronshi naji inaji wallahi gaskiya ya iya mugunta,Kokuma dan hadda uban gyaran danasha ne oho dai amma dai naji jiki yanda ya kamata.


Tuni barci yafara surata saidai kamin yai nisa naji yai sama dani yana dariya,Lallai yarinya wato inacan ina jiranki kekuma kina nan zakiyi barci ko?


Banza nayi dashi dannaga alama soyake inbiyemishi ya halakani.


Kan gado ya kwantar dani tare da shigewa cikin jikina alokacin jinai kamar in yankashi in huta da saida yakuma biji biji dani sannan yai shirin fita office lokacin ko motsin kirki sainayi da gaske nake iyashi.
Sumbatar goshina yayi tare da cewa Allah yaimiki albarka ni zan wuce amma idan anyi sallar azahar zandawo insha Allah.
Kaina kawai nadagamishi,Sannan na maida na rufe bayan yabar dakin.Bansan lokacinda barci yai awongaba daniba dan inata tunanin farkon aurena da yanzu wanne nafishan wahala saidai bankaiga gano amsarba barci yai awon gaba dani.
Kai gaskiya umma ba k'aramin kaunata takeba wallahi ko girki haka ta hanani inyishi ayinin sannan ko yaran idan har ba kuka sukafaraba to bazata kawosuba,inko ta kawosun dasunsha nono take komawa dasu.


Tunda taga bezo da madararba bayan magriba kawai saita kyaleshi saidai ta kudurce dakanshi zai siyota idan yaji uwar bari.




Da dare.
Nagama sallar i'sha,I kenan saiga umma da yaran kuma gaidata nayi sannan nakoma na zauna muka fara hira domin yau koso daya banfitaba.


"Uhum kinga Ruma mijinki wani irin murdadden mutunne wallahi yau tunsafe nake fama dashi akan yasiyoma yarannan madara amma ya kiya kinga ko dawowa gidan ma beyiba kuma nasan hadda maganar danhaka amatsayinki na matarshi kuma saukinnan ke ake nemarmashi danhaka saiki dage wajan ganin fin fahimtar dashi tunda da gaske yake beson ahadama yaran wani Abu da nono yakasa fahimtar nono ba lallai ya wadatar dasuba tunda kullun wayau sukekuma yi indai baso akeyi aga kinata tsotsewaba danhaka yau zan barsu nan ku kwana tare dasu nasan idan suka hanashi rawar gaban hantsi zaisai abinyi kuma kice nace kadda akaimin su matukar kinga yanaso ya kaimin su kinji ko?


" To umma zanyi komai insha Allah.



Sallama taimin tabar falon tare da tambayata nako shanye tsumin dataimin?
Nidai amsawa nayi da eh amma kofi daya kawai nasha nazuba sauran cikin frij haka kawai intashama kaina abinda zai wahal dani.


Ina rungume dasu duk ajikina sunata wasansu ina biyemusu sosai yaran sukai wayau idanun nan kyar idan suna kallonka daga gani kasan zasuyi wayau na gasken gaske.
Da sallama ya shigo idanunshi na kanmu fuskarshi cike da walwala da farinciki.


Sannu da zuwa naimishi tare da tashi zaune shikuma yaran ya kwashe gabadaya daga jikina bayan na karbi kayan da yashigo dasu, Sosai yakemusu wasa suna bangale baki oh ni wai harsun San wasa🤔 Koda yake yaran yanzu da wayansu ake haihuwarsu.


Gefenshi na zauna ina ragemishi kayan dake jikinshi da safa da takalmin kafarshi dan babu abinda ya cire hasalima hankalinshi kacokan yanakan yaran.
Shigewa nai bedroom dinshi da kayan sannan na had'amishi ruwan wanka saida na d'aukomishi marasa nauyi wa inda zaisa inya fito sannan nakoma falon.


Dady ga ruwan wanka can,Kasancewar tun bayan Dana haihu haka nake kiranshi dady ko dadynsu dan banso sutaso suji ina kiran sunanshi.
Rungumoni yayi jikinshi yana murmushi"Babyna kinga yarannan dariyar da suke ko?


Nima murmushin nayi tare da nunamishi yaran da yatsana yanda suka zubamishi ido suna kallo ni tsoroma naji bazasuyi kiwaba dan da alama kallon sani zasufara daganan kuma sai kiwa.


Dakyar nasamu yatashi zuwa wankan kamin yadawo nagyara naman da yashigo dashi dan dama banyi girkiba.

Dawani kallon soyayya nabishi kai gaskiya dady karshene wajan kyau da gayu sai k'amshi yakeyi.
Kusan cin abincinma ashirice akayishi dan hankalinshi nakan yaranshi wa inda keta haurinshi da kafafunsu batare da sanin mesukeyiba,Shikuma hakan da sukeyine shine yakejin dadi.


Lokacin kwanciya nayi na shirya yaran na shayar dasu yana zaune dan kaddama sufara rigima yace laifinane danhaka agabanshi duk saida sukai taf dasu sannan na kwantar dasu atsakiyar gadon dadynsu ya kwanta farko nikuma k'arshe🤣.


Manyan idanunshi ya zubamin kamin yace"babyna yanaga haka? Yau bazasuje wajan umman bane?


Cikin alamun rashin damuwa nai shirin shiga wanka tare da cewa"Aiko yau tacemin bazasuje kwana wajantaba dan bata da abun basu.




Bece komaiba yaci gaba da jijjiagasu koda nafito wankan har sunyi barci abinsu kamar suyita barcin su Amma nasan anjima kadan labari zai canza.


Saida nagama jamishi rai sannan naje gareshi,Yaudin madai kamar koda yaushe yi yake kamar zai cinyeni tsabar zalama,Saidai yanayin gurnanin da yakeyi da uban nishin da yake saki gakuma sheshshekar kukan da nakesaki nima yasa yaran tashi kamin yasami nutsuwa.
Yanajin kukan yaran amma yakasa sakina har saida yasami nutsuwa,Mikewa yai dani kawai muka gyaro jikinmu kamin mudawo nacigaba da kula da yaran,Yanaso ko rungumeni yayi amma ina ko yaya ya motsa suma yaran saisun motsa.


Da asuba ma saida tafiya tai nisa sannan abdurrahim Yakama ihu dole saidai ya kyaleni ammafa beji dadiba dan sosai yaita jan tsaki.
[4/2, 3:09 PM] Re@l💍 K@usy🌹: Rumana 53




Wani farinciki ne naji ya lullubeni lokacinda na hangi mijina kuma uban yarana,Saidai tuni na gimtse fuskata karma yai tunanin naji dadin ganinshi dan har yanzu ina tuna maganar daya yabamin na inje in k'wada abuna in cinye danhaka sainagama wanashi akan hakan.


Tsakanin umma da Abba har rige rigen daukar yaran suke yayinda nikuma takaicin batani sukeba yasani turo bakina gaba cikin yanayi na shagwaba.


Ummace ta rungumoni jikinta tana dariya tare da cewa"ke Kyalemu munga jikoki mun manta da diya yi hakuri diyar albarka sannunku da hanya Harun!


Shigewa mukai bangaren umma cike da farinciki musamman Abba Wanda hakoranshi sunki rufuwa ganin yanda yaran sukai manya dasu kuma nono kawai sukesha.


Harun da haidar muka bari tsakar gidan duk wani Abu daya danganci tsaraba sai harun yayi wajan umma dashi sukuma kayanmu sai haidar ya nufi bangarenmu dasu jikinshi har rawa yakeyi tsabar murna da farinciki sannan gashi ya ganni nawani canza yasan ba k'aramin jin dadi zaiyi ba.


Kasancewar yanzu ban wasa da cikina shiyasa ina hutawa na lodi dadd'adan girkin umma sannan ta hadamin da lemon kankana Wanda yaji madara,Nadaisan da biyu akaimin wannan hadin.




Har karfe Tara na dare ina wajan umma yayinda oga harya gaji da lewa ya zauna hirar shima sai tsomoni cikin hirar yake nikuma ina basar dashi,Dan so nake yagane yaimin laifi ko yayane.
Umma tai musu wanka tare dayimusu shirin barci,Kasancewar nayi sallolina yasani cewa umma bari inje Indan watsa ruwa jikina duk ciwo yakeyi idan zaku kwanta sai inzo in karbesu.
Abbane ya amsa da shikenan ai saimungama hira zasuyi barci,Ya idasa maganar yana dariya kallo daya zakaimishi kasan yaufa yana cikin kwanciyar hankali da farinciki.




***




Sam Bambi ta kanshiba duk da yanda yaketa wani takalata da magana hasalima shigewata nayi bayi danyin wanka.


Saida na gama wankan sannan na fara lekenshi ta kofar makulli aiko can na hangeshi zaune bakin gado ya zubama kofar bayin ido.


Wani irin shegen murmushi nasaki kamin ince mujedai zuwa malam nima ai da wayau na.


Yamutse fuska nayi sannan na fito kai tsaye na wuce wajan madubi nafara shafa manshi dake dakin domin ni duk ban kwance kayanba.


Ina sane na janye tawul din nai k'asa dashi ina shafama kirjina mai Wanda ya cika sosai sabida shayarwar da nakeyi.


Kasa hakuri yayi yataso sai jinshi kawai nayi ajikina yana sauke numfashi tuni ya zagaye kirjina da hannuwanshi harwani lumshe idanu yakeyi.


Tureshi nayi daga jikina nasaka rigar barcin Dana ciro nakoma gefen gado ina sawa.


"Dan girman Allah kiyi hakuri Rumana komaifa ya wuce damme zaki maido abinda ya wuce?


Cire hannunshi nayi daga jikina Wanda yake lalubata dashi kamin ince" Yo mekuma zaka cemin aini kawai nasan dama baka tausayina shiyasa kullun inbakasani na zubar da hawayeba bakajin dadi yanzu kuma mezakace dankaga na dawo ko?


"Naji na dauki laifina dan Allah kiyi hakuri bazan kumaba kiji tausayina mana wallahi nayi kewarki da yawa kamar zan mutu nakeji fa!


Tuni ya birkice min sabida tsabar zalama jikinshi babu inda be tsuma.


Kwace jikina nayi " Yo mezakayi da abinda kace inje in k'wadashi in cinye ai tuni na cinye abuna.


Matseni yayi jikinshi yana fidda numfashi awahale tsabar yanda ya kwadaitu da yawa"Kidubi girman Allah kibar maganar nan ai nasan kedin tawace abunma nawane sannan babu yanda za ai kicishi dole dai nizan cimikishi ko? Kiyi hakuri na tuba autar mata.




Yanayin yanda yake jagulani yasa wani mugun tsoro darsuwa cikin raina sabida nasan bafa k'aramin gyara nashaba dan akwai wani Abu danai amfani dashi tunban jima da haihuwarba nida kaina saida nai mamakin yanda gabana yayi dan bazakace nai aureba balle ai maganar haihuwa.


Tuni uban tsumi da gyaran danasha yafara aiki bansan lokacinda na biyemishiba.
Ba k'aramin nisa mukaiba mukaji sautin umma nata kwalamin kira sabida yaran na kuka.


Dakyar na samu na yakiceshi daga jikina ina jawo nutsuwata sannan na amsa mata.


Kifewa yayi akan gadon yana matse cinyoyinshi idanunshi sunyi jajir tsabar fitana.


Saida na kintsa sannan nafita wajanta tana daga falo sai naji yana cewa kibarsu can wajanta idan sunsha please.


Kunya kamar zata kasheni haka na k'arasa wajanta na karbesu aiko kamar zasu kasheni duk Wanda ya cafka saiyayi kamar zai shanye nonon dukanshi ummadai na zaune tana kallona.

Cikin tausayawa tace" Kina hadamusu da madara ne?


Kaina na girgiza kamin ince "umma tunda aka haifesu naimishi magana yace be yardaba.


Tsaki taja kamin tace dallah kyaleshi shi wani tsotso yasani shi gobe ai dole a nemomusu inba hakaba shima bazai sami nutsuwar da yake buk'ataba kawosu.


Mikamata su nayi kamin ta mike tabar falon nidai kasa tashi wajan nayi,Saida yaji shirun yai yawa saigashi ya fito dagashi sai gajeran wando,Jinai kawai yai sama dani yana nanata lallaima yarinya nadaiga alamar bakisona yanzu Neman kasheni kawai kikeyi.


Cikin shagwaba na rikeshi nidai kaimin ahankali gaskiya idan ban kashekaba aikai ka kasheni din ko?



Tun kamin tafiya tai nisa nafara gane kurena dan sosai yake gwadamin irin kewar daya kwasa akaina.
Abun mamaki saigani ina kuka tare da rokonshi kadda ya kasheni,Amma shi ina banda sambatu da sakin nishi ai be iya komai.





Da Asuba. Saida yaimin ruwan zafi sannan nasamu nai sallah saidai yana dawowa yakuma yowa kaina ko tausayi babu.
Kuka nakeyi sosai tare da hadashi da Allah yai hakuri nagaji kilama yajimin ciwo amma ina da alama ko jina beyi saidai fadin infa saki jikina da yakeyi kadda ya cutar dani,Yo cutarwa ta nawa kuma mutumin dake Neman mahalakata.


Matseni yayi jikinshi yana jijjiga gamida lallashi yayinda naketa sakin ajiyar zuciya da sheshsheka bansan lokacinda barcin wahala yai gaba daniba.


Wani irin murmushin nishadi yake saki akai-akai yana kuma sumbatar goshina da gashin kaina wata irin nutsuwa yakejin tana saukomishi wadda ya kwana biyu rabonda yaji irinta danhaka saidai yai murmushi tare da kuma shigardani jikinshi,Saima lokacin ya tuno da yaran koya suka kwana oho dan garama su saba koda babu umma beda tsarin kwana da yara haka kawai da anyi motsi yaro yatashi kuma ace sai anbashi nono shikuma me gida yana kwance yana jira kai ina bazai iyaba.


Yana nan rungume dani yaji jikina yafara dumi alamar zazzabi ga barcin da nakeyi da alama banjin dadinshi.


Gyaramin kwanciya yayi sannan ya wuce yai wanka yafita kitchen dan tuni gari ya waye saidai idashe.


Inata barcina shikuma ya hada abunda zamu karya dashi.

Yana zaune afalo yana kwallo hankalinshi kwance saiwani murmushi yake saki akai akai sabida maganar gaskiya ba k'aramin dadi ya kwasaba kai bayan yana tsoron cutar dani to da lallai ya dawwama cikin wannan ni'ima.


Ummace ta shigo da yaran hartai musu wanka ammafa ko wanne sai wawure wawure sukeyi damma umma nata duramusu zamzam Abba na aikin jijjiga.


Gaisheta yayi gwanin kunya dan sai yanzune yaji wata kunya na dabaibayeshi.


Abdurrahaman ya amsa hannunta tare da sakamishi Lib's dinshi cikin baki aiko nan da nan ya karbe tunaninshi ko nono ne.
Basaita tambayaba tunda taga bani falon jikinta yagayamata ya bazar dani.
Kallon shi tai tana kankance ido "to kai ya za ayi da yarannan naga kamar mamarsu bata tashiba kuma yunwa sukeji dan har cikin dare kuka sukaitayi! Kaje ka samo madara adinga hadamusu da nonon yanda zasufi koshi ko?




Wani irin bata fuska yayi yana kallonta.
[4/2, 3:09 PM] Re@l💍 K@usy🌹: Rumana 55




Washe gari: Yana karyawa yanayima yaran mitar sun hanashi rawar gaban hantsi Sabida mugunta kalar tasu,Nidai inaji saima dariya dayabani.


Hararata yayi kamin yace"Humm karma kifara dariya Dan yau bazan yadda da hakanba,Badai yunwa ke hanasu barciba? To yau insha Allah zan dauki mataki.




Yinin ranar wajan umma na yini nida yaran saida akai sallar Azahar saiga d'an sako daga dadynsu madarace me yawan gaske ta baby ya aiko da ita kuma wai a ajiye bangaren umma.
Ni wallahi ma dariya yabani balle kuma umma wadda taita dariya hadda kwanciya.


Kallona tayi kamin tace"Kinga anyi maganin mijinki ko?Aidama nasan abunda zai tankwarashi kenan,Shima nan alhaji haka yaita faman cewa inje in dauko yara nace a a abarsu can yau sukwana da iyayensu kinga gashi ya siyo madarar yanzu da rana saiki dinga basu nono nikuma saisu dinga kwana wajena sunashan madara kema kindan sami sukuni tunda hidimar da yawa ko?


Murmushin kunya nayi tare da cewa"Nagode umma Allah yasaka da alkhairi,Ubangiji yasa agama da duniya lafiya.


"Ameen ya Allah kema Allah ya albarkaci rayuwa data iyali aike cikon faruncikinmuce Ruma dole muyi duk yadda zamuyi Dan ganin kinsami farinciki musamman da kike marainiya babu uwa kuma babu uba.




Inaga dai daga hakan bazance inada wata matsalaba Dan ko girki anan wajan umma nayishi gabadaya Saina dibarmana na darenmu nakai bangarenmu tunda dai bedawo da ranaba nasan sai dare Zai dawo.


Saida Abba yadawo sannan naimusu sallama bayan nagama cikama yaran cikinsu da nono,Dan Abba kai tsaye ya nuna shifa be yadda mudinga kwana dasuba harwani lallashina yakeyi akan inyi hakuri inbarmusu yaran su dinga kwana tare dasu,Bawan Allah besan mungama tsara komai da umma ba.




Wanka nayi da ruwa me zafi naji dadin jikina dan yinin yau da ciwon cinyoyi nayishi.


Ina niyyar hayewa gado saigashi ya shigo yai wani biji biji dashi daga gani yauma agajiye yake,Amma nasan wannan gajiyar bazata hana ya suburbudeniba kamar wasu kayan wanki.
Ruwan wanka na hadamishi bayan naimishi sannu da zuwa yo goma saura bammasan inda ya tsayaba daga wajan aikin.


Saida zai shiga wankan sannan yacemin"Ya yaran yau sunsamu madara shine umma ta daukeso ko?
Ban nuna na san maganarba danhaka sainace tadai daukesu yau.




Kamar kullun yauma saida nai kuka da idanuna sannan nasamu ya sararamin.
Ganin naki daina kukan ne yasashi fara lallashina amma banza nai dashi Sabida yaban haushi wlh.


Bayan munfito wanka ya rungumeni jikinshi yana bubbuga bayana"Shikenan kiyi hakuri akwai zafinne har yanzu?
"Kaina na daga ina sharben hawaye.


Dariya yasaki kamin yafara magana cikin Lallashi" Dan Allah dubeki da girmanki da komai hadda yara amma kinayima wannan 'yar abin kuka, Wannan ai abun kunyane kallifa Dan Allah"


Kauda kaina nai ga barin kallonshi Sam beda kunya wlh jifa abunda yakemin,Kaimishi duka nayi cikin shagwaba nace Ammadai idan katashi cin zalinka ai girma Abun ke k'arayi ko?


Rungumeni yayi yana tausamin cinyoyina"Kedai kawai kincika raki wallahi sannan kinada jiki me kyau irin Wanda ake bukata shiyasa har yanzu baki budeba sannan ni kadai nasan irin dadin da nake kwasa aduk lokacinda nashiga shiyasa nake rudewa afuwan please idan zanyi anjima ahankali zanyi.
Kwanciya kawai nayi balle danaji yana maganar wai anjima ma zai kuma saikace wani cin abinci.






** **** **




Bayan watanni shidda.
Dama ance shekara kwanace ga me yawan rai,Wannan batu haka yake.


Yau tunda natashi nakejin tashin zuciya Shiyasa ma duk aikin da nayi akasalance nayishi damma yaran na wajan umma watansu takwas kenan yanzu amma rarrafe babu inda basu zuwa ga bak'ar barna har kama Abu su mike sukeyi inko sukaga abun banna ai babu magana.
Ina tunanin yanda suka saba da umma da Abba basu saba damuba can suke yini indai ka ganni dasu to nono ya kawosu dasunsha kuma zasu kama gabansu.


Kwance nayi nai lamo cikin kujera Sabida jin yanda cikina keta yamutsawa kamar zanyi amai wlh.
Dagashi sai jallabiya ya shigo falon kasancewar yau yakoma
nasan ba wani waje zashiba,Be zaunaba ya fice wajan umma babu dadewa saigashi da yaran,Yarane masu matukar kyau da shiga rai gasu bul-bul dasu kuma kamarsu daya idan bamuba babu Wanda zai gansu ya iya banbancesu ko Harun dake ganinsu akai akai kusan koda yaushe saiya tambaya ina babban.
Gaba daya kaina sukayo danshan nono niko haka kawai naji raina yabaci,"Haba Dan Allah inafama da kaina zaka kwasosu suzo su tsotseni tas kuma sunemi abinci ko?


"Sorry baby bansan zasu nemi nonon ba Ai tunda naga wasansu suke"


"Hummm tunda suka ganni aikasan saisunsha hankalinsu zai kwanta.


Yana rungumeni dani sunashan nonon sai murjemin jiki suke Dan Sam basu nutsuwa idan sunasha,Dacan daya nakefara ba kamin daya amma tunda sukai wayau basu yadda danafara ba daya ko wasa dayan yake saiyabari yadawo yasha.

" Dady amai fa nakeji wallahi ko naman danaci jiya ne ya

Please Login or Register in order to submit comment