Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

tashi ba, ita kuma tuni ta fara nisa da shafar da take mishi sai kawai ta jiyo tafiya daga bakin k'ofa.

Da sauri ta gyara tsayuwarta tayi wani kalar tausayi da ita. Mudi ne ya shigo da kayan Haidar d'in a hannunshi da alama daga shanya ya d'ebo su. Kallonta yayi itama ta kalleshi kamin tace.


"Sannu Mudi ya yarona da jikin?'' Kallonta yayi sannan ya kalli Haidar d'in sannan yace mata.


''Da sauki bacci yake yi.'' Juyawa tayi tare da fad'in.


''Dama lekowa nayi in ganshi daga unguwa nake ma sai anjima a kula da abincin shi dan Allah.'' Ficewa tayi tana cewa.


''Allah ya kai damo ga harawa na san ko baici ba zai yi birgima.''

Hajiya Saude kenan mace mai matukar had'arin gaske ta iya fuska biyu kai ita har fuska hud'u ma ta iya. Da kallo Mudi ya bita har ta b'ace mishi kafin ya girgiza kai dan shifa wallahi matan alhajin nan tsoro suke bashi.


****


Bakori.... Taro ya tashi lafiya kowa sai fad'in albarkacin bakin shi yake yi, Yayin da malamai suke ta yin nan-nan dani domin ba k'ananun kud'i suka samuba ta dalilina banda kyautuna wa inda aka dinga bani hannu da hannu ba, Inna na gefena takasa ta tsare sai yamma lis muka koma gida domin bayan taron ya watsema ni hanani tafiya akayi. 'Yan uwan mahaifina dana Ummana da suka zo tuni suka koma gidan zaman jiran dawowarmu.

Wai dadi kasheni yau inna ce hadda kaimin ruwan wanka bayi, har cewa take. ''Ki gasa jikinki sosai danki sami nutsuwa domin wannan jaganiyar da kikai yawa gare ta, Allah dai yayi miki albarka ya jikan iyayenki.''


Ina wanka ina tunanin anya nice kuwa, ashe dama haka mutum yakeji idan har dad'i yai mishi yawa? ni dai yau gaskiya dad'i yayi min yawa, najima a bayin dan tunani yai min yawa, sai da naji inna na kwalamin kira sannan nai azamar watsawa jikina ruwa na fito ina na fito ta.

Gwanin dadi ta washe baki kamin tace. ''Yauwa 'yar albarka zokici abinci dan ina sane duk yau ko ruwa baki sama cikin kiba.''


Ina fara cin abinci sai ga baba ya shigo da sauri yana fad'in. ''Ina Ruma take d'auko hijab d'inki ga baki zaku gaisa chairman ne yayo aike basu iso da wuri ba.''

Kirjina yai wata irin bugawa nan da nan jikina ya d'auki rawa na fara hawaye.


Dariya suka fara yimin ganin yanda duk na rud'e jikina ya d'auki rawa. Da fani baba yayi kamin yace min.


''Ki kwantar da hankalinki gaisawa kawai zaku yi kinji ko?'' K'anin mahaifina baba Rabi'u shima dafani yayi kafin yace.


''Jeki mana 'yar baba.''


Kamar zasu kamani haka na dinga labe-labe Baba na biye dani yana dariya. Duk'awa nayi har k'asa na gaida su, ban tashi a wajan ba sukaci gaba da sakamin albarka, Lokacin ne Baba yake cewa.


''Ai da yake marainiyace babu uwa babu uba shi yasa sam bata da walwala sosai.''

Nan fa suka kuma cika da mamaki tare da tausaya min, musamman da suka kasan ce manyan mutane kowa cikin zuciyar shi fata yake ina ma ace d'iyar shi ce. Wani kunshi ne suka miko min.


''Gashi wannan tallafi ne daga shugaba, Allah yayi miki albarka yai miki jagora.''


Hannu nasa na amsa wanda yake ta faman yin rawa dan dama can ni haka nake maza masifar tsoratani suke yi balle yau duk jina nake yi a takure.


Kasa cin abincin nayi a haka har dare gidan mu bai rabu da mutane ba anata shigo mana barka da Allah sanya alkhairi.


Cikin dare ina can ina bacci su kuma suna can d'akin inna ana bud'e kyautukan dana samu tare da makudan kud'i wanda yawan su duk sai da ya firgita su da yake akwai kannan mahaifina dana mahaifiyata wa'inda basu tafi ba nan zasu kwana.


**** ****


Alhaji Yusuf ne a zaune shida yayansa suna kuma tattaunawa akan lalaurar Haidar wacce tuni ta gama danne zukatan su da tsananin damuwa.


''Gaskiya yaya Allah ya sani nidai nayi iyakar abinda zan iya yi mishi amma yanda yake haka yake narasa ta yanda zan bullowa wannan larurar gashi har yanzu neman Fatima nake amma babu ita ba alamarta kuma ni wallahi ban saketa ba amma ta manta damu baki d'aya nida yaron ta.''

Numfasawa Alhaji Yahaya yayi sannan yace.


''To Yusufa nikam a wannan gabar ban san abinda zanyi ba kasan dama da kyar da sid'in goshi aka baka auranta sabida suna tunanin matanka zasu iya cutar da ita, Sannan lokacin da ka turani naje labarin abinda suka bani kayiwa ita Fatiman ai babu dad'in ji kuma sunce sunsan sharrin matanka ne amma kafara d'aukar mataki a gidanka sannan su fara tunanin mai da maka da matarka, idan ma zasu iya kenan dan haka ni abinda nake gani a farabi ta neman maganin Haidar d'in tukunna sannan akoma takan Fatima domin ita nata mai sauki ne tunda ta san cewar akwai aure akanta, ka gane ko?''


"Eh yaya na gane, amman ni wallahi da Haidar lafiyar shi lau dana nema mishi auran wannan yarinyar dan ta tsaya min a rai, gaskiya iyayenta sunyi sa'ar haihuwa ta wallahi.'' Murmushi yayi kafin yace.


''WaivRumana kake nufi? Ai haka Allah ya hore mata wannan baiwar kowa sha'awarta yake yi, amma marainiyace nan dakake gani bata da uwa balle uba malam shi ne yake rikonta, amma ko yanzu bata b'aci ba zan tuntubi shi malam d'in idan har zai iya bamu sai muyi dabarar yanda babu wanda zai gane sai ace mishi yaron na k'asar waje karatu muna sone daya dawo ya tararar da matarshi, sabida gaskiya nima hankali ya karkata ga hakan tana da nutsuwa da hankali sannan tabbas zata kula dashi kaga idan ma anfara maganin itace zata tsaya tsayin daka wajan ganin yasha ko amfani dashi, amma wallahi Yusufa banga amfanin wad'annan ruguza-ruguzan matan naka ba nasan kullum makasarka suke nema.''

Shi dai alhaji Yusuf shiru yayi tare da sunkuyar da kanshi k'asa shi abinda yasa ya kasa d'aukar mataki akan su ya zai yi tunda babu wacce ya tab'a kamawa da wani mugun laifi' sannan ko wacce tana kula dashi, shi tsoran shima kadda yaje ya saki wacce bata da laifi amma yasan yana nan yana saka musu ido akan komai nasu.

Zuciyarshi ta cika da farin ciki jin cewa yayanshi zai tuntubi marik'in Rumana ko zai bashi aurenta, lallai yasan Haidar ya gama morewa idan Allah ya bashi lafiya.


****


Cikin wannan dare Hajiya Saude zigidir take haihuwar uwarta agefen d'an k'aramin wajen shak'atawar gidan, wanka take yi da wani koko da magani a cikin shi tana yi tana sambatu tare da kiran sunan Alhaji Yusuf tana nanata sunan matanshi d'aya bayan d'aya, Itakam bata ta Haidar domin dashi da matacce duk daya ne a wajanta.

Tajima tana wannan surkulle sannan ta yafa zaninta tabar wajen bayan ta d'aurewa wajan gudun kadda wani yazo wajan da safe ya gani ya gane.


Adai-dai wannan lokacin shi kuma Alhaji Yusuf yana tsaye gaban Allah yana kai kukanshi gareshi na matsalolin rayuwa da suka addabeshi, tabbas ba dan yana da tsananin matsi akan addininshi ba da tuni anyi babu shi, ko kuma wata lalurar ta same shi.


****


Yana kwance a gefenshi yake jin wani irin nishi tare da nunfarfashi, da sauri ya bud'e idanunshi tare da lalubo wayarshi dan tashi ya kunna musu haske zai iya yi mashi wahala. Ji yai kamar ya saka kuka lokacin da yaga halin da Haidar d'in yake ciki ganin gabanshi ya mike sosai kamar zai fasa mishi gaban wando, sai zufa yake yi yana wani irin gurnani.

Mudi wanda ya gaji da ganin halin da Hydar yake ciki bai son lokacin da ya jawo Haidar d'in zuwa jikin shi ba, a tsorace ya fara shafa masa wajan jikinsa yana kyarma burinsa kawai Allah yasa Hydar d'in ya samu sassaucin wannan sha'awar da take bijero masa dan ya kudure a ranshi Alhaji na dawowa zai gaya mishi gaskiya a samu a yiwa Hydar aure tunda dai yanzu ya rage dukan mutane bare ace zai bigi matar da za'a auro masa. Wani irin abu Mudi ya gani domin......
















*MAMAN KHADY*🙇🏻‍♀
[4/2, 11:15 AM] Re@l💍 K@usy🌹: 💞💞💞 *RUMANA* 💞💞💞


Na


*MAMAN KHADY*🙇🏻‍♀
(Mk)


*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡
(Home of expert and perfect writer's)




Page 1






Zaune yake cikin d'aki ya zabga tagumi hawaye kawai ke ziraro mishi daga cikin idanunsa, 'lallai bawa ba abakin komai yake ba wajan ubangijin mu, yanzu nan Haidar d'in shine a haka amatsayin mahaukaci mai hauka tuburan, Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un, wannan wace irin k'addarace wadda ta tsalleke duk shekarun da aka baro baya sai yanzu da Haidar ya zama cikakken mutun saurayi mai hankali, lokacin da yake murna kwai d'ayan da Allah ya bashi ya rayu zai amfana da shi makusantansa da masoyan sama na taya shi murna da samun shi, sai kuma kawai a wayi gari da wannan babbar lalurar? Mai yai zafi haka? menene silar faruwar wannan lalurar? waima waye zai bashi amsar wannan tambayoyin da suke cikin ransa?


Dr.Bashir dake zaune gefen Haidar d'inne yai gyaran murya kamin yace.


"Alhaji wannan kukan da kake yi fa ba mafita bane kuma ba zai zama mafitaba, wannan yaron addu'a yake buk'ata tare da taimako amma gaskiya lamarin akwai daure kai musamman da Dr. is'hak kemin bayanin irin lalurar tashi, amma dan Allah kabar kukan nan da girmanka da komai.''


Cikin yanayi na tsantsar damuwa yace.


"Dr. barni kawai nayi kukana ko Allah zaisa na samu saukin zafin da zuciya ta keyi min rad'ad'i, ina cikin matsanancin tashin hankali Dr wannan yaron shi kad'ai Allah ya bani, na kwallafa raina akan shi gaba d'aya burina na duniya akan shi yake amma kalli yanda ya koma lokaci guda, Ina cikin wani hali Dr ban tab'a tunanin dukiya zatai rashin amfani ba wataran sai a yanzu, ashe dama akwai ranar da kud'in mutun basu amfanar dashi ba akan buk'atar sa?'' Dr.bashir yace.


"Bawai naki ta taka bane alhaji amma dai ya kamata ka duba damuwartaka bata da wani amfani cikin lamarin nan, addu'arka kawai Haidar yake buk'ata.''


''Dr. Kallifa abokan shi sunata aikin su harda wad'anda suka dawo Nigeria tare amma shi yana kwance ba zai amfanin kanshi ba balle ya amfani wani, gashi na rasa wanda zai kularmin dashi tsakani da Allah.'' Dr. Bashir ya mike tsaye tare d cewa.


''Alhaji zo muje waje na baka wata 'yar shawara.''


Gyarama Haidar d'in lullubin da aka yi masa da bargo yayi kamin ya manna mishi wani zazzafan sumbata akunci sannan yabi bayan Dr d'in yana mai addu'ar Allah yasa shawarar mai bullewa ce. Sai da yasha lemon da aka kawo mishi sannan ya kalli alhajin yace dashi.


''Alhaji ina mahaifiyar yaron nan take?'' Wani yawu alhajin ya had'iye kamin yace.


"Dr bansan inda take ba, amma tabbas nida kaina na koreta kuma wallahi babu abinda tayi min.''

''Innalillahi Alhaji lafiyarka kuwa? uwar d'an naka zaka kora ka zauna da matan da sai dai kawai suyi ta b'annatar maka da dukiya? Haba alhaji dan Allah, toh gaskiya bari na tashi domin shawarar da zan baka baza tai aiki ba tunda mahaifiyarshi bata gidanka.''


Hannuwanshi yasa ya rufe fuskarshi yana nanata kalmar innalillahi musamman daya tuno ranar da abun ya faru. Wata biyu da fara lalurar Haidar d'in ya tashi da wani irin mummunan kunci daya addabi zuciyar shi, kai tsaye d'akin yaron shi ya nufa nan ya tarar da ita zaune gaban shi tana bashi abinci tana hawaye sabida ganin yanda yake cin rabi yana watsar da rabin tana ta tunanin 'wai Haidar d'inta mai cike da tsafta yau shine a haka.


Ko sallama beyi ba ya shiga tare da fincike Haidar din daga jikinta yana huci yake cewa.


''Ke dallah tashi kibani waje.'' Shine abinda ya fito daga bakin shi. Da mamaki take kallonshi domin tun da take dashi ko kallon banza bai tab'a yi mata ba balle ai maganar tsawa.


Mikewa tayi tsaye kafin tace dashi. ''Abban Haidar lafiya kuwa?''

Yarfa mata wani mari yayi kafin yace da ita. ''Ban sani ba, maza ki kwashe kayanki kibar min gida na kafin na wulakantaki wallahi.''


Idanunta waje take kallonshi amma tsabar tashin hankali tama kasa magana sabida fargaba yau ita alhaji ke mari kamar wata 'yarsa.

"Zaki tashi kosaina tattakaki anan wajan?'' Abun yanzu ya daina bata mamaki sai dai tsoro, Muryarta na rawa tace.


''Naji zan fita daga rayuwarka gaba d'aya ba gidan kaba ma, amman dan girman Allah ka barni da yarona kaga dai halin da yake ciki babu kuma wanda zai kulamin dashi kamar yadda zai samu agareni, dan Allah kaimin wannan alfarmar kaji Alhaji.''

Alokacin kallon banza ya bita dashi kafin yace mata.


''Wallahi koda mutuwa nayi yaro na ba zai koma hannunki ba ballenta ina raye.''


Sautin kukanta ya dinga ji akunnuwan shi kamar alokacin ne take yi masa kukan. Hawayen idanunshi ya share kamin yace a fili.


''Allah ka kawo min mafita.''


Yana cikin wannan halin yana tufka da warwara saiga matarshi ta shigo, Hajiya bilkisu,Idanunshi ya lumshe bayan yai mata kallo guda.

"Alhaji barka da wannan lokacin?''

"Yauwa sannunki da gida.'' Cikin yanayi na kwarkwasa da iyayi tace dashi.


"Alhaji dama cewa nayi ko Haidar yaci abincinsa kuwa?'' Kallonta yayi kamar yana son gano wani abu a fuskarta sannan yace.


"Na bashi tun d'azu harma Dr. yai mishi allurar shi yayi bacci, amma wallahi hajiya kun bani mamaki matuja wallahi, ace wai idan bana gida a cikin ku babu wacce zata iya kula da gudan jinina ko? amma idan anyi magana kuce wai kuna sona ta yaya zan yadda bayan kun bar gudan jinina babu kulawarku? ai shikenan na gode lalurace dai kuma Allah zai iya jarabtar kowa.'' Harara ta bishi da ita bayan ya wuce tana cewa.

''Allah ya kyauta naba wannan katon saurayin abinci a baki balle ai maganar wankin kazantar shi, Allah ya tsare ni dama ka samu nake ta yi maka addu'a Allah yasa ya mutu kowa yama ya huta.'' Fuuu ta tashi tabar falon ta nufi b'angaren ta tana ta faman sababi a cikin zuciyar ta.


Gefen Haidar d'in ya rab'a ya kwanta har lokacin tunani nukurkusar zuciyar shi yake yi wanda har wani zafi-zafi yakeji daga cikin zuciyar shi ya rasa wane kalar ciwo ne wannan da duk wata k'asa da take takama da manyan asibitoci da likitoci ya kai shi amma a banza babu wani cigaba da aka tab'a samu ballantana ace ai an gano abinda yake damunsa ko kuma ace da sauki.

Zubawa fuskar Haidar d'in ido yayi yana kallon yanda yake ta baccin shi haka kamar mai lafiya amma yana tashi shikenan kuma wannan nutsuwar duk zata kama gabanta.


Wani tuna nine ya fad'o mishi, nan da nan ya mike addu'a ya tofawa Haidar d'in sannan yabar gidan bayan ya kuma duba d'akin ya tabbatar da cewa babu wani abu da zai iya zama makami a gareshi.


Kai tsaye wajan wani abokin shi ya wuce dake can wata unguwar daban, ya koyi sa'a domin yana zuwa ya ganshi ya fito da mota da alama shima fita zai yi. Da dariya ya fito daga cikin motar yana yi tare da cewa.


"Abban Haidar baka kirani ba sai dai kawai na ganka? da ka tarar da bana nan ai da kaji babu dad'i.''


Kai tsaye cikin falon mutumin suka wuce, hira suke yi sosai cike da kaunar juna daga gani abokai ne na gaske. Sai da ya huta kafin yace.


"Wato alhaji aminu akan maganar Haidar ce na dawo gareka domin tabbas na fara lura da abinda kake gaya min game da matana, tabbas sud'in ba masu kaunata bane, toh amma kasan hidima irin wannan tunda har ba kama su nayi dumu-dumu ba bazai yiwu na titsayesuba da zargin.''


"Haka ne alhaji Yusuf shi yasa ai tun farko nace maka kafara bincike tukunna, domin ni wallahi ban yarda dasu ba gaba d'aya dan son duniya ya gama rufe musu ido, nasan zasu iya aikata komai, toh amma yanzu me kake tunanin yi?''


"To nidai a tunanin da nayi cewa nayi inda zan sami wanda zai kular min dashi tsakani da Allah to hankalina zaifi kwanciya tunda kaga yanayin kasuwancina bana zama bane yau bana wannan kasar gobe bana waccan kaga sai hankalina ya tsaya waje d'aya amma wallahi dana tafi hankalina rabuwa biyu yake yi shi yasa kaga bana iya jimawa yanzu duk inda naje zan kokarta na dawo da wuri.''


"Eh wannan gaskiya ne, toh amma alhaji aikin ne da wahala wallahi shi yasa duk wanda aka nema sai ya zille musamman daya kasance yana duka wani lokacin, toh da nayi tunanin ko aure zai zama maslaha agare shi musamman danaji kace kana ganin yanayin tashin sha'awarshi wani lokacin to inda matsalar take matar da zata aure shi din...!''


Duk shiru sukai na wani lokaci kowa da tunanin da yake sak'awa cikin ranshi, kafin alhaji Aminun ya kuma gyara zama yana cewa.


"Amma ka koma gidan su Fatima kuwa?''


"Eh wallahi na koma amma babu wani bayani wai tama koma wajan kanin mahaifinta dake zaune a kasar India harta koma makaranta.''


"kai Abu beyi kyauba wallahi kaga inda tana nan ai da duk ba'a yi wannan doguwar wahalar ba, toh amman duk da haka zancigita kaima saika cigita, ammafa namiji za'a samu ba mace ba kamin Allah yasa asamu wadda zata aureshin a haka.''


"Toh shikenan insha Allahu nima zan cigita bari na koma kafin ya tashi daga bacci ya hargitsa d'akin nasa.''


Har ya koma gidan bacci Haidar yake yi, lokacin har anyi sallar magriba yaje yayi shima, sai da ya sai mishi fura mai kyau da dad'i a hanyarsa da dawowa sannan ya shiga d'akinshi. Ido ya zuba mishi ganin yanda yake ta mutsu-mutsu amma yaki bud'e idanunshi, dafashi yayi yana cewa.


"Haidar...! Kai haidar..!!'' D'agoshi yayi yana kallon fuskarshi kafin yace.


''Yanzu haka fitsari zaka yi kaketa wannan mutsu-mutsun...,Yauwa ai dama na sani.''


Maganar shi ya yanke lokacin da yaga fitsari na biyo kafar wandon Haidar d'in dake kwance. Wasu irin hawaye ne yaji sun zubo mishi kamin kuka me sauti ya biyo baya yana furta.


''Innalillahi wayyo Allah ka kawo min d'auki.''

Sai da ya gyara mishi jikinshi sannan ya bashi furar yasha ya koshi, sannan ya bashi magungunan shi wanda kusan duk na bacci yafi yawa a ciki sabida yanayin ciwon nashi hankali yafi kwanciya idan bacci yake yi.


Fuskarshi yake kallo duk tayi gashi sam baya yadda a aske mishi shi yasa duk sai yai wani irin duguzun dashi sai dai farar fatar shi tana nan yanda take saima k'ara sheki da take yi sabida zama waje d'aya.


Bugun da yaji afuskar shi ne ya katse mishi tunanin da yake yi, ya maida kallonshi akan Haidar d'in yana zaune yana kallonshi shima yana dariya irin dai ta marasa hankalin nan. Gorar da ya gama shan furar ce ya kwalama uban ganin ya zuba mishi ido amma yai nisan kiwo a wajan tunani. Jawoshi yayi jikinshi ya rungume yana shafar bayan Haidar d'in zuciyar shi fal addu'ar Allah ya bawa yaron shi lafiya.

Ranar a nan cikin d'akin ya kwana wanda sai da Haidar d'in ya gama hargitsa ko'ina kamin maganin da ya sha ya fara yi masa aiki lokacin shima Abban shi ya samu ya runtsa.


*****


Tafe nake ina nanata haddar karatuna wanda ya kasance shine abokin hirata a koda yaushe, ban damu da ruwan da yaima jikina sharkaf ba balle na damu da mutanen dake kallona musamman matasa, basu gabana haka zalika bawai ta tasu nake yiba Kawata dije na had'u da ita a dai-dai kwanar gidan mu tana cewa.


"Kai Rumana duk kin jike karfa mura ta sargafeki kin dai san batai miki da sauki ko?'' Dariya nayi kafin nace.


''Uuhum aini yanzu mun zama k'awaye da murar ma kina ganin yanzu wankan asuba inna kesawa inyi kullum duk safiyar duniya wai sai taji ina d'an tsami-tsaki.''

"Allah yagani inna bata kyautawa wallahi kenifa inda nice da tuni na koma garinmu wallahi, da gata da komai amma in like inda ba'a san daraja taba, kai ina wallahi bazan iya ba.'' Cewar dije. Kallonta nayi kamin nace.


''Lallaima Dije, kindai san bani da uwa bani da uba yanzu komawa nayi, kilama gara nan d'in da can tunda can d'inma da ai neman kai suka dinga yi dani, kedai kawai Allah ya kyauta amma wallahi kunji dad'i tunda kuna tare da iyayenku.'' Cikin tausayawa Dije tace.


"Haka ne Ruma to kema Allah ya saka miki ya kuma k'ara miki hakuri da juriya Insha Allah zakiga sakamako nan gaba.'' Da murmushi a fuskata nace.


''Amin dije na gode, wai ya maganar haddarki kingama kuwa?" Hab'a ta kama tana cewa.


''Tab inafa na tsaya wasa kedai na san kingama ai.''


Anan muka rabu kasancewar akwai gidaje hud'u tsakanin gidan mu da nasu. Wani mugun rankwashi ta bini dashi lokacin da na ajiye ruwan da alama shine sanun daya dace dani a wannan lokacin. Baba dake kwancewa kaza dabaibayi yace.


''Inalillahi mai tayi miki haka dan Allah?" Mtwsss taja dogon tsaki kafin tace.


''Yoo a ban zama zan sauke mata kenan? Ai kaima kasan bazai yiwu ba tunda na sauke mata ruwa dole na bata ladan ta.'' Kai ya girgiza kafin yace.


''Akwai Allah wallahi zaki mamakin ranar da zai kamaki akan zalintar yarinyar nan da kike yi.''


Nidai shigewa nayi d'akina ba tare da ko d'igon hawaye ya zabo min ba, duk da irin mugun zafin da naji kuwa, to yaushema zanyi kuka bayan inda sabo yaci ace na saba da duka da rankwashi....










*MAMAN KHADY*🙇🏻‍♀
[4/2, 11:15 AM] Re@l💍 K@usy🌹: 💞💞💞 *RUMANA* 💞💞💞


Na


*MAMAN KHADY*🙇🏻‍♀
(Mk)


*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡
(Home of expert and perfect writer's)




Page 5.






Domin duk a tunanin shi zaiga yana wani hauka na daban lokacin da ya kama masa, sai yaga inaa..dan tuni ya lafe a jikin Mudin idanunsa a lumshe bakinsa a bud'e har wani miyau yake fitarwa da alama yana jin dad'in abinda Mudin yake yi mishi har cikin ranshi.

Cike da tausayin Hydar Mudi ya taimaka mishi har sai da yaga ya koma wani baccin sannan shima ya samu ya kwanta, sai dai zuciyarshi cike da tsoron Allah akan abinda ya aikata yanzu duk da cewar taimako yayi kuma shi ba wani abin yaji a cikin zuciyarsa ba, ya fara tunanin. yanzu ya san inda lafiyar Haidar qalau ai ko wajan motarshi bai isa yaje ba balle ai maganar kwanciya kusa dashi harma ya tab'a mishi jikinsa. Lallai komai na Allah tsare yake sannan bawa baya tab'a wuce k'addararshi.

****


Washe gari cikin garin BAKORI: Da kyar na samu na yakice baccin dake damuna na mike lokacin iyayena suna d'akin inna har lokacin suna maida yanda akai akan yanayin hidimar data gudana ajiya.


Da sallama na shiga tare da makurewa a gefe ina gaida su. Inna da kanta ta kawo min abin karyawa ta tana fadin.


"Sannu Ruma ya gajiyar ciwon kan ya sauka ko?''


Kaina na d'aga mata kawai naja kofin shayi zuwa gabana da biredi, yau da kayan dadi zamu karya kenan. Zuciya ta tayi murnar hakan dan ba sabawa aka yi ba.


Baba rabi'u da baba ne suka shigo, suma gaida su nayi na cigaba da karyawa ta ina jin duk abinda suke fad'a.

"Ruma duba rigunan nan kigani duk cikin kyautukan da kika samu ne.'' Cewar gwaggo lami.

Wasu riguna ne dogaye masu masifar kyau dan ban tab'a ganin irin suba bakina har kunne nake cewa.


''Amman dai sunyi kyau sosai na gode Allah ya saka da alkhairi.''


Baya na tashi da sauri ina niyyar guduwa lokacin da baba ya zube min wasu kud'i masu tsananin yawan gaske dami-dami dasu a jikin kaure, ba sabun ba.


Innace ta rikeni tana dariyar itama tare da cewa.


"Kedai wallahi Ruma kin cika tsoron masifa, dallah gani zaki yi kud'in da kika samu ne dubu dari bakwai da hamsin ne, amma mun yanke shawarar za'a sai miki kadara na dubu d'ari biyar sauran kuma za'a rabawa dangi, d'ari da hamsin nida malam d'arin kuma sai a ajiye miki kisai sababbin kaya da sauran abin da kike buk'ata muna fatan hakan yai miki?''


Kaina a k'asa

Please Login or Register in order to submit comment