Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

batamin ciki?


Wani irin bugu kirjinshi yayi kai karfa hasashen da yakeyi ya zama gaskiya Dan tun wancan satin yake ganin alamomi ammadai ganina qalau yasashi share tunanin.
Da gudu na yakice yaran daga jikina nai toilet nafara shek'a amai tun inayi da k'arfina harsaida na koma kwance,Yana rike dani yanamin sannu Amma bunu bunu zai leka yaran Dan yanzu saisuyi wata ta'asar.
Saida ya wankemin jikina ya watsamin ruwa sannan ya kaini kan gado shikuma yakoma ya gyara wajan kwasar yaran yayi ya maidama umma sannan yadawo ya zauna gefena.


"Babyna Anya ba cikine dakeba kuwa?


Aibansan lokacinda natashi zauneba tsabar tashin hankali.
Rikeni yayi yana fadin bi sannu bari insamo Abu ingwada idan shine sai musan abinyi ko?


Tuni idanuna sunciko da kwalla aiko nabani idan cikine dani wallahi Saidai azubar dashi Dan banga dalilin da zaisa inada wa innan yaranba kuma inkuma haihuwa yanzu kai ina bamafa zai yuwuba toma basainayi jiniba sannan za ai maganar ciki,To tun haihuwarsu haidar da sati biyu ban kuma yiba.[4/2, 3:09 PM] Re@l💍 K@usy🌹: Rumana 57






Cikin sanyin jiki ya zauna gefena hankalinshi yai masifar tashi,Beta tunanin zanyi tunani irin wannan ba musamman yanda yaga duk na gama tashin hankalina.


"Kiyi hakuri Ruma Dan Allah ki rufamana asiri yanzu Sabida Allah Sabida kinada ciki shine zaki tashi hankalinki haka harma da wa inda ke zageye dake? Cewar Abba.


Cikin marairaicewa nace kayi hakuri Abba.


Wata uwar harara abban ya wurgama haidar din kamin ya Dora da fada sosai" Kai yanzu nan da kasan tanada wannan lalurar shine har kake hantararta haka?Meyasa kai idan ranka yabaci kakeyin abinda bedaceba eye?


Shidai shiru yayi sai shashshekar kukana data cika dakin.


"Abbane yafara magana cikin alamun lallashi, Haba rumana Dan Allah kadda kibani kunya mana yakamata ki tausayamana ki duba halin damuke ciki mana na rashin yawa yanzu munata murna Allah yafara baku zuri'ah wadda zamudinga gani munajin dadi kuma shine zaki mana haka?Meyai zafi Dan girman Allah kadda ki nuna bakiso Ruma ko yara nawa zaki haifa munaso kuma zamu rike koda zaki haifi cikin gidannan ne,Danhaka kiyi hakuri dani da ummanku zamu temakamiki da komai da kike bukata nidai fatana kiyi hakuri kibar cikin jikinki Dan Allah munaso kuma muna maraba dakoma menene.


Nasiha sukaitamin tsakanin umma da Abba mecike da lallashi har saida naji zuciyata tafara sanyi amma duk da haka zuciyata acinkushe take Sabida tsabar zullumin wahalar danasha lokacin cikinsu abdul.




*** ***


Sai magriba nakoma bangarena lokacin tuni nagama galabaita da amai Dan saikace abun jira tunda aka gano da cikin shikenan kuma sai ciwace ciwace musamman amai,Ga raina dayake abace har lokacin Sabida Marin da dadynsu yaimin.
Bunu-bunu umma taimin sannu kuma ta hana yaran takurani Dan bayan la'asar ma data cika musu ciki da abinci sai Abba ya kwashesu sukai cikin gari.




Ruwan dumi na hadama jikina nai luf ciki har saida aka fito sannan sannan nai wankan nafito daure da Alwala.


Sai bayan sallar isha'i sannan yashigo cikin gidan ko kallon inda yake banyiba balle yasaran sannu da zuwa kamar yadda nasaba.
Girgiza kai yayi sannan ya wuce wanka.


Saida nagama gyara jikina sannan nai kwanciyata duk da inajin yunwa amma bankulada cin abincinba.




Saida yagama shirinshi sannan ya jawo ledar dayashigo da ita ya hawo gadon"Tashi kici abinci"


Ko motsi banyiba balle yasaran zan kulashi.


Cikin tsawa-tsawa yace "Tashi nace kaddafa ki kureni inyimiki abinda banyi niyyaba wallahi"


Bakina atunzure natashi zaune tuni idanuna suncika da kwalla gani nakeyi kamar ya daina sona.
Gadai yunwa inaji amma haka nakeci ina zubar da hawaye,Shiko yawani tsare gida duk da irin tausayina dake kuma narkar da zuciyarshi saidai yasan matukar yace lallabani zaiyi to bazanyi abinda yakesoba.
Saida naci na k'oshi sannan na wanko bakina,Tsaye nayi tsakiyar dakin tare da kin kallon gadon Sabida kaddama in kalli inda yake.


Murmushi yayi kamin ya furta"please babyna yi hakuri kizo kinji?


Wata harara na ballamishi hadda murguda baki Dan jinake kamar na shakeshi inga yadaina motsi.
Ganin dai bazuwa zanyiba yasashi tashi yazo ya jani jikinshi zuwa gadon, Kuka kawai nasakamishi Dan har lokacin banjin dadin zuciyata musamman idan natuna ya fallamin mari kawai Dan nafadi abinda ke raina.
Shiru yayi yana sauraren kukana Wanda ke konemishi zuciya saidai dole yabarni nai kukan ko hakan zai samar min da nutsuwa,Yanadi rungumedani yanadan shafar bayana zuwa dokin wuyana har saida yaji nafara sauke ajiyar zuciya sannan muka kwanta yana rungume dani.


"Kiyi hakuri kinji Ruma nasan nine nabatamiki rai Amma bazan kumaba kinji?
Bakina na turo gaba kamin nace" Ni babu wani hakuri da zanyi gobe wajan inna zanyi tafiyata farawa da iyawa ka mareni inaga nan gaba rufeni da duka zakayi,Gara inkoma wajan innata wadda ke sona.


Dama yasan laifinshi bewuce hakan,Kuma yashirya bayarda hakuri,matseni yayi jikinshiyanadan bubbuga bayana"Shikenan ban kyautaba kuma nabaki hakuri yanzuma ga fuskata idan zaki rama marin da naimiki Amma Dan Allah ki daina maganar zuwa gidan inna idan kikatafi kika barni ya zan kasance?Kiyi hakuri kinji bazan kumaba natuba babyna.
Nidai shiru naimishi.


Tuni yafaramin salonshi Wanda ke matukar gigita tunanina bansan lokacinda nabada kaiba.
Aiko ya murjeni son ranshi tuni nasakamishi Kuka amma yanajina yai biris dani har saida yasami nutsuwa,Sannan ya rungumeni yana dariya.


Da asuba ma haka yaimin lilis sannan yabarni kwance ina sakin numfashi daya daya.




****




Cikin sati biyu nagama fita hayyacina zazzabin dare ya tasoni gaba ga tsotso duk da dai sunacin abinci inasamin sauki ga kuma ciki Wanda laulayinshi ke wahal dani.
Sosai suke tausayamin musamman shi Wanda muke kwana tare daga dare yayi zazzabi ke damuna kuma hakan behana ya kusanceni Sabida abin ya zamemishi kamar ibada sosai nake gane kurena kodan hada gyaran da nakesha ne dominyanzu bani da wata cima data wufe farfesun naman k'aramar dabba ko na kaji kullun sai umma taimin sai fruit sune kadai nakeci yazauna banyi amanshiba.
Jikina ya sauya sosai ammafa na rame nakyara kyau sosai.

Watansu Sha uku suka dainashan nono aiko ba k'aramin dadi najiba Dan wallahi dama daurewa kawai nake idan sunashan nonon.
Shiko uban ai tuni hankalinshi ya tashi ya tasasu tare da zubamusu ido yana kallo wasansu suketayi amma shi yakasa sukuni daga karshema kwasarsu yayi ya nufi wajan wani abokinshi dayake shi likitan yara ne.
Komai qalau saidai shawarwari dayabashi tunda sunacin abincinsu,Sannan suna yawonsu.


Shikenan sainasami nutsuwa,Abba har kirana yayi yana kuma lallashina tare da nunamin gashinan danayi hakuri Allah yasakama yaran hakuri da dangana akan nono danhaka in kwantar da hankalina koda zan dinga haihuwa duk bayan watanni Tara to lallai bazasu bari in wahala da rainoba.
Nidai murmushi kawai nayi Abba besan wahalar ciki da nak'udaba shiyasa.
[4/2, 3:09 PM] Re@l💍 K@usy🌹: Rumana 58



Bayan watanni biyu komai na tafiya kamar yadda Allah ya hukunta, Su Abdul sunyi girma abinsu Dan yaran Sam basu da matsala,Gasu da shiga rai duk Wanda yagansu saisun birgeshi,Niko wani lokacin shegiyar bannarsu ke hadani dasu gasudai yara sosai amma idan sukaima banna saikai tunanin wani babbane yayi,Shiya sa na gwammace suyi zamansu wajan umma Sabida ita dai babu ruwanta abinda na lurama shine kamar dadi sukeji idan sukaga yaran na kacaniyarsu.
Tsananin kamar da sukai da juna kesa mutane da yawa sonsu,Dan indai bamu na gidaba tofa da wuya mutun ya ganesu.


Cikina yanzu watanshi uku da sati biyu,Bikin dijee yanata matsowa amma naji dadynsu ko maganar beso humm kadan daga aikin namiji.



Zaune nake gaban madubi ina taje kaina Sabida tsifar danayi dazu wajan takwas da rabi na dare,Saigashi ya shigo yana rike da hannuwan yaran wa inda keta lilo da hannunshi.
Zama yai gefen gado yana sauke numfashi,Sannu da zuwa naimishi lokacin yaran harsun dawo kusa dani k'okarin takani suke su wuce saman madubin suyimishi kaca-kaca aiko duk maidosu k'asa nayi ina harararsu duk sai suka koma wajan uban.
Ruwan wanka na hadamishi Sabida naga da alama yaudai agajiye yadawo gakuma yaranshi daketa murzarshi hayaniyarsu kadai ta ishi kunnan mutun.
Abdurrahim yana saman kanshi yana yamutsar kunnuwan uban shikuma abdurrahaman yana saman cikinshi yana doki,Shidai idanunshi alumshe amma fuskarshi cike take da murmushi,Hummm na furta cikin zuciyata tare da cewa ai kuma kunji ajikinku indai yara ne.




Ya shiga wanka saiga umma tabiyo sawun 'yan jikokinta ni dariyama tabani wai kadda muce nan zasu kwana.
Dariya nayi kamin ince kai umma suna jarirai basu kwana nan ba sai yanzu da sukai girma suna tare da shine sai yanzu yashiga wanka nasan dayafito zai maidosu wa innan masu kunnuwan tunna haihuwa.


Dariya kawai tayi ta sabesu tanamana saida safe.


Ganin yanda yake da zalamarshi akusa yasani hakuri da maganar da nayi niyyar muyi.
Dannasan konafara bawani fahimta zaiyiba tunda ga abinda yake bukata,Da zafi zafi yake komai saikace betabayiba nimadai biyemishi nayi duk da cikin zuciyata cike take da zullumin kadda ya kusa kasheni.
Cikin fitar da numfashi dakyar nace"please kabi ahankali Dan Allah kadda ka cutar dani fa"


Ko tankamin beyiba sai uban nishin da yake fitarwa jikinshi na kyarma.


Saida yasami nutsuwa sannan ya rungume ni yana sauke numfashi guda-guda.
Kuma matseni yayi jikinshi yana lasar kunnena ,Wanda yasani kuma shigewa jikinshi.


Allah yaimiki albarka babyna Allah ya barmu tare kece farincikina Ruma.




Bayan munyi wanka muka koma muka kwanta,Saidanaga ya nutsu sosai sannan nace"dady bakace komaiba akan maganar zuwa bikin dijee kasanfa ranar asabar dinnan ne bikin"


Kuma shigar dani jikinshi yai tare da mannamin Sumba agoshi"Nasani babyna kawai banso kiyi nesa dani ne sabida bazan iya jurewaba,Kawai kibari zanbada sako akaimusu basaikinjeba.


Kwace jikina nayi ina harararshi duk da cikin duhune,Gaskiya ni bazan iya hakuriba haba kaima wasa kakeyi bikin dijee fa ni nan da ina tunanin tafiya gobe ko jibi ma sabida insamu ko sati daya inyi yaushe rabona da Bakori harna manta kai ko irin alkunyar nan bakamin kace shirya ki gano mutanen gida,To gaskiya ka canza ka gayamin kwana nawa kawai zanyi amma bazai yiwu ace da raina da lafiyataba inkasa zuwa bikin dijee ba.


Juyamishi baya nayi nai kwanciyata jinake kamar naita Kuka wallahi dama ga gajiyar dayaga jawomin.


Lamo yayi yana sauraren fitar numfashina saida ya tabbata nai barci sannan yajani jikinshi ya rungume yana murmushi kai Ruma iyayen rigima yanzu ai dole nadingamiki uzuri musamman yanda kike da saurin amsar sako.


Dasafe.
Koda garin Allah ya waye da fishina na tashi amma ogan yaiwani biris dani saima kamani dayayi yaimin wanka kuma yabani abinci kamar yadda yakemin lokuta da yawa.
Ganin yana Neman ficewa bayan mungama karyawa yasani taremishi hanya sannan naiwani cidin-cidin da fuska.
Murmushi yasaki kamin ya kamamin hannuwa ya zauna tare da zaunardani saman cinyarshi yana kallon idanuna,Babyna yanzu kin koyi rigima da rikicin gan-gan sabida Allah yanzukuma menayi koso kikeyi in makara wajan aiki?
Harararshi nayi tare da turo bakina gaba.


"Kinga yi hakuri inje indawo saimuyi magana yanzu sauri nakeyi.
Kuka nasaka mishi me sauti tare da kwantar da kaina akirjinshi.


"Oh ya Allah Ruma meyasa hakane so kikeyidai dole saikin tashi hankalina ko?
'Daukata yayi gaba daya ya nufi bedroom dinmu saida ya kwantar dani sannan ya tube kayanshi ya hauro gadon.
Tunanin abinda zai iya aikatamin yasani saurin tashi ina niyyar sauka gadon.
Jawoni yayi yana dariya " ai karya kikeyi yarinya saina lallasheki tukunna.
Wani salo yabidani me matukar tsayawa arai kamin wani lokaci namik'a wuya.
Saida yagama lallasani sannan yabarni,Nikuma nasakamishi kukan sangarta.
Lallashina yaitayi bansan lokacinda barci yai gabadaniba.


Ajiyar zuciya ya sauke me karfi yana murmushi, Bakina yakuma sumbata kamin ya lallaba yabar gadon tsabar beso intashi.
Agurguje yai wanka yabar gidan Dan yasan idan yakuma bari natashi to akwai matsala.


Niko wawuya ai tuni barci yai dadi😁
[4/2, 3:09 PM] Re@l💍 K@usy🌹: Rumana 60




Hankalina kwance nagama hada kayana duk wani Abu danasan zan bukata saida na had'ashi sannan tsarabar inna da gudummawar da zanbawa dijee.
Koda yashigo nagama salla kenan,Sannu da zuwa naimishi sannan nabashi abinci.
Bewani saki jiki yaci abincinba idanma na canka daidai sainaga kamar beda walwala yanda yakamata,Nidai babu ruwana dannasan duk wannan bazai wuce fushin tafiyarba.
Riko hannuwana yayi yana kallon idanuna kamin yace"Ruma kinyi wankane?


Jinai kamar in fallamishi mari ma Sabida aishi ba makaho bane tsabar Neman batamin lokacine kawai gashi nasan yanzu anrigama an daura auren ko dazu saida ta kirani bazanzo nace mata zanzo banda lafiyane gashi shikuma sai Neman batamin lokaci yakeyi.
"Uhumm" Shine abinda nace kawai,Maidani yayi saman gado ya fara lalubata kamin wani lokaci munkoma gidan jiya,Saida yaga na daina motsin kirki sannan ya barni ya rungumeni yana saukar da numfashi.
Saida ya temakamin sannan na kintsa jikina,Koda muka fito agurguje muka shirya,Sannan ya fitarmin da kayan wa inda yagama jinjinawa yana mitar saikace shekara zanyi na dauki jaka guda to shidai kwana biyu yabani shima idan yaji bai iya jurewa to zaizo lokacinda yaga dama nidai ban biuemishiba balle ya botsare yace ya fasa nasan kadan daga aikin shi.




Kayan k'amshi umma tabani inkaima amarya lokacinda nashiga yimata sallama,Yaranne suka makalemin da ihu Saina daukesu,Kai yarannan akwai 'yan Jan sharri Sabida Allah ni yaushe ko fita nakeyi dasu shine yanzu zasuwani aza rigima saisunbini.
Jin shiru ban fitoba yasa yabiyoni Aiko sai ranshi ya kuma baci musamman dayaga yanda yaran ke kuka,Wata harara ya wurgamin kamin yace wai biki saikace dole kiwuce muje ni.


Saida mukai nisa da tafiya shiru babu me magana nidai Saidai yai hakuri na tabbata idan banje bikinnanba babu ranar zuwana bakori musamman yanda suke kaffa-kaffa da cikin jikina.
Shiko tunani yakeyi kenan duk irin dadin da yaran sukeji wajan umma hakan bazai hanasu Neman mahaigiyarsuba shima yayi tunanin Sam yaran basu damu da mamansuba Ashe suna sane tsabar iya ahegene tunda idan ina gidan saisunga dama suje bangarenmu amma tunda yanzu sunsan unguwa zani shine suka saka ihun saisunje yo ai shayake yaran bama su shaku daniba idan yai duba da yanda kusan gabadaya rayuwarsu umma da abba ne ciki.
"Hummm shine abinda ya furta kamin ya sauke ajiyar zuciya ya kamo hannuna ya dumtse da nashi" Zamuyi kewarki Dan Allah kadda ki wuce kwanaki biyu kinji?


Jinai yabani tausayi danhaka na amsamishi da kaina amma cikin zuciyata inajin sainayi kwanaki biyar ko sati.


Mun sauka lafiya inda yabani kudi masu yawan gaske tare da jaddadamin lallai in kasance tare da wayata,Sabida kira sannan yaimasu inna sallama ya wuce be hadu da dijaa ba Sabida lokacin har motocin daukarta sunzo.
Nima zuwana besa na zaunaba danhaka nasaje cikin 'yan biki har tsawon kwanaki biyu,Sannan na nabba'a waje guda tunda biki yatashi kwanana uku na wuce maska nida inna wayatako tuni na kasheta Sabida tsaro.


Bayan kwanaki uku,Kwance yake yai filo da hannuwanshi idanunshi alumshe yanajin yanda yaranshi ke tsalle saman cikinshi amma tsabar tunani ya hanashi ko motsin kirki balle ya biyemusu kamar yadda yasaba"Kai anya Ruma Nada hankali kuwa yau kwananta shidda amma bata da niyyar dawowa kuma takama waya ta kashe"


Matse yaran yakumayi cikin jikinshi dole sukai lamo daganan sai barci,Gyaramusu kwanciya yayi sannan yajawo wayarshi akaro na ba adadi saidai wannan karon ya juya akalar kiran wayarshine akan inna.
Da sallama ta dauki wayar lokacin tagama matsamin nasha magani kenan na kwanta barci duka lokacin shadaya nasafe Dan jiya nadawo maska.
Cikin girmamawa suka gaisa kamin yace "Inna Ruma fa?

" Gatanan kwance Aliyu da yake bata da lafiya ai shanake tagayamaka!!


Besan yatashi zauneba saida yaga yaran sun motsa sannan ya lallaba yakoma gefe,Haka kawai yaji hankalinshi yai mugun tashi,Samun kanshi yai da furta dama cemata zanyi tashirya ina hanya Sabida yaran sunfara kukan nemanta.
"To shikenan saikazo Allah ya tsare,Ka gaishe da mutanen gidan.


Da kanta ta hadamin kayana dayakema duk na rabar dasu sai 'yan kadan wa inda nasan haidar naso sosai,Tunda gaskiya idan sutura nayima mutun yawa zan iya cewa tawa taimin Dan koda yaushe cikin sabbin sutura nake Abba yaimin umma taimin ga kuma oga.


Bayan azahar ya iso lokacin harnai wanka na kintsa amma zuciyata cike take da zullumin fadan da zaimin dannasan inada laifina.


Wayata na dauka na cire layikan na boye sannan nabawa inna ta aikama dijee da ita Dan tafi ta hannunta tsada, Itadai inna ko tambaya bataiba saidai tai godiya be jimace yace muwuce beson tafiyar dare zai kaini asbt kamin mu isa gida.
Ahaka mukai musu sallama.


Shiru-Shiru becemin komaiba sai hannuna dayaketa murza yana tukinshi,Saida mukai fara nisa sannan yace" Babyna bazaki gaushenibako?


Akunyace na kauda kaina gefe Dan naji kunyar nai tunanin zai balbaleni da fadane shiyasama nake atsorace"Kayi hakuri"


"Nayi Autar mata amma ina wayarki naita kira shiru?


" Tun ranar bikin ai aka dauketa"


Ayya! Sorry,Ya jikinki? Kinga kin wahalar da kanki hadda ciwo ko?


Ahankali nafurta kayi hakuri bazan kumaba.


"Uhumm to Ammadai ki shirya biyan bashi Dan marata cike take taf kinga kinjama kanki ko?


Shiru naimishi tare da zullumi domin nasha gyara Dan wacce taima dijee gyran amarya nima inabawa kudi taimin hadin su caccabi da kaza hadda dahuwar zabbi.

Jikinshi nai kwanciyata sai barci dannikaina nasan hadda zirga-zirga danai da yawa ya haifarmin da ciwon jiki.




Sai bayan magrib muka shigo gida Dan saida mukabiya yaimin allura sannan Dan har muka iso jikina akwai Dan zazzabi.

Da mamaki umma taita kallonmu yaran ko tuni suka likemin suna murna,Bakinfa ahangame tace" Wai dama cankaje d'aukota memakon kabari takuma kwanaki haidar?


Bakinshi yadan turo kamar k'aramin yaro kamin yace "Kai umma kwananta shiddafa daga zuwa biki inda raboma ai yanzu amaryar ta kunshi ciki,Muje kiyi wanka.


Ni wallahi kunyama kamani tayi musamman yanda yake Neman Jana ga yaran sun makaleni so sukeyima in daukesu ko wanne hannu asama.
Kwashesu yayi kawai ya dire cinyar umma yana dariya tare da Jan hannuna mukabar falon.


Yanata yamutsata cikin toilet daga wanka mukaji sautin yaran na kiran dady Dan dama sunanshine kawai suka rike daidai.
Manyan idanunshi ya fiddo yana murmushi kamin muyi saurin dauro alwala muka fito.
Duk suna tsaye bakin kofar toilet din sunajira,Lallai sunyi kewata 'yan yarana,Rungumesu nayi inajin dadi,Inason yarana fiye da duk yanda zan misalta amma dole in dauke kai kodan yanda su umma ke kaunarsu dason kasancewa tare dasu.


Duk maitarshi dole yai hakuri Dan yaranshi sunkasa suntsare.


Dayafita sallar isha'i nikuma nakwashesu mukai wajan umma hira mukeyi sosai Dan itama nai kewarta kamin Abba yashigo aka Dora dashi,Dan Wallahi wani lokacin ma mantawa nakeyi dashi sirikinane Dan nafi sabawa dashi akan umma dandai ita umma ta kasance macece.




Nagama shirin barcina na kwanta saigashi ya shigo"Babyna ko jira babu ai dare beyiba sosai ko?


Cikin alamun gajiya nace barci nakeji dannagaji sosai shiyasa na kwanta yanzu nadawo wajan umma ai.


Ruwa ya watso yazo yai shirinshi lokacin harna fara barci naji hawowarshi gadon tare da maidani jikinshi yana sunsunarjikina tare da mannama ko ina na jikina Sumba me karfin gaske.


Wayyo alokacinda aka fara harka ai tuni yafara sambatu da sakin gurnani saikace bijimin sa nikam ai kamin wani lokaci nai laushi shiyasa na gwammace yaitayi kullun tunda becika wuce so dayaba amma matukar zaiyi kwana biyu ba aiba to idan yarikeni saiyaji jiki Dan tuni na fahimci matsayinshi.


Mata adage da gyara koda bazakisha maganin mataba tunda bakowanne keda inganciba saiki dage da ciye ciye wa inda zasu inganta lafiyar jin dadinki Dana megida musamman wannan zamani da k'ananun cutuka sukaima mata yawa,Ko 'yar kwakwarki da dabino kikeci su kankanta aya da sauransu kikeci zaki sami ni'ima basaikin kaita da nisaba,Irinsu caccabi dahuwar kaza koda bayan duk watanni uku zuwa biyarne kikeci jikinki bazai lalaceba balle kiyi zurfin da megida beso.
Dan gyara shine mace.
[4/2, 3:09 PM] Re@l💍 K@usy🌹: Rumana.
End.




Koda garin Allah ya waye haka yaimin biji biji sannan yabarni harwani murmushi yake saki tsabar nishadin dayake ciki.
Tea ya hadamin infarasha kamin umma ta dundumamin tuwo kamar yadda tace amma ina ko zama beyiba nai amanshi.
Todai saidai shi yadamu amma nikam banwani damuwa tunda maganace ta laulayi matukar ciki ya shiga jikinki dole saikinyi hakuri yau nan gobe can sai kuma Allah yayi anrabu lafiya.
Dan garama ni inda nagodema Allah inacin abinci in koshi.
Shinedai dayaga jikina ya sauya yanzu saiya gigice yafara kiran aje asbt.






BAYAN SHEKARA biyar.
Akwace kwanci tashi asarar merai yaudai gani cikin gidan haidar akalla da shekara biyar da aure, ga kuma yara biyar da Allah ya albarkaceni dasu Wanda nasan Allah ne yaji tausayina yasamin haihuwar Dan jinkirtawa tunda kamin yaro ya shekara nakuma samun wani.
Abdurrrahman sai Abdurrahim sune manya tagwaye sai zahra mesunan umma sai kuma sadiq da saddika,Kusan gaba dayansu Kansu daya haka kama suke da juna sosai duk sunbiyo mahaifinsu Dan wani lokacin har mamaki nakeyi babu Wanda yabiyoni saidai d'an dibar yanayi haka.


Alhamdulillahi haka rayuwata ta sauya yanzu natashi daga rumana wadda akasani Mara gata da galihu wadda maraici ke walagigi da ita,Nakoma rumana me aji kuma abar so ga kowa.
Ga soyayyar mijina data iyayenshi data kewayeni babu meson yaga damuwa afuskata yanzu hankalinsu ya tashi.
Naso kwarai inkoma makaranta kamar yadda yatabamin alkwari amma ina bak'in kishi irin nashi yahana ya amince,Tunda gashi ko ina beso inje inko zamuje bakori ko maska to k'afata k'afarshi balle insa ran zan jima,Hakan besa na butulcemishiba sainabishi yanda yakeso danmu zauna lafiya.


Zaune nake cikin falona inashan tatacciyar kankana harwani lumshe idanu nakeyi tsabar jin dadi,Kamshin turarenshi ya sanarmin da zuwanshi,Sannu da zuwa naimishi tare da mikewa da niyyar rungumarshi saurin kaucewa nayi akunyace ganin yaran sunshigo

Please Login or Register in order to submit comment