Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

da nutsuwa da kuma sanyi yace.
“Asma'u zo muje ki rakani gidansu.
Khausar akwai tambayoyin da nake so nayi mata”.
Kai Asma'u ta gyaɗa cike da jin daɗin hukuncin da yake son ɗauka tace.
“Toh Shikenan Yah Moddibo bari in kira Ummi in Faɗa mata”.
Cikin sauri ya girgiza mata kai kana yayi ƙasa da muryarsa yace.
“A'a kada ki faɗawa Ummi, zata hana mu binciken idan kika faɗa mata zata hana amma yanzu kiyi sauri muje kafin ta dawo yanzu zamu dawo”.


Jinjina kai tayi tare da faɗin.
“Toh shikenan”,Sannan tashiga ta dauki Maroon hijabinta har ƙasa kana ta kalli Bashir dake karatun wani littafi na addini tace.
“Bari muje gidan su Khausar nida Yah Moddibo”.
Ta Ida maganar tare da fitowa.


Miƙewa Bashir yayi tare da fita kana yace.
“Laa Yah Moddibo Sannu da zuwa”.
Kai Moddibo ya gyaɗa kana yace.
“Yawwa Bashir koda Ummi ta dawo kada ka faɗa mata can mukaje kace gidan Innayi muka je”.
Ahankali Bashir ya gyaɗa masa kai kana yace.
“Toh shikenan Yah Moddibo sai kun dawo”.
Suna fita suka shiga mota kana Moddibo yaja suka tafi.


Acan gidan Lamiɗo kuwa cikin sauri Khausar ta fita daga side dinsu ta nufi sashen Gimbiya Bunayya tun kafin ta ƙarasa shiga tace.
“Ummah!, Ummah!!Ummah!!!”.
Daga ciki Hajiya Bunayya tace.
“Na'am”.
Khausar na karasa shiga tace.
“Ummah Raudat tashigo?”.
Kai Hajiya Bunayya ta gyaɗa kana tace.
“Eh tashigo”.
Ƙarasa shiga Khausar tayi tare da Hararan Raudat dake ɓuya tace.
“Raudat kizo muje in miki wanka amma sai wani bauɗewa kikeyi tun ɗazu kina ta gudu”.
Maƙale ka faɗa Raudat tayi tare da tura ƙaramin bakinta tace.
“Ni dai na faɗa miki bana son wankan nan akwai sanyi”.
Cikin rarrashi Khausar tace.
“To ai da ruwan ɗumi zan miki”.
Girgiza kai Raudat tayi tare da tura bakinta tace.
“Ni dai Banason gaskiya”.
Ganin tana son ɓata mata lokaci yasa Khausar ta shiga tare da janyo hannunta tace.
“Maza wuce muje in miki zan baki waya kafin fito kiyi game”.
Bubbuga kafa Raudat tayi cike da Shagwaɓa tace.
“Addah Khausi Ni dai ki ƙyaleni bana so”.


Ahankali Khausar tayi ƙasa da muryanta tace.
“Harda Game ɗin bakya so?”.
Ware Ido Raudat tayi tare da ƙyalƙyala dariya kana tace.
“Allah dagaske Addah Khausi zaki bani?”.
Murmushi Khausar tayi tare da lakace mata hanci tace.
“Eh”.
Suna shiga Bedroom ɗin Raudat ta zauna gefen gado sannan Khausar ta mika mata wayar bayan tasa mata game ɗin _Subway surf_ ta bata murmushi Raudat tayi kana ta fara buga game ɗin.
Khausar kuwa dogon rigar jikinta ta cire tare da ɗaura towel iya ƙugunta ta shiga toilet.


Akuma dai-dai lokacin Moddibo yayi Parking afarfajiyar gida dai dai nan Lamiɗo ya fito da motarsa ganin Moddibon yasa Lamiɗo yayi Parking din motarsa ya fito cikin sauri Moddibo ya ƙarasa kusa dashi tare da basa hannu sukayi Musabaha cike da kulawa Lamiɗo yace.
“Moddibo bar kadai ya gida ya kuma Ƙarin haƙurin rashin Jameelu?”.
Cikin sanyin Murya Moddibo yace.
“Alhamdulillah hakuri mungode Allah”.
Cike da kulawa Lamiɗo yace.
“Allah ya gafarta masa ayi ya masa addu'a”.
Cikin sanyin yace.
“Ameen Mai Martaba Nagode.
dama munzo wajen Khausar ce”.
Cike da kulawa Lamiɗo yace.
“Toh ba matsala Asma'u ku isa”.
Ahankali Moddibo yayi ƙasa da kansa tare da cewa.
“A mai Martaba baza'a a bari daga nan ba”.
Girgiza kai Lamiɗo yayi kana yace.
“Ku shiga ba matsala bari na kira Aysha in Faɗa mata”.
Hannu ya sanya a aljihunsa tare da ciro wayarsa yayi dearling number Mommy tana ɗagawa yace.
“Aysha ga baƙi Moddibo da Asma'u zasu shigo”.
Cike da kulawa Mommy tace.
“Toh ba damuwa su shigo mana”.
Katse wayar Lamiɗo yayi tare da yi musu Sallama kana ya shiga motarsa ya fita.
Moddibo da Asma'u kuwa suka nufi sashen Mommy suna isa bakin barandar Moddibo ya tsaya Asma'u ta ƙarasa shiga falon tare da cewa.
“Assalamu Alaikum”.
Shiru falon ba Kowa sai dai ko ina tsaf-tsaf kana ga ƙamshin dake tashi. Ajiyar zuciya Asma'u ta sauƙe tare da nufar Bedroom din Mommy tana cewa.
“Mommy!, Ta ƙarasa tare da shiga Bedroom din Mommy dake sanye da hijabi tace.
“Asma'u kun ƙara so Ina Moddibo?”.
Kai Asma'u ta gyaɗa tare da cewa.
“Eh amma yana waje”.
Mommy na zama gefen gado tace.
“Toh kice masa yashigo mana ya zaki barshi atsaye”.
Kai Asma'u ta gyaɗa tare da cewa.
“Toh Mommy”.
Sannan ta juya tare da fita falon ta leƙa ƙofan Falon cikin sanyin Murya tace.
“Yah Moddibo wai kashigo”.
Ahankali ya ɗago kansa tare da buɗe Idanunsa dake lumshe yace.
“Toh”.
Sannan ya shiga falon da komai ke kintse yana fitar da sanyayyan ƙamshin ahankali ya zauna akan 1sitter dake fuskantar ƙofar Bedroom din Khausar.


Asma'u kuwa juyawa tayi tare da kallon Moddibo kana tace.
“Yah Moddibo bari in sanarwa Mommy ka ƙara so”.
Bata jira amsar saba ta nufi Bedroom ɗin Mommy.


Khausar kuwa ahankali ta fito daga toilet tare da juya kanta yalwataccen sumar kanta dake jiƙe ya mannu da wuyanta da kuma gefen fuskarta dake da damshin ruwa fararen cinyoyinta masu haske da santsi na ɗauke da damshin ruwa.
Ware Ido Raudat dake Game tayi tare da kife wayarta akan gadon kana ta dira tare da ficewa da gudu saida ta isa kofar Bedroom din kafin ta tsaya.
Cike da mamaki Khausar ke kallonta kana tana tafiya ahankali tace.
“Raudat ina kuma zaki je?”.
Tura baki Raudat tayi tare da juya Idanunta tace.
“A ni dai Banason wankan nan da kwai sanyi”.
Sake baki Khausar tayi wato ita Raudat zata yiwa wayau, ɓata fuska tayi tare da cewa.
“Aikuwa baki isa ba kisa in. Baki wayata kiyi game sannan yanzu kinga na fito kice zaki gudu”.
Gwalo Raudat ta mata tare da fita da gudu.
Ware ido Khausar tayi tare da bin bayanta da gudu dariya Raudat ta ƙyalƙyale dashi tare da nufar hanyar fita sai kuma ta karya kwana ta nufi Bedroom ɗin Mommy.
Khausar kuwa garin zata karya kwana ta nufi Bedroom din Mommy santsin ruwan dake ƙafarta da kuma santsin tlyes ya jata tayi baya Suuuuuu ta faɗi a ƙasa kana towel ɗinta ya since ya zame yayi ƙ...!






Littafin SAKAYYAH na kuɗine ƴar uwa ki biya ki karanta cikin Aminci da salama 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA.




By
*GARKUWAR MARUBUTA* Downloaded from GNOVELS.COM.NG




This Novel is downloaded from https://GNOVELS.COM.NG
to download more hausa novels visits our site at www.GNOVELS.COM.NG

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/gnovels

Twitter : https://twitter.com/gnovels

Telegram : https://t.me/gnovels


Please Login or Register in order to submit comment