Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

yauba sai marching ɗin ya iso”.


Numfashi mai sanyi Momy ta fesar tare da kamo hannun Khausar suka juya suka tafi.


Ganin tafiyar sune yasa Hajia Bunayya yin kwaffa tare da cewa.
“Uhum zanyi mgnin kine, shegiyar yarinya mai masifar wayon tsiya da sa ido, tama fi mahaifiyar tata wayo da fahimtar manufar mutum”.


Su kuwa, suna shiga falon Khausar ta juyo a hankali tace.
“Dan Allah Momy kada ku bari Haiydar yaja marching yayi ƙarami dudu du fa shekarunsa sha 13 ne kawai dan yanada saurin girma”.
Da sauri ta juyo ta kalli Haiydar da yanzu shigowarsa, kanshi ya nuna da yatsarsa manuniya tare da cewa.
“Ni ne ma yaron? To da shekaru nawa kika fini dabino uwar tsufa, ba shekara ɗaya rak kike bani”.
Yes tabbas kam shekarunsa 13 ne, amman in ka ganshi zakayi zaton yaje 16, domin yanada girman jiki, kuma irin masu wayo da halin girman nanne shiyasa sam bazaka tantance shekarunsa ba, ya fita jiki da tsawo sosai.
Dan in ka gansu zakayi zaton shine babban irin ya bata shekara ukun nannan ne”.
Kai ta jujjuya tare da rumtse tafin hannunta, kana cikin sanyi tace.
“Dan Allah Momy kada ki bari dan Allah a wannan karon dai ki yarda dani”.
Kai Hajia Aysha ta gyaɗa mata tare da cewa.
“Zan duba."
Cikin kwaɓe fuska Haiydar ya turo baki gaba tare da cewa.
“Plesse Momy kada kibi ta kan mgnar ta”.
Still kai ta gyaɗa masa shima tare da cewa.
“Toh zan duba”.
Cirko-cirko sukayi a gabanta.
Dan dama da haka take yanke musu taƙaddama.
Idanu ta ɗan lumshe jin an kira sallan magrib cikin fesar da sassayan numfashi tace.
“Lokacin salla yayi, maza muje muyi salla”.
Ba musu duk suka juya, shi Haiydar waje ya fita yana cewa.
“Ramadan zomu tafi masallaci”.
Ita kuwa Khausar ɗakinsu ta nufa tana cewa.
“Raudat zomuje muyi salla."
Da sauri kuwa sukabi bayansu.




A can gidansu Moddibo kuwa,
M Jamil ne, ya kalli dun-duniyar sawun Moddibo lokacin da suka fito kan barandar da alamun al'wala sukayi.
A hankali yake taku cikin nitsuwa, yayinda yake motsa laɓɓan bakinsa yana taibihi.


Sai kuma ya maida kallonsa kan sumar ƙeyarsa dake kwance lip-lip tayi irin naɗin nan mai kamar taburma.
Kusan a tare suka sauƙo,
Hango Ummi da Innayi zaune bisa sallayunsu, da kaskon rushi a tsakiyar su ne, ya sasu juyawa suka nufi waje, sabida tafiya masallaci.


A hankali Moddibo ya zira tafukan hannunsa cikin aljuhun jallabiyar jikinsa, sabida wani irin masifeffen sanyi dake fesowa, duk da rigunan sanyin da suka ɗaura kan jallabiyoyin bai tsare musu sanyi irin na garin Gembila ba, musamman ma, a lokacin da magrib ta ƙarato, wanda lokacin sanire ke sauƙa.


Kasan cewar masallaci babu nisa da gidan ne, yasa suka, tafi da sawu.


A hankali M Jamil ya lumshe idanunsa sabida yadda yake jiyo sautin muryar Moddibo can ƙasa yana zikirin tafiya masallaci.


Shi kuwa Moddibo cikin yanayin sanyin da yakeji yake motsa laɓɓan sa a hankali cikin dadɗan sauti can ƙasa-ƙasa yake cewa.
اللَّهُـمَّ اجْعَـلْ فِي قَلْبِـي نُوراً، وَفِي لِسَـانِي نُوراً، وَفِي سَمْعِي نُوراً، وَفِي بَصَرِيِ نُورًا، وَمِنْ فََوْقِي نُوراً، وَ مِنْ تَحْتِي نُوراً، وَ عَنْ يَمِينِي نُوراَ، وعَنْ شِمَالِي نُوراً، وَمِنْ أَماَمِي نُوراً،,وَمِنْ خَلْفِي نُوراً، وَاجْعَلْ فِي نَفْسِي نُوراً، وأََعْظِمْ لِي نُوراً، وَعَظِِّمْ لِي نُوراً، وَاجْعَلْ لِي نُوراً، واجْعَلْنِي نُوراً، ألَلَّهُمَّ أَعْطِنِي نُوراً، وَاجْعَلْ فِي عَصَبِي نُوراً، وَفِي لَحْمِي نُوراً، وَفِي دَمِي نُوراً، وَفِي شَعْرِي نُوراً، وفِي بَشَرِي نُوراً، أَللَّهُمَّ اجِعَلْ لِي نُوراً فِي قَّبْرِي... وَ نُوراَ فِي عِظاَمِي، وَزِدْنِي نُوراً، وَزِدْنِي نُوراَ، وَزِدْنِي نُوراً، وَهَبْ لِي نُوراً عَلَى نُوراً
Dai-dai lokacin da yazo ƙarshen addu'ar suka isa bakin masallacin.
Kusan a tare suka haɗa baki wurin yin addu'ar shiga Masallaci.
”أَعوذُ بِاللّهِ العَظِيـمِ، وَبِوَجْهِـهِ الكَرِيـمِ وَسُلْطـَانِه القَدِيـمِ، مِنَ الشَّيْـطَانِ الرَّجِـيمِ، بِسْـمِ اللّهِ وَالصَّلَاةُ وَالسَّلامُ عَلَى رَسُولِ اللّهِ، اَللَّهُـمَّ افْتَـحْ لِي أَبْوَابَ رَحْمَتـِكَ“
Kana a nitse suka shiga cikin masallacin.
Shi Moddibo gefen daman sahun forko ya zauna, yayinda shi kuma M Jamil ya nufi wurin kiran salla...


Kasan cewar M Jamil ke ladancin masallacin Moddibo kuma limancin...


Bayan an idar da sallane, Khausar ta juyo ta kalli Raudat tare, da miƙa mata littafin Dua azkar, amsa tayi kana ta buɗe daga shafin forko ta fara cikin sassayan sautin yarinta.


Ita kuwa Khausar Alqur'anin ta, ta ɗauka tare da fara, rero karatun Alqur'ani cikin zazzaƙar muryarta take biya suratul Nisa'i.


A haka har aka kira isha sukayi kana, suka fito.
A falon suka zauna baki ɗayansu suna cin abinci.


Misalin ƙarfe tara da rabi, Ummi ce zaune gefen Innayi da hijabi a hannunta alamun ta gama shirin tafiya.
Cikin kulawa da martabawa tace.
“Toh Innayi Allah Ubangijin talikai ya baki lfy yasa zakkan jikine, in Sha Allah gobe koda dare zan zo in kuma dubaki da jiki”.
Kai ta gyaɗa cike da jin daɗin kulawar Ummin Jamil cikin ƙarfin guiwar da ta ɗan samu tace.
“Amin ya rabbil izzati Fatima ngd matuƙa Allah ya raya miki ahlinki yasa suyi miki fiye da abinda kikeyi min”.
Cike da jin daɗin addu'ar tace.
“Amin ya Allah”.
Moddibo kuwa, kai ya tankwara gefe yana kallon kakartasa, sosai ta rame a dare ɗaya da wuni ɗaya.


Haka dai sukayi sallama Jamil ya ɗauke ta suka tafi.


Har bakin gate Modibbo ya rakasu.
Kai ya ɗan juya ya kalli wata motar dake gefen damansa ƙirar BMW irin dai wacca M Jamil yaja sukaje makaranta, sai dai wacce baƙace wannan kuma farace ƙal mai masifar kyau.
Murmushin M Jamil yayi sabida ya fahimci kallon da yayiwa motar ma magana ce.
kanshi ya juya tare da cewa.
“Lafiyarta ƙalau kawai na barta a nanne sabida nan ya dace da ita, tunda ba gida ɗaya mukeba, Allah ya kiyaye wani uzurin zai iya tashi da dare, kaga kamar jiya da kasan Innayi ba lafiya kawai ɗaukarta zakayi ku tafi hospital ko Ummi?”.
Ya dire ayar mgnar yana kallon Umminsa da shima Moddibo ita yake kallon.
Cikin gamsuwa Ummin tace.
“Sosai ma kuwa”.
Cikin yin ƙasa da kai Moddibo yace.
“Ummi har kema haka zakice, kamar baki san me ake faɗi a cikin gariba, ba cikin gari, bama har cikin gidansu fa, ganin kaskas akemin wasuma ɗaukar abotarmu ta tun yarinta sukeyi a matsayin na maida J saniyar tatsa."
Cikin sanyi Ummin tace.
“To Moddibo ai shi ɗan adam ba'a biye masa”.
Da sauri Jamil yace.
“Yauwa Ummi gaya masa dai kam”.
Cikin tsare M Jamil din da ido yace.
“Motace dai ta hannunka ta ishemu, kuma ga waccar ma, kasan in bawai baka nanba always muna tare”.
Da sauri Jamil ya jujjuya mishi kai tare da jan motar ya tafi.


Sashin Innayin ya nufa, cike da zurfin nazari.
Tv ya kunnamata tashar Sunna, inda aka sa sautin karatun Alqur'ani mai girma.
Ido Innayi ta lumshe jin nitsuwa da salama na diro mata,
Saida safe yayi mata kana juya ya fita zuwa Part ɗin sa.


Washe gari ranar Alhamis ne, yau babu makaranta ko yan haddan bazasu jeba, shiyasa su Khausar suna gida,
Bayan sallan la'asar Asma'u Ahmad ta shigo falon Momy cikin sakin fuska tayi sallama.
Da sauri Khausar ta fito daga ɗakin Momy tana cewa.
“Wa alaikissalam Giɗaɗo".
Murmushin Asma'u Ahmad Giɗaɗo tayi, ƙanwar M Jamil kenan da suka haɗa uwa.
Cikin sakin fuska tace.
“Jauro”.
Fuska Khausar ta kwaɓe tare da cewa.
“Wai jauro gsky ni an cuceni”.
Murmushin sukayi baki ɗaya sabida daƙuwar da Mamy tayi musu.
Cikin kunya Asma'u ta ɗan rusuna, tare da cewa.
“Barka da yamma Mamy”.


“Barka dai Asma'u ya Umminki?”.


“Tana lfy tace in gaidaki”.


“Masha Allah Ina amsawa”.


Da sauri ta miƙe tsaye jin Khausar ta kamo hannunta.
Ɗakinta suka nufa, suna shiga suka zauna bisa gado.
Raudat dake kwance kan gadon riƙe da wayan Mamy tana game ne ta miƙe da sauri ta faɗa kan Asma'u.
Ruggumi yarinyar tayi tare da cewa.
“Autan Mamy tsifa ake yi ne”.
Kai ta gyaɗa mata tare da cewa.
“Eh kuma gashi har yanzu Adda Khausi bata gama minba, tsifanta zafi”.
Hararanta kausar ta ɗanyi tare da cewa.
“Da Allah tashi daga nan, nawama da yaya nake tsifan, kin samu ma inayi miki”.
Ta ƙare mgnar tana fita daga ɗakin.
Jim kaɗan ta shigo riƙe da filas da kofuna guda biyu bisa tray da kuma kayan tea, kan bed side drower ta ajiye tiran kana ta haɗa musu tea mai zafi, sabida rage sanyin da suke rayuwa cikinsa, yasa tea ya zame musu tamkar ruwa, madadin in kaje baƙunta a baka abin sha mai ɗan sanyi, sai a tarbeka da zazzafan shayi.


“Gidado bar tsifan nan ga tea".
Khausar ta faɗa tana zama gefenta tare da miƙa mata, kofin.
Amsa tayi tare da kallon Raudat da ta fice da gudu sabida jin Abbansu ya shigo yana kiranta.


Riƙe cup ɗin tayi ba tare da tasha ba,
Ido Khausar ta ɗan zuba mata kana tace.
“Ya dai Giɗaɗo lfy kuwa?".
Numfashi mai nauyi Asma'u ta fesar kana cikin sanyi tace.
“Kamar zan biya ɗazu ki rakani”.
Ajiye cup ɗin hannunta tayi tare da cewa.
“Ina?”.
Murmushin Asma'u tayi tare da cewa.
“Gidan su Moddibo”.
Fuska ta kwaɓe tare da cewa.
“Allah ya kiyasheni, me zai kaini gidansu wannan mugun, mutumin da duk duniya bana da maƙiyi sama dashi, duk abin da nai laifine, ni zanje gidansu yace na kai musu fitsara ya dakani a banza”.
Murmushin Asma'u tayi tare da cewa.
“Yoh ai shiyasa ma ban biyaba dan nasan bazaki taɓa yarda kijeba, kuma dai don shine sarkin masifa da mugunta kawai daga zuwa gidansu sai ya kama dukanki”.
Baki ta taɓe tare da cewa.
“Yoh ai bazanma jeba ma”.
Kai Asma'u ta jinjina a ranta tana raya wata rana zatayiwa Khausar tsiya, ta kwasheta ta kaita.


Ajiye kofin tea ɗin tayi tare da cewa.
“A'a dubiyar mara lfy cefa Innayinsa ce ba".
“Can musu”.
Ta faɗa tana kwaɓe fuska
Murmushin Asma'u tayi tare da cewa.
“Toh naji”.


Daga nan sukaci gaba da hira.


Washe gari ranar jumma'a, misalin ƙarfe biyar dai-dai Khausar da ta shigo cikin gidan riƙe da hannun Raudat da alamun kitso ta kaita.
A bakin mashigar gidan nasu tayi kiciɓis da Amina da Samira sani,


Sun iso bakin ƙofar a tare, dole sai ɗaya ya kaucewa ɗaya kafin a samu wurin wuce.
Wani masiyacin kallo Samira ta cillawa Khausar tare da jan tsaki.
Ita kuwa Khausar tsuke fuska tayi cikin rashin shakka ko tsoro ta goga kafaɗarta da na Samira duk da kuwa Samira ta girmeta ainun.
Cikin izza Samira tace.
“Ke karere ki nitsu kisan da waye kikeyi”.
Ba tare da ta cire idanunta cikin nataba tace.
“Toh dodon gori”.
Cikin fahimtar caguben baƙar mgnar da Khausar ɗin ta yaɓa mata wanda yafi abinda ta gaya mata ciwo, tace.
“Ke nifa uwarki zanci”.
Wani bauɗeɗɗen harara da dogon tsaki Khausar taja tare da cewa.
“Raudat mu tafi, kada mu tsaya muji, kukan tsuntsaye marasa tushe da gurbatacciyar tarbiya”.
Daga nan, ta juya tayi gaba.


Samira sani kuwa wani irin masifeffen kallo mai cike da tsana take Binta dashi.
Cikin takaici tace.
“Wallahi na tsani wannan yarinyar sam bana son ganinta, domin ta zame min madakatar nasarata".
Kwaffa Amina tayi tare da cewa.
“Bar shegiyar yarinya zanyi mgninta”.


Cikin tarin tsana Samira tace.
“Kune ma kuka bata dama ai, tana agola sai iyayi take muku, an wani dai-dai ta komai naku da nata, wai hatta makarantarku ɗaya da ita, ni wlh da nice ke sai na zuga Umma ta zuga Lamido tasa an cireta a wannan makarantar, shegiyar yarinya mai kama da ƴan ruwa.”
Kwaffa Amina tayi tare da cewa.
“Bar hegiyar yarinya, zanyi maganinta”.


Ita kuwa Khausar a falo suka samu Mamynsu kishingiɗe bisa carpet saƙale da wayarta a kunne, da alamu waya takeyi, ido ta zuba mata jin tana cewa.
“Eh Hajja Nana in Sha Allah, zata zo, don dama cikin azumi suna hutu to kuma rashin lfyar ne ya hanata zuwa, amman yau suka koma makaranta, kuma an ƙara musu hutun mako uku guda, sabida gyaran da akeyi a makarantar in Sha Allah zata zo, a satin nan,".
Sai kuma ta ɗan yi shiru, na wasu ƴan daƙiƙu, cikin sanyi da girmamawa tace.
“Eh gata nan ma”.
Tayi mgnar tana miƙawa Khausar wayar, cikin kwaɓe fuska kamar zatayi kuka ta amshi wayar tare da karawa a kunne murya ciki-ciki tace.
“Njam ɓanɗu.
Ina yini?".
Daga can kuwa cikin irin isa da kasaita ta tsofi masu iko Hajia Nana tace.
“Lafiyata lau, ki shirya kuna gama jarrabawar jarabar taku ta bokoko a wutan zakizo nan Jauro yaya inada buƙatar ganinki”.
Cikin sauri da alamun akwai zaunanniyar tsama a tsakaninsu tace.
“Toh ai muna da hadda yanzuma da aka ƙara mana hutun, kuma zamuna zuwa leson”.
A faɗace tace.
“Leso mato nace leso mato, ita haddar mu nan ɗin ce miki akayi garin kafuraine, kizo liman Sadu zai baki duk ilimin da kikeso in dai na addinine, na kafurcine dai bamu dashi”.
Cikin takaici tace.
“Nifa ki dena kafurta mana ilimin mu".
Cike da mamaki da al'ajabi Hajja Nana tayi wani dogon salati, tare da sanar da Ubangiji wai itace tana mgn ana bata amsa, ita da mgnar ta take tamkar wahayi a cikin rugarsu kasancewarta itace babba.
Da sauri ta katse kiran tare dasa wayar a Airplane mode, ta kifeta gefenta sabida kada Mamynta ta gane.


Cikin yin rau-rau da ido tace.
“Mamy dan Allah kice mata tayi haƙuri sai ran babban sallah zanje muyi kwana biyu kafin a koma makaranta”.


Da sauri Momy ta fara jujjuya mata kai tare da cewa.
“Ban isaba Khausar ni dai kam bani da bakin yin taƙaddama da umarni Hajja Nana, ki kwana da sanin can zakije kiyi hutun nan, da kika samu ma bakije kinyi azumi a canba, tun tsawon shekaru takebi tana son hakan kuma bai samuba sabida uzurin da ita kanta ke fadarsa na zuwan ta Umara, bana kuma tace, saboda ke, bazata je Umrar ba, saboda tana so kije ki daɗe kisan yan uwanki su sanki.”
Cikin jan dogon numfashi tace.
“Mamy ni dai kin san ba shiri nakeyi da ita ba, ko zuwa nan tayi a wuni ɗaya sai tayi min masifa da sharri sama da sau biyar”.
Cikin haɗe fuska Mamy tace.
“Kuma dole kan umarnin ta da izininta mizanin muhallin zamanki yake, ki fara shiri kawai ma in Allah ya kaimu gobe zan gayawa Abbanku, zuwa ranar jumma'a mai zuwa sai ki bisu in sunzo cin kasuwa kije RUGAR JAURO YAYAH tabbas d....!






Littafin SAKAYYAH na kuɗine biya ki karanta cikin Salamah yar uwa.




By
*GARKUWAR MARUBUTA*


📝🍇✨💫⏰🤴🏻👹❤️❤️❤️🍇


*SAKAYYAH*
_Page 3_


_NA_
_AYSHA ALIYU GARKUWA_


🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


*FREE PAGE*


*Littafin SAKAYYAH na kuɗine 1k ne kacal ƴar ki biya ki karanta cikin Aminci ba haƙƙin wani a kanki 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276*




*GARKUWAR* taku ce dai MA'AURATA, da masu shirin aure, da masu jego, da yan gayu masu son k’amshi kece raini, da gyaran da zaike maimaita muku dararen forkon kuruciya*


Ko kunsan Jikinmu na da sinadaran hormones da suke taimakawa dan’adam akan komai musamman lokacin da mace take mu’amalar aure da mijinta. Mafi akasari wannan hormones din ne ke samun matsala ko su yi sanyi koma su daina aiki kwata-kwata shi ne dalilin da zai sa mace tace bata jin sha’awa ko bata san dadin aure ba. Albishirinku ina da kayan da ke taimakawa wannan sinadaran su dawo aiki tukuru don karkato miki da kimarki wajan mai gida sannan su taimakawa wannan sinadaran hormones dinki su dinka secreting din ni’ima wadatacciya da zata taimaka miki ki gamsu mijinki ya gamsu fiye da tunaninki. Note: Kayana ba sa tsinka ruwan ni’ima suna dai taimakawa hormones dinki ne su tsattsafo da ni’imar musamman wacca cutar sanyi ko dattin mahaifa ya dankarar da su ya hana su yin aikinsu yanda ya kamata. Haka zalika idan kina da kyau ki kara da wanka. Zaki iya amfani da magani na na gargajiya wanda zai gyara miki sex hormones din kullum ki kasance cikin humidify wato cikin damshi mai albarka kamar yanda ake son mace. Yana gyara miki mara.


Sai kamshi. Hajiyata daure ki fara amfani da turarena ki ji irin salon kamshin sa salo ne da zai daidaita ki da mijinki ya kankaro miki da kimarki a wajansa. Siyan na gari mayar da kudi gida.


Ga masu buƙata ga number' wayata wanda nake whatsApp dashi 09097853276 kimin mgn ta whatsApp in har kin tabbatar kin shirya saya mu dai-dai ta, kayana ba ƙanana bane, shiyasa bana harkan karanta, muddin kinsan baki shirya sayaba Please kada kiyi min mgn ki bari sai kin shirya kuɗinki a hannu, ba ina nufin kayana bana talaka bane, no akwai ƙananan set na masu karamin karfi, banson aimin mgn a ɓatamin lokacin aiyukana a shirme baki shiryaba. Shine karantan da bana so.
0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU. In kin shirya ga number ta ga kuma account number ta wanda in mun gama mgn zaki turo kudin ki, kana insa miki kaya a mota, duk jihar da kike kayana zaije gareki, amman fa in kinada dalilin zuwan nasune🤝🏻sayan na gari meda kudi gida. Set ɗina akwai manya akwai ƙananan set akwai kuma na tsakiya, ƙananan set ɗin daga 40k 35k 30k 25k 20k 15k 10k shine ƙara ɗan cukulan haɗiba bana haɗin kasa da 10k sai kuma haɗin kwanon ƙasaitacciyar mace shi 8k set ɗin tsakiyan su da 50k 60k 70k 80k 90k ne manyan kuma daga 100k ne zuwa yadda zaki iya Hajia ta*




GARKUWAR MA'AURATA




Cikin sanyin jiki Khausar ta miƙe tsaye tare da juyawa a hankali ta bar falon Mommy ta wuce ɗakinsu.


Ɗakin mai girmane wanda ke ɗauke da matsakaici gado ƙiran Italian bed sai durowarsa dake gefe wanda ke ɗauke da ƙofa shida, daga kusurwan gabas babban TV plasma ne da DStv sai tattausan canis carpet pinch color dake shimfiɗe Atsakiyar ɗakin wanda shi ke ɗan rage musu masifeffen sayin tayis ɗin,
komai na ɗakin pinch colour ne sai ɗan ratsin fari.


Cikin jagulewar zuciya ta kwanta bisa gadon tare da lumshe manyan Idanunta dake cike da ruwan hawaye.
Allah ya sani sam bata ƙaunar zuwa Jauro Yaya ko kaɗan, ya zame mata dole ta newa kanta mafita.
Ɗan gajeren tsaki taja tare da mirginawa ta juya tsakiyar gadon, kana ta lumshe idanunta, da wannan tunani bacci ya ɗauke ta...


Cikin nutsuwarsa da kuma sanyinsa kamar koda yaushe yake tuƙa motar, yayin da M Jameel ke gefen hagunsa kamar wanda akace ya dubi madubin dake gefensa se kuma yayi saurin kallon Moddibo dake Driving cike da mamaki yace.
“Kai A.J kaga kamar binmu akeyi fa ko?”.
Kai Moddibo ya jinjina tare da ɗan yamutsa fuska anitse yace.
“Eh binmu akeyi sai munje gidan Ummi zan tsaya”.
Cikin sauri M Jameel ya juyo gareshi tare da ɗan ware idonsa yace.
“Kama san ana binmu kuma shine ka ƙi tsayawa? Idan kuma wanda zasu cutar da mune fa A.J?”.
Kai Moddibo ya girgiza yana mai cigaba da tuƙinsa tare da buɗe lips inshi a sanyaye yace.
“Ai nasan wanda ke binmu fa Alhaji Bashir ne”.
Da sauri M Jameel yace. “Waye Alh Bashir?”.
Ɗan juyow Moddibo yayi tare da ɗan kallonshi kafin yace.
“Babban yaron Malam Arɗo ne”.
Cikin sauƙe Numfashi M Jameel yace.
“Ok to Meyesa ba zaka tsaya ba?”.
Ba tare da ya juyo ba yace.
“Nasan magana ce mai yawa yazo dashi, koda na tsaya ma, ba zamu gama ba kuma kaga agefen titi muke baya ga hakama na masa signal ya fahimta”.
Kai M Jameel ya gyaɗa tare da faɗin.
“Ok shikenan”.
Daga nan sukaci gaba da tafi.


Suna isa ƙofar gidan Ummi M Jameel ya buɗe ƙofa ya fita dai-dai lokacin da Alh Bashir ya ƙara so fuskarsa ɗauke da murmushi ya miƙa wa Alh Bashir hannu sukayi musabaha cikin sakin fuska Alh Bashir yace.
“M Jameel Ko?”.
Kai M Jameel ya gyaɗa mishi tare da cewa.
“Ya gida ya iyalai ya kuma Baba Arɗo?”.
Cikkn sakin fuska Alhj Bashi yace.
“Duk Suna lafiya”.
Murfin motar M Jameel ya buɗewa Alh Bashir tare da cewa.
“Bismillah kashiga”,


Sannan ya zagaya gefen da moddibo yake wanda har zuwa lokacin bai fito ba yace.
"Bari nashiga ciki sai ka shigo”.
Kai Moddibo ya gyaɗa cikin yanayin sanyin magarsa yace.
“Nima Ina Shigowa yanzu”.
“To sai ka shigo”.
Ya fadi tare da juyawa ya nufi cikin gida yashiga bakinsa ɗauke da sallama.
Ba lefi madedecin gida ne mai kyau daga farkon gidan ze iya ɗaukan motoci biyu se tank na ruwa dake can gefe tsakar gidan shimfiɗe yake da interlock sai babban sashe guda ɗaya cikin gidan zagaye yake da fulawa wi masu kyau wanda keda alaƙa da Moddibo dan duk inda yake da dama sai ya ƙawatasa da fulawowi, sabida suna samishi farin ciki.
Tsarin ginin yayi matuƙar kyau duk da cewa ba babba bane amma komai fess dashi haka zalika madedecin falon nasu da befiye girma ba yayi matuƙar kyau falon na ɗauke da manyan setin kujeru kalar ash da baƙi cai Centre table dake tsakiya da kuma ƙaton TV dake maƙale abango daga gabar da TV akwai ƙaton fanka bayan AC dake maƙale da bango daga yamma da TV zagaye yake da wasu flowes masu kyau da ɗaukar hankali sai tattausan carpet mai ɗan kare kyau dake malale a tsakiyar falon...


Cike da so kulawa ƙauna irin ta uwa Ummi ta kalli Jameel dake shigowa tare da sakar masa da murmushin da bata san ya subce mata ba,
bayan ta amsa sallama.


Cike da farin ciki Asma'u ta miƙe tare da gyara wuyan abaya ɗan baby himar dake zage da fuskarta da ɗauke da murmushi cike da jin daɗi ta rungume M Jameel da faɗin.
“Oyoyo Yaya Jameel na Ina yini”.
Kanta ya shafa cike da son yar uwar tasa yace.
“Lafiya lau my blood ya karatu?”.
Cikin murmushin ta amsa da.
“Alhamdulillah”.
kana ta zauna daga ƙasa kusa da ƙafafunsa,
Ummu kuwa miƙewa tayi tana ɗan leƙan bayansa.
Murmushi M Jameel yayi domin ya fahimci Moddibo take leƙawa ganin basu shigo tare ba.
Cikin yanayin fara'arsa yace.
“Kai Ummina ki bari mugaisa kafin ki tambayi 'yan biyun nawa??”.
Ka ta girgiza tare da cewa.
“A'a gwara in tambaya naji, domin shi yace na muku dambun couscous shiya keso kaga kuwa ai bazan ji daɗi ba in ban ganshi ba”.
Murmushi M Jameel yayi yana mai jin daɗin yadda mahaifiyarsa ke nunawa amininsa ƙauna tamkar ita ta haifeshi, yana murmushi jin dadi yace.
“To yana mota”.
Da sauri ta sake dubansa tare da cewa.
“To me yakeyi amota da bai shigo ba?”.
Ashagwaɓe yace.
“To Ummina mu gaisa mana”.
Dawowa tayi ta zauna bisa kujera 2 str,
shi kuwa M Jameel zamewa ƙasa yayi zauna daɓas bisa carpet kana ya ɗaura kansa acinyarta murya a sanyaye yace.
“Ummina daga shigowa ko gaisawa ba muyiba sannan baki samin albarka ba kika tsareni da tambayar Moddibo”.
Hannunta ta ɗauka bisa tsakiyar kasan tare da shafa kansa tana mai cewa.
“Ubangiji Allah ya Albarkanci rayuwarku! Allah ya dafa muku acikin dukkan lamuranku!!
Ubangiji ya tsareku daga sharrin abinƙi tsakanin mutum da aljan!!!
Allah ya baku 'ya'ya masu biyayya tamkar yadda kuke mana kaida Amininka”.
Cike da tsananin jin dadi da sassayan salama yace.
“Ameen thumma Ameen Yah Ummi”.
Hannunta ta ɗan janye daga kansa tare da sake tambayar sa.
“Ina Moddibo?”.
Ƴar dariya mai sauti yayi tare da miƙewa ya zauna akusa da ita kasancewa kujeran 2sitter ne.
gyara zamansa yayi yana fuskantar ta yace.
“Moddibo zai shigo amma ba yanzu ba”.
Da sauri tace.
“Meyasa?”.
Cikin saurin shima yace.
“Bari dai in miki bayani hankalinki ya kwanta.
Muna tahowa ne Alh Bashir babban yaron Malam Arɗo ya biyo mu to suna mota suna tattaunawa.
Nasan bazai wuce ƙorafi ya kawo akan mahaifinsu ba”.
Tsaresa da ido Ummi tayi kana tace.
“ƙorafi akan Babansu kuma?”.
Kai ya jinjina tare da cewa.
"Eh Ummi saboda Malam Arɗo wani irin mutum ne wanda zamuce mai dukiyar lukudi gashi dai Allah ya bashi dukiya na ban mamaki amma babu wanda ya isa yaci wannan kuɗin kamar abin masifa”.
Gyara zama Ummin tayi tare da cewa.
“Ikon Allah to sabi da me?”.
Numfashin M Jameel ya ɗan fesar tare da cewa.
“Tun bayan rasuwar mahaifinsa abubuwan suka ƙazanta.
Domin baya sauraron shawarar kowa koda kuwa ƙannensa ne domin shine babba acikinsu dan haka babu mai tanƙwarashi.
To fa saidai Allah ya ɗaura masa son Moddibo a zuciyarsa duk abinda Moddibo yace ko kuma ya kawo shawara akai to zaiyi koda kuwa ransa baya so.
Duk da wani lokaci zakiji yana yiwa Moddibon ma faɗa akan cewa zaisa shi kashe kuɗi amma koda ya gama surutun daga baya zakiga yayi abin da ya fadan.”
Gyara zama M Jameel yayu tare daci gaba da cewa.
“To fa wannan dalilin ne yasa muddin 'ya'yansa suna buƙatar wani abu saidai su biyo ta hannunsa Moddibo”.


Ka saƙe Ummi tayi tana kallon Jameel din kana cikin sanyin murya tace.
“To kada fa hakan yasa

Please Login or Register in order to submit comment