Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

shaƙan nunfashin juna kana ta sanya hankief ɗin ta shiga share masa hawayen cikin wata Sanyayyar murya mai cike da nutsuwa da kuma rauni tace.
“Yah Jameel Addu'ar mu yake buƙata ba kuka ba idan kai kana kuka.
Toh Ni kuma ya zanyi addu'a za muyi masa kaji ko Abu J”.
Ta ida mgnar da kiransa da sunan da ta raɗa masa, tare da faɗawa jikinsa ta fashe da sassayan kuka dai-dai lokacin kuma ya farka.
Kansa ya dafe tare da miƙewa ya shiga toilet ya ɗaura al,wala kana ya dawo ya shimfiɗa Sallaya ya fara nafillah yana cigaba da yiwa M Jameel addu'a.
Ba tare da yabi ta kan mafarkinba, domin yanzu kam idan da sabo ai yaci ace ya saba da yawan ziyarar kutse da nacin da Khaisar keyi masa cikin rayuwar baccinsa.


Washe gari Ummi ta tattara baki ɗaya Sarkoƙi, ta da ɗan kunnen zobe da awarwon Gwal nata dana Asma'u ta shirya ta tafi Tarata.
Tana isa kai tsaye babbar kasuwar su ta wuce kana tashiga shagon saida gwala-gwalai ta bayar aka gwada cikin sa'a ta samu sunyi farashi sosai kasancewar Manyan Sarƙoƙine nata dana Asma'u wasu nata tun tana gidan Abban Jameel ne, suka haɗa mata kuɗin ta Naira Million biyu da dubu ɗari huɗu da hamsin sukayi mata transfer dinsu.

Daga nan gidan kai tsaye gidan Ƙawarta Hajiya Salma Wanda mijinta ke saida Motoci yawanci awajensa M Jameel ke siyan mota ko kuma can zawa.


Mai A dai-dai-tan na sauƙeta ta miƙa masa kudinsa kana ta shiga cikin tangamenen coumpund ɗin daya tsaru kai tsaye ciki ta nufa tare da Knowking ɗin ƙofar kana ta murɗa handle ɗin tashiga bakinta ɗauke da sallama.
Hajiya Salma dake zaune akan kujera ta miƙe cikin sauri kana tace.
“Hajiya Fatima sannu da zuwa ga wajen zama”.
Kai Mommy ta gyaɗa tare da cewa.
“Yawwa Nagode”.
Sannan ta zauna tare da sakin Ajiyar zuciya.
Bayan sun gaisane.
Cikin sanyin murya Hajiya Salma tace.
“Ayyah Hajiya ashe ga abinda ya faru da ɗana Jameel kuwa?”.
Cikin yanayin sanyin ɗaya zamewa Ummu jiki, ta gyaɗa mata kai tare da cewa.
“Ummm bari ke dai Hajia Salma duniya tayi min zafi”.
Cikin tausayawa Hajia Salma tace.
“Ba komai in sha Allah, kada ki damu Hajia Fatima.
Ubangiji Allah ya bayyanar da Jameel aduk inda yake Ubangiji ya karesa daga sharrin mai sharri”.
Cikin sanyin Murya Ummi tace.
“Ameen ya Allah ameen ya hayyu ya ƙayyum”.
Cike da tausayawa Hajiya Salma tace.
“Wallahi Koda wasa banji ba sai ɗazu da safe Alhj na duba jarida ya gani shine yake sanar min”.
Kai Ummi ta gyaɗa kana tace.
“Allah sarki ai yanzu anshiga kwana na huɗu kenan.
Uhmmm dama nazo kiyiwa Alhj Abdallah magana ne akan ya duba motata ya siya”.
Ajiyar zuciya Hajiya Salma ta sauƙe kana tace.
“Ubangiji Allah ya tsare Malam Jameel aduk inda yake”.
ta faɗa tare da shigewa ciki tsaye ta samu mijin nata yana ƙoƙarin fita Kallonsa tayi kana tace.
“Alhj Hajiya Fatima ce ta zo mahaifiyar Malam Jameel”.
Kai ya gyaɗa tare da cewa.
“Ikon Allah muna shirin zuwa kuma sai gata”.
Ya faɗa tare fitowa a tare, a inda Hajiya Salma ta barta anan suka sameta tayi ta gumi.
Ahankali Ummi ta ɗago jai tare da cewa.
“Alhj Abdallah ina kwana ya gida”.
Zama yayi kana yace.
“Lafiya lau Hajiya ashe kuma ga abinda ya faru da Malam Jameel”.
Kai Ummi ta gyaɗa kana cikin sanyin murya tace.
“Eh”.
Ajiyar zuciya Alh Abdallah ya sauƙe kana yace.
“Wallahi bamu da labari sai ɗazu ina karanta Jarida na gani nake faɗawa Salma tace itama bata da labari dake akwai wani fitar gaggawa daya kamani nace idan nadawo zan kaita da yamma ta gaishe ki”.
Ajiyar zuciya Ummi ta sauƙe tare da gyada kai kana tace.
“Allah sarki dama Motata ce nazo ka tura adauƙa maka ka ga lafiyarta zan saidata in zaka siya”.
Ɗagowa yayi tare da kallonta kana yace.
“Motar da Malam Jameel ya siya miki nan?”.
Kai ta gyaɗa masa tare da cewa.
“Eh shi”.
Zaman hular kansa ya dan gyara kana yace.
“Amma ai motar bata daɗe ba Hajiya Fatima”.
Kai ta gyaɗa Muryanta na rawa tace.
“Eh bata daɗe ba Uzurin gaggawa ne ya kama Ni shiyasa zan siyar”.
Jinjina kai yayi tare da cewa.
“Aikam dama mota ce mai kyau sannan bai daɗe da sayanta ba za tura yaro yaje ya ɗaukota kuma yanzu mugama magana tunda abu na gaggawa ne”.
Cikin sanyin murya tace.
“Tun baka gani ba”.
Girgiza kai yayi tare da faɗin.
“Baki da matsala Indai wannan ne zan baki Million shida”.
Cikin sauri Ummi tace.
“Alhj har Million Shida kuma dama motar yana da tsada kenan?”.
Kai ya gyaɗa mata tare da zaro wayarsa acikin aljihu kana yace.
“Eh dama Million biyar ne haka ya siyeta toh nasiyeta biyar ɗin kamar yanda ya siya sannan Million ɗayan kuma na bada nawa gudunmawar Ubangiji Allah ya bayyana Malam Jameel”.
Ajiyar zuciya Ummi ta sauƙe tare da cewa.
“Ameen ya rabbil izzati, ngd Matuƙa".
Da sauri ta kalleshi jin yana cewa.
“Ki bani account number ki zan miki transfer”.
Kai Ummi ta gyaɗa tare da kiramasa number's ɗin.
Atake ya mata transfer.
Miƙewa tayi tare da yi masa godiya sosai kana ta fito, har ƙofa Hajiya Salma ta rakata kana ta Wuce.


Kai tsaye tashar motar Gembila ta nufa, tana zuwa kuwa tayi sa'a mutun ɗaya ya rage, haka yasa ta shiga motar ta tashi.


Alhamdulillah sun isa Gembila lfy.


A hankali Ummi ke tafiya tana jin wani irin sanyi a ranta tare da Comfedance ga Million ɗaya da dubu ɗari huɗu da dake account ɗinta ga kuma Million biyu da dubu ɗari huɗu da hamsin na Sarkoƙi kana ga Million Shida na mota ya zama tana da tsuran kuɗi ahannunta har Naira Million tara da dubu ɗari takwas kenan.
A hankali ta sauƙe wani zazzafafar ajiyar zuciya kana ta nufi gida.
Acan ɓangaren Moddibo kuwa ya haɗa duk wasu kuɗaɗe dake hannunsa ya samu Million huɗu da dubu ɗari biyu da hamshin kai tsaye gidan Ummi ya nufa yana Parking ɗin motarsa mai A dai-dai-tan sahu na ajiyeta atare suka shiga falonta.
Suna shiga Bayan sun gaisa Ummi tashiga Alart massage tare da miƙawa Moddibo wayarta tare da cewa.
“Babana ka kalli kuɗi sunyi gwaɓi”.
Amsar wayar yayi tare da Kallon Alart massage ɗin kuɗin kana ya sauƙe ajiyar zuciya tare da cewa.
“Masha Allah kuɗi sunyi gwaɓi bari na haɗa dana wajena”.


Kallonsa Ummi tayi haka nan taji hawaye na ciko mata kwarmin Idanunta.
Cikin sanyin murya Moddibo yace.
“Ummi na wurina na bashi da yawa Million huɗu da dubu ɗari biyu da hamsin ne”.
Cike da tausayinsa tace.
“Toh Allah ya biya. Babana Allah yabamu yanda zamuyi Ubangiji ya saka maka amma ka rage wani abu aciki ka samu na kashewa”.
Girgiza kai yayi cikin raunin murya yace.
“Ummi wani abu zan rage idan ina da abinda yafi wannan zan ɗauka in bayar akarɓo J naje. nayi magana da dillalai gidan mu na sashi akasuwa in dai za'a samu siyansa akan lokaci.
Cikin sauri Ummi ta kallesa tare da cewa.
“Gidan ku kuma Babana!?”.
Kai ya gyaɗa mata tare da cewa.
“Ummi Meye amfanin gidan mai zamuyi da gidan babu wani farin ciki acikisa.
Muddin J baya nan fa wanne farin ciki zamuyi. kuma komai da muka rasa zamu iya samu idan J ya dawo gare mu”.
Jinjina kai Ummi tayi, Account number dake wayarsa ya fito dashi ya mata transfer kuɗin tare da miƙa mata wayar karɓa tayi ta duba Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da kallon kuɗin Naira Million goma sha huɗu kenan cib.
Numfashi ta fesar tare da kallon Moddibo kana tace.
“Alhamdulillah Babana kuɗi sun cika Million goma sha huɗu bari muje gidan Abban sa tare”.


A hankali yace.
“Amma Ummi ki bari sai gobe muje wataƙil yau ba zasu kira ba sai goben, amma ni yanzu idan nafi ta zanje wajen Abba muji nawa aka samu awajensa”.
Kai ta gyaɗa cikin sanyi tace.
“Toh shikenan Babana Allah yasa muji al'khairi”.
Kai ya gyaɗa tare da miƙewa kana yace.
“Amin.
Toh shikenan bari naje yanzu”.
Ya faɗa tare da ficewa.


Kai tsaye gidan Abba ya nufa bayan yayi Parking ya fito tare da shiga Falon bakinsa ɗauke da Sallama.
Abba dake zaune kan 2 sitter ya jingina bayansa da jikin kujera ya amsa masa Sallamar cike da tausayinsa ya zuba masa yana ganin yadda yake tafiya duk ya faɗa acikin kwanaki huɗu ya rame yayi shafal.


Ƙara sawa Moddibo yayi tare da zama gefensa kana yace.
“Abba ina yini ya kuma haƙurin rayuwa?”.
Ajiyar zuciya Abba ya sauƙe tare da cewa.
“Alhamdulillah Aliyu ya wajen su Innayi?”.
Kansa a ƙasa yace.
“Lafiya lau Abba basu sake kira ba ko?”.
Girgiza kai Abba yayi tare da fesar da numfashi kana ya runtse Idanunsa cikin sanyin murya yace.
“Basu sake kira ba Aliyu”.
Jinjina kai Moddibo yayi tare da cewa.
“Toh yanzu Abba kuɗi kimanin nawa aka samu awajenka?”.
Abba kuwa ahankali ya zame daga kan kushin ɗin ya zauna akan capet tare da fuskantar Moddibo kana yace.
“Aliyu na tattara duk abinda yake wajena kana duk wanda nake binsu bashi na tattarasu sannan na nemi temakon bashi duk wanda zan nemi temakonsu sunban bashi baki ɗaya kuɗin dana samu awajena Million hamsin da shida ne, iya adadin kudin dake hannu na kenan, duk ta inda zan buga na buga Aminaina ƴan uwana duk na nemi temako awajen su wasu sun bani kyauta wasu kuma aro na buga shine Million hamsin da shida”.


Jinjina kai Moddibo yayi tare da cewa.
“Toh Abba kuɗi dai sun ɗanyi gwaɓi gashi awurin Ummi an samu Million Sha uku yanzu kenan muna da Million Saba'in dai-dai a ƙasa.
Ajiyar zuciya Abba ya sauƙe tare da fesar da numfashi kana yace.
“Alhamdulilah kuɗi sun fara taruwa Amma ɗari biyu fa suka ce gashi ko ɗari cikekke bamu samu ba”.
Cikin raunin murya Moddibo yace.
“Abba bari mugani idan sun sake kira sai mu rokesu su rage mana idan sun tallafa sun tausaya mana ko bashin banki ne zamu ci sai mu ƙara akai kuɗin ya cikata”.
Kallon sa Abba yayi tare da jinjina kai kana yace.
“Toh shikenan ba laifi Allah yasa mu dace”.
Ameen Moddibo ya amsa kana suka cigaba da hira har Misalin ƙarfe goma.
Abba najin ringing din wayarsa Yayi saurin zabura tare da picking kana yayi Sallama.
Daga ɗaya ɓangaren cikin bauɗaɗɗiyar murya mutumin yace.
“Alhj Bashiru ka haɗa kuɗin?”.
Cikin raunin Murya Abba ya gyaɗa kansa kana yace.
“Kuyi haƙuri bawan Allah dan Allah kuyi haƙuri wallahi kuɗin nan da kuka faɗa babu su awajena kwata kwata babu”.
Daga ɗaya ɓangaren mutumin ya juya tare da kallon M Jameel dake zaune a ƙasa kana cikin wata dakakkiyar murya mutumin yace.
“Da alama dai mahaifinka baya sonka”.
Jin muryan mutumin agefe yasa Abba saurin cewa.
“Don Allah ku bani inji muryarsa”.
Cikin wannan bauɗaɗɗiyar murya Mutumin ya wurga wa M Jameel wayar kana yace.
“Gashi kaji muryan sa”.
Cikin sauri M Jameel ya cafke wayar tare da kaiwa Kunnensa kana cikin sanyin mai cike da rauni mai tada hankalin ɗan Adam cikin murya mai cike da galabaita yace.
“Abbana”.


Cikin sauri Moddibo ya karɓi wayar a hannun Abba kana yasa a handsfree tare da danna record.
Cikin raunin Murya M Jameel yace.
“Abba kabasu kuɗin Abba dan Allah ka basu abinda suke so ka fitar dani awannan wajen mana Abbana”.
Runtse Idanu Abba yayi kana yace.
“Babana zan fitar da kai ina nan ina har haɗawa kuɗin insha Allah zan fitar da kai amma Jameelu duka-duka kuɗin da muka haɗa anan Million Saba'in ne su kuma sunce Million ɗari biyu suke so”.
Cikin wata raunan'niyar murya mai cike da masifaffiyar galabaita da neman jin ƙai M Jameel yace.
“Abba a saida motocina duka sannan aduba ɗakina akwai kuɗi amma bai cika Million biyu bama dan Allah ahaɗa Abba abasu azo a karɓe ni”.
Cikin rauni ya runtse Idanunsa da hawaye suka cika kana yace.
“Abba bana son zaman nan babu daɗi ba Ummina ba A.J sannan kaima ba kai wuri ba daɗi dan Allah Abba ka basu duk abinda suke so kazo ka karɓe ni ku saida komai nawa a haɗo kuɗin”.
Kai Abba ya gyaɗa tare da ƙoƙarin hana hawayen sa zubowa kana yace.
“Babana Insha Allah zan zo in karɓe ka koda raina suke so zan basu amadadin ranka”.
Modibbo kuwa tuni wasu irin hawaye masu masifar zafi ke kwaranyo mishi tamkar mace.


Fisge wayar sukayi daga hannun M Jameel kana cikin wannan bauɗaɗɗiyar murya Mutumin yace.
“Toh kaji dai abinda ɗan ka ya faɗa zamu baka dama ta karshe”.
Cikin sauri Moddibo da idanunsa ke rintse ya buɗe tare da cewa.
“Dan Allah! Dan Allah!! Dan girman Allah!!! dan darajar Annabi Muhammad (S.A.W) badan muba kamar yanda kuka ce J nada mutunci da kamala toh dan Allah saboda wannan kamalar tasa ku rage mana kuɗin zamu yi muku duk kan biyayya amma ku faɗa mana abinda zamu iya kawo wa”.
Daga ɗaya ɓangaren shiru mutumin yayi ba tare da yace komai ba kana bai katse kiran ba.
Cikin raunin murya Moddibo yace.
“Dan Allah kuyi haƙuri ku rage mana Insha Allah ba zamuyi gardama ba, amma kuɗin hannun mu munyi munyi sun kasa kai adadin da kuke buƙata mu samu su kai adadin da kuke buƙata wannan shine matsalar mu ku temaka ku ragar mana”.
Ajiyar zuciya mutumin ya sauƙe tare da cewa.
“Wannan Moddibo ne ke magana ko?”.
Kai Moddibo ya gyaɗa kana cikin sanyin murya yace.
“Eh”
Cike da gadara Mutumin yace.
“Toh shikenan ku bada Million ɗari da hamsin”.
Cikin raunin murya Moddibo yace.
“Mungode amma dan Allah ba zaku ƙara rage mana ba?”.
Cikin wata razananniyar tsawa Mutumin yace.
“Dan ubanka dan ka samu na zabge Million hamshin.
Atake to wallahi acikin Million ɗari da hamsin Naira biyar ba zamu rage ba kuma wallahi idan ku ka yarda kuka sake yi mana batun ragi kuɗi to wallahi akan ran Jameel domin kuɗi ne dai mu ki ya rayu ko ya mutu zamu samesu”.
Cikin tsanananin tsoro da kaɗuwa Moddibo ya dafe ƙirjinsa yayin da kansa ya sara da masifan ƙarfi.
Cikin tsawa Mutumin ya cigaba da cewa.
“Yanzu Moddibo gashi kayi magana dashi na ƙarshe wanda ko bacci yake yana kiran sunan ka gashi kayi magana dashi dan wataƙil shine maganarka na ƙarshe kenan dashi matukar dai baku haɗa kuɗin nan ba ku kasake yi mana batun ragin kuɗin to kayi magana dashi na ƙarshe kenan”.
ya faɗa tare da wurgawa M Jameel wayar.


Cikin sauri M Jameel ya cafke wayar tare da maƙalawa akunnensa kana cikin raunin murya yace.
“A.J”.
Cikin sauri da zaƙuwa Moddibo yace.
“J ina kake?”.
Girgiza kai M Jameel Yayi tare da cewa.
“A.J ban san inda nake ba ina Ummina!?”.
Runtse Idanu Moddibo yayi tare da taune lips ɗinsa kana yace.
“Tana lafiya J?”.
Cikin sanyin Murya M Jameel yace.
“J ka tabbata?”.
Cikin raunatacciyar murya yace.
“Na'am”.
jin haka yasa yaci gaba da cewa.
“Kace mata kada tayi kuka tayi ta min. Addu'a A.J ina sonka Ina son Ummina Ina son Abbana Ina Son Asma'u Ina son Bashir”.
Da sauri Moddibo ya dafe ƙirjinsa dake harbawa da masifan ƙarfi cikin raunin murya M Jameel ya cigaba da cewa.
“A.J Ina son Khausar tashigo rayuwar mu”.
Cikin tsanananin rauni Moddibo yace.
“Na sani J nasan kana son mu muma muna sonka, kuma in sha Allah duk zamu kasance a tare, zata shiga rayuwarka J zan mutunta abinda kakeso J”.


Girgiza kai M Jameel Yayi still cikin raunin murya yace.
“Ngd A.J in kayi haka kayi min komai, kayiwa Ummina magana idan akwai wani abu a hannunta ta bayar ahaɗa azo a karɓeni awajen nan dan Allah katemaka min”.
Araunane Moddibo yace.
“Insha Allah J zan taimaka da duk kan iyawa ta da kuma duk kan damata J koda ace da raina ne zan fanshi ranka da rayuwarka Insha Allah zamu fito da kai”.
Jinjina kai M Jameel yayi tare da faɗin.
“Nagode Nagode A.J ina maka fatan al'khairi acikin rayuwarka ga Amanar Ummina, Asma'u, Bashir,Abba da.... ka kula dasu kafin in dawo sannan kada ka mance batun Kh”...
Fisge wayar akayi daga kunnensa tare da katsewa.


Dafe kai Moddibo yayi cikin wani irin azabebben rauni ya fashe da matsanancin kuka tare da miƙewa batare da yace komai da Abba ba ya fice yana fita ya shiga motarsa tare dayi mata key.
Kana ya ciro wayarsa tare da dearling number Ummi tana ɗagawa murya a raunace yace.
“Ummi”.
Cikin sanyin murya tace.
“Na'am”.
Cikin ƙoƙarin hana kansa kuka yace.
“Ummi munyi waya da J yanzu”.
Ajiyar zuciya Ummi ta sauƙe kana tace.
“Dagaske Babana?”.
Kai ya gyaɗa kamar tana gabansa.
Cike da tsoro Ummi tace.
“Babana to Meyesa kake kuka?”.


Fashewa yayi da kuka kana cikin sheshsheƙa yace.
“Ummi ina kukan rashin J akusa dani ne Ummi wanda suka sai motarki Alhj Abdallah kice ya tura Azo aɗauki motocina da na J duka azo asiya ahaɗa kudin duka”.
Numfashi Ummi ta fesar tare da rintse idanunta kana tace.
“Sunƙi ragewa ko?”.
Girgiza kai yayi tare da cewa.
“A'a Ummi sun rage mana Million hamsin akai yanzu ya zama Million ɗari da hamsin suke buƙata”.
Ajiyar zuciya Ummi ta sauƙe tare da cewa.
“Toh Alhamdulillah wataƙila zamu iya cin nasara".
Cike da rauni Moddibo yace.
“Insha Allah Ummi da izinin Ubangiji”.
Ya faɗa tare da katse kiran jin wani kuka na neman kufce masa.


Kai tsaye hanyar gida ya nufa ba abinda ke yawo acikin kunnensa face sautin Muryar J ɗinsa yana isa gida yayi Parking tare da rufe musu gate.
Kai tsaye sashen Innayi ya nufa yana isa ya zauna abakin baranda tare da riƙe kansa da hannu duka biyu,
Kana ya fashe da wani irin kuka mai masifar ciwo a zuciya.
Wani irin azaban zogi yaji zuciyarsa na masa hadi da zafi da raɗaɗi yayin da wani masifaffen rauni ya lulluɓesa.
Innayi da bacci ya fara fisgarta ne, ta miƙe da sauri jin kamar sheshsheƙan Kukan Moddibo kana ta fito tare da Kallonsa yayin da gaba ɗaya ilahirin jikinta ya ɗauki rawa cikin sanyin murya tace.
“Ya dai Moddibo lafiya kuwa mai ya faru da Jameelu?”.
Cikin matsanancin kuka yace.
“Innayi ya zamuyi taya zanyi in.
Samu in taimaki J duk kan tattalina ya ƙare babu abinda zan samu in saida cikin gaggawa.
Zan saida tsohuwar motar da kika siya min da wannan sabuwar da kuma na J duka za'a siyar sannan Innayi nasan koda an siyar dasu duka, kuɗin ba zasu ciki Million ɗari ba”.
Sai kuma ya kife kansa bisa guiwowinsa ya sake fashewa da sabon kuka kana yace.
“Innayi sunce idan muka sake neman ragi akan kuɗin kamar mun nemi akashe J ne”,.
Jingina kansa yayi jikin fillan dake gefenta tare da fashewa da matsanancin kuka hadda sheshsheƙa.


Cikin Sanyin jiki Innayi ta zauna kusa dashi batare da tace yayi shiri ko kuma ya daina kukan ba, domin ta tabbata duk abinda yasa Moddibo kuka ba ƙaramin abu bane, kana idan har bai yiwa wannan abin kuka ba to mai zai yiwa kuka arayuwarsa.
Moddibo kuwa kuka ya cigaba da yi tamkar ransa zai fita har shidewa yake.
A ƙalla ya ɗauki Mintuna masu tsawo yana kuka kafin ahankali ya ɗago kansa tare da kallon Innayi kana yace.
“Innayi”.
Cikin sanyin murya tace.
“Na'am Moddibo”.


Cikin Muryansa daya dishe da kuka yace.
“Innayi ta wace hanya ce wace damace wane daliline kike samu kike mana duk kan buƙatun rayuwarmu?
Innayi in dai har adana kuɗi kikayi in dai har basu ƙare ba Innayi ki fito mana dasu ki taimakeni aceci J dashi”.
Jinjina kai tayi kana tace.
“Moddibo gaba ɗaya tattalin da mukayi na zaman rayuwar mu awannan yanki awannan gari a wannan ƙasar anje matakin da gaba ɗaya tattalin namu yazo ƙarshe sabida lokacin komawa muhalli ya kusan cimmmana”.
Sai kuma ta kalli Moddibo da har zuwa lokacin hawaye ke bin Fuskarsa kana tace.
“Na tanadi komai ne domin sanin cewa muna da bukatar su kama daga karuntaka, ci, sha, Jinya, sutura.
Da dai sauransu to yanzu kuma lokaci ya tafi rayuwa ta juya abubuwa sun tafi baki ɗaya tattalin namu yayi ƙasa tsadan rayuwa ya cinye kaso mafi tsoka”.
Numfashi Moddibo ya fesar kana yace.
“Innayi koma wani irin tattaline shin babu ragowa ne ko kaɗan ne?”.
Kai ta gyaɗa tare da cewa.
“Akwai ragowa”.
Cikin kuka yace.
“Menene amfanin ragowan duk tattalin arzikin da kike dashi matukar dai ba zai fito atemaki J ɗina da shiba Jamelunki fa ya fito daga inda yake fa”.
Ya ƙare mgnar cikin ƙunan rai, domin gani yake kamar ma duk duniya ba'a damu da J ɗinsa ba.
Ita kuwa Innayi cikin tafiya wani sashi nazarin Jinjina kai tayi tare da cewa.
“Bashi da amfani Indai bazan fito dashi ba, amma bari na fito dashi amma yanzu ka fara yin shiru tukunna kana kayi min al'ƙawarin cewa bazaka tambayeni komaiba akan duk abinda zaka gani”.
Kai ya gyaɗa mata kana yace.
“Innayi muga abinda zan fara samu awajenki tu kunna zanfi jin sanyi, ni yanzu a duniya babu tambayar da ke bakina daya wuce ina J yake , wanne hali yake ciki”.
Sai kuma ya fesar da zazzafan numfashi tare da cewa.
“Wallahi Allah ji nakeyi tamkar naje na zauna abakin masallacai inyita bara asamu ahaɗa kudi in cikata in karɓo J Innayi ya zanyi”.
Cike da rauni Innayi tace.
“Ba zakayi bara ba Moddibo Bari muga abinda Allah zai mana”.
Kai ta gyaɗa tare da jan hannunsa suka nufi bayan ɗakinta inda randunan ƙasa ke ajiye.
Kallon Moddibo da har zuwa lokacin hawaye ke zuba a idanunsa tayi kana tace ɗaga min randan nan”.
Sauri kallonta yayi kana ya Kalli randan ƙasan tare da cewa.
“In ɗaga miki randa kuma?”.
Ba tare data kallesa ba tace.
“Kada kayi min musu idan na baka Umarni kabi”.
Kai ya gyaɗa cikin sanyin yace.
“Toh”.
Tare da ɗaga randan ya matsar gefe.
Ajiyar zuciya ta sauƙe kana tace.
“Toh ɗaga fantekar”.
Kai ya ɗaga tare da matsar da fantekar dake cike da ƙasa gefe.
Yana janye fantekar yaga ƙasan wajen alailaye.
Ahankali Innayi ta zauna agaban wajen Moddibo kuwa cikin sanyi jiki ya durƙusa agefenta.
Itako Innayi hannunta ta sanya ta fara tono ƙasan dake wajen ganin duhu agarin yasa Moddibo sanya hannunsa acikin aljihu ya ciro wayarsa tare da kunna tochligt ya haska mata inda take tonawan.
Innayi kuwa ahankali ta cigaba da tono ƙasan bayan ta gama kwashe ƙasan ya rage sauran wasu manyan duwatsu ahankali ta ciresu duka.
Cike da mmki Moddibo ya tsaida idanunsa akan fafakekken rami an lailayeshi da siminti yana rufe da murfin tukunya kamar na lamba uku, da ɗan ƙarfi ta ɗago Murfin tukunya.
Cikin sauri Moddibo yayi saurin rintse idanunsa da karfu sakamakon wani haskene mai masifar sheƙi daya ɗauke masa idanu daya kashe masa idanu,
A hankali ya kuma saƙe buɗe inadunsa, da sauri ya mitso ganin yadda cikin ramin ke sheƙi da ƙelƙeli mai ɗauke ido yake fitowa daga cikin ramin, acan ƙasan ramin kuwa cike yake da ƴan ƙananan sulallan gwala-gwalai wanda basu fiye yawa ba sosai hasken ya ɗauke masa idanu saboda hasken wayarsa daya haske cike da tsanananin mamakin ya sunkuyo tare haska cikin ramin da kyau kana ya sanya tafin hannunsa acikin ramin ya ɗebo guda huɗu tabbas sulallan Gwalne...!




Littafin SAKAYYAH na kuɗine ko kin ganshi a wani wurin na satane. Ki biya ki karanta cikin Aminci 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA.




By
*GARKUWAR MARUBUTA*
*Littafin SAKAYYAH dai na kuɗi ne ba free book bane 1k ne kacal ki biya ki karanta cikin Aminci kada ki karanta na sata na Allah ya isa. 0661110179 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276 sai in saki a Group ɗina*




Cappande. Acikin tafin hannunsa ya ɗebo sulallan Gwal ɗin da wasu yan guntu-guntun sanduna tare da birbiɗin yashin kana ya shiga jujjuyasu, ahankali ya maida kallonsa kan Innayi data gyaɗa masa kai alamar ya fito dasu hannunsa ya zura acikin tukunyar yashiga kalato salullan wanda na ainihin Gwalne aƙalla sun kai guda ashirin, karkaɗe yashin yayi tare da fitowa dasu kana ya ɗaura su akan rigarsa tare da gyara zaman sa abakin ramin ya tsura mata Ido Innayi ma ido ta zuba masa ganin yanda ya zauna yasa tashiga maida yashin ta rufe ramin kana ta sanya duwatsun ta rufe tare da tura fantekar kan ramin kallon Moddibo dake binta da kallo tayi kana tace.
“Ɗaura min randan nan akai”.
Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe still Idanunsa na Kanta cikin sanyin murya yace.
“Innayi wannan kamar Gwal?”.
Kai ta gyaɗa masa kana tace.
“Eh Gwal ne”
Still ba tare daya motsa ba ya sake kallon Gwal ɗin kana yace.
“Ina kika same su Innayi?”.
Girgiza masa kai tayi kana tace.
“Wannan ba lokacin tambayar ina nasamu gwala-gwalai bane. Moddibo lokacine daya kamata ace ka lissafa su muga adadin su kana musan nawa za'a samu mu haɗa mu karɓo Jameelu yanzu tashi mubar wajen nan mushiga ɗaki kaga dare ya tsala”.


Kai ya gyaɗa mata tare da cewa.
“Toh”,Kana yabi bayanta tare da tsira mata idanu cike da ɗumbin mamaki tare da tarin tuhuma ahankali ya sake kallon sulallan Gwal ɗin dake haɗe da waɗanan sanduna guntaye aciki asaman laɓɓansa yayi sallama tare da shiga ɗaki.
Wutan ɗakin Innayi ta kunna Atake haske

Please Login or Register in order to submit comment