Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

cikin sauri Ummi ta juya tare da kallon Moddibo kana tace.
“Bari na ɗauko hijabina muje tare”.
Bata jira jin abinda zasu ce ba ta juya da sauri ta koma tare da ɗaukan hijabinta ta fito coumpund ɗin kallon Asma'u da Bashir tayi wanda har zuwa lokacin suna cikin ruɗani, cikin Muryan kuka tace.
“Asma'u ku kula da kanku zamu duba hanya ko Allah zaisa mu gansa”.
Cikin sauri Asma'u tace.
“Ummi zamu biku”.
Girgiza kai Ummi tayi tana tafiya tace.
“A'a ku zauna kada ku fito”.
Daga haka ta fice Malam Ahmad na ƙoƙarin ɗauko mota Moddibo yace.
“Ummi kuzo ku shiga motata kawai”,


Kai ta gyaɗa kana tashiga bayan motar kusa da Innayi.
Malam Ahmad kuwa a gaba, kana suka fara tafiya koda da irin tunanin da yake Aransa duk wani inda suke tunanin mota zai iya maƙalewa ko kuma hatsari sun duba amma babu M Jameel da motarsa babu dalilinsa har unguwar su Abba suka koma amma still Babu shi babu dalilinsa.


Cikin yanayin gajiyawa da ɗimuwa Abba ya buɗe Murfin motar ya fito kana Moddibo da sauran ma duk suka fito.
Cikin raunin murya me nuni da razani Abba yace.
“Gashi mun biyo har nan ma amma baya nan, to mu gwada zuwa asibiti mu duba ko dai yayi hatsari ne ko yaya”.
Cikin raunin murya Moddibo ya Girgiza kai kana yace.
“Abba hatsari kuma? Ai da hatsari ne da munga mota kuma da ankira mu”.
Kafin Abba yace wani abu Innayi ta kalli Moddibo tare da cewa.
“Eh muje dai asibitin saboda Kore shakku”.
Jinjina kai sukayi tare da shiga motar kana suka nufi Asibitin.
Ahankali Moddibo ya kalli Innayi kana yace.
“Toh wani asibitin zamuje kin san dai bawasu manyan asibiti muke dasu ba”.
Cikin sanyi malam Ahmad yace.
“Mu fara zuwa babban asibitin idan yaso sai mu duba sauran daga baya”.
Kai Moddibo ya gyaɗa tare da nufar babban asibitin Abba na biye dasu.
Suna isa suka tarar da gate din asibitin arufe kasancewar har biyu tayi,sauran asibitin suka shiga zagayawa amma ko wanne arufe in sun buga an buɗe musuma in sun shiga bashi ba lbrinsa.
Cikin han zari Abba ya cewa Moddibo su nufi Private hospital ɗin Abba haka kuwa akayi.
Suna isa Moddibo ya sauƙa tare da nufar cikin Hospital kana ya tambayi Norse dake aiki ko M Jameel yazo suka ce a'a juyawa yayi ya shiga motar kana suka ci-gaba da nemansa.
Wasa gaske fa babu Jameel ba dililinsa ba motarsa, gaba ɗaya sun shiga ruɗu da zulumi gamida tsoro.


Misalin ƙarfe uku hankalin su ya kai ƙololuwa wajen tashi baki ɗaya sun cika da damuwa zuwa wannan lokacin sun tabbatar ba lafiya domin M Jameel baya yawo sannan Gembulan ba wani babban gari ne da keda charking point ba bare su kai report.
Moddibo kuwa banda tasbihi da kiran sunan Allah babu abinda yake Aransa yayin da kasala da mutuwar jikinsa ke ƙaruwa fiye da farko kana ga hadarin da zuwa yanzu yayi gangami asama da alamar ruwa na gab da sakƙowa, dan tuni aka fara yayyafi.


Abba kuwa tunda suka fito a asibiti ya kifa kansa ajikin motar zuciyarsa na bugawa da masifaffen ƙarfi cikin raunin murya yace.
“Acikin wannan daren ga hadari na kira layukan Jameeluna duka basa shiga a wannan yanayin ina Jamilu na ya shiga”.


Cikin raunin murya mai cike da karaya Modibbo ya fesar da numfashi mai zafi kana yace.
“Yanzu acikin daren nan ina J yake?.
Wani hali yake ciki?.
Wani irin yanayi yake cikin a wannan daren da kuma hadarin da yake tasowa ina J ɗina yake!?”.


Cikin ƙarfin hali Malam Ahmad ya numfasa kana yace.
“Insha Allah ba komai mu bari muga zuwa safiya abinda Ubangiji zai yi”.


Cikin tsanananin rauni Ummi ta kife kanta da jikin kujeran Motar kana ta fashe da wani Marayan kuka mai gunji”.


Cikin damuwa da kuma tausayawa Abba ya juya tare da kallon Malam Ahmad kana yace.
“Malam ku tafi gida kaima Moddibo ku koma gida da Innayi kada ruwan nan ya saƙƙo muna nan duk inda ya kamata mu duba mun duba baya nan bari mu gani zuwa safiya”.


Girgiza kai Moddibo yayi Araunane yace.
“Abba ya za ayi mu koma mu shiga cikin gida mu samu mafaka bayan bamu san halin da J yake ciki ba. Abba ina kake tunanin zamu koma mu samu nutsuwa acikin wannan yanayin bayan bamu san ina J yake ba!?”.


Kallonsa Abba yayi cike da rauni yace.
“Toh Aliyu ina zamuje mu duba?, Duk inda ya kamata mu duba mun duba sannan wayoyinsa basa shiga wannan shine babban tashin hankalina mu koma gida muyi alwala mu sanar wa Ubangiji halin da muke ciki Aliyu”.
Jinjina kai sukayi atare cike da gamsuwa da abinda yace sam tashin hankali da ruɗanin da suke ciki yasa sun kasa samun nutsuwar da zasuyi addu'a.
Kai Moddibo ya gyaɗa kana yace.
“Toh Abba”.
Sannan suka shiga mota Abba yaja ya nufi gidansu cikin tashin hankali da ɗimuwa yayin da Hajiya Karima ke kuka Abba kuwa ko da kallonta ya gagara yi bare kuma ya iya lallashin ta.
Ya yinda Moddibo ya nufi gidan Ummi babu abinda ke tashi acikin motar banda sheshsheƙan Kukan Ummi ta rasa shin wani irin tunani zata yi shin ina Jameelunta yake awannan tsohon daren Akuma irin wannan lokacin.
Moddibo kuwa cikin tsananin damuwa da zulumi da macewar jiki ya cigaba da Driving har ya isa kofar gidan yayi Parking.
Fita Malam Ahmad yayi Ummi ma ta sauƙa suka nufi cikin gidan.
Ganin hasken mota yasa Bashir miƙewa da sauri tare da buɗe ƙaramin gate ɗin.
Cikin sauri Asma'u da har zuwa lokacin take zaune ta ɗago kanta tare da miƙewa ta riƙe hannun Ummi kana tace.
“Ummi Ina Yaya Jameel Ummi kunga Yah Jameel?".
Cikin sanyi Ummu ke jujjuya mata kai.
Ita kuwa a ɗimauce tace. “Ummi to ina yashiga awannan daren dubi hadari fa wani hali yake ciki?”.
Girgiza kai Ummi tayi tare da fashewa da kuka kana tace.
“Ban saniba Asma'u Bansan inda Jameelu na yake ba, bansan halin da yake ciki ba Asma'u zuciyata zafi take jinake tamkar kaina zai rabe gida biyu!”.
Aruɗe Asma'u tace.
_“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n Allahumma Ajirni fii musibati wa'ahlifli khairan minha_, nashiga uku Yah Jameel”.
Cikin sauri Malam Ahmad ya riƙe hannun Asma'u ganin kamar bata hayyacinta kana yace.
“Subhanallah Asma'u da iliminki kike kirawa kanki shiga uku kada ki sake haka Addu'a ya kamata mu masa kunji ko?”.
Kallonsa ya mayar kan Bashir kana yace.
“Kuzo mushiga muyi masa addu'a ayanzu ba kuka Jameelu yake da buƙata daga wajen muba face adduoi”.
Kai suka gyaɗa sannan ya sake hannun Asma'u ya riƙe na Ummi Bashir kuma yarike hannun Asma'u suka shiga ciki kai tsaye ko wannensu toilet yashiga ya ɗaura Al'wala kana ya fito suka shimfiɗa Sallaya tare da fara jera nafillah suna roƙon Allah daya fitar da M Jameel aduk halin da yake ciki.


Moddibo kuwa suna isa gida yayi Parking tare da rufe ƙofar kana ya wuce falonsa yayin da Innayi ma tashige sashen ta yana shiga kai tsaye toilet dake falon ya shiga ya ɗaura alwala kana ya fito ya shimfida Sallaya cike da nutsuwa ya fara Sallah kana duk sujjadar da zaiyi sai ya roƙi Ubangiji ya kare J ɗin sa aduk inda yake”.
Baki ɗaya su haka suka raya wannan daren cike da bautar Ubangiji tare kuma da rokon Allah daya bayyanar da M Jameel kana Allah yaraba sa da duk kan sharrin Mutum da Aljan.


Bayan an kira Assalatu Moddibo ya fito ya nufi masallaci ana idar da sallah kai tsaye gidan Abba ya nufa.
Yana isa kiran Ummi na shiga wayarsa ciki. Sanyin jiki ya ɗaga wayar tare da kaiwa kunnensa kana yayi Sallama.
Cikin dashashshiyar murya Ummi ta amsa Sallamar sa kana tace.
“Babana ya labarin Jameelu na?”.
Cikin sanyin murya yace.
“Ummi nima gashi yanzu nazo wajen Abba naji ko ya dawo gida”.
Dai-dai lokacin Abba ya buɗe gate ya fito ganin Moddibo tsaye yasa ya isa wajensa ahankali Moddibo ya zare wayar daga kunnensa bayan yace anjina zai kirata.


“Aliyu dama yanzu zanje wajenka”.
A hankali Modibbo yace.
“Abba to yanzu ya zamuyi”.
Numfashi Abba ya fesar tare da cewa.
“To mu tafi police station Jiya Baki ɗaya ba muyi tunanin zuwa can ba”.
Kai Moddibo ya gyaɗa kana suka shiga motarsa yaja Abba kuwa jingina da jikin kujera yayi baki ɗaya zuciyarsa ta tushe ya rasa wani irin tunani zaiyi yayin da Idanunsa suka tsats-tsafo da ruwan hawaye.
Moddibo kuwa Driving yake amma baki ɗaya baya fahimtar komai ko gilmawar mutum ya gani sai yaga kamar J ɗin sane.
Suna isa yayi Parking atare suka fito daga motar tare da shiga station din Dpo dake ƙoƙarin fita yayi Murmushi tare da cewa.
“Alh Bashiru maidala Barka da zuwa kaine da kan ka?”.
Jinjina kai Abba yayi kana cikin sanyin murya yace.
“Na kawo report ne ɗana Jameelu ne bamu ganiba”.
Cike da mamaki da kuma al'ajabi Dpo da sauran folisawan suka ce.
“Ɗan ka Jameelu kuma?”.
Kai Abba ya gyaɗa kana yace.
“Eh tun jiya ba agansa ba kuma babu motarsa sannan akira layukan sa basa shiga”.
Cike da jimami Dpo yace.
“Subhanallah Alhj mai yasa baku kawo report tun dare ba!?”.
Numfashi Abba ya fesar kana yace.
“Yanayin hadari ne sannan baki daya hankalin mu baya Jikin mu sai mukayi tunanin bari muyi addu'a mu kaiwa Ubangiji kukan mu”.
Daga nan yayi miki bayanin dukkan abinda ke tafiya.
Kai Dpo ya gyaɗa tare da cewa.
“Toh shikenan Alhj insha Allah yanzu zamu kira hedquater mu na cikin Taraba afaɗa musu halin da ake ciki”.
Kai Abba ya gyaɗa kana yace.
“Toh shikenan mun gode”.
Moddibo kuwa tun da suka shiga ya jingina da jikin bango Ya Lumshe Idanunsa yana motsa laɓɓansa alamar tasbihi bai ce komai.


Wunin wannan ranan baki ɗaya haka gidaje uku sukayi sa cikin zullumi,fargaba da kuma tsantsar tashin hankali Moddibo kuwa duk bayan minti biyu sai ya kira Number M Jameel aƙalla daga Jiya da daddare zuwa yau ya kira wayarsa yafi sau ɗari.
Acan ɓangaren Ummi ma haka yakasance bini-bini zata kira layin sa amma amsar ɗaya ake basu shine Switch off.
Haka zalika Abba time to time zaiyi try number M Jameel amma akashe Wunin wannan ranan baki ɗaya sunyi zuru-zuru dasu kallo ɗaya zaka musu kasancewa suna cikin tsananin tashin hankali da ɗimuwa duk inda ya kamata su nema ko su bincika duk sun nema sun bincika amman ba lbri.
Abba kuwa zama yayi afalonsa tare da kira duk wani danginsa ko kuma abokin arziki ko zaiji Jameelu yaje amma kowa amsa ɗaya yake basa baije ba.
Haka zalika Ummi baki ɗaya ta kira danginta ko M Jameel yaje amma suma dai amsar ɗaya ce baije ba.


Wunin wannan ranan har dare babu M Jameel babu labarin sa zuwa wannan lokacin tsananin tashin hankali da ruɗun da suke ciki ba zai misaltuba.


Da daddare Misalin ƙarfe goma Moddibo ne zaune a falon Abba kansa aƙasa yayinda idanunsa suka kaɗa sukayi ja jawur kana jijiyoyin kansa sun tashi sunyi ruɗu ruɗu rabonsa da bacci tun daren shekaran jiya haka zalika yauma koda runtsawa ne yakasa kana ya sanya duka hannunsa biyu ya dafe kansa dashi zuwa lokacin baki ɗaya ya kasa control ɗin kansa kife kansa yayi ajikin kujera tare da fashewa da kuka mai gunji.
Cikin wata raunan'niyar murya mai cike da karkarwa yace.
“Abba ina J yake? Abba ina J ya tafi ya barni Abba wani hali J yake ciki?”.
Hajiya Karima ce tashigo falon bakinta ɗauke da Sallama tare da kallon Moddibo dake kuka tamkar ƙaramin yaro lumshe Idanunta tayi tare da cewa.
“Haba Aliyu kuka kuma kai da ya kamata ka tausashi Mahaifinsa sannan kuma ka zauna zakuyi ta kuka atare kenan?”.
Karo na farko kenan arayuwar data yi masa magana cikin taushin lafazi.
Ahankali Moddibo ya ɗago kai ya kalleta still yana kuka yace.
“Aunty Karima ina J yake Ina J ɗina yashiga ya barni?”.
Cikin rauni Abba ya ɗago idanunsa da hawaye ke zuba Akuma dai-dai lokacin wayar Abba ta ɗauki ruri yana ɗagawa yaga number ce ba suna sai ya mayar ya ajiye.
Kallonsa Moddibo yayi tare da faɗin.
“Abba waye ne?".
Ciki Sanyin Abba ya kalli wayar kana yace.
“Numbar ce ba suna”.
Cikin muryan kuka Moddibo yace.
“Toh Abba ka ɗaga mana ko za'a faɗa mana anga J ne”.
Cikin sauri Abba yayi Picking call ɗin tare da cewa.
“Assalamu Alaikum”.
Daga ɗaya ɓangaren cikin wata bauɗaɗɗiyar murya aka amsa da.
“Wa'alaikum Salam kaine Alhaji Bashiru Maidala mahaifin Malam Jameelu?”.
Cikin sauri Abba ya gyaɗa kai tare da miƙewa tsaye kana yace.
“Eh nine mahaifin Jameelu”.
Cikin sauri Moddibo ya miƙe tsaye,
itama Hajiya Karima cikin sauri ta miƙe tsaye.
Gyaran murya yayi kana yace.
“Toh Jameelu yana wajen mu”.
Cikin rawan baki Abba yace.
“Jameelu yana wajen ku yana cikin halin lafiya? To a ina kuke?”.
Kai tsaye yace.
“Eh gashi ma kaji muryarsa”.
Ya faɗa tare da miƙawa M Jameel wayar.
Cikin sauri Abba yace.
“Jameelu”.
M Jameel kuwa cikin wata raunan'niyar murya me cike da galabaita da tashin hankali kamar wanda yayi kuka yana sauƙe ajiyar zuciya yace.
“Abbana”.
Cikin rawan jiki da rauni Abba yace.
“Na'am Jameelu Meye sameka?,Aina kake?”.
Ajiyar zuciya mai nauyi M Jameel ya sauƙe cikin rauni da yanayi wahala yace.
“Abba nima ban sani ba bansan inda nake ba Abba ina A.J”.
Cikin muryan kuka Abba ya kalli Moddibo da jikinsa ke rawa kana yace.


“Gashinan".
Ahankali M Jameel dake sakin ajiyar zuciya yace.
“Abba ka bashi wayar”.
Miƙawa Moddibo wayar Abba yayi cikin sauri Moddibo ya amsa tare da mannawa akunnensa kana Yace.
“Jyyyyyy”,yaja sunan cike da taraddadi.
Fesar da numfashi M Jameel Yayi tare da cewa.
“AJ”.
Cikin yanayin rauni da tausayawa ya lumshe idanunsa tare da cewa.
“J ina kake?”.
Girgiza kai M Jameel Yayi kana yace.
“AJ ban sani ba bansan inda nake ba, ban san ida suka kawoni ba”.
Cikin sauri aka Fisge wayar daga hannun M Jameel kana cikin wannan bauɗaɗɗiyar murya akace.
“Ka bawa mahaifinsa waya”.
Ahankali kuma cikin sanyi Moddibo yace.
“Waye kai ina J yake?”.
Cikin wata razananniyar tsawa yace.
“Kabawa mahaifinsa waya ba da kai muke son magana ba?".
Moddibo kuwa Girgiza kai yayi kana yace.
“Toh me kuke so ku faɗa min ko mameye”.
Cikin sauri Abba ya janye wayar daga kunnensa tare da sa wayar a handsfree kana yace.
“Gani mahaifin Jameelu".
Daga ɗaya ɓangaren mutumin yace.
“Jameelu yana hannunmu bawai mun sace sa dan mu kashe sa ko wani abu bane amma idan kuka yi mana taurin kai zamu iya kash”...






*Littafin SAKAYYAH na kuɗine ƴar uwa 1k ne kacal ki biya ki karanta cikin Aminci ba haƙƙin wani a kanki 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA. Sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276*






*By*
*GARKUWAR MARUBUTA*






*Littafin SAKAYYAH na kuɗine ki biya ki karanta cikin Aminci da salama babu haƙƙin kowa a kanki littafin 1k kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276, sai in saki a Group ɗin*


“Idan har kana son rayuwar ɗanka to.
Kabi sharaɗin mu kabi tsarinmu, sannan kabi dukkan dokokin, muddin kana so Jameel ya rayu idan kuma ka kuskura kayi mana taurin kai kayi mana gardama kan sharuɗan da muka ginda ya maka to zakaga abinda zai biyo bayan gardama”.
Cikin tsanananin kaɗuwa Abba ke girgiza kai yayin da bakinsa ke rawa ya gaza furta komai.
Cikin wannan bauɗaɗɗiyar murya mutumin ya cigaba da cewa.
“Dama kai tsaye mu aikin kashe sa aka bamu. Toj amma saboda nagartansa da mutuncinsa yasa mukaji bama buƙatar kashe Malam Jameelu munfi ɓuƙatar abada kuɗi musakeshi domin shi Jameelu na kowane, kauda irinsu a doron kasa asarace data shafi, dukkan al'umma, dan haka kabi sharuɗanmu mu sakeshi salamun-salaman ya dawo hannunku hankali kwance, idan kuma ka kuskura kayi mana gardama duk da na gartan Jameel zamuyi abinda muma ranmu bai soba!”.
Cikin tsanananin tsoro da tashin hankali Abba ya dafe ƙirjinsa da hannu ɗaya kana yace.
“Innalillahi.
Dan Allah ku faɗa min koma me kukeso zan baku bazan muku gardama ba da Izinin Ubangiji”.
Cikin wata kakkausar murya mutumin yace.
“Bayan kai wanda mu kejin sa agefenka kada ya mana gardama domin shine Amininsa Moddibo”.


Girgiza kai Abba yayi still jikinsa na rawa kana muryarsa cike da rauni yace.
“Ba zaiyi gardama ba”.
Gyaran murya Mutumin yayi kana yace.
“Kasa amsa kuwwa shima Moddibo yaji abinda ake magana akai”.
Kai Abba ya gyaɗa still muryarsa na rawa yace.
“Nasa, nasa, nasa”.
Cikin bada umarni mutumin yace.
“Ku nutsu ku zauna ku jini”.
Kai Abba ya gyaɗa kana yace.
“Toh”.
Gyara murya mutumin yayi cike da isa yace.
“Baku zauna ba nasan atsaye kuke”.
Atare Abba, Moddibo da Hajiya Karima suka zauna Araunane Abba yace.
“Toh mun zauna wallahi”.
Kai Mutumin ya gyaɗa tare da faɗin.
“Yayi kyau sharaɗin mu na farko da zamu ƙidanya muku idan ka bishi Jameel ya rayu idan kuwa baka bishi ba Jameel ya mutu wannan shine sharaɗi na farko kuma shine mafi tsauri”.
Ajiyar zuciya kawai Moddibo ke sauƙewa zuciyarsa na cigaba da bugawa da masifar ƙarfi.
Mutumin ya cigaba da cewa.
“Sannan yanzu rayuwar Jameel yana hannunka da kai da Amininsa da kuma mahaifiyarsa da ma sauran Makusantan ku, idan kuka mana gardama kamar kuna wasa da rayuwar Jameel ne”.


Atare Moddibo da Abba suka haɗa baki wajen cewa.
“Meye kuke buƙata menene sharaɗin naku?”.
Kai Mutumin ya gyaɗa kana yace.
“Sharaɗin namu shine wannan maganar kada ku yarda kada ku kuskura koda agigin bacci koda amafarki kusa hukuma acikinta!”.
Moddibo kuwa ƙirjinsa ne ya buga cikin sauri ya dafe kansa da hannunsa biyu tare da kifa fuskarsa ajikin kushin kana ya furta.
“Innalillahi wa'inna Ilahi rajiu'n”.
Cikin ƙasa da murya Abba ya runtse Idanunsa tare da cewa.
“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n La'ilaha Illah anta subhanaka Inni kuntu Minal Zhalimin”.
Cikin tsawa mutumin yace.
“Zaku faɗa kenan!?”.
Da sauri Moddibo ya girgiza masa kai dake kife akan kushin kamar yana gabansa kana yace.
“Ba zamu faɗa ba wa kowa ba, mudai fatan mu J ya kasance cikin ƙoshin lafiya, kada ku cutar dashi”.
Taɓe baki Mutumin yayi kana yace.
“Kada ku yarda kada ku kuskura ku sanya hukuma aciki”.
Ajiyar zuciya Abba ya sauƙe tare da fesar da numfashi kana yace.
“Ba zamu faɗa ba da izinin Ubangiji zamu bi sharaɗin ku.
Amma sai dai kafin ma ku kiramu mun kaiwa hukuma maganar amatsayin Jameel ya ɓata tunda mun kwana babu shi sannan mun wuni babu shi toh munje wajen hukuma amma bawai munje amatsayin mun kai ƙorafi akan ku bane”.


Jinjina kai Mutumin yayi tare da taɓe baki kana yace.
“Toh wannan sharaɗine Idan hukuma sun dawo dan suna nan kamar Mayu, daga sunji babu mutum idan sun sake kawo kansu kada kuce mun nemi kuɗi awajenku”.
Yarfe hannu Hajiya Karima tayi tare da girgiza kai ta ƙurawa Abba Ido tamkar shike maganar.
Cikin bauɗaɗɗiyar murya Mutumin ya cigaba da cewa.
“Muddin kana son ran Jameel to.
Kayi shiru da bakin ka idan mun kafa maka sharaɗi na biyu ko kuma mun faɗi abinda mukeso kun bayar to Jameel zai dawo amatsayin ɓata yayi sannan ba sace sa akayi ya dawo ba”.
Abba kuwa buɗe idanunsa dake lumshe yayi kana yace.
“Insha Allah zamu bi sharaɗin ku amma yanzu mai kuke so ku faɗa min”.
Cikin sauri ya janyo wayar tare da kallon screen ɗin jin ɗit-ɗit-ɗit alamar an kashe.


Ajiyar zuciya Abba ya sauƙe tare da rintse idanunsa da karfi kana yace.
“Innalilahi wa'inna ilahi rajiu'n Hasbunallahu wani'imal wakin”.
Moddibo kuwa da still hannunsa ke dafe akansa yana taune lip ɗin sa na ƙasa babu abinda ke fita abakinsa face kalmar Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n.
Hajiya Karima kuwa Girgiza kai kawai take tare da yarfe hannu kana tana mai maimaita kalmar Hasbunallahu wani'imal wakin ta juya tare da kallon Abba da idanunsa suka kaɗa suka yi jawur sannan tace.
“Innalillahi wa'inna Ilahi rajiu'n wannan wani irin zamani Allah ya kawo mu kenan ƴan Kidnapping ne suka ɗauke Jameelu”.


Lokaci ɗaya Moddibo ya sake dafe kansa da karfin yana cigaba da taune lip ɗin sa na ƙasa.
Girgiza kai Hajiya Karima tayi kana ta cigaba da cewa.
“Amma Alhj wannan sharaɗin nasu zancene na banza ina muke da yaƙinin zasu iya kare Jameelu ba zasu cutar da shiba ba gwara mu faɗawa hukuma ta shiga cikin maganar nan ba”.
Cikin sauri Moddibo ya ɗago kansa daga jikin kushin wanda sai alokacin ya samu damar hakan hannunsa biyu ya haɗe waje ɗaya alamun roƙo kana ya runtse Idanunsa da ƙarfi ya shiga.
Girgiza kansa muryarsa na rawa yace.
“A'a,a'a,a'a Aunty Karima kiyi wa Allah da Manzonsa kada ki sako hukuma acikin maganar nan Wallahi kina sa hukuma zasu iya yiwa J komai kiyiwa Allah kada kisa hukuma aciki kiji abinda suka faɗa mana”.


Abba kuwa jujjuya kai ya shiga yi kana idanunsa akan Hajiya Karima yace.
“Karima ban yarda ba ban yafe ba wannan maganar ya fita muddin kinaso Jameelu na ya dawo kada ki faɗawa hukuma wannan maganar”.
Kai ta gyaɗa cike da damuwa.
Kallon wayarsa Abba yayi tare da cewa.
“Yanzu bari na sake kiransu naji me suke buƙata”.
Ya faɗa tare da dearling number amma swich off”.


Ɗagowa Abba yayi tare da kallon Moddibo kana yace.
“Aliyu Wayar akashe”.
Cikin sauri Hajiya Karima tace.
“Ai dama zaiyi wuya yashiga ya za ayi ya shiga ai ba zai taɓa shiga ba”.
Daga Abba har Moddibo babu wanda yace komai Allah ne kaɗai yasan abinda suke ji aransu.


Dai-dai lokacin Hajiya Turai ta shigo bakinta ɗauke da Sallama kusa da Hajiya Karima ta zauna Idanunta sun kaɗa sunyi jawur har sun kumbura alamar tayi kuka ta gaji Idanunta akan Abba tace.
“Alhj har yanzu babu labarin Jameelu”.
Kafin Abba yace wani abu Hajiya Karima tayi saurin cewa.
“Yan zun nan ƴan Kidnapping sun Kira su suka ɗauke sa!”.
Cikin sauri Hajiya Turai ta dafe ƙirjinta tare da cewa.
“Hasbunallahu wa niimal wakil Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n,Ƴan Kidnapping kuma Alhj!?”.
Girgiza kai Abba yayi sai kuma ya riƙe tafin hannunta kana yace.
“Ki zauna”.
Ba musu ta tazauna jikinta na rawa saboda tashin hankali da take ciki.


Ajiyar zuciya Abba ya sauƙe kana ya maida kallonsa kan Hajiya Karima tare da cewa.
“Wannan maganar daga mu sai mu iya mu nan kada ku kuskura maganar nan ta fita iya mu nan ban amince ba kuma ban yafe ba daga ke har Karima ban amince ku kai maganar nan kunnen hukuma ba, duk wacce takai abakin igiyoyin auren ta duka saboda sun sa sharaɗin idan na yarda hukuma ta shiga zasu kashe min Jameelu”.
Ya ida maganar cikin raunin murya.


Kai Hajiya Turai ta girgiza cikin Muryan kuka tace.
“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n in sha Allah ba zamu faɗa ba Alhj yama za ayi mu faɗa ai wannan ba abin faɗa bane!”.
Hajiya Karima ma cikin sauri ta girgiza kai kana tace.
“Insha Allah ba zamu faɗa ba, zamu kiyaye”.
Moddibo kuwa har zuwa yanzu yana dafe da kansa da hannu biyu still Idanunsa aruntse.
Ahankali Abba ya kira sunan sa tare da cewa.
“Aliyu”.
Araunane Moddibo ya ɗago idanunsa da sukayi Jawur kana sun kumbura ga lip ɗin sa na ƙasa sunyi ja kana ya ɗan kumbura.
Cikin rauni ya kalli Abba tare da cewa.
“Na'am Abba”.
Ajiyar zuciya Abba ya sauƙe kana yace.
“Aliyu ya zamuyi?”.
Zazzafafar ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe tare da cewa.
“Abba sai dai mu jira kiran su na biyu muji mai suke buƙata magana ce dai na kuɗi atanadi abinda suke bukata a ajiye tun wuri”.
Kai Abba ya gyaɗa tare da cewa.
“Toh Aliyu amma yanzu ya zamuyi da mahaifiyarsa inaga kada ka faɗa mata halin da ake ciki”.
Moddibo kuwa kallon Abba yayi kana ya girgiza kansa tare da cewa.
“Abba kar afaɗa mata kuma? Ai gwara tasan cewa J yana raye, domin zuciyar Ummi zata iya bugawa da idan ba afaɗa mata ba gwara in Faɗa mata tasan cewa J yana raye tasan cewa munyi magana da shi naji muryansa, kaima kaji muryan J fa yanda muka yi magana dashi ƙilan sun dake shi!”.
Ya faɗa cikin raunin murya.


Runtse Idanu Abba yayi da ƙarfi hawaye masu zafin gaske suka shiga bin kuncinsa Shar-shar-shar.
Moddibo kuwa still Idanunsa na runtse ya gagara buɗewa har zuwa yanzu yana jin muryan M Jameel na cewa A.J bansan inda nake ba ban san ina nake ba.
Cikin rauni ya ɗago kansa muryarsa na rawa yace.
“Abba kaji fa J cewa yake baisan inda yake ba Abba ina suka kaisa ina suka cusa sa”.
Dafa kansa Abba yayi kana yace.
“Aliyu duk yanda za ayi idan ka faɗawa Fatima kada ta faɗawa kowa, sannan ka kiyaye yanda zaka faɗa mata kada hankalinta ya tashi!”.
Girgiza kai Moddibo yayi kana yace.
“Abba ba zata faɗawa kowa ba idan na faɗa mata halin da ake ciki”.
Jinjina kai Abba yayi tare da cewa.
“Toh shikenan Aliyu ka kula”.
Kai Moddibo ya gyaɗa dai-dai lokacin kiran Ummi ya shigo wayar Moddibo kallon Abba yayi kana yace.
“Abba ka gani ko kirana ma take yi yanzu kafin na wuce gida ma saina biya wajenta”.
Cike da rauni Abba yace.
“Toh shikenan tashi kaje Aliyu gashi kaima har ƙarfe goma na dare yayi tsoro nakeji, jiya a irin ya wannan lokacin suka ɗauki

Please Login or Register in order to submit comment