Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

yawa haka?”.
Murmushi tayi kana tace.
“Wannan ɗumame ne Innayi tayi muku ɗayan kuma ɗumamen perpesoup ɗin jiya ne wannan kuma jollof nayi muku na Spaghetti”.
Jinjina kai M Jameel yayi kana yace.
“Ni dai kamar nafi son ɗumamen Amma bari naga jollof ɗin naki”.
Ya ida maganar tare da buɗe Kulan cikin sauri ya lumshe idanunsa jin ƙamshin daya ratsa hancinsa.
Kallonta yayi kana yace.
“A'a bazan ci ɗumame ba”.
Juyawa Moddibo yayi tare da kallon M Jameel kana yace.
“Ai kuwa baka Isa ba ɗumame zaka ci, Asma'u Allah ya miki albarka”.
Sai kuma ya sake kallon M Jameel dake murmushi kana yace.
“Ai dolenka ɗumame zaka ci dan kaine Innayi ke yin ɗumame ko wani shekara sai ka ishemu da ɗumame saboda kai ake liƙa mana”.


Murmushi M Jameel yayi kana yace.
“Ai ɗumamenta yana da daɗi kai kan ka in faɗa maka zakayi missing ɗumanenta idan baka kusa yanzu ma dan kana tare dashi ne”.
Murmushin gefen baki Moddibo yayi kana yace.
“Um naji amma dai yau shi zaka ci”.
Dariya M Jameel yayi tare da cewa.
“Ba matsala ai ɗumamen Innayi nace”.
Miƙewa Asma'u tayi tare da ficewa Moddibo da M Jameel kuwa Matsawa sukayi tare da fara cin ɗumamen kaɗan suka ci sannan suka ci jollof ɗin taliya suka sha tea perpesoup din kazar kuwa ko buɗewa basuyi ba bayan sun gama suka miƙe suka tafi masallaci tare da idar da sallah saida sukayi Azkhar kafin suka dawo gida suka kwanta bacci kafin wani lokaci su tashi su tafi Tafseer acikin makarantar su.


Ƙarfe Goma da rabi dai-dai suka farka atare Moddibo ya miƙe bakinsa ɗauke da addu'a kana yashiga toilet yayi wanka tare da daura al'wala zama yayi tare da shafa lotion mai ƙamshi sannan ya sanya Jallabiya Marron colour tare da ɗaura baƙin Alkyabba akai kana ya naɗa hirami akansa sosai yayi kyau tamkar balarabe kana ya feshe jikinsa da turarukansa masu daɗin ƙamshi sallah walha ya gabatar tare da zama ya fara ƙira'a cikin Suratul Maryam.
Sha daya da rabi dai-dai M Jameel ya fito daga ɗaya Bedroom din cikin shiri da alama ya gabatar da sallar walhar shima kallon hadaɗɗen agogon dake ɗaure atsintsiyar hannunsa yayi kana ya maida kallonsa kan Moddibo tare da cewa.
“A.J sha biyu ta kusa fa mutafi kasan ana jiranmu”.
Dai-dai lokacin da wayar Moddibo yayi ruri kallon screen ɗin yayi tare da kallon M Jameel kana yace.
“Gashi ma malam Arɗo ke kirana da alama zai ce mu ake jira masallaci ya cika”.
Jinjina kai M Jameel yayi kana yace.
“Mu tafi”.
Kai Moddibo ya gyaɗa tare da ɗaukar mukullin motar suka fice.


Kai tsaye masallacin dake cikin makarantarsu suka nufa wanda yake cike da maza da mata ko wanne na ɓangaren su sai dai mata sunfi yawa ƙarfe 12:00 ya musu acikin masallacin.
Gyaran Murya M Jameel yayi cikin nutsuwa da kuma yanayin zafin jinjinsa ya gyara zamansa tare da cewa.
_“Innalhamdulillah Nahmaduhu Wanastainuhu wanastaghfiru wa'nazubillahi billahi min shuriri anfusna wamin sayyi ati a'amalina manyah dillahu fala hadiyala waman mudillah fala hadiyala Wa'ash hadu Allah ilahalillahu Wa'ash hadu anna Muhammadu Abduhu warasulu amma ba'ad faya Ikhwatul musulmi Assalamu alaikum warahmatullah wabarkatuhu”_.


Suka amsa da.
“Wa'alaikum Salam warahmatullah wabarkatuhu”.
Ya numfasa tare da kallon Moddibo da idanunsa ke lumshe sai kuma ya gyara zamansa kana yace.
“Duk kan yabo da godiya su tabbata ga Allah subhanahu wata'ala mai kowa mai komai daya sake nuna mana wannan wata mai cike da falala da kuma rahma Allah ya nuna mana ƙarshen sa lafiya kamar yanda ya nuna mana farkon sa Awancan shekarar mun tsaya aƙarshen Suratul Jinni insha Allah yau zamu ɗaura acikin Suratul Muzammil Aramma jeka cikin suran muji mai Allah yace”.


Gyaɗa kai Moddibo yayi tare da gyara zamansa cikin nutsuwa da sanyin Muryansa tare da kamala kana yayi A'uziyya tare da basmala ya fara kamar haka;.
_“1-Ya Ayyuhal Muzammil,2-Ƙumullaila illa ƙaliliah 3-Nisfshu awinƙus minhu ƙalila”_
Atake masallacin yayi tsit tamkar babu mahalukin dake numfashi yayin da karatun ke ratsasu.


Shikuwa M Jameel Kai ya gyaɗa da faɗin.
“Yawwa Aramma ci gaba mai Allah yake cewa acikin aya ta gaba”.
Jinjina kai Moddibo yayi tare da manna bayansa da jikin kujera ya cigaba da cewa.
_“4-Auzidhu alaihi warartilill ƙur'ana tartila5-Inna sanulƙi alaika ƙaulan sakila”_.


Numfashi M Jameel yayi kana yace.
“Suratul Muzammil Makiyya ce tana da ayoyi guda ashirin.
Ya numfasa tare da lumshe idanunsa kana ya cigaba da cewa.
“Suratul Muzammil tana karantar da tarbiya da juriya ga Muslimi,domin susami damar tsayuwar da umarnin Allah”.
Still wajen yayi tamkar babu mahalukin dake numfashi jama'ar dake wajen su tattara duk kan nutsuwarsu suna sauraron abinda Allah yace Moddibo kuwa System ɗin gabansa ya zubawa Idanu tare da lumshe idanunsa.
M Jameel ya numfasa tare da cewa.
_“Ya Ayyuhal Muzammil,Ma'ana ya kai wanda ka lulluɓa da mayafi”_
Atake masallacin ya kaure da kabbara suna faɗin.
“Allahu akbar, Allahu akbar Allah yakareka Malam”.
Zama M Jameel ya gyara tare da kallon jama'ar bayan sunyi shiru ya ɗaura da cewa.
_“ƙumillayla illa ƙalila,katsaya domin yin Sallah acikin dare(suka) face kaɗan”._
Nanma kabbara suka sake kaurewa dashi.
Shi kuwa M Jameel numfashi ya sauƙe kana ya cigaba da fadin.
_“Nisfshu awin minƙushu ƙalila,Rabinsa ,ko ka rage Abu kaɗan daga gareshi._
Haka suka cigaba da tafsirin ayoyin.
Ƙarfe ɗaya dai-dai suka tashi ɗaya da kwata sukayi Sallar azahar zama sukayi acikin masallacin suka fara Muraja'a tun daga suratul tauba zuwa Nahal jin kiran la'asar yasa suka dakata kana suka tashi Moddibo ne yaja Sallar M Jameel kuwa shi yayi ladanci bayan sun idar ne suka fita kai tsaye masallacin dake Unguwar su Moddibo suka nufa ƙarfe biyar suka fara gabatar da tafsirin acikin suratul hujurat wannan kuma na maza ne zalla ƙarfe shida dai-dai suka tashi.


Bayan sun tashi M Jameel yashiga mazaunin Driver Moddibo kuwa gefen mai zaman banza ya zauna tare da lumshe idanunsa yana sakin numfashi Kallonsa M Jameel yayi tare da murmushi kana yayiwa motar key.
Wayar Moddibo ne ya hau ruri Anutse ya sanya hannu ya ɗauka ganin sunan Ummi yasa ya gyara zamansa cike da nutsuwa yayi Picking tare da Sallama kana yace.
“Ummi ina yini”.
Daga ɗaya ɓangare cike da so da kulawa Ummi tayi murmushi kana tace.
“Babana".
Moddibo ya amsa da.
“Na'am Ummina”.
Murmushi Ummi tayi tare da cewa.
“Babana sannuku da ƙoƙari nasan yanzu baki da hutu Ramadan ya shigo”.
Jinjina kai Moddibo yayi kana yace.
“Ga munan dai kam Ummi muna fama”.
Cike da kulawa da kuma ƙaunar su tace.
“Allah sarki Allah ya biya ku Allah yaƙara rufa asiri”.
Ya amsa da.
“Ameen”.
Ummi ta gyara wayar akunnenta kana tace.
“Babana nashirya muku abin buɗa baki kuzo kusha ruwa”.
Kai Moddibo ya gyaɗa kana yace.
“Toh Ummi mun gode muna nan tafe yanzu ma Insha Allah zamu zo”.


Kasancewar M Jameel na Jin Komai saboda wayar a handsfree yake yasa ya juya akalar motar zuwa hanyar gidan Ummi adai-dai ƙofar gidan Ummi M Jameel yayi hong mai gadi ya buɗe musu suka shiga...!


Yau dai ba editing. Dan muna cikin hidiman bikine




By
*GARKUWAN MARUBUTA*
📝✨💫⏰🤴🏻👹❤️❤️❤️🍇


*SAKAYYAH*
_Page 15_

_NA_
*AYSHA ALIYU GARKUWA*


🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇






*Saura ƙiris FREE PAGE dai yazo ƙarshe in sha Allah mun kusa gamawa. Yar uwa ki biya ki karanta cikin Aminci domin littafin SAKAYYAH na kuɗine 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA. Sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP. 09097853276. Kana in saki a Groups ɗin da zamuci gaba da posting.*




*GARKUWAR* taku ce dai MA'AURATA, da masu shirin aure, da masu jego, da yan gayu masu son k’amshi kece raini, da gyaran da zaike maimaita muku dararen forkon kuruciya*


Ko kunsan Jikinmu na da sinadaran hormones da suke taimakawa dan’adam akan komai musamman lokacin da mace take mu’amalar aure da mijinta. Mafi akasari wannan hormones din ne ke samun matsala ko su yi sanyi koma su daina aiki kwata-kwata shi ne dalilin da zai sa mace tace bata jin sha’awa ko bata san dadin aure ba. Albishirinku ina da kayan da ke taimakawa wannan sinadaran du dawo aiki tukuru don karkato miki da kimarki wajan mai gida sannan su taimakawa wannan sinadaran hormones dinki su dinka secreting din ni’ima wadatacciya da zata taimaka miki ki gamsu mijinki ya gamsu fiye da tunaninki. Note: Kayana ba sa tsinka ruwan ni’ima suna dai taimakawa hormones dinki ne su tsattsafo da ni’imar musamman wacca cutar sanyi ko dattin mahaifa ya dankarar da su ya hana su yin aikinsu yanda ya kamata. Haka zalika idan kina da kyau ki kara da wanka. Zaki iya amfani da magani na na gargajiya wanda zai gyara miki sex hormones din kullum ki kasance cikin humidify wato cikin damshi mai albarka kamar yanda ake son mace. Yana gyara miki mara.


Sai kamshi. Hajiyata daure ki fara amfani da turarena ki ji irin salon kamshin sa salo ne da zai daidaita ki da mijinki ya kankaro miki da kimarki a wajansa. Siyan na gari mayar da kudi gida.


Ga masu buƙata ga number' wayata wanda nake whatsApp dashi 09097853276 kimin mgn ta whatsApp in har kin tabbatar kin shirya saya mu dai-dai ta, kayana ba ƙanana bane, shiyasa bana harkan karanta, muddin kinsan baki shirya sayaba Please kada kiyi min mgn ki bari sai kin shirya kuɗinki a hannu, ba ina nufin kayana bana talaka bane, no akwai ƙananan set na masu karamin karfi, banson aimin mgn a ɓatamin lokacin aiyukana a shirme baki shiryaba. Shine karantan da bana so.
0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU. In kin shirya ga number ta ga kuma account number ta wanda in mun gama mgn zaki turo kudin ki, kana insa miki kaya a mota, duk ƙasar da kike kayana zaije gareki, amman fa in kinada dalilin zuwan nasune🤝🏻sayan na gari meda kudi gida.




GARKUWAR MA'AURATA




Anutse Moddibo da M Jameel suka fito daga motar dai-dai lokacin da Malam Ahmad ya fito daga harabar gidan ganinsu yasa ya faɗaɗa fara'ar fuskarsa tare da faɗin.
“A'a Masha Allah tagwayen Ummi kunzo?”.
Murmushi sukayi Atare kana suka ƙara sa kusa dashi.
Kallonsu Malam Ahmad yayi fuskarsa ɗauke da murmushi kana yace.
“Sannunku da zuwa ku isa daga ciki zan dawo mu gaisa”.
Kai suka gyaɗa masa atare kana suka nufi haraban cikin gidan shi kuma ya fice.
Bakin su ɗauke da Sallama suka shiga farfajiyar gidan,
Kusan a tare suka juyo suka kalli juna lokacin da idanunsu, ya sauƙa akan shimfiɗar ƙaton taburma da Ummi ta shimfiɗe asaman baranda kana ga wani lallausan Chanis capet dake fitar da ƙamshi da wasu manyan tuntuna guda uku ɗaya na tsakiya biyu na gefe da gefe sai manyan tire guda huɗu akai tiren farko na kayan fruit ne kama daga,Tuffa, Inabi, Gwanda, Dabino, Abarba, Ayaba, Kankana, Lemo duk anyi slinzing ɗinsu.
Ɗaya tiren kuma Flaks ɗin tea ne da ma dai-dai-tan kofina masu kyau sai gongomin madara da Bounvita.
Sai kuma ɗayan dake ɗauke da Flaks din kunu agefe, sai kuma na ƙarshe wanda yafi su girma manyan kulo-line masu kyau kula na farko Perpesoup ɗin jan naman rago ne daya dahu ligif yana fitar da ƙamshi sai ɗaya kulan kuma soyeyyen dan kalin ne da ƙwai gwanin ban sha'awa.
Jin Sallamar sune yasa Ummi saurin fitowa daga falo tare da faɗaɗa fara'ar dake Samar fuskarta kana tace.
“Lale marhaba sannunku da zuwa Babana”.
Murmushin gefen baki Moddibo yayi wanda ke ƙara masa kyawun fuskarsa kana ya lumshe idanunsa tare da faɗin.
“Barka dai Ummina”.
M Jameel kuwa baki ya tura cike da Shagwaɓa kana ya langwaɓar da kai Idanunsa akan Umminsa sai kuma ya kalli Moddibo dake ƙoƙarin zama akan shimfiɗar da Ummi tayi kana yace.
“Ni dai gaskiya na fara kishi Ummi mai yasa tun da har haka kike son Aliyun nan bakisa min sunan Babban naki ba nima ki riƙa cemin Babana?”.


Murmushi Ummi tayi Idanunta akansa ta zauna kana tace.
“To ai kaima Babana ne ko ka manta Kai takwaran kakan kane Baban-Babanka.
Dariya mai sauti yayi kana ya shafa sajensa tare da cewa.
“Ƙwarai kuwa haka Abbana ke kirana da Babana munyi raba dai-dai Ummi ta kiraka da Babanta Ni kuma Abba na ya kira ni da Babana”.


Gyaɗa kai Moddibo yayi cikin yanayin sanyin Muryansa ya Kalli M Jameel kana yace.
“Oho dai amma nine na hannun daman Ummi”.
Murmushi Ummi tayi cike da ƙaunarsu kana ta zauna daga gefensu Idanunta akan Moddibo dake motsa bakinsa idanunsa alumshe alamar tasbihi yake.
Ganin haka sai ta miƙe dan kar ta takura masa ta ɗan ɗaga sautin Muryanta tare da cewa.
“Bashir ga Yayanka sun zo baka zo kun gaisa ba”.
Cike da ladabi Bashir ya fito kana yace.
“Ummi kaya na nake gyarawa yanzu nake so in fito”.
Ya Ida maganar tare da zama agefen Moddibo kana yace.
“Yaya Moddibo ina wuni ya Ibada?”.
Moddibo kuwa buɗe idanunsa dake lumshe ya buɗe tare da ɗaura hannunsa akan Bashir yana shafawa kana yace.
“Lafiya lau Alhamdulillah ya karatu?”.
Bashir ya amsa da.
“Alhamdulillah”,Kana ya maida kallon sa kam M Jameel dake motsa baki da alama shima tasbihi yake ya kallesa tare da cewa.
“Yaya Jameel Ina wuni ya ibada?”.
M Jameel ya Amsa da.
“Alhamdulillah”.
Miƙewa Bashir yayi ya koma ya cigaba da aikin da yake.


Moddibo kuwa bayan yayi tasbihi sai ya koma Azkharul masa ƙarfe shida da minti Ashirin da biyu aka kira Sallar maghariba Plate din Dabino da Ummi ta ajiye musu agabansu Anutse Moddibo ya miƙe tare da ɗaukan ruwa ya kuskure bakinsa kana ya dawo ya zauna.
Shima M Jameel miƙewa yayi ya wanke bakinsa dabino Moddibo ya ɗauka ya buɗe sanan ya sanya abakinsa bayan ya furta.
“Zahabazzaba'u Wabitallatil,Uruƙu wasu batul Ajri Insha Allah”.
Anutse ya ke cin dabinon inda yaci sai ya sanya ƙwallon atafin hannunsa na hagu.
Guda bakwai yaci kana ya dakata.
M Jameel kuwa dabino Uku yaci kana ya janyo faranti kayan friut ɗin ya fara da Abarba.


Lumshe idanu Moddibo yayi tare da ɗaukar Inabi ya kai bakinsa sai kuma ya buɗe Idanunsa akan Ummin data ƙara so wajen zama tayi tare da tsirawa M Jameel idanu baki ɗaya hankalinta da nutsuwar ta yana kansa.


Iska Moddibo ya furzar daga bakinsa tare da jingina bayansa da jikin bangon ya lura da tun zuwansu wani irin kallon da Ummi ke bin M Jameel dashi kallone mai nuni da tsantsar so, da kuma ƙauna da shaƙuwa irin wanda uwa ke nunawa ƴaƴan ta.
Ƙasa da kansa yayi yayin da yaji ruwan hawaye masu ɗumi na tsata-tsafo masa saboda ganin shi ya rasa wannan damar bazai samu irin wannan ba arayuwarsa ba still Kansa na ƙasa ba tare daya ɗago ba ya dai-dai-ta muryarsa tare da faɗin.
“Ummi kiyi buɗa baki mana”.


Sai asannan Ummi ta lura da kallon da take bin M Jameel dashi, Malam Ahmad ma murmushi yayi domin ya lura da kallon da Ummi kebin M Jameel dashi Shikuwa M Jameel sai alokacin ya ɗago kansa ya lura da irin kallon da Umminsa ke binsa dashi.
Murmushi yayi mai cike da so da ƙauna.
Kana yace.
“Ya dai Ummina nayi kyaune ko muni kike ta kallona?”.


Ajiyar zuciya ta sauƙe kana ta ɗan lumshe Idanunta tare da girgiza kai kana tace.
“A'a kawai dai naga azumi ɗaya akayi ana biyu har ka rame”.
Murmushi yayi tare da gyara zamansa kana yace.
“Hmmm Ummi kenan ai kinga mu ba azumin ne kaɗai ba. akwai yawon zirga-zirga sannan abincinma bama nutsuwa mu cisa yanda ya kamata musamman ma idan na biyewa Babanki”.


Jinjina kai Ummi tayi kana tace.
“To yau kam anan sai kunci kuncika cikin ku sannan in dafa muku na Sahur ma ku tafi dashi”.
Girgiza kai Moddibo yayi kana cikin sauri yace.
“A'a Ummi ki zauna Innayi na mana sannan ga can Asma'u na taya ta yanzu idan mun koma sai mun rasa inda zamu sanya abincin a cikinmu”.
Jinjina kai tayi kana tace.
“Toh shikenan Babana”.
Murmushi Moddibo yayi kana yace.
“Ummi kici abinci mana”.


Kai ta gyaɗa sannan ta janyo Plate ɗin dabinon ta ci guda uku Bayan tayi addu'ar buɗa baki.
Malam Ahmad ma danino uku yaci sannan Ummi ta ɗauki Flaks da niyyar haɗa musu tea Moddibo dake cin friut yayi saurin cewa.
“A'a Ummi bari sai munyi Sallah”.
Kai ta gyaɗa kana tace.
“Toh shikenan sai kun dawo”.


Miƙewa sukayi M Jameel da Moddibo suka ɗauki buta kana suka ɗaura alwala suka fice Malam Ahmad kuwa ya riga su fita.
Kai tsaye masallacin ƙofar gidan su Ummi da Baban Asma'u ke limancin suka shiga. Suna idar da Sallar Maghariba bayan sun idar suka dawo cikin gida shigowarsu yayi dai-dai da rurin da wayar M Jameel keyi.


Kallon Moddibo M Jameel yayi kana yace.
“Innayi ce ke kira”.
Jinjina kai Moddibo yayi tare da cewa.
“Uhm”.
picking call din yayi ya kai kunnensa.


Daga ɗaya ɓangaren Innayi tayi gyaran murya kana tace.
“Jamilu lafiya baku dawo kunyi buɗa baki ba mai kuke yi har yanzu awaje?”.
Sajensa ya shafa kana yace.
“Innayi wallahi Ummi ce ta riƙe mu wai saidai muyi buɗa baki agidan ta”.
Murmushi Innayi tayi kana tace.
“Toh mu kuma na gidan mu ya zamu yi dashi”.


Kallon Moddibo yayi sai kuma yayi Murmushi kana yace.
“Innayi abawa Almajirai dai sai kibar mana na Sahur dan nasan kinyi miyarki mai daɗin nan miyar me kika mana ma tukunna?”.


Dariya Innayi tayi kana tace.
“Miyar roman da kake so na daddawa da ƙarago shi zanyi muku na Sahur”.
murmushi ya saki tare da faɗin.
“Yauwa ina son wannan miyar”.
Kai ta gyaɗa kana tace.
“Toh shikenan sai kun dawo ka gaishe da Ummin”.
Ta faɗa tare da katse kiran.


Suna ida shiga gidan suka samu wajen suka zauna Ummi ta miƙe tare da ɗaukar Flaks da kofina ta haɗa musu tea mai kauri yana tururi kana ta zuba musu soyeyyen dankali da ƙwai.
Anutse suka fara ci kaɗan Moddibo yaci ya janye hannunsa daga ciki.
Kallonsa Ummi tayi kana tace.
“Ya dai Babana kaci mana”.
Murmushi Moddibo yayi tare da ɗaura hannunsa na dama akan shafefen cikinsa ya shafa kana yace.
“Ummi na ƙoshi”.
Girgiza kai Ummi tayi tare da cewa.
“Kai Babana me ma kuka ci?”.
Ɗan kwaɓe fuska yayi kana cikin sanyin murya mai kama da shagwaɓa ya lumshe idanunsa tare da cewa.
“Ummi kar muje muna sallah abinci yan fitowa ta hancin mu”.
Kallonsa Ummi tayi tare da murmushi kana tace.
“A'a Babana me ma kuka ci da zai zazzago ta hancinku?”.
Murmushi yayi tare da shafa sajensa zuwa gemunsa kana yace.
“Allah Ummi mun ƙoshi ko ba haka ba J?”.
Kai M Jameel ya gyaɗa tare da Hararan Moddibo ya cire hannunsa a Plate din dan kalin.
Hira suka sake taɓawa kana Moddibo ya miƙe tare da kallon Ummi kana yace.
“Ummi zamu tafi”.


Jinjina kai Ummi tayi tare da cewa.
“Idan kunyi sallah Isha'i zaku dawo ta nan?”.
Girgiza kai Moddibo yayi kana yace.
“A'a Ummi sai wani lokaci”.
Gyaɗa kai tayi tare da cewa.
“Toh ku tafi da kunun nan”.


Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe tare da gyara tsayuwar sa kana yace.
“Toh Ummi ina son kunun abamu zan tafi dashi”.
M Jameel ya juya ya kalli Ummi tare da langwaɓar da kai kana yace.
“Ummi Ni dai ba abani abinda nake so ba”.
Cike da kulawa da kuma so ta juya ta kallesa kana tace.
“Me kake so?”.
Murmushi yayi kana yace.
“Inabin za'a bani in tafi dashi”.
Saurin Kallonsa Moddibo yayi sai kuma ya juya ya kalli Ummi tare da cewa.
“Ummi kar ki basa yasha muna dashi agida”.
Tura baki M Jameel Yayi kana yace.
“Iyeee to na haƙura tunda ba aso ayimin kyautar”.
Ummi Kam murmushi take Cike da ƙaunar su, ji takeyi tamkar su duka biyu a cikinta ta rainesu ta haifesu.
Sallama suka mata kana suka fice suka shiga mota Moddibo ke mazaunin Driver yayin da M Jameel ke gefen mai zaman banza kai tsaye Masallacin da suke limancin na ƙofar gidan Sarki suka nufa sunyi tafiya mai ɗan tsayi kafin suka isa lokacin da suka isa ankira sallar Isha'i suka shiga Moddibo ne yayi limanci suka idar da Isha'i kana sukayi Asham bayan an watse kana suka fito suka shiga mota wannan karon M Jameel ke driving Kai tsaye gidan Innayi suka wuce.


Ƙarfe takwas da rabi suka isa gidan bayan sunyi parking sun fito kai tsaye sashen Innayi suka shiga bakinsu ɗauke da sallama a farfajiyar gidan suka tarar da Innayi da Asma'u zaune Innayi dake gashin nama akan mangal da tarin gawayi agefenta ta daga kanta tare da Kallonsu kana ta amsa Sallamar su.


Ƙara sawa kusa da ita sukayi M Jameel yaja kujera ya Zauna kana ya Kalli Innayi tare da cewa.
“Innayi ya dai mai ake gasa wasa ne?”.
Murmushi Innayi tayi kana tace.
“Nama nake dan gasawa nasanku da cin nama kamar kuraye!”.
Dariya M Jameel Yayi kana yace.
“Aikam Innayi kin kyauta gashi asalin gashi na gargajiya kike yi”.
Kai ta gyaɗa tana ɗaukar Plate tace.
“Eh ai nasanku”.
Ta ida maganar tare da miƙa musu naman data yayyanka ta zuba a Plate tare dasa musu yaji agefe sannan ta yaryara ɗa musu man shanu.
Kallon Asma'u dake yi musu sannu da zuwa tayi kana tace.
“Asms'u ɗauko musu capet su zauna”.
Cikin murza kai gefen dama da hagu Modibbo yace.
“Uhmm Innayi kin dai sanshi shi J ɗinki da son nama kamar kura”.
Murmushi M Jameel yayi dan yasan tabbas Modibbo bai cika damuwa da namaba, asalima in dai gasheshene ko soyayya in dai yaci yanka huɗu zuwa biyar zaice muƙa-muƙinsa sun gaji da taunawa, in kuma dafaffene wani lokaci da haƙorin gaba zai ɗan tattauna in yaji ya gaji sai ya tura masa naman gabansa.
Shi kuwa M Jameel Allah ya sani yana masifar son nama, shi kuwa Moddibo yafi bawa ƴaƴan itatuwa mahimmanci.
Cikin murmushin yace.
“Yoh in ban so namaba me zanso A.J Namafa shine maƙurar daɗi”.
“A wurinka ba, gashi kuma kana son koyamin”.
Cewar Moddibon,
Asma'u kuwa ganin Innayi na kallonta cikin mamakin tace.
“A'a Asma'u ɗauko musu abin zama mana”.
Kai Asma'u ta gyaɗa kana ta miƙe ta shiga falon ta ɗauko capet ɗin ta shimfiɗa musu awajen da yake agyare tass babu alamar ƙazanta.
Zama sukayi akai, Innayi ta sake kallon Asma'u tare da cewa.
“Haɗa musu Tea sannan kisa musu zuma yaji”.
Kai Asma'u ta gyaɗa kana ta miƙe ta zuba musu shayi tare da zuba wadataccen zuma aciki ta kawo musu.


M Jameel kuwa Anutse ya kai yankan naman bakinsa lokaci ɗaya ya lumshe idanunsa tare da buɗe su akan Innayi kana yace.
“Kai gaskiya gashin nan yayi daɗi sosai”.
Murmushi Innayi tayi tare da kallon Moddibo dake cin naman kamar ko yaushe kamar dai dole, yana ɗan taunawa kaɗan-kaɗan cikin kula tace.
“Kai kuma fa Moddibo?”.
Ɗago kansa yayi ya kalleta kana yace.
“Uhm yayi”.
Girgiza kai tayi kana tace.
“Wato kai dai baza ka iya Yabawa ba kenan?”.
Kansa ya sake ɗagowa tare da kallonta kana yace.
“Ai gashinan J ya yaba kuma danɗanon harshen mu ɗaya ne ai”.
Murmushi M Jameel da Asma'u sukayi.


Innayi kuwa baki ta taɓe M Jameel da Moddibo suka cigaba daci Ahankali Moddibo ya ɗago hannunsa tare da kallon tsadedden agogonsa kana ya mayar da Kallonsa kan M Jameel tare da cewa.
“Sai munyi sauri lokaci ya kusa J”.


Kai M Jameel ya gyaɗa tare da cire hannunsa a Plate din kana yace.
“Toh shikenan mu tafi”.
Miƙewa Moddibo yayi tare da kallon Innayi kana yace.
“Bari naje na canza kaya”.
Daga haka ya juya ya nufi sashen sa, shima M Jameel bayansa yabi.


Moddibo nashiga Bedroom ya sauya kayansa zuwa Jallabiya Coffee color tare da ɗaura farin hirami irin na samarin larabawa kana ya feshe jikinsa da turarukansa masu daɗin ƙamshi.
Anutse ya fito falo ya samu M Jameel da shima ya canza kayansa buɗe fridge M Jameel Yayi ya ɗauki goran faro mai sanyi sannan suka jera tare da Moddibo suka sauƙa.


Kai tsaye sashen su Innayi suka koma batare da sun shiga farfajiyar gidan ba .


“Toh Innayi mun tafi”.
Cewar M Jameel
Tana rufe roban yajin da suka ci nama dashi ta ajiye kana tace.
“Toh Allah ya tsare muma yanzu muna bayanku”.
M Jameel na gyara ɗaurin agogon dake tsintsiyar hannunsa ya kalleta kana yace.
“Toh idan za kuje kuzo mu tafi mana sai mu sauƙe ku”.


Girgiza kai tayi tare da cewa.
“Ai akwai Napep zamu hau”.
M Jameel kuwa kai ya Girgiza kana yace.
“A'a ai abin baiyi ba bayan tanan muke tafiya kuma kuce zaki shiga Napep kawai kuzo mutafi”.
Jinjina kai Innayi ta gyaɗa kana tace.
“To bari mu tattara da sauri sai mu tafi”.
“Toh”,M Jameel yace Shi kuwa Moddibo bai ce komai ba sai harɗe hannunsa da yayi aƙirji.


Cikin sauri Innayi da Asma'u suka tattare wajen sannan suka sanya hijabansu kana suka rufe kichen da

Please Login or Register in order to submit comment