Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

gyada kansa ba tareda ya amsa ba, saida yasake kammala paper hannunsa sannan ya amsa gaisuwar Danladi.

Hafeez ya qarewa Almajiran dasuke karatu kallo,yatuna shekarun baya lokacin da shima yake shiga cikinsu suyi karatu tare, cikin nutsuwa yadawo da kansa qasa yana tunanin ko Malam zai tambayeshi Hassana da Hussaina,saide har yayi yagama zamansa uffan malam bai sake cewa ba, bai tambayi Kaka ba, haka suma su Hassana dasuke tsatsonsa ko harafin H bai kamaba bare ya tambayi lafiyar yaran.
Ahankali Hafeez ya sauke ajiyar zuciya sannan yasaka hannunsa acikin aljihun Babbar rigar sa ya dauko kudi yan dubu-dubu dami uku,ya ajiye agaban malam sannan ya kalleshi yace"zan koma"

Malam baice dashi uffan ba, saide ya gyada masa kansa alamun amsawa,amma ko addu'ar Allah Yakiyaye hanya bata futo daga bakinsa ba,Shima Hafeez bai sake magana ba yamiqe yanufi motarsa ya tsaya yana jiran Danladi dayake jibge kayan abinci da su katan katan din taliya a qofar gidan, saida yagama jibge uban kayan abincin sannan yaciro kudi a aljihun sa dami daya na yan dubu daya yafara bin Almajiran yana raba musu, wanda hakan umarni ne daga Hafeez tun suna hanya yabashi kudin yace yaraba wa yaran sadaka.

Ahankali malam yadago kansa ya kalli Hafeez dayake tsaye can ajikin Mota, suka hada ido, saide kuma cikin sauri kowa ya janye idonsa, Hafeez yayi sauri yabude mota yashige ko kallon hanyar dazata kaishi cikin gidan beyi ba, daga 6angaren malam shima yana tunanin Hafeez din zai shiga cikin gidan su gaisa da mutanan ciki dakuma MAMA, amma saiya ga sa6anin haka, domin kuwa Hafeez kam yana shiga motar ya lumshe idonsa, hanyar cikin gidan ma baisan gani bare yakai kansa ciki har su had'u da MAMA.

Bayan Danladi yagama rabar da kudin ya qarasa yayiwa malam sallama sannan yashiga yaja motar suka bar qofar gidan.

Kai tsaye gidan Aunty suka nufa, yana qoqarin shiga gidan yana turawa abokinsa I.b saqo ta waya, gidan nata shiru alamun babu kowa yaran sun tafi makaranta, kansa tsaye yashige har cikin falo kamar yanda bashida shamaki da gidansa na kano,wata mata ce a tsaye afalon tana qoqarin ajiye magungunan akan wata loka, aqalla zatayi shekaru Arba'in, qamshin turaren da ta riga tasan na waye shita shaqa, cikin sauri ta juyo idonta ya sauka a cikin na Hafeez, lokaci daya fuskar ta ta washe bakinta yabude, cikin tsananin farinciki tace"Hafeez!"

Shima daga nasa 6angaren murmushin sa mai aji yasaki,tareda bude mata hannayen sa, cikin sauri ta qaraso ta shige qirjinsa, lokaci daya suka saki ajiyar zuciya, daga nata 6angar 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~en hawaye takeyi na farincikin ganinsa, yayinda shikuma ya lumshe idonsa yanajin kamar wata damuwar sa zata ragu sakamakon ganin Auntyn nasa, sun jima ahaka kafin su koma kan kujera su zauna, hannunsa cikin nata ya kalleta da kyau yace"idan zan koma wajan aiki ya kamata ki shirya mutafi, likita saiya dubaki acan"

Cikin jin dadi tace"haba Hafeez, likitocin nan ma suna iyaka kokarin su,kuma ina shan magani, yanzu ma abinda yasa jikin nawa yatashi, gurasa ce nagani tabani sha'awa sainaci, daga nan naji yanayin jikin nawa yana sauya wa"

Cikin sanyin jiki yace"Aunty nifa ciwon suger dinnan yana tsorata ni gaskiya, dan Allah kubar garin nan keda mijinki mu koma Kano zanfi kulawa dake yanda yakamata,yanzu kinga bansan bakyajin dadi ba, Shima kuma Ib ya 6oyemin,hankalina yatashi akan hakan,shiyasa yau nashigo"

Murmushin qarfin hali tayi sannan tace"naji sauqi Hafeez,ka kwantar da hankalin ka,cuta aiba mutuwa bace, kaje gida ne?"

Ahankali ya gyada mata kansa, daga haka bata sake yimasa tambaya akan yashiga cikin gidan ko be shiga ba, saboda tariga tasan cewa abu ne me mutuqar wahala Hafeez yasa qafarsa acikin gidan.

Cikin jin dadi ta tashi takawo masa fruit, sannan ta zauna tasake kama hannayen sa ta riqe, tace"Hafeez ina yanmata? kana zaune kaqi kayi aure ko?"

Ahankali ya zame yadora kansa akan cinyarta tareda lumshe idonsa, maganar yanmata datayi masa tasa ya tuno Hafeeza,yanaso yafada mata damuwar sa amma yakasa, yanaso yayi mata batun Hafeeza amma yarasa qwarin gwiwar hakan.



*** *** ***


Bayan an idar da sallar azahar Kawu Hamza yanufi gidansu Ma'aruf akaro na biyu, bayan megadi yayi masa sallama da Ma'aruf yabashi hannu suka gaisa,kunya ta kama Ma'aruf saboda bai yiwa Hafeez maganar da sukayi shida kawu Hamza ba, daga gefe guda kuma yana mamakin yanda kawu Hamzan yadawo, yana mamakin yanda uba zai dage yana nemawa yarsa miji kamar mazaje sun qare,saide a yanda yaga kawu Hamzan ya dage ya tabbatar da cewa lalle da gaske yakeson hadin.

Kawu Hamza ya kalli Ma'aruf yace"kaga nadawo ko?, dama zan tambayeka ne inji Yaya kukai kaida abokin naka? ya amince da maganar da nazo da'ita kuwa?"

Ma'aruf yayi murmushi yace" wallahi Baba nayi laifi,saboda har yanzu banyi masa maganar ba, ni a yanda nakeso inaso ne in sameshi fuska-da fuska muyi maganar, amma insha Allah yau zanyi masa maganar"

Kawu Hamza yayi murmushi yace"to ba laifi, ka sameshi kuyi maganar, saboda harga Allah ni hankali na ya kwanta da yaron,naga yanada nutsuwa sannan babu ruwansa da samari masu rawar kai, sannan nima nasan halin yata zatayi masa biyaiya yanda yakeso"

Ma'aruf yayi ajiyar zuciya yace" insha Allah zanyi masa maganar,duk yanda mukai zakaji"

Kawu Hamza yabashi hannu suka sake gaisawa sannan yayi masa sallama yatafi.


*** *** ***


Agidan Aunty suka wuni,shida kansa yashiga kitchen dinta yayi musu girki, yaranta suna dawowa daga makaranta gida ya kacame da hayaniyar su, shida yaran nata kana gani zakasan cewa ba qaramin sabo sukai dashi ba, tare sukaci abincin cikin jin dadi da walwala, rabon sa da yaji nutsuwa irinta yau harya manta, daga qarshe Danladi ya dauki yaran sukaje shopping kowa taza6i abinda takeso,bayan sallar azahar yayi sallama da Auntyn bayan yagama jiqata da kudad'e dakuma jan kunnanta akan ta kiyaye abubuwan da zata dinga ci, ta kuma dage akan shan magungunan ta.

Daga nan gidansu Ib sukaje, inda ya gaida mahaifin Ibrahim din, sannan yayi musu ihsani, yafuto, shida Ib suna zaune abayan motar, yayinda Danladi yake tuqi ahankali ganin sun kusa zuwa inda zasu sauke Ib din, sukuma su dauki hanyar kano, saida sukaje inda Ib zai sauka sannan Danladi yafice daga motar ya barsu su kadai ko zasuyi wata maganar.

Yana fita kuwa Ib ya kalli abokin nasa yace"meyake damunka ne? Naga kasake zama silent ko da wata damuwar?"

Dan qaramin tsaki yayi sannan yace"rashin lafiyar nan ta Aunty UMMI tana damuna, inaso in dauketa but naga kamar tana son zama agarin nan,Bansan Yaya zanyi ba wallahi "

Ib yayi murmushi yace" banda abunka Hafeez Yaya mata tana zaune da mijinta,sannan mijinta yana aikinsa zaka raba shi da inda yake ka maida su kano? kabarta anan tareda yaranta, kuma naga ai jikin nata ma da sauqi sosai"

Ajiyar zuciya Hafeez ya sauke yace"itama haka tace"

Ib yayi murmushi yace"bayan haka sai menene yake damunka? Hafeez, Koda kayi niyar 6oyemin abinda yake damunka kariga kasan cewa nasanka fiyeda kowa,idan ma ka 6oyemin zan gane"

Cikin damuwa Hafeez yace"akwai wata yarinya da al'amuranta suke damuna,Bansan dalili ba, amma naji ina damuwa da al'amuran yarinyar,kowacce safiya ina ganinta awajan sana'ar ta,ban ta6a yin magana da'ita ba,but I think tanada aure, kokuma tata6a yin auren"

Ib ya gyara zamansa yace"baka ta6a magana da'ita ba? how kagane cewa tanada aure?"

Hafeez yayi shiru yakasa yiwa Ib maganar yaganta tana bawa Baby Nono,saiya kawar da maganar yana fadin" tanamin kwarjini sosai Ib, koda nayi niyyar tunkararta inajin gabana yana faduwa,sai in kasa yimata magana"

Ib yasake yin murmushi yace"kaifa haka kake, narasa yaushe ne zaka dena tsoron yiwa mata magana Hafeez, ka tunkareta kuyi magana, idan ma tanada aure kana yimata magana zata fadama"

Kafin Hafeez yayi magana Ma'aruf yakira wayar Hafeez, cikin nutsuwa yadauki wayar yace"ma'aruf"

Daga d'ayan 6angaren Ma'aruf yace"Hafeez kana gida ne? Inaso inzo akwai maganar da zamuyi"

Cikin aji yace"no naje Niger State, what happen?"

Ma'aruf yace" wallahi akwai wani bawan Allah dayamin maganar ka, so naso inzo muyi maganar kuma bamu hadu ba tunda nadawo, to dazu ma yasake zuwamin da maganar, yacemin akwai yarsa da yakeson baka aurenta idan babu damuwa, sannan a yanda na fahimta da gaske yake, kuma yana yabon halayenka dana yarinyar yana fadamin cewa idan ka aureta zata yima ka biyaiya yanda yakamata,ina ganin da zaka samu dama da munje munga yarinyar idan kaji kana sont...."

Tun kafin Ma'aruf yagama cewa in kaji kana sonta, Hafeez ya katse shi da sauri yace" idan naji inason wa? kai kata6a ganin mahaifin dayake neman kai da 'yarsa? kaga Ma'aruf mubar wannan maganar haka,bana sonta,ba kuma zan ta6a sonta ba, saboda haka ka dakatar dashi da wannan shirman dan Allah"(=F<
@&)

Ma'aruf yace"Amma Hafeez....."

Kafin yagama magana Hafeez yakashe wayar sa tareda dafe kansa, Ib daya gama jin komai yace" to kagani, na tabbatar acan qasar da kake aiki ma bazaka rasa yanmatan dasuke sonka ba, gashi yanzu iyaye sun fara kawo ma yaransu,ina ganin kawai kacire shakka ka tunkari wannan yarinyar kuyi magana inde har kanajin ta aranka"

Hafeez ya girgiza kansa alamun amsawa, daga nan sukai sallama, Danladi yaja motar suka dauki hanya.


*** *** ***


Saida ya sauka agida sannan yake sanarwa Kaka cewa Niger State yaje,taso ta tambayeshi mutanan gidan Wato su MAMA, amma shakkar sa dakuma shakkar abinda zai iya biyo baya yasa tafasa tambayar.
ko abinci baici ba yayi wanka yashirya yatafi masallaci saboda anfara kiran sallah, bayan an idar da sallah yafuto zai tafi gida daga bayansa yaji ana masa sallama.
Zuciyarsa d'aya yajuya yaga wani magidanci,yabashi hannu suka gaisa.

Kawu Hamza yayi murmushi yace"yaro ashe kadawo, ai dazu da rana nasamu abokinka nayi masa maganarka"

Hafeez yanajin haka yadauki Haske, yanajin haka yagane cewa wato shine mutumin dayake neman kai da 'yarsa, ahankali yasaki ajiyar zuciya sannan yace" Bande gane abinda kakeson cewa ba"

Kawu Hamza yayi murmushi yace"to ga wajan zama can mu qarasa zaifi kyau muyi maganar a zaune"

Babu musu Hafeez ya bishi suka zauna, kawu Hamza yace"Yaro ina yawan ganinka a unguwar nan, sannan ina yawan ganinka a masallaci,ina yin nazari akan halaiyar ka har naji cewa zan'iya daukan auren yata nabaka, idan babu damuwa inaso nabaka auren yata,tanada nutsuwa sosai, ina yima sha'awar ta, sannan kaima ina yimata sha'awar ka, nasan cewa zamanku zaiyi kyau idan ka amince da'ita, amatsayina na uba awajanta inada haqqin dazan nema mata mijin aure, nikuma hankali na yafi kwanciya dakai"

Hafeez ya kalli Kawu Hamza yace"kayi haquri, amma hakan bazai iyu ba"

Kawu Hamza yayi murmushi yace"kada kace haka yaro,idan ma akwai yarinyar dakake so, ai ba laifi zaka iya auren yata amatsayin ta biyu, kokuma kafara auren yata daga baya saika auri wacce kakeso, na tabbatar bazakai dana sani akan zama da yarinya ta ba"

Hafeez ya Sosa girarsa guda daya sannan ya kalli Kawu Hamza yace"to amma ita yarinyar taka batada manema ne?"

Kawu Hamza yace"tanada manema, ni dinne de naga dacewar ace ka sameta, saboda shi abu me tsada wajen da akasan za'a adana shi dakyau nan ake ajiyeshi"

Hafeez yayi wani miskilin murmushi sannan yace"to ina ganin kawai acikin maneman nata ka nemi wani ka hada ta dashi" (=F<
@&)

Jikin Kawu Hamza yayi sanyi kalau, be ta6a tunanin cewa akwai namijin da zaiyi wa tayin auren HAFEEZA yayi rejecting ba, yasa yaqini sosai akan yaron, bai tsammaci haka daga gareshi ba,ahankali ya kalli Hafeez sannan yayi murmushin yaqe, yace"Yaro haka kace?"

Babu tantama Hafeez yace"ina ganin hakan zaifi"

Cikin sanyin jiki Kawu Hamza yace"to madallah"










(>y>yaradu Hafeezu yakira wa kansa ruwa=#=#)
(Nima de Ta Rasulu banida ta cewa saide ince TO MADALLA>)

Complete document 1k

8621296018
Amina Muhammad
fcmb

kokuma Katin Mtn ta wannan number 08033300034, tareda shedar biya ta wannan number 08033300034





Amnah El Yaqoub
'<
[5/28, 12:53 PM] El Yaqoub: =ؘMATAR ABBANA=ؘ
(Luv Story)



Writing By Amnah El Yaqoub

Kuyi following WhatsApp Channel dina domin samun sababbin update=G<
https://whatsapp.com/channel/0029VbBR7naJ93wTuOypQV45




9


Daga nan kawu Hamza yamiqe, Hafeez yamiqa masa hannu da nufin musabaha, kawu Hamza bai bashi hannu ba yajuya yatafi, Hafeez ya kalleshi tareda dage kafadunsa alamun abun be dameshi ba.

Kawu Hamza kuwa jiyayi gaba daya qafafunsa sun saki sunyi sanyi,be yi tunanin haka daga wajan Hafeez dinba, qaran shigowar saqo yaji, yaduba wayarsa anan yaga alert ne na kudin Hafeeza wanda tasamu ranar saukar su, lokaci daya fuskarsa ta washe da annuri, kai tsaye yajuya yanufi gidan Inna Ta Rasulu.

Bayan sun gaisa Hafeeza takawo masa ruwa, sannan ta nemi waje ta zauna adan gefe dasu.
Kawu Hamza ya kalli Inna sannan yace"Ta Rasulu kudin Hafeeza yashigo, amma naga sun rufemin account dina saboda qaramin account ne, kuma bai saba daukar kudi masu yawan wannan ba, zan samu lokaci naje banki saisu bude min shi"

Inna tasaki wata Uwar guda tana sake godia ga Allah, kawu Hamza yace"sannan munyi magana da shugaban makarantar tasu yacemin sunata shirye-shiryen tafiyar ta saudia, yanzu Yaya za'ai da wannan kudin?"

Inna tace" eh ai naga wani malami yazo ya dauketa wai zasuje ayi mata fasfo(passport), Hamza ina ganin kawai karaba wannan kudin agyara mana gidan nan, inda muke yoyo da damuna duk agyara mana, sannan asiya mata kayan dakin, duk dade bamu San yaushe ne auren zaizo ba"

Kawu Hamza ya sunkuyar da kansa cikin damuwa sannan ya dago yace"da nayi tunanin in hadata dawani yaro, da farko na yaba da hankalin yaron, to dana sameshi da maganar saiyace min bayaso"

Inna ta gyara zama tace"dan waye?"

Kawu Hamza yace" acan layin suke, bansani ba ko zaki San kakar yaron, gidan Hajiya Rabi'atu, na yiwa Hafeeza sha'awar yaron saboda naga bashida hayaniya kamar de ita,sannan itama Hafeeza zataji dadin zama dashi, amma yaron nan yadubi idona yace bai amince ba,anawa tunanin duk wanda ya dauki kyautar 'yarsa yabaka ai yayima komai arayuwa"

Inna tace"wai gidan Matar da ake cewa Hajiya Kaka?, gidan ta kake nufi?"

Kawu Hamza yace" eh gidan ne"

Inna tace"ai Hajiya Kaka yayanta manya ne,gaskiya ba yaronta bane inaga jikanta ne, amma kuma Hamza, wani hanzari ba gudu ba gara fa da ba'a yi wannan hadin ba, saboda inajin rade-radin cewa Hajiya Kaka tanada wani jikanta Babba, kuma iyayen yaron suna nan araye,amma baya Shiri dasu, wanne da ne zaiyi watsi da iyayensa ya wanye lafiya aduniyar nan Hamza? to ai har gara Gaddafin data liqewa"(>-)

Kawu Hamza yayi murmushi yace"Ta Rasulu wannan duk zancen mutane ne,sanin gaskiyar al'amari sai Allah sai kuma tsatstsauran bincike,babu damuwa Allah yasa hakane yafi Alkhairi, Allah yabata nagari, idan kuma Gaddafin ne Allah yabasu Zaman lafiya"

Inna tace"Amin"

Hafeeza datake zaune agefe tana jinsu, saide tunda suka fara maganar gabanta yake faduwa,batasan wacece Hajiya Kaka ba, bata gane akan waye suke magana ba, amma koma wanene shi ta tabbatar bazata juyawa Gaddafi baya saboda shi ba.


Da daddare suna kwance a gidan sauro Hafeeza tana tattara tilun gashin kanta tana daure shi, Inna ta kalleta tace"jiya na kwanta da safa a qafata gaba daya sai naji ni adaure"

Hafeeza tace"to Inna ai gara haka, ko sauro yashigo bazai cijeki ba, kinyi maganin sauro"

Inna tasake gyara kwanciyar ta tace"ba saboda sauro nasaka ba, abinda yasa nasaka qafata ce take kama gidan sauron saboda kaushi"(>-)

Hafeeza tayi murmushi batare da tace komai ba.

Inna tace"Hafeeza gobe da sassafe kije wajanda kike soya qosai, kitafi da Almajirai kisa su tone duk wannan baqar qasar da muka tarawa Alhaji na sidi a qofar gidansa, naje har gida nayi masa godia nace to mungode shekara da shekaru muna sana'ah a qofar gidan duk mun baqanta masa qasar qofar gida yace babu komai, wannan bulon damuke amfani kisa Almajiran su debesu gaba daya"

Hafeeza tace"uhm..."
batare data tanka ba, saboda tafara karanta addu'ar bacci acikin zuciyar ta.


*** *** ***


Cikin dare yana bacci wani irin masifaffan ciwon ciki ya ta dashi, mararsa ta riqe yarasa yanda zaiyi sai hada gumi yake.

Cikin tsananin tashin hankali ya janyo wayarsa ya dokawa Kaka kira.
Kaka tana bacci taji qaran waya, tamiqe ta zauna tana fadin "la'ila ha illallahu,Muhammadur rasu lullah"
Ta juya gefenta ba taga Hassana ba, da alama yau ta gudu wajan Hussaina acan dakinsu zata kwana,tayi sauri ta dauki wayar ta Kara a kunne, daga nasa 6angaren yace"Kaka zan mutu"

Gabanta ya yanke yafadi tace"Hafeezu!, gani nan zuwa"

Cikin azama tatashi tafuto daga nata dakin tashiga nasa,ta kunna wutar dakin anan tayi tozali da abun Hafeez ya miqe qyam, gabanta yasake faduwa kanta ya Sara, ta kalli Hafeez din taga yana runtse idonsa ga gumi ya jiqe masa fuska sharkaf kamar an watsa masa ruwa, cikin sauri ta qarasa taja bargo ta rufe masa jikinsa duk da akwai jallabiya ajikinsa, sannan ta dauki wayarsa tace"nemo min lambar Jamilu in kirashi"

Kansa ya girgiza alamun bazai iyaba.

Cikin sauri tafuto daga dakin tashiga dakinsu Hassana, tatashi Hussaina cikin magagin bacci Hussaina ta kamo mata number, sannan Kaka tafuto daga dakin ta zauna afalo da wayar a kunnanta, harta kusa katsewa sannan jamilu ya dauka, cikin muryar sa me yanayin bacci yace"gaye ya ne?"

Kaka tace" Jamilu ba Gayen bane kakar Gayen ce da kanta"(=)

Jamilu yayi sauri yabude idonsa, yace"Kaka meyafaru? lafiya kuwa?"

Kaka tace"abokinka yana nan rai a hannun Allah, inaga de lalurar sa dayake fama da'ita ne tadawo masa,dan naga yanayin jikin nasa sai ahankali,idan zai iyu de kazo"

Jamilu yace"to gani nan zuwa"

Yakashe wayar yasauko daga gadonsa ya zura jallabiya, yadauki abubuwan da yasan cewa zasu iya buqata, sannan yafuto acikin wannan dare, yanufo gidansu.

Kaka kuwa shayi ta hado masa da lemon tsami aciki, takoma dakin, anan ta ganshi ya kifa cikinsa ya kwanta akan abun nasa, yayinda kansa yake cikin fillo yana yamutsa fuskarsa cikin azaba.

Zama tayi akusa dashi tace"Hafeezu tashi kasha wannan shayin"

Cikin dauriya yace"Kaka mutuwa zanyi bazan iya shaba"

Kaka ta ajiye shayin tace"ni fa duk yanda nake dakai banason ka dinga kawo min zancen mutuwa Hafeezu,gaba dayanku kaida qanannka kuna nan tare dani babu inda zaku tafi ku barni, Hafeezu idan nace kayi aure bakason maganar,yanzu wannan abun dame yayi kama Hafeezu?"

Suna cikin wannan magana Jamilu yashigo, yadora hannunsa awuyan Hafeez yaji babu zazza6i sosai, ya yaye bargon anan yayi tozali da abu me girma, cikin nutsuwa ya maida bargon ya rufe, sannan yahada allura yayi masa, yana tunanin da alamun maganin da Hafeez din yakesha ne yaqare shiyasa har akazo kan wannan ga6ar, kuma rannan yaje asbiti kafin yadawo ya nemi Hafeez yarasa, yabude brief case dinsa yabawa Kaka wasu magunguna yace"gashi, dasafe a bashi wannan yasha, insha Allah zai samu sauqi, yanzu ma idan allurar ta sakeshi zaiji sauqi insha Allah"

Kaka tace"to shi wannan ciwo na Hafeezu babu makari ne Jamilu?"

Dr. Jamil yayi murmushi yace" Kaka ki masa aure kawai,shine abun nasa zai rissina insha Allah"

Cikin damuwa Kaka tace"to Jamilu mun gode, muje na rakaka qofar gida"

Cikin sauri yace"Haba Kaka, kiyi zamanki tareda driver nafuto, Allah yabashi lafiya"

Kaka ta yiwa jamilu godia sannan tasake gyara wa Hafeez bargon jikinsa, tasake qara masa qarfin esi, sannan tafuto daga dakin, bayan taga bacci me nauyi ya daukeshi.


Cikin ikon Allah zuwa asuba yaji shi kalau yadawo normal babu ciwon cikin ko kad'an,saide kafin yayi sallar asuba saida yayi wanka, bayan ya idar da sallah zama yayi a daki dayake agida yayi sallah ba'a masallaci ba,gari yanayin Haske, yafuto daga dakin kai tsaye yashiga mota yafice daga gidan.

Su Hassana da suke gyaran gidan Kaka tafuto daga dakin Hafeez tana sallallami, Hussaina tace"Kaka me aka miki?"

Hajiya Kaka tace" ku taimakeni jama'ah, ina Hafeezu yashiga ne?"

Hussaina tace" kamarya? haba Kaka kamar wani yaro, may be yafita wani waje"

Kaka ta zauna agefen hannun kujera tace"bazaki gane ba,bashida lafiya jiya kwana mukai bamu runtsa ba"(>-)

Hassana dake goge dining table tace"Kaka yanzu fa kika tashi, na tabbatar sallar asuba ma kin makara, kuma kince kwana kukai baku runtsa ba"

Kaka tace"keni banason jarabar musun tsiya,kiramin shi a wayarki inji ina yake"


*** *** ***


Yana futowa daga gida kai tsaye inda yasaba ganinta yawuce,yau akusa da inda take soya qosai ya faka motarsa, ya zauna acikin motar yana Addu'ah Allah yasa tafuto,yau sosai yakejin qwarin gwiwar yimata magana kamar yanda Babban abokinsa Ib yabashi shawara.
Wayarsa dake gefe tafara qara, yaduba yaga Hassana ce,yasa hannu yakashe wayar baki daya.

Kasancewar hankalinsa yana kan wayarsa yana kasheta,hakan yasa dagowar da zaiyi yaganta awajan tareda wasu Almajirai su biyu, akan idonsa Almajiran suka fara tone duk wata baqar qasa me maiqo data dade awajan, sannan suka debe qasar suka tafi zasu zubar, ita kuma tafara qoqarin motsa manyan dutsinan datake amfani dasu wajan dora abun soya, gabansa ne yafara wani irin fad'uwa, ya lumshe idonsa yana karanta duk addu'ar da tazo bakinsa,fuskarsa babu alamun dariya kokuma sakewa kamar de yanda take kullum, haka yabude motar yafuto,hannunsa zube cikin aljihun wandon sa,kai tsaye wajanda take tsugunne ya tunkara,saida yaje gab da ita sannan yaja ya tsaya yazuba mata ido yana kallonta,fuskarta kamar kullum babu kwalliya ko daya, amma tayi kyau cikin hijabin dayake jikinta.

Jin takun mutum daga gefenta yasa ta dago fararen manyan idonta ta kalleshi,idonsu ya sarqe dana juna, lokaci daya ta tuna haduwarta dashi a asbiti, kuma agabansa ne tabawa Fadila nono,nan da nan tashin hankali ya wanzu a fuskarta, gabanta yafara fadawa,wani irin tsoro ya kamata tanajin tsoron karfa ace mutumin nan ya santa.

Wata tsohuwa ce tazo wucewa ta hanyar,ta kalli Uwar motar datake adane agefe, sannan ta kalli Hafeeza da Hafeez tayi murmushi sannan tace"masha Allah kun dace kuwa"

Cikin sauri suka juya suka kalleta gaba dayansu, ganin yanda suke kallonta yasa tasake magana tayi tunanin Hafeeza suyar qosai tafuto kamar kullum, hakan yasa tace"inma ba saurayin ki bane to me irin wannan motar tunda ya tsaya awannan wajan to yau zakiyi ciniki"

Hafeeza ta kawar da kanta gefe tareda daure fuskarta, ta d'an dage Hijabin ta kad'an tafara qoqarin ture dutsin datake suya zuwa gefe, lokaci daya idon Hafeez ya sauka akan bajajjan hips dinta sakamakon dan janye hijabin datayi, sosai yake kallon qugun nata yakasa dauke idonsa akanta.
Hafeeza ta juyo ta kalleshi nan take ta kamashi yana kallon qugunta,cikin sauri ta saki hijabin nata sannan cikin zazzaqar muryar ta tace"miye hakan?"

Hafeez ya d'an gyara tsayuwar sa sannan yayi gyaran murya, duk da gabansa yana fad'uwa haka ya dake yace"Normal"

Hafeeza tasaki ajiyar zuciya sannan ta dauke idonta daga kansa, tarasa tsaiwar meyake mata awajan,gashi yazuba mata ido sai kallonta yake, gaba daya saita jita wani iri atakure,kafin tagama tunanin datake sai taji Hafeez yace"Dama nace a asbiti....."

Iya abinda yafada kenan,gabanta yayi wani irin luguden faduwa,ta zaro idonta, sannan ta juya ta kalleshi tareda dora d'an yatsanta akan pink lips dinta tace" Kamin shiru"(>+)

Mamaki da wata irin dariya ta kama Hafeez,ya d'an dage girarsa guda daya,yaga alama kamar batason yayi mata maganar asbitin,duba da yanda gaba daya ta rikice sai zare ido take.


Ahankali yatako yaqaraso wajanta ya tsugunna dab da ita kamar jikinsu zai hadu dana juna,har yanzu fuskarsa a daure take babu walwala saide shi a hakan fuskar asake take,hannunsa ya dora akan dutsin da hannunta yake kai,da hannu daya ya juyo da dutsin bai damu da baqin dayake jikin dutsin ba,cikin dakewa dakuma saka qwarin gwiwa yace"ina zankai miki?"

Cikin sauri ta girgiza kanta gabanta yana fad'uwa,kusancin nasu yasake takura ta,bata ta6a kusanci da namiji har hakaba,ahankali tadan ja baya ta matsa daga kusa dashi,gashi taga layin nasu shiru kamar an hana kowa wucewa,Hafeez ya kalleta yaga yanda gumi yake yanke mata agaban goshinta,yazubawa d'an qaramin bakinta ido yana kallo,sannan ya maida idonsa kan gashin idonta masu ban sha'awa, yaga yanda take matsawa daga kusa dashi,ya d'an ta6e bakinsa, cikin wata irin muryar rada wadda sai iya su biyu shida ita ne zasu iya jin abinda suke fada yace"ina son qosai,dayawa nakeso kiyi,sannan kiyimin sadaka dashi, but... wannan yarinyar ta hannunki a asbiti...."

Gaban Hafeeza yasake faduwa,taga alamun mutumin nan tona mata asiri yakeson yi,cikin sauri tafara kad'e hannunta zata tashi tabar masa wajan.

Hafeez yaga alama kamar so take ta gudu tabar wajan,gashi yanason suci gaba da magana, bayason tatafi batare daya sake jin zazzaqar muryar ta ba, hakan yasa cikin sauri yaciro dala dari daga aljihun wandon sa yabata tare da fadin "gashi, kiyimin qosai, kuma kibani canji"

Bata kalli kudin dayake bata ba,so take kawai su rabu ko zata samu yadena tuna mata zancen asbitin nan,cikin sauri ta bude yar qaramar fos din dake cinyarta,Hafeez yana kallonta yaga akwai sababbin kudi acikin fos din miqaqqu.
sai lokacin ta dago kanta ta kalli kudin dayake bata,taga dala ce, kuma tasan

Please Login or Register in order to submit comment