Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

zogale agidan naku, aida nasani da nazo nacira nayi dambu"

Inna tace"Um muna dashi zoki tsigeshi gaba daya munbaki, dama a wannan yanayin ma waye yakeda kud'in dazai sai kayan had'in zogalen?"

Kafin Lami tace wani abu, Inna ta kalli Hafeeza datake wanke-wanke tace"Hafeeza zoki dauko min wannan sauran garin kwakin namu ki jiqamin Nasha"

Hafeeza ta wanke dogoyen yatsun hannunta sirara,sannan ta taso tawuce daki ta dauko mata ledar gaarin tace"gashi Inna"

Inna tace"bude ki zuba a Kofi saiki jiqo"

Hafeeza tace"A a Inna debi da kanki"

Inna tace"ki zuba nace"

Hafeeza ta bude ledar tafara zuba mata gaarin a Kofi, Inna taga Hafeeza tana zuba gaari kamar bata so, tasa hannu ta qwace ledar tace"bani ni"

Tasake bude kan Leda tana zubawa dayawa, Hafeeza ta kalleta tace"ya kike qoqarin juyeshi duka muda muke lalla6ashi Inna?"

Inna tace" naki ko nawa? bataki d'aya tame garin jamaga, zubo min ruwa aciki kigani"

Hafeeza ta jiqo mata gaarin takawo mata, Inna tana gani tace"qara masa ruwa ki barshi ya juqu karnaje yajuqu aciki na, tayaya zansa wannan abu aciki na? ai juquwa zaiyi acikina, kar6o min aron cokali awajan Maman Fadila,duk Cokulan nawa babu kin kwashe kin zubar, lokacin da muke zuwa legas, haka nake kar6ar Cokula bashi, dozin d'aya nera dari"

Lami tayi murmushi bayan tagama bin bayan Hafeeza da kallo, sannan tadawo da kallonta wajan Inna tace"Ta Rasulu Hafeezan taki tagama zama budurwa sai had'a uban qugu take kamar babbar mace,gata kyakykywa kamar bafulatana"

Inna tayi dariya tace" tabdi toko zo in kasheki da fullanci bata sani ba"(=)

Lami tayi murmushi tace"ikon Allah amma tana kama dasu sosai"

Adede lokacin Hafeeza tadawo gidan,da goyon Fadila abayan ta,yarinya yar sati biyar da haihuwa, tabawa Inna cokali sannan taje tana share wajan datayi wanke-wanke.

Inna tasaka cokali acikin kofin garin kwakinta tafara Sha, ta d'ago kanta ta kalli Lami tace" mahaifiyar Hafeeza ba bafulatana bace,ita tasan yaren mecece, yaqi akayi a qasar su suka dawo Nigeria itada iyayenta, iyayen nata suka rasu, sai mijina ya auro ta,lokacin da'aka kawo ta gidan nan karkiga yanda nacika nayi fam ina Kishi da'ita kamar zan fashe, saboda kyau ne da'ita kamar aljana,ga uban gashi kamar 'yar ruwa,yanda kikaga sadaka yalla yan Niger, haka uwarta take, mijina yaje ya auro min ita saboda bana haihuwa,tana zuwa Allah da ikonsa ko shekara ba'a rufa ba ta haifi Hafeeza,ashe ni aka haifa wa, uwar ta mutu, Shima mijin Namu ba'a dade ba yarasu"

Lami tace" Allah sarki,ashe Zaman bane dorewa bane"

Inna tace"to ya za'ai, kwana yaqare, yanzu duk babu kowa dagani sai Hafeeza sai Qanin Babanta dayake qoqarin yimana hidima lokaci zuwa lokaci"

Hafeeza ta qaraso cikin Rumfar ta Shimfida Sallaya ta kwantar da Fadila,yarinyar kyakykywa da'ita fara.

Lami tayi musu sallama tatafi.

Inna ta kalli Hafeeza tace"Hafeeza banji kinyi waya da saurayin kiba yau, ko kunyi wayar nice bansaniba?"

Hafeeza tace" A a bamuyi waya ba Inna"

Ta Rasulu tace"to saboda me? ki kirashi mana Kiji Yaya yake,sai kice masa dama kira nayi mu gaisa,ina laifi mai sonka ai yafi me qinka"

"Inna idan nakira ba lalle ya dauka ba,jiya da mukai waya dashi ya fadamin yanada uzururruka dayawa,baya zama agida suna asbiti an yiwa qanwar sa aiki a qirjinta,wannan shine karo na uku ana yi mata aikin"

Ta Rasulu tace"Subhanallah,Allah yabata lafiya,inajin qari ne da'ita, a qirji yace anyi mata aikin ko a Nono?"(=J)

Cikin sauri Hafeeza ta zaro idonta tana kallonta sannan tace"nashiga uku na, a a Inna bankai nan ba, ban tambayeshi nan ba"(=)





littafin kudi ne, Complete document 1k


8621296018
Amina Muhammad
fcmb

tareda shedar biya ta wannan number 08033300034








Amnah El Yaqoub
'<
[5/22, 9:20 AM] El Yaqoub: =ؘMATAR ABBANA=ؘ
(Luv Story)



Writing By Amnah El Yaqoub

Kuyi following WhatsApp Channel dina domin samun sababbin update=G<
https://whatsapp.com/channel/0029VbBR7naJ93wTuOypQV45



3


Washegari sassafe suka tashi sukai aikin komai suka gyara gidan sannan suka zauna suna break fast saboda yau sunada gyaran tulawa da safe, Husna de fruit takesha, yayinda Hassana take shan tea mai kauri idonta yana kan d'an qaramin Alqur'anin dake hannunta tana dubawa.
Hajiya Kaka tafuto daga dakinta taga har sun gyara gida, hadaddan falon nasu sai qamshi yake,ta zauna akan kujera tana fadin" Allah de yamuku albarka yaran nan,Allah yakawo muku mazaje nagari,ni bansan meyasa nasa goro a bakina ba, yau Alhamis da yanzu nawuce da azumi na kuma wai sainasa goro,kunga kuwa ai babu Azumi"

Husna ta ajiye Bananar dake hannunta ta kalli kaka tace"Dama fa Kaka ba niyya,inaji lokacin da Hassana ta tasheki Sahur tace ko zakiyi Azumi kikace Anya kuwa?"

Kaka tace" Au haba?, yaushe akai hakan? to bansan anyi ba"(=)

Husna tace"dama ai bazaki sani ba"

'Dan ladi direba ne yayi sallama falon yakawo wa Kaka qosai kamar yanda yasaba siyo mata duk lokacin datake so,bayan yafita Kaka taja hadaddiyar food flask din tasu ta zamani, tafara qoqarin budewa da qarfinta amma taqi buduwa,ahankali tasaki d'an qaramin tsaki tace" wataran zan 6alla kwano kuwa, haba gaba daya kwanukan mu na arziqi tunna da can kunsa anbayar ankawo mana na zamani gashinan kanaso ka bude kwano amma kayi-kayi abu yaqi budewa me ake da irin wannan rayuwar?"

Hassana tace"qarfi kika Sawa flask din,ana bude abu ahankali amma Kaka ke kullum kin kasa zama 'yar gayu saiki sawa flask qarfi"

Husna tace"kuma fa ba qarfin ne da'ita ba, ko ina abun yake oho"

Kaka ta kallesu kawai ta girgiza kai sannan tabude ahankali, aikuwa flask ya budu,qamshin Qosai da zafinsa ya bugi hancinta, ta dauki guda daya ta saka abakinta tace"dan masifa qosai yakoma uku nera hamsin,kayi magana ace wake yatashi"

Daga Hassana har Husna suna jin qamshin qosan suka matso suma suka saka hannu,qosan yanada dad'i sosai ga wani yaji aqefe me shegen dad'i.
Husna tace"wai Kaka a'ina ake siyo miki wannan qosan ne me dad'in tsiya?"

Kaka tasake jefa qosai a bakinta tace"can ne layin can na baya dede gidan Alhaji Munzali"

Husna tatafi tunani tana fadin"Alhaji Munzali,Alhaji Munzali...."
Sannan tadawo da duban ta wajan Hassana tace"bangane shiba, ke kin ganeshi?"

Hassana ta girgiza kanta alamun itama bata gane ba,Kaka ta kallesu tace"bakusan Alhaji Munzali ba? Alhaji Munzalin? saina d'ura muku zagi"(==J)

Husna ta hada ido da Hassana sukai murmushi, sannan suka juya suna kallon Kaka.

Hajiya Kaka tace"Alhaji Munzali fa,wanda matarsa tayi hatsarin mota ta rasu,har mukaje daku gaisuwa 'yan'uwan matar sai faduwa suke suna aljannu"

Cikin sauri Hassana tad'an bugi kafadar Husna tace"ke natuna,kusa da gidan wannan 'yar ajin namu HAFEEZA KHALEED"

Husna tace"ok dama adede nan gidansu Hafeeza yake? kai wannan ai aitaci Sunanta Hafeeza din,akwai karatun Alqur'ani kamar ruwa,ga muryar ta dad'i idan tana karatu,but in hakane meyasa tana kusa da islamiya amma kusan kullum saita makara inde haddar safe zamu bayar?"

Hassan ta dangwali yajin qosai, takai bakinta tacinye, sannan tace"gaskiya de inde haddar safe zamu bayar zakiga amakare take zuwa,amma idan da yamma ne kinga bata makara,gata kyakykywa kamar aljana,suma malaman namu naga sai nan-nan suke da'ita kamar ma sonta suke"

Husna tace"su sukasan me suka gani,ai rannan kafin kidawo daga toilet tashigo late, tana sauri zata shigo ajin ashe qusa ta riqe mata gefen hijabinta ita kuma dayake sauri take bata sani ba, aikuwa Hijabin nata yad'age sama, karkiga uban qugun wannan yarinyar, shi kansa malam Sabo bakiga idonsa ba kamar zai fado, ya qwarawa guqun baiwar Allah ido,kuma ahakan kullum tana cikin Hijabi, gashi batada qawaye kullum ita kadai zaki ganta, to dan Allah tanasa Hijabi ma malamai suna mata haka idan wataran tasa mayafi tafita gari ai baza'a rasa samari masu kawo mata Hari ba"

Kaka dake sauraron firar su tace"ikon Allah, aikuwa taji dad'in ta,Hijabi ai shine cikamakon mace mai hankali da tarbiya"


*** *** ***

Da yamma tana zaune tana wanke musu kayan su itada Inna sai Yatsina fuska take tana runtse idonta saboda yanda marar ta take murd'awa, tun safe take jin ciwon marar har zuwa yanzu,kuma maganin ta ya qare gashi aiki yahanata fita ta siyo wani maganin.

Inna dake zaune daga cikin Rumfa tana jin Radio a wayar Hafeeza, wayar ma har tayi ja babu caji, tana qoqarin kashe Radion aka sako wa'azin wani malami,bata fasa ba ta kashe tana fadin''aikuwa bawan Allah saide kayi haquri baqin wa'azin naka nayi ba,caji saura yanka d'aya"(=)

Maqociyar suce tayi sallama ta shigo gidan, Wato Maman Fadila, mace me kimanin shekaru 35, tana dauke da Fadila a kafadarta, adede lokacin Hafeeza tadena wanki ta sunkuyar da kanta qasa tana tauna siraran lips dinta.
Maman Fadila tace"Subhanallah,Auntyn Fadila meyake damunki naga kina runtse ido?"

Inna Ta Rasulu tace" wankin ne bataso,tun dazu taketa faman yatsina fuska ina kallonta"

Maman Fadila tayi murmushi tace"haba Inna ita ta'isa tace haka?"

Tajuya wajan Hafeeza tace" ko cikin ki ne yake ciwo?"

Cikin sauri ta girgiza mata kai tace" marata ce take ciwo tun safe,kuma yaune ranar dazan gama hutun sallah ta,bansan meyasa takemin ciwo ba,qila wannan aikin ne wallahi,kullum mutum bashida aiki daga wannan sai wannan"

Inna tanajin haka tace"Hafeeza ki kiyaye ni, karki sani abakin duniya,yanzu inda wasu baqi ne agidan Namu kika fadi haka ai sai azata naman jikinki nake yanka saboda azaba,wani ma cewa zaiyi azaba na ganawa uwarki harta mutu, nan kuwa ciwon naqudarki ne ya kashe ta,Shima Babanki majanunin Laila bata dade da mutuwa ba shima yabita,idan baki mana wanki ba wanne kaya zamu sa?, Ya zakiyi? haka zaki daure ki qarasa wankin, ni wallahi badan wannan ciwon qafar tawa ba ni Ta Rasulu har a fadamin aiki?"(=2)

Maman Fadila tayi murmushi tace"Inna da Hafeeza drama, kinga riqe min Fadila inje gida in kawo miki magani,nida nakawo raino Uwar raino ba lafiya ai banga ta zama ba"

Daqyar Hafeeza ta kar6i yarinyar ganin idon yarinyar akanta ko qyaftawa batayi, sai taji tausayin yarinyar, ta kar6eta ta goya ta, sannan ta dauraye kayan tafara shanya wa.

Bayan tagama shanya kayan tadawo cikin Rumfar ta zauna akan kujera.
Daga qofar gida Inna tajiyo wani dan gwangwan yana cewa"tsohon kwano mataccen kaya akawo mu siya..."

Daga inda suke zaune Ta Rasulu tace" me za'a kawo ku siya? asato kusiya de, nan almajiri yashigo da sassafe muna baccin asara, ya sace min sabon bokiti na yakawo muku kuka siya, kwana ki dana fita Unguwa wata tukunya dana gani awajansa sabuwa dal nace a'ina kasamu wannan tukunyar yace siya nayi, nace a a, aka sato kuka siya dai, kudena siyan kaya awajan yara yawanci duk na sata ne, nayi masa nasiha de yace yadauka, shine dan tsaurin ido yanzu ma kinji ya dawo"

Dataji Hafeeza shiru bata tanka mata ba, saita kalleta tace"Hafeeza kinyi waya da saurayin ki yau kuwa?"(>)

Hafeeza ta dago kanta da qyar tace" Inna ba kincinye cajin wayar kinajin radio ba?"

Inna tace"Af....haka akayi fa, na manta, sannu Hafeeza, Allah de yabaki lafiya"
Kafin Hafeeza tayi magana Maman Fadila tashigo takawo mata magani tasha, sannan ta shinfida mata tabarma ta kwanta, ta dauki Fadila zasu tafi, Hafeeza ta meqa mata hannu daga kwancen tace "Bani ita"

Babu musu Maman Fadila ta miqa mata yarinyar tanajin dadin yanda Hafeeza take dawainiya da Fadila,duk maqota kowa yasan yanda Hafeeza take son Fadila,hatta shima Baban Fadila kasancewar yasan Hafeezan tanada hankali da nutsuwa uwa uba duk unguwar kowa yasan cewa Hafeeza ta amsa Sunanta, mahaddaciyar Alqur'ani ce, hakan yasa shida kansa Baban Fadilan wani lokacin yake cewa akai Fadila raino wajan Hafeeza.

Hafeeza ta kar6i Fadila ta d'orata akan ruwan cikinta, tadora mata kanta akan tudun tsayaiyun nashanunta, yarinyar kuwa tayi luf kamar ta tada kai da nonon uwarta.(=H)

Cikin sati biyu su Hafeeza suka gama bitar tilawar su gaba daya,har makaranta ta saka musu ranar da za'a yayesu tareda bikin saukar su,acikin sati biyun nan bata zama, kullum tana cikin neman kudi ta hanyar qosai, da daddare bata baccin kirki saboda yanda take raba dare tana tulawar Alqur'ani kasancewar an riga an tantance su itace daliba ta farko dazata fara karatun Alqur'ani aranar saukar tasu, hakan yasa takowanne 6angare take shirye-shirye cikin farinciki.

Yau bayan tadawo daga wajan suyar qosai tabawa Inna kudin kamar yanda tasaba, zata wuce tashiga wanka Inna tace"zo muyi lissafi Hafeeza"

Cikin nutsuwa ta dawo ta zauna,Inna ta janyo asusun dasuke tara ribar su ta fasashi, tahada da kud'in cinikin ranar suka qirgasu,Inna tace"to Islamiyar taku nawa sukace zaku bayar kudin saukar?"

Hafeeza tace"Dubu hamsin ne Inna,kuma tun ranar da suka fada mana nabiya gidan Kawu Hamza nafada masa"

Inna tace"toga ribar mu kinga munsamu kusan dubu saba'in da shida,kidauki dubu hamsin din kikai musu,kuma naga man suyar tamu ma yaqare,ki biya ki siyo mana, ki auno wake, sannan kitahomin da irin naman nan dakika siyomin rannan, dan qafar nan tawa har yanzu jinta nake"(==J=2)

Lokaci d'aya farinciki ya kama Hafeeza, saboda bata ta6a zaton Inna zata bata kudin ba,shiyasa ma kai tsaye tawuce gidan Kawu Hamza tafada masa,tace"to Inna zan siyo insha Allah,bari nayi wanka"
Tafadi hakan bakinta a washe da tsantsar walwala dimples d'in nan nata kuwa sai lotsawa sukeyi.

Tana miqewa zata shiga bandaki Kawu Hamza yayi sallama yashigo gidan,hakan yasa ta fasa shiga wankan ta dawo ta Shimfida masa tabarma takawo masa ruwa a kofin silba, bayan sun gaisa yadubi Hafeeza yace"Hafeeza ya shirye shiryen saukar?"

Cikin farinciki tace"Alhamdulillah kawu"

Yayi ajiyar zuciya sannan yace"to masha Allah,Allah yatemaka, ubangiji Allah yayi miki Albarka"

Cikin nutsuwa tace"Amin Kawu"

Kawu Hamza yadubi Inna yace" Ta Rasulu Hafeeza taje gida tayi min maganar kud'in saukarsu, to nayi niyar zuwa tun ranar in kawo mata kudin dasuke hannu na to kuma sai wani uzurin yashigo, yanzu de ga dubu Hamsin d'in nan tasamu takai musu kafin muga abinda za'a yi kuma"

Inna ta washe bakinta tace" to madalla,Allah yasaka da Alkhairi"

Saikuma ta fashe da kuka tace"Allah yabar zumunci Hamza, Allah yajiqan Haladu,addu'ar Haladu a kullum itace yanda yasawa wannan yarinya suna Hafeeza Allah yasa sunan yabita, kuma gashinan Hafeeza ta tabbata Hafeeza saide baya raye,sun tafi sun barmu nida Hafeeza"

Kawu Hamza yace"Haba Ta Rasulu,menene abun kuka kuma,insha Allahu daga Yaya har Mahaifiyar Hafeeza suna Aljanna, Allah ya musu Rahma ni zan tafi"

Inna ta goge hawayen idonta tace"to Hamza mungode,agaida mutanan gida"

Bayan yafita Hafeeza tamiqe zata shiga wankan ta, Inna tace"ina zaki Hafeeza, zoki dauki kud'in mana"

Hafeeza ta dawo ta zauna tace"Inna ai kin riga kin bani,basai mu ajiye wannan dinba?"

Inna tace" A a, wancen dana baki dama ai kece me wahalar nemowa, wannan kuma kyauta yabaki, ki ware dubu ashirin ki siyo mana taliya da macaroni tunda munada sauran shinkafa, dubu talatin din kije dashi gidan Maman Fadila saiku tsara abubuwan da zakuyi na rabo, ranar saukar "

Hafeeza tace"to Inna baza'a sake siyo miki wani abun ba? kodan lemo haka?"

Inna Ta Rasulu ta yatsina fuska tace"barshi Hafeeza, karki siyo min lemon komai,banajin d'and'ano abakina Hamza yatuno min da mutuwar mijina data mahaifiyar ki,gaba daya naji komai yafita akaina,tsiren de damukai magana dake d'azu shi kawai zaki siyo min" (=J=)

Hafeeza tayi murmushi tace"to Inna"

Bayan tafuto daga wanka kai tsaye gidan Maman Fadila ta wuce, tabata dubu talatin din tafada mata kayan rabo zasu siya dashi, maman Fadila tayi lissafi zasuyi cin-cin da meat pie da dublan, ragowar kudin kuma tace sai Hafeeza tasai kayan kwalliya dashi.

Bayan sungama tsara komai Maman Fadila ta dauko Alqur'anin ta dakuma littafin Akhdari Hafeeza tayi mata qarin karatun.
Sannan tayi mata sallama tatafi, kai tsaye tawuce ta siyo kayaiyakin da sukai lissafi itada Inna, bata fasa ba saida ta siyo mata lemon gora guda biyu samfirin Limca ,sannan tadawo gida.
Inna ta debi naman ta ragewa Hafeeza sannan taja nata gabanta tanaci tana korawa da lemo,Hafeeza sai mamaki take yanda Inna take lumshe ido idan tana shan lemon, amma qarfi da yaji tace batajin d'and'ano abakinta. (=)


*** *** ***


Spain
(Barcelona)

Futowar sa daga wanka kenan, skin dinsa sai sheqi take najin dad'i dakuma hutu daya ratsa fatar,tun daga gefen wuyansa 6angaren hannun dama har zuwa hannayensa anyi masa zanen tattoo, ko d'ar baiji ba ya qaraso cikin dakin kasancewar babu komai a jikinsa ko towel bai daura ba, qa'idarsa baya ta6a daura towel inde yafuto daga wanka kasancewar yasan cewa shi kadai yake rayuwa acikin gidansa,yanda yafuto haka naked shine yasa murd'ad'd'an jikinsa yafuto fili,yawan motsa jiki dayake yasa hatta cikinsa yayi wani hawa-hawa kamar wanda yake dambe,balance din daya samu shine yabawa Abunsa damar tsayawa qyam. (=H)

Ingarman matashi me jini ajika,yanada kimanin shekaru ashirin da takwas wanda girman jikinsa ya6oye shekarun nasa,yanada sexy eye's kamar mejin bacci,jikinsa jikin girma ne,yanada faffad'an qirji, yanada skin me kyau kalar wankan tarwada wadda take shining najin dad'i dakuma hutu.
Wayarsa dake ajiye akan gado tafara ringing,ahankali yajuya manyan idanuwansa ya kalli wayar,idonsa ya sauka akan sunan me kira wato MAMA, duk da cewa fuskar sa batada walwala,lokaci d'aya fuskarsa tasake dinkewa zuwa baqin ciki sakamakon ganin kiran wayarta,ransa yayi baqiqqirin cikeda tsantsar baqin cikin ganin kiran nata,ahankali ya lumshe idonsa ya bude yanaso ya daidaita nutsuwar sa,yanajin yanda wayar take qara ahaka har wayar tayi tagama ringing bai dauka ba.
Cikin rashin fara'ah yake shiryawa cikin tsantsar aji dakuma qwalisa,atarihin rayuwar sa bai ta6a soyaiya ba,bai ta6a furtawa mace cewa yana sonta ba, asali ma shi tsoron matan yake.

yadauki tsawon lokaci yana shiryawa yagoge can ya gyara can,iya gyaran sumar kansa ma kadai saida ya 6ata lokaci,cikakken d'an qwalisa ne dakuma gayu,idan ya dauki wanka da gayu saika rantse ba d'an asalin qasar Nigeria bane,sosai qananun kayan jikinsa sukai masa kyau saide fuskarsa ce babu kyau domin kuwa a daure take babu walwala akanta, gefen kunnansa guda daya na dama ya sakala masa d'an kunne,yazuba hannayen sa cikin aljihun wandon sa yafuto daga dakin yana zuba wani uban qamshi na turaruka kala-kala, babu yanda za'ai ka Kalle shi kace shidin musulmi ne, kokadan yanayin shigar sa batayi kama data musulmai ba.


Cikin takunsa na jajirtacaccen namiji kuma Ingarma yafuto daga gidan nasa, driver yadaukeshi suka tafi wajan aikinsa.
Suna qarasawa kamfanin dayake aiki yayi sauri yafuto yabude masa mota,cikin sauri dakuma takunsa na qaqqarfan namiji yashiga cikin kamfanin, yanda mutane da dama suke rissinawa suna gaidashi da girmamawa hakan ne zaisa kasan cewa ba qaramin mutum bane acikin kamfanin.

Saida yasaka tafin hannunsa ajikin wata na'ura dake manne agaban office dinsa, kafin qofar office din ta bude yashiga, daddad'an qamshi dakuma sanyin esi yadaki hancinsa,cikin sauri wani ma'aikaci dake tsaye abayan sa yayi sauri yashigo cikin office din yakara wata na'ura akan kujerar da'aka tanada domin me office din, saida yagama caje jikin kujerar tas ya tabbatar babu abun cutarwa sannan yakoma gefe ya tsaya.

Ahankali mamallakin office din ya qarasa kan kujerar ya zauna yana fuskantar tangamemen enlargement din photonsu shida Kaka da kuma yanbiyu,sunyi bala'in kyau sosai a photon,har yanzu fuskarsa a daure take, zaka iya cewa wani abun aka masa saide bahaka bane tsantsar shegen miskilancine dayake damunsa, ma'aikacin dake tsaye agefe ya kalla cikin muryar sa mai cikeda aji yace"Coffee"

Cikin sauri Yajuya yaje yakawo masa coffee din,saide kafin ya ajiye masa saida yasaka na'ura yaduba ya tabbatar babu abin cutarwa acikin coffee din, sannan yabashi.

Hannunsa kawai ya kad'a masa alamun zai iya tafiya, cikin ladabi ma'aikacin yajuya yafice daga office din, shikuma yafara shan coffee din ahankali kamar bayaso, yayinda hannunsa na hagu yabude computer yana shafata cikin wani irin salo na qwarewa da tsantsar sanin makamar computer.

HAFEEZ M. BABA kenan,cikakken madatsin na'ura, ya qware sosai a Fannin datsar na'ura komai tsaronta kuwa, mu'amular dayake da mutane masu harkar shige-shigen waya da computer hakan yasa yakeda mutuqar wayo,yanada kaifin basira da zurfin tunani,wannan dalilin yasa ya kawowa kamfanin nasu cigaba, har suka sake bude wasu sassan a Nigeria,matashi me jini ajika, ma'abocin yawan motsa jiki, yanda yake yawan motsa jikinsa hakan yasa jikinsa ya murde ta yanda ko suit yasaka zaka hango yanda dantsan hannunsa da jikinsa yake a murd'e, inde bashida aiki to zaka sameshi a dakin motsa jikinsa yana dambe shi kadai yana faman daga qarfe me mutuqar nauyi.

Yayi nisa cikin aiki a Computer vedio call yashigo cikin computer tasa, muhinmancin masu kiran ne yasa yadauki kiran batare da 6ata lokaci ba, lokaci daya kyakykywar fuskar yanbiyu suka bayyana a screen din computer tasa,duk da yagansu cikin kwanciyar hankali kamar yanda yakeso hakan baisan fuskarsa ta washe tayi annuri ba.

Husna ce tafara magana tace"Good Morning Yaya...."

Bai bude baki yayi magana ba sai kansa daya gyada mata tareda daga mata hannu,Hassan tasaki murmushi tace" Yaya ansaka mana date din sauka a islamiya,kuma taro za'a yi sosai, za'a gayyaci manyan mutane, governor, sarki, masu Unguwa da Sauran baqi, sannan Yaya kowa YAYANSA da BABANSA da MAMA...."

Lokaci d'aya annurin fuskarsa ya 6ace 6at, ransa ya 6aci, saboda sunan MAMA data ambata,baisan jin sunan kwata-kwata.
lokaci daya Hassana da Husna suka fahimci sauyin yanayin nasa,sun Riga sun San cewa sunan MAMA dasuka Kira shine yasa fuskar tasa tasake dinkewa, cikin sauri Husna ta kawar da zancen cikin d'ari-d'ari da shakka tace" Yaya kaima da zakazo da zamuji dad'i...."

Cikin mamaki yake kallon qannan nasa,yanaso yace tunda ga Kaka nan meyasa dole sai yazo? tunda ga Kaka nan meyasa zasu kawo maganar MAMA da BABA? shin Hajiya Kaka dakuma shi basu wadatar dasu ba kenan? saide kafin yayi magana Hajiya Kaka dake zaune agefe tanajin duk abinda yake faruwa ta daga murya yanda zai iya jiyota tace" mezai hana yazo kuwa? ai shine ma zai rigamu zuwa wajan Saukar,Hafeezu ai dashi za'a bud'e taro da Addu'ah"(=)




Complete document 1k



8621296018
Amina Muhammad
fcmb


Kokuma katin mtn ta wannan number 08033300034, tareda shedar biya ta wannan number 08033300034







Amnah El Yaqoub
'<
[5/23, 11:40 AM] El Yaqoub: =ؘMATAR ABBANA=ؘ
(Luv Story)



Writing By Amnah El Yaqoub

Kuyi following WhatsApp Channel dina domin samun sababbin update=G<
https://whatsapp.com/channel/0029VbBR7naJ93wTuOypQV45


4


Shiru yayi yana sake kallon screen din computer ko zai hanqo Kaka domin yahada ido da'ita kafin ya tattara amsar dazai bata, saide ko second goma baiyi ba kira yashigo cikin wayarsa dake ajiye agefe, zuciyarsa daya ya kalli wayar, yanzun ma de Sunanta ne yake yawo akan screen din wayar tashi, ba kowa bace face MAMA.
Ahankali yasaka lallausan hannunsa yakashe vedio call din dasuke yi, sannan yamaida kansa jikin kujera ya lumshe idonsa yanajin yanda qaran wayarsa yake tashi ahankali amma ya gagara daukar wayar,mezata fada masa? Meyasa take kiransa?, lokacin daya ta6a daukan wayarta bisa kuskure yanajin muryarta ya birkice yashiga damuwa a ranar wuni yayi cikin baqin ciki.(=F)

Yana cikin wannan halin akai nocking, batare daya bude idonsa ba yabada umarnin shigowa cikin office din.
Babbar mace kamila a fuska,me kimanin shekaru arba'in dawani abu tashigo cikin office cikin shiga ta Alfarma dakuma takun iya duniyanci da salon daukar hankali,fara ce sosai, hamshaqin wuyanta wanda babu ko digon qashin wuya yacika da sarkar gold, haka yatsun hannunta cike suke da zoben gold saide hannun nata kana gani zaka tabbatar da cewa farin nata bana Allah da Annabi bane.

Cikin murmushi ta qarasa inda yake,ta zauna akan hannun kujerar dayake zaune, batare da tantama ba tadora hannunta akan kafadarsa ta hagu tana shafa murdaddan dantsan hannunsa cikin wani iri Salo tace"waye ya ta6a min Hafeez dina?"

Lokaci d'aya yaji muryarta,dama yana cikin damuwa gashi itama tazo zata sake sakashi acikin tata damuwar,kokadan bayason ta, yarasa Yaya zaiyi da'ita, tabi ta maqale masa, kai tsaye babu 6oye-6oye tafuto ta nuna masa cewa so take su dinga yin soyaiya a aikace, shikuma bazai iya hakan ba saboda yana Alfahri kasancewar sa Virgin ya zauna a saurayinsa harsai lokacin da zaiyi aure tukunna,yanayin jikinsa kadai mata suke kalla su liqe masa, yarasa meyasa.
Ganin yanda take matsa masa hannunsa cikin salon yaudara baice komai ba hakan yasa tasaka dayan hannunta tana shafo faffadan qirjinsa kasancewar baigama rufe botir din rigar jikinsa ba, tayi qasa da muryarta zuwa setin kunnansa cikin Salo irinna mata yan duniya tace"zaka bani dama domin in kawar ma da wannan damuwar ne Hafeezzzz....?"

Tafadi hakan tana Jan sunansa cikin salon tada sha'awa,wani irin abu yaji yana masa yawo acikin jikinsa, yaji numfashinsa yana neman sauyawa sakamakon nipples dinsa data riqe guda daya tana murza masa shi, kafin yayi magana wayarsa tasake daukan qara,ahankali takai dubanta zuwa wajan wayar tasa, lokaci daya taga Sunan MAMA yana yawo a fuskar wayar, asanin datayi dashi, tun lokacin datake bibiyar sa tana yawan ganin kiran wayar Mamansa amma batasan meyasa ba ko kad'an baya dauka, tasaki murmushi sannan ta kalleshi cikin kissa tace"meyake faruwa ne tsakanin ka da Maman ka?"

Lokaci d'aya annurin fuskarsa ya dauke 6at, yadawo hayyacinsa daga abinda take aikata masa, cikin zafin nama ya daga mata hannu alamun

Please Login or Register in order to submit comment