Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register


Downloaded from GNOVELS.COM.NG




This Novel is downloaded from https://GNOVELS.COM.NG
to download more hausa novels visits our site at www.GNOVELS.COM.NG

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/gnovels

Twitter : https://twitter.com/gnovels

Telegram : https://t.me/gnovels

ο»Ώ[8/31, 3:39 PM] Nana BMB: πŸ€πŸ’žπŸ€πŸ’ž
RABON KWADO....
BOOK 3
πŸ’•πŸ’•πŸ’•πŸ’•πŸ’•
NA NANA BMB.
πŸ’žπŸ’žπŸ’žπŸ’ž
BISMILLAHIRRAHMANIR RAHIM.
🀍❀️🀍❀️
page 1 -2
Shirune yakasance a parlour din domin kowa dahalinda yashiga cikin yanayi me tsanani mummy tace shin yaya menene wannan dalili dazesa kahana mujaheed auren meenal?
Shiru be tankataba,
Muhammad cikin wani yanayi yataso shima yazauna gefen mujaheed wanda yakejinshi kamar ba aduniyaba saboda tsananin tashin hankalinda yashiga,murya a raunane muhammad yace daddy kayi hakuri katallafawa farin cikinsu kada kayi musu haka suna kaunar juna daddy tunda yafara maganar daddy yake zuba masa wata muguwan harara.
Ganin daddy bazeyi magana bane yasashi kama hannuwansa yana cewa ina rokonka daddy kada kayi haka na tabbatar mujaheed zebata farin ciki har karshen rayuwarta,
Cikin tsawa daddy yace, MUHAMMAD KAENE MIJIN MEENAL!karigada kazamo miji agareta mijibincinta arayuwa!
To me karatu kowa poster yay a cikin parlour dinnan nepa din kowa seda tadauki, shikuwa mujaheed hannu biyu yasa yadafe kirjinsa saitin heart dinsa yana kallon daddy cikin firgita,
Galala da baki muhammad yace daddy kamar yaya? banganeba kamanta ni yayan meenal ne?
No muhammad yau komae zezo karshe tunda haka tafaru kacire wannan aranka daga yau domin kae mijine agareta,
Wata irin mikewa auntie tayi cikin firgici tace " WHAT" daddyn muhammad kasan mekakeson aikatawa kuwa? daddy beko kalletaba, Inna tafara salati tana sallallami yanzu dannan saboda danka zaka hana mujaheed yarinyar nan wani irin haline wannan kuma kake shirin daukarwa kanka?
Mikewa yayi yacewa da inna ina zuwa yanzu,
Koda yahaura sama befi yan mintinaba yasauko daukeda wani dan box me kyau yazo yazauna zuciyan auntie jitake kamar zata faso waje saboda tsananin bugun datakeyi mata,
Yar akwatun yabude yaciri wato farar takadda aciki yabudeta koda zefara karantawa seda yadago yakalli kowa yaga yadda suka maidashi TV kae tsaye yasoma cewa..
SHEKARA TA DUBU BIYU DA SHA UKU GA WATAN BAKWAI RANAR JUMA AH DUNMIN AL UMMAH SUKA SHAIDA DAURIN AUREN MUHAMMAD DA AMINA BISA SADAKI DUBU HAMSIN A BABBAN MASALLACIN JUMA AH, LIMAMIN MASALLACIN MALAM SHEHU IBRAHIM SHINE YAJAGORANCI WANNAN AUREN, ALLAH UBANGIJI YASANYA ALBARKA ARAYUWAR AURENSU.
Jisukae yaraf mimi tayanke jiki tafadi asume itakuwa auntie tundaga zsaye tayi zaman dabaro saboda tashin hankali mummy ce tayi gun mimi tana salati itada innah itakuwa nana saboda rudu batabi takan mimin bah ta isa gaban daddy tana cewa yanzu daddy duk wannan shekarun meenal tanada aure kenan?
Daddy be kulataba sema ruwa daya dauka ya guntsa abakinsa yaje yasoma fesawa mimi ahankali kuwa taja wani dogon numfashi tasoma bude idanunta tana wani marayan kuka mikar da ita daddy yayi yakamata yaje yazaunar da ita gefen muhammad wanda shida mujaheed dukansu sunyi suman zaune, kudi yaciri cikin akwatun yadanka mata yace meenal ga sadakinki nan daga rana irin ta yau muhammad mijine agareki wanda badon komae nahada auren nan nakuba sedan nawanke zargin da wasu mutane sukemin akanki.
jada baya mujaheed yafara yana girgiza kae yana karanto duk addu ah datazo bakinsa ba abinda yake tunawa se abinda ya aikatawa mimi a garden din gidansu, mimi na kuka tace daddy taya aure ze hallata tsakanina da yayana meyake shirin faruwane? kafin tarufe baki shima mujaheed yasome ya mimmike akayi kanshi shima se ruwa ake antaya masa amma ba alamun motsi atare dashi daddy yace sukamashi atafi hospital muhammad dukda jikinshi yana rawa haka yatemaka akasa mujaheed a mota mummy tanata kuka haka mimi a sukwane muhammad yaja motan suka tafi,
auntie tana zaune takasa ko motsi se nanace takula da halinda take ciki ta isa gareta tariketa tana girgizata auntie menene yasameki sam bata fahimtar me nana kematama,
Kallonsh mimi kawae take gaba daya al amarinnan ya cukwi kwiye mata kwanya hawayene keta ambaliya a idanunta tabbas tana cikin tsaka me wuya gaskiya takusa yin halinta cikin zuciyanta tana cemewa meenal kina cikin wani hali kina kaunar yousep sedae ayanzu kedashi sedae kallo daga nesa, koda muhammad yafado mata arae kukanta yakara kwacewa cikin zuci tana cewa nashiga ukuna ni mimi yazanyi da wannan bawan allah wata zuciyan tana cemata kawae ki gudu gidanku kome ze faru yafaru....


TAKU A KULLUM NANA BMB.


08147110349
[8/31, 3:39 PM] Nana BMB: πŸ€πŸ’žπŸ€πŸ’ž
RABON KWADO....
BOOK 3
πŸ’•πŸ’•πŸ’•πŸ’•πŸ’•
NA NANA BMB.
🀍❀️🀍❀️
page 3-4
Suna zuwa hospital aka soma bawa mujaheed temakon gaggawa seda awanni biyu suka shide tukunna yafarka yasoma kuka kamar karamin yaro muhammad yana gefenshi yarike masa hannu nujaheed cewa yake meyasa allah ze jarabceni da aikata laifi ya ubangiji kaga zuciyata kagafarceni, muhammad kayi hakuri kayafemin dumin matarka dana faraji kayi hakuri kallonshi kawae muhammad yake yarasa gane inda magan ganun mujaheed suka dosa dob basosae yake iya ganewa ahalinda yake ciki yanzu, hawaye yasoma share masa yana cewa babu laefinda da ka aikata my sweet broda kadena kuka ka kwntar da hankalinka indae masoyiyar kace zaka sameta saurin girgisaamasa kae yayi yace no muhammad kada ka kuma farta wannan maganar ko bayanraena kasaki meenak ban yafe makaba abinda daddy yayi yay daedae kuma ina goyon bayanshi,
Shiru muhammad yay masa akan maganar yanata rarrashinsa shikuwa inya tuna da abinda ya aikatawa mini a garden seya rintse ido zuciyanshi tana masa zafi yanzu matar muhammad ya lalube gaskiya kam yay asara,
Se aka sallameshi suma tafi gida mummy koda taga lokaci daya yadda dan nata yakoma inaga nan gaba tasoma zubar hawaye tana matukar tausayin dan nata, dama yau bamagar dinner kowa takae takae seda aka dawo sallar ishah ne baba yace kowa ya hallara a parlour zeyi magana, auntie taci kukanta takoshi tana ganin kuma takama ranar tonin asirintace sam bata taba tsammanin daddy zeyi mata hakaba arayuwa, seda kowa ya hallara a parlour baba yay gyaran murya yadora dacewa...
Ita rayuwa dum ayadda tazowa mumini hakuri yake ya ansheta duk wannan abun daya faru makkadarine daga allah shekara kusan shidda kenan da auren muhammad da amina zuwa bakwai dalilin yin wannan aure kuwa shine, zariginda mutane sukeyi masa akan amina wasu suna ganin amina 'yarsace tacikinsa shiyasa ya yanke wannan hukunci cikin masu zarginsa kuwa harda matarsa maryam mun boye batun aurenne smse muhammad yakara mallakar hankalin kanshi ya isa rike iyalanshi tukunna kuma ALHAMDULILLAH, Yanzu anyi abu akan gaba komae yau yazo karshe,dubanshi yakae kan mimi yace amina nasan zuciyanki ciki take da rudani to amma kiyi hakuri ki fawwalawa allah duka lamarinki maganar gaskiya marainiyaceke abubakar rikonki yayi kuma kigodewa allah daya hadaki da marika nagari kicire komae azuciyanki kiringumi mijinki kibisi sauda kafa, allah ne kadae yasan nufinshi yasaka kaunarki azuciyan mujaheed, inaso kaima mujaheed kayi hakuri karumgumi kaddara dadage da addua ah allah ya saukaka maka abinda kakeji azuciyanka sannan ga kanwar kanan nana indae zuciyanka ta aminta da ita munkaba ita sedae bazamuyi maka auren doleba, wata zabura mimi tayi zata mike caraf suka hada ido da muhammad yana mata wani irin kallo dole tagyara zamanta dama yana facing dinta sabida haka taki dagowa seyanzu hawaye kawae ke bimata fuska yanzu tanaji tanagani ua ah rabata da mujaheed abin kaunarta wanda saboda shine taki furta gaskiya akan kowacece ita,
Itama nana a kidime tamike jin furucin kakan nasu datayi daddy kuwa yadaga mata hannu takoma tazauna tana hawayen takaeci mujaheed kansa a sunkuye tunda suka zauna yace duk hukuncinda kuka yanke akaena daedaene banida zabi ayanzun baba yay murmushi yace yayi kyau allah yazaba maka mafi alkhairi arayuwarka suduma sukace ameen,nasihohi yashiga yiwa mimi da muhammad mussamman shi kan cewar yarike marainiyar allah tsakaninshi da allah kada yabasu kunya yakuma amince, tambaysrsu yay inda wanda yakeda abin cewa se a lokacin mummy tabawa daddy hakuri akan haushinsa data faraji ayanzu kuma tafahimceshi,shima mujaheed haka yabashi hakuri yace abinda yay daedae ne yana goyon bayan hakan kuma yaywa muhammad addu ah zaman lpy shida matarsa, sosae daddy yaji dadin hakan da mujaheed ye fuskanceshi ,
Hka taron yawatse kowa yanufi makwanci yana sake sake azuciyansa kotakan auntie daddy bebiba yaje yasama kofansa key don karma tashigo tamasa shirme,
Mujaheed yakasa bacci haka muhammad kowa da abinda kemasa ciwo a zuci to bangarensu mimi hakan take kowacce tana matsar kwalla taya zasuga samu suka rashi koma meze faru mimi taci alwashin bazata bari a rabata da mujaheed bah, to wannan kenan
WASHE GARI
Duka gidan babu wanda yatashi dawuri da alamu daren jiya babu wanda yadamu ishasshen bacci,.
Koda karfe 1 taharba su mummy sungama shirinsu tsaf natafiya bauchi mimi taki fitowa tace batada lpy harsu ka tafi bata saukoba muhammad bekuma bi takantaba yacigaba da sabgarshi da la asar shima yakae daddy airport don yaune zewuce dubae shima, jiki na tsuma nana takira mardiyya tasanar mata duk abinda yake faruwa tasoma rabka salati tasa kuka daga tsaye tasaki wayan saboda dimuwa ta tawarwatse,nana wayan meenal tasoma bincike acikinta daedar nan kuma mimi tafito awanka nana tae saurin aje wayan takwanta da ido mimi kawae tabita,
Da daddare mimi tana kwance abin duniya ya isheta nana tace yanzu meenal yazakiyi da yousep kenan? mimi bata ko kalletaba bare ta tankata zuwa yanzu tasoma sabawa ma da wannan iskancin na mimi seda takuma tambayarta anan tace mata nabar mikishi,nana tai shiru batae tsammanin jin haka daga bakintaba basarwa tayi tace to wae ayaushene kuka fara soyayya da ya mujaheed bamu saniba?mimi tagaji da tambayoyin nan na nana ga halinda take ciki cikin jinhaushi tace nafara sonsane asanda nagono kina son ya yousep cikin cikin jin haushi nana tace to ubanwayace miki ni inasonshine?dukda halinda mimike ciki behana tayin murmushi ba tace am sorry yaya namanta ay kincewa su daddy kinada wanda kikeso shikenan shizan zaba masa mata wadda ta dace,
Nana tayi murmushin bakin ciki tace to matar ya muhammad yazakiyi da mardiyya masoyiyarsa natabbatar yanzu tana hospital bayadda banyi dakeba kidena biyewa mardy komae nashi kina gaya mata ashe sirrin mijinkine kike barbada mata kinyi kunnen uwasshegu da abinda nake gaya miki aihmga irin tanan harda cemin kinyi alkawarin seya aureta inzuba ido insha kallo ido yanzu nasoma zubawa ma, sam mimi taki tankata don takasa gane inda maganarta tata ta dosama, wayar nana ce tayi ringin koda taga mekiran nata kuwa tasaki dariyar mugunta tana dagawa yace turomin yarinyar nan tasameni a garden kit ya yanke wayanshi, nana tace sabon salo yaukuma sweetien ce tadawo yarinya kallon mimi tayi tana dariya tace to ke gareki mijinki yace kisameshi a garden cikin kidima mimi tamike tasaki kukan tausayi tace narokeki yaya kice masa nayi bacci,
Nana takuma bushewa da dariya tace narasa yaushe ya muhammad yazama dodonki dabaki kaunar zuwa inda yake mimi takuma cewa narokeki yaya mikewa itama nana tayi tace wlh bazan gaya masaba kinsan yanzu zeshigo yakama zazzaga masifa kitashi kawae kitafi abinki yarinya garama kiriki mijinki shene mafi a ala agareki,mimi jitake kamar taringa falla mata mari suna cikin jayay yakuma kiran wayan tana dagawa yace bata wayan, takuwa saka mata akunne don tasan bazata amsaba cikin hassala yace shin zaki zone ko kuwa inzo in sameki dakaena? koda taji hakan bata jira komaeba tasuri hijab tafice,.
Ayanayinda tahango muhammad ne yakara sawa zuciyanta ta karaya tajuma a tsaye sannan yace zamanne bazaki iyabane?haka dae tasamu tadan dosana agefenshi kasa yay da voice dinsa yace kinason mujaheed? tayi saurin daga masa kae tace ina sonsa inna rasa shi bansan ya rayuwata zata kasanceba,muhamammad yay murmushi yace good zakuwa kisameshi amma idan kika fadamin gaskiya kifadamin abinda yake faruwa shin wacece kene kuma ina matata take kiyimin bayani harta daddy yasoma tantama akanki cikin zubar hawaye tace yanzu nan yaya baka yarda dani harseda ka gayawa daddy,shiru tayi tana tunanin gidansu tabbas tasan yanzu bikinsu yakusa itada bassam muddin tayadda takoma kodame take yawo se abbansu ya daura arennan kuma abind babazata iya juraba kenan bazata yadda takoma gidaba tana fada masa gaskiya tofa gidansu za ah tafi ita yazatayi yanzu katseta muhammad yakuma yi da tambayarta, cikin wani irin yanayi tace meyasa wae ka kasa aminta danine muhammad yay murmushin mugunta yace sorry my wife nadena miki wani tunani dama ina cikin yanayine nakirakine domin kisani cikin shauki yanzunan idanunta kamar zasu zazzago tadago tana kallonsa ido cikin zubar hawaye tace nibansan mezanyi makaba kayi hakuri, seda yagama nazartatta tukunna yace kiss me! saurin barin gurin tayi tamike tsaye tana girgiza masa kae hannu yasa zedawo da ita inda take takara jada baya cikin daure fuska kuwa ya fisgota taizaman dabaro harseda taji zafi tarintse idanunta, i said kiss me yakara gaya mata mimi tasaki kuka tace wlh yaya bazan iyaba meyasa zakayi min haka,
muhammad yajinjina kae yace ok naji bazaji iyaba namiki uzuri yanzu nasan kinajin kunyata amma gaba zakiyi nasan tashi kitafi ciki abinki,tamike jiki nabari kuwa tai cikin gidan yakuma kiranta kamarta kurma ihu ta juyo yace shiga bedroom dina ki daukomin wayata yanzu ina jiranki kada kuma kibatamin time sanyi mimi taji azuciyanta tashiga ciki harda gudunta muhammad yasaki murmushin kyeta yace yarinya kenan yau zakiyi bayani don wlh yau sekin fadamin gaskiya zan kyaleki donnaga kinada taurin kan masifa mikewa yay yarufa mata bayashimaπŸ‘€...


TAKU A KULLUM NANA BMB.


08147110349
[8/31, 3:39 PM] Nana BMB: πŸ€πŸ’žπŸ€πŸ’ž
RABON KWADO....
BOOK 3
πŸ’•πŸ’•πŸ’•πŸ’•πŸ’•
NA NANA BMB.
🀍❀️🀍❀️
page 7-8
Auntie tana cikin waya taga nana ta fado mata daki a firgice da mamaki ta kashe wayan tana kallon nana tace lafiyanki kuwa? cikin kuri kuri da ido tanata haki tace wlh auntie meenal aljanune suka shigeta nifa tun wannan tafiyar datayi gaba daya meenal tasauyamin gayamikene kawae banba kullum cikin baccinta inajin tana wani yare to wlh yanzu harshen natama yajuye se hauka take ita kadae nidae bazan iya kwana a dakinba wlh wae seta auri ya mujaheed tanata hauka, cikin tsananin farin ciki auntie tamike tasoma babbaka dariya harda tafawa sannan tace zokiyi kwanciyarki anan nana aljanun su haukata ta itakadae ninasan abinyi yikwanciyarki kinjee nana jiki a sanyaye tahau kan makeken bed din na auntie takwanta tae tsumu mamakin mimi gaba daya yahanata sakat,
WASHE GARI
Nana dakyar ta iya tunkarar dakin nasu tana tsoron kada mimi ta danketa shahada tayi ta tura kofan ahankali tashiga dae dae lokacin kuma mimi tafito daga wanka idanunta sunyi luhu luhu saboda kuka ko inda nana take bata kallaba tazauna gaban dressing mirror tana mutsika mae duk abinda nana take tana ankare da ita sedae taki kallon inda takema, wankan nana tashige itama abinda haka zalika koda sukazo breakfast su hudu a dining nana se kallon mimi take takasa cin nata abincin haka itama mimi yanayin datake ciki yasa takasacin komae, gyara zama muhammad yay yana murmushi yakalli mimi yace my wife kici abincin mana haba kinsan banason damuwan nan naki ina tare dakefa akowani lokaci so kada kikara sama kanki damuwa kinji kodae dakaena kikeso in baki? daga mimi har nana baki sake suke kallonsa saboda yadda yay maganar shagawaba, harda kanne mata ido daya,wani dogon tsaki auntie taja tana antaya musu harara,lura da hakan da yayine yasashi gyara zama yace yawwa inaso natambayeki dama shekararki nawane yanzu?cikin sanyinta mimi da mamaki kuma tace 18 years WOW kinga kingirme 6ter dinki ita tana 17 yanzu mimi tayi murnushi jin yadda muhammad yake mata magana ashe haka yake shine jiya harda sharara mata mariπŸ˜…πŸ˜… cikin jin dadi tace kundace kaeda matarka inayaku da murna yabaku zaman lpy gashi bantaba ganinta ba,muhammad yaji dadin addu ar tata yace ameen ya allah kada kidamu indae 6ter dinkice zaki ganta cikin kwana biyunnan, nan danan idanun mimi suka kawo ruwa tana kallonsa tana girgiza masa kae zatayi magana yadaga mata hannu yace no dolane ne fah kisa aranki wannan tafiya anyishi angama tayama zan kyale banason kukan nan naki babu abunda ze faru ki kwantar da hankalinki, kukan nana ne yasa su suka juya suduka suna kallonta ta rukumkume auntie tana cewa wlh maganata gaskiyace ashe ba meenal bace aljanune ashe ya muhammad ma yasani jiya inajinta tana sumbatu muhammad yasaki murmushi bekae karsheba dariya ta kufce masa haka mimi tana darawa tana kallon ikon allah gurin nana, dukda magan ganun nasu sunsa auntie aduhu hakan behanata dakewa ba cikin tsawa tace banason hauka nana meyake damunkine?
Muhammad mikewa yayi yace wify muje garden mukarasa tattaunawa tunda naga tunyanzu anfara tsorata haka inaga nan gaba kuma?cikin bakin ciki auntie tace to don allah daga garden din ku bulla ta China kada kudawo mana nan karamin mara kunya kaega me mata koh!
Shidae muhammad ficewa yayi yana dariya mimi tabi bayansa sebayan sun zaunane yake cemata mimi inason kigayamin gaskiya shin kece mujaheed yatabawa jikinta ko meenal ce?wata irin kunya kuwa takama mimi kanta aduke tace nice ba meenal bace, muhammad besan sanda yasaki ajiyan zuciyaba yana godewa allah a zuciyansa tanason magana takasa, seda yabudi baki zeyi maganar ne ta tareshi da cewa dama abisa tsautsayi abin yafaru yatabani badon yana...Sekuma tayi shiru,
Muhammad yasaki shu umin murmushi yana cije lips dinsa azuciyansa yana cewa shegennan bakada dama wlh ayzamu hadu, sunjima suna tattaunawa a garden din wanda hakan yakara samusu fahimtar juna yafahimci so silent ce ita amma yana mamakin yanda kowa yaki fahimta duk karadi irinna meenal.
Yau talata takama ranar tafiya adamawa duka an hallara su inna da baba mummy da daddyn mujaheed dashi din kansa harda kanwar mahaifiyar muhammad hafsa,mimi kwallace tacika mata idanu ganin mujaheed yadda yakoma a 'yan kwanaki yawani rame se 'yar fuska, daddy tinda yadawo yake kallon mimi yana kara gasgata maganar dannasa dasukayi awaya, tunda garin allah yawaye auntie taketa faman sababi da masifa da tujara akan me za ah kirkirar musu tafiya adamawa kuma aki fadan abinda za aje yowa shidae daddy ta tafasa bece mataba yamayi kamar besan tanae bah anata shirin tafiya donkosu baba da inna basusan neza ahje yowa canba,
Mujaheed suna bedroom suna shiryawa yakalli muhammad yace waekae waca irin tafiyace wannan muhammad ka kaga mana anki kuma sanar mana abinda zamuje yowa,muhammad yay murmushi yace to maida wuyar aure zamuje nema maka wani irin kallo mujaheed yamasa yace kamarya? banganeba!manta kawae to inmunje can ka gane,
Wae kuwa majaheed dakukaje bikin sameer babu abinda yafaru da meenal,mujaheed yay shiru yana tunano abinda yafaru,cikin rashin fahimta yace kamarya ba abinda sameta?muhammad yay murmushi yace ina nufin bata tafi wani gurin kunnemeta kunrasaba?mujaheed cikeda mamaki yake kallon muhammad taya akayi yasan hakan kodae meenal tagaya masa komaene kallonshi yayi yace eh bamu nemeta munrasaba ya akayi kake tambaya, muhammad yace babu komae tasowa mujaheed yay yana cewa wlh karya kake da akwae wata akasa,
Muhammad yana murmushi yace to shikenan kabar komae semunje can zaka fahimci komae basena yimaka bayani bama pls kayi kashirya kasan da tafiya agabanmu, cikin jin haushi mujaheed yace a ah tafiyace a bayanmu ba agabanmuba! muhammd yakuwa bushe da dariya mujaheed yakyaleshi yacigaba da saka kayansa,muhammad kuwa turaruka yake fesawa kala kala zuciyanshi taf da farin ciki yau zega sweetienshi shigan dayayi tamatukar yimasa kyau yasha shaddi brown light tanata zuba uban kyalli haka hukansama daya dora shikansa daya kalla kansa a mirror seda ya kanne ido daya, shikuwa mujaheed boyel ne yasaka me tsadar gaske peach color kalarda mimi take matukar kaunar soh sosae yahadu inkace zaka tsaya tantance wanda yafi wani kyau acikinsu bata time ne ma, suka fito a tare abin sha awa, mimi koda tahango sahibinta batasan dmsanda tai gunsaba tarikeshi tana murna tace ya mujaheed baka taba yimin kyau irin na yauba pls katsaya muyi selfie,zuciyan mujaheed kamar zata fado dama yaya karfin hali kawae yake koda camera tahaskasu kasa fara ah yayi seda tasaki nata murmushinne tukunna besanda sanda yay nashi smile dinva shima tabbas yabada kala wadannan couple din abinda sha awa, mota biyu sukayi abinsu ta tafiya sunbata lokaci sosae gurinyin hotuna kafin akadauki hanya kuma dodar muhammad baki yaki rufuwa....


TAKU A KULLUM NANA BMB.


08147110349
[8/31, 3:39 PM] Nana BMB: πŸ€πŸ’žπŸ€πŸ’ž
RABON KWADO....
BOOK 3

NA NANA BMB.
🀍❀️🀍❀️
page 5-6
Sam mimi bata kawo komae azuciyantaba tana shiga tawuce bedroom dinsa kae tsaye tana shiga wani ni imtatceb kamshi yadoki hsncinta harseda ta lumshe idanunta, dube dube tasoma sedae bataga wayanba sema photon meenal dataci karo dashi amanne ajikin bango kamar zaka kirata ta amsa tayi dariya bakaramin kyawu tayiba a hotun tabbas ta tsaya gaban hoton aka kalleta anan za aga banbancinsu tana duniyar tunani taji huci a gefen face dinta ta dago a tsorace suka hada idanu yasakar mata murmushi kuwa, cikin tsaraka da idanu tasoma cewa yaya wlh bangantaba seda yakarewa hoton meenal kallo sannan yakalleta yace kema kinyi mamaki koh shiyasa kika tsaya kallonta, wani irin yawo tahadiye don tama rasa bakin magana, muhammad kallonta yake cike da mamaki shin wacece wannan haka datazo tarainawa kowa hankali haka kodae fuska tasakane irinta meenal dinshi, mimi kanta yana kasa sejin hannun muhammad tayi a face dinta kamar ze yage mata fuska tasaki kukan azaba zataja baya yakuma riketa sam bega wani alamuba cikin masifa yace tell me who are you?kuka mimi kawae take taki tankashi kara matsowa yayiyace ina saurarenki cikin kuka tace bansan mezance maka ba kuma kadena min haka banaso, rintse idanunsa muhammad yay saboda takaeci da bakin ciki cak kuwa tajee yadagata bedireta ako inaba se akan bed zuwa lokacin idanun mimi zazzagowane kawae basuyiba don firgici kallonta muhammad yake kuzata saduda haka tagaya masa gaskiya amma ina sema kokarin sauka datakeyi yakuwayi mata wata fisga takifa a bed din yay mata rumfa yasoma kokarin cire mata hijab din tarikeshi gam kuwa cikin shashhseka take cewa pls yaya narokeka kayimin rae kayi hakuri ka kyaleni banaso, cikin tsananin bacin rae idunshi yay jajir yace why dazan bari aiba haramun zan aikataba so kibarni na amshi hakkina tunda kin amshe kudin sadakinki yakarashe magana gamida fisge hijab din nata takarfi tasaki kara kuwa don jitae kamar ze tuge mata wuya koda yakae hannu kan rigarta tarikeshi jikinta yana karkarwa tace pls ka kyaleni haramunne abinda kake shirin aikatawa...Muhammad se a time din yadago yakalleta da rinannun idanunsa yace meyasa ze zama haramun mimi takasa cewa komae se kuka besanda sanda yadaga hannu ya sharara mata mariba yace cikin tsawa MEYASA ZE ZAMA HARAMUN? hannu biyu mimi ta dafe gefen fuskar tata cikin tsananin kuka tace saboda bani bace meenal, koda yaji haka yasaki rigan nata yasauka daga kan bed din yana furzarda iska mezafi daga bakinshi koda yajuyo yaga harta maida hijab dinta tasauko itama tanata kuka meban tausayi don taji azaba kam cikin bacin rae yace kin fiya taurin kan masifa tun a garden naso kiyimin wannan bayanin amma kika bari harta kaemu ga haka sannan kika fadi gaskiya kin batamin rae, kuma tambaya tafarko itace menene sunanki?
Cikin kuka mimi tace sunana safiyya amma ana kirana da mimi, DUM muhammad yaji kirjinshi yabuga safiyya yakuma nanata sunan yaname zuba mata idanu jin yadda yakuma nanata sunan ne yasata dagowa takalleshi fargaba takara dirar masa saboda koda tadago ayanzun fuskan auntie safiyyansa kawae yahango a tata fuskan cikin wani irin yanayi ya lumshe idanunsa nadan lokaci kana yasauke ajiyan guciya yanemi gu yazauna sannan yakalleta yace zoki zauna, sam mimi batae masa musuba tazo tazauna zuciyanta haryanzu tana mata dancing,
Murya a raunane yace mimi ina meenal take?kanta a sunkuye tace tana gidanmu

Please Login or Register in order to submit comment