Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kai yace." Lallai ne yaranne dole"
Yajima yana knocking kafin su bude masa kofan, yana zura kai yaga usain a tsaye daganin shi yanzu yatashi, haba ya rike yace." dakyau 'yan hutu ayse a tashi haka koh, anata shiri ku kuma kuna nan kun jibge"
Hassan nadaga kan bed yajiyo maganar ta muhammad, yana murmushi yace." Ay dole tunda ango yatashi yanzu kowama zai tashi" tura kofan yakarasa yi yashiga yay kanshi hassan yamike da gudu yashige bathroom yana dariya, usain yace." mara kunya da katsaya babban yaya yayi maganinka," murmushi kawai yay yafita yabasu guri, suna azune a parlour anata hira lokacin nana tafito itama, har tazauna muhammad yana kallon ta muryanta ma baya fita sosai data gaisheshi,


" Zonan nana" shine kawai abinda yace da ita, kanta a sunkuye ta taso tazauna gefensa koda yarike hannunta zafi yaji sosai a hannun nata tausayin tane yakara kamashi murya a sanyaye yace


"Kinason yin magana da auntie ne?" hawaye ne suka zubo mata ta girgiza masa kai, hannun nata kawai yarike suka mike tsaye yana cewa "tashi muje" saurin kallon sa tayi amma se bekula taba har suka kai bakin kofah sukayi karo da safiyya,da mamaki take kallonsu tace "ina zaku haka" dan guntun murmushi yayi yace.
" Zata gana ne da mahaifiyar ta kafin a kaita gidan miji kada zafin yamata yawa" saboda duk abinda ke wakana tsakanin ta da yousep yana gani,
" Yayi kyau hakan sosai, ay nayi magana da yousep din yace yau da yamma ze turo a tafi da ita, yanzu dai rakitomin wani abu nasaka mutafi don bazan bari ku tafi ku kadai bah"
Sakin hannun nana yayi yakoma palour din sam barka yana shiga yaci karo da wani hijab yadauka abinsa yaje yakai mata suka shiga mota suka tafi su ummi basusan meke faruwa bah,
Abin mamaki suna shiga gidan suka ganshi dankam da mutane har sama suka haye safiyya kuwa tasha nuni aka fara nunata, daddy da kawu musa suka gani a bakin kofar dakin na Dr sunata bugunta amma ko gezau kofan yakiyi, da kallon tuhuma daddy yasoma binsu amma se sukayi kasa da kansu don karma su hada idanu, 'yan uwan Dr kowa yana zaune jugum jugum, cikin ikom Allah da muhammad ya tayasu bugun kofan da temakon wani karfe kofan ya budu, suduka tsayawa sukayi kallon dakin nata yadda yayi kaca kaca da glasses komai an hargitsa shi haka suka kutsa kansu ciki can gefen bed suka hangeta wanwar a kasa kamar matatta, ga ciwukan dake jikin ta jini dukya bushe, sungumar ta daddy kawai yay suka sauko kasa kowa ya hangosu se salati dakifah ya kaure wasu na kuka wasu na salati safiyya kuwa tasoma shan zagi ay matar sace tajawo ibar albarka iri iri sedai bawanda yabi takan suma nana kuwa kankame safiyya tayi tana kuka me tsuma zuciya har suka fita motar su daddy na tafiya safiyyan tace da muhammad su bisu kawai, yadata mota kuwa suka rufa musu baya, sunjima a wajen hospital din tanata kallon shi abubuwa da dama suna dawo mata, lokacin da fahaifi meenal a cikin sa itama a hankali hawaye yasoma bimata fuska kafin sushiga ciki, a office din Dr bello suka sami daddy yana masa bayanin akan halinda auntie take ciki, shigowansu ce tasashi dakatawa suna kallon su,magana zeyi tayi saurin cewa" pls kabarmu kodan nana mah" dauke kansa kawai yayi don beso zuwan su hospital din bah, zama sukayi jikin safiyya a sanyaye ta kalli Dr din tace." Ya jikin nata yanzu Dr meke faruwa da itane haka?"
Kallon daddy Dr bello din yayi, shikuma yay masa a lama daya cigaba da magana kawai,


" Maganar gaskiya tabbas Dr maryam tana cikin hadari sosai da alamu akwai abinda yamatukar firgita mata rayuwa harya so taba mata kwakwal warta domin har zuciyan ta tana cikin hadari Allah ne yay da tsawon cin kwanan ta a gaba zuciyan ta bata bugaba gaba daya, a takaice dai yanzun bazan iya shaida muku yanayin dazata farka bah zata iya yiwu wa hankalin nata ya gushe, so amma indai aikin da mukayi mata anyi nasara zata tashi lpy dayar dar Allah"
Kuka safiyya tafara tana share hawaye tana cewa " Allah sarki wlh danasan abinda ze faru dake kenan sam da bandawo Nigeria bah, duka nice najawo miki wan nan bala in" mikewa daddy yay yakamo hannun ta seda sukazo bakin kofa tukunna ya kalli muhammad yace." Taso ka kaita gida, bakuma nasan hakan yadaga miki hankali don banason wani abu yasame ki koda wasa kada nakara ganin hawayen ki a kan wan nan abinda yake faruwa"


Jikin muhammad a sanyaye yazo yakama mata hannun suka fita taname zubar hawaye, nana kuwa tana zaune hawaye ne kawai ke silalowa daga idanunta ko baki takasa budewa tayi kukan ma.
Koda suka koma gida ummi harda hara rar safiyya saboda takira muhammad yagaya mata komai dake faruwa magun gunan ta ta dauko ta bata tasha ganin yanayin da take ciki cikin damuwa tasoma cewa." Haba safiyya akanme zaki sawa kanki damuwa akan waccan azzalumar matar akan me ma zaki damu, ay dole dama bazata gama da duniya lpy bah, somin tabine wan nan bataga komai bama" da mamaki muhammad yake kallon ummi irin kalaman dake fitowa daga bakinta tun anan yasan tafi auntie safiyyan su zafi,koda mujaheed yaji abinda ke faruwa shima jikin sane yay sanyi nan danan gida kuma ya dauka da maganar,
Safiyya bata dena hawaye bah har daddy yadawo daga hospital din,anan yake shaida musu duk wanda yakeson zuwa bauchin ya shirya a tafi dashi saboda anfasa kai nana yau sakamakon abinda yafaru da mahaifiyar ta, ada yadda aka tsara biyu aka raba abin wasu suje kai nana wasu kuma suje kai mimi, kiran safiyya yayi ya kwantar mata da hankali sosai san nan tadan sami nutsuwa,
Hassan da usain da nabiha daddy cayay sutafi gidan muhammad su zauna kafin sudawo kada kuma su kuskura su sanar mata abinda yake faruwa,
Biyu da wajan rabi aka dunguma 'yan tafiya akayi bauchi bayan angama shirya amarya tsaf tanata kuka mimi domin ganin abin dai yi za ayi suka dauki hanya,da iyalan sameer dasu innah da mummy se 'yan adamawa amma badukan suba ummi da safiyya, yanata musu Allah kiyaye don shi bandashi za ayi tafiyanba,


Se yamma lis suka isa gidan su mujaheed kamar bashi bah saboda yadda yadau gyara musam man bangaren amarya ya tsaru kam ba karya su innah basu zauna bah suka sa muhammad yamaida su gidan su, dukda gajiyan da aka kwaso hakan behana su cigaba da shirya bangaren amarya bah, har seda dare yayi tukunna safiyya da mom ne suka kara yiwa amarya nasihohi masu ratsa jiki, aka soma tattara kan kowa ana komawa part din mummy ram kuwa tarike ummin tasu tana kuka dole haka suka tafi suka barta anan, itama daga karshe wayau tayi mata tace tashiga wanka, koda tashiga wankan cikin sanda tafice abinta, don bata zaunaba abin kunya ango yazo yasame ta,


Su muhammad dakin mujaheed suka sauka, ango yana gaban mirror anata kalkale kal kale yafito wanka yanata musu ibar albarka kan cewar babu wanda ze shigar masa dakin amarya shima, tsaki muhammad yay yashige ya juya yaname gyara kwanciyar sa kan bed yana cewa " aikin banza jarababbe kawai zamu ragune don bamujeba, yau dai nasan mimi tabani a gurin ka don kai lamarinka ba daga kafa, ko kunyar su ummi baji zakai bah"


Girgiza kai sameer yay yace " To Allah yakyauta maka mujaheed dama tayi maganin ka inga ta kwazzaba," murmushi kawai mujaheed yay bace musu kalaba seda yagama shirinsa tsaf tukunna yace " kwayi kwa gama nidai ai yau angona nake amarcina zanyi yanda yakamata" da pillow sameer ya jefeshi yana cewa" To mara kunya san inda dare yamaka" mujaheed yafita yanata dariya, muhammad yana jinsu be tankaba sabida tunanin abar kaunar sa dayakeyi meenal yanata zuba murmushi, abinda yawakana tsakaninsu kawai yake tunani....




TAKU A KULLUM NANA BMB


08147110349
[8/31, 3:39 PM] Nana BMB: ❣ RABON KWADO!!


BOOK 3


NA NANA BMB




GARKUWA WRITTER'S ASSOCIATION
{ Marubuta masu garkuwa da alkalami domin fadakar da al'ummah }




page 39 - 40


Zuwa lokacin da daddy ya sallami kowa, time din dare yayi sosai su muhammad haka suka nufi makwanci zuciyansu kal da farin ciki su safiyya kuwa sabuwan hira aka bude ta yaushe gamo,ummi ce tabawa hajiya labarin duka abinda yafaru da safiyya taname zubda hawaye gamida tausayin 'yar tata, nana tayi tsumu da ita don kunyar su ma takeji a yanzun bata iya furta komai sedai zubar hawaye,
Wan nan dare basuyi bacci ba kam ummi farin ciki ya isheta jitake tafi kowa sa ah yanzun wai yau gata ga 'yar uwarta! Allah kenan, sunata fira cikin farin ciki har akayi sallah asuba kowa kuma ya dakufa bacci bah.


To me karatu fada ne kuma yake shirin kaurewa tsakanin dangin auntie dana daddy, sam anata buga kofa auntie taki bude kofa juyin duniya taki koda magana, harzuwa wan nab lokaci rana ta hantse, danginta daddy suka dorawa laifi cewar ay komaeye yasameta shine sila shiya jawo komenene don be mata adal ciba ay munafur tatta yayi donme zeyi mata haka, kasancewar suna goyon bayan 'yan adamawa ne yasa abin yakara harzuka su, mussam man matar yayan auntie tafi kowa zakewa da rashin mutumci akan me anyi mata ba dai daiba kuma 'yan uwansa sunyi shiru ko ajikin su abin bedame suba seta kira iyayen ta tasanar musu,
Duka kuma bawanda ya kulasu shi daddy sammakon barin gidan ma sukayi, se su mummy da inna kuma bawanda ya sauraresu, To azhar nayi kuma aka soma jidar mutane zuwa gidan safiyya inda za ayi walima,abin mamaki ga gidan nata gana muhammad dukansu sun hadu babu karya, koda mutum daya a cikin 'yan uwan Dr bawanda yaje sunata ikirarin cewa wan nan ma ay cin mutumci ne, koda aka kira yayan na auntie ya shaida musu cewar kada wanda ya kuskura ya kira iyayensu yadaga musu hankali kome yasamu maryam itace tajawa kanta kada ma wanda yakara kiransa karshema kashe wayansa yayi gaba daya,
To gashi kuma Dr haryanzu taki bude kofah!


Gidan auntie safiyya kuwa anata shagali ana shirya amare cikin wasu lafiyayyun abaya, koda wasa meenal taki yarda su hadu da muhammad, wanda shikuma nemanta yake ruwa a jallo, seyanzun da dole gurin zama ya hadasu bayadda zatayi, ram yarike mata hannu kuwa yana tuhumarta itakuwa takasa dagowa mah saboda bayan kunyar data addabe ta mah harda tsoronsa dayake kara linkuwa a zuciyanta har yanzun tagaza yarda wai ya muhammad mijinta, mamakin shi yaki barinta akan abinda yamata ashe ya muhanmmad haka yake! 😀yanzu shine yake mata wan nan magan ganun dasuka fi karfin kanta sam jitake kamar mafarki take duka wan nan abinda yake faruwa,


'yan uwan youseep suma sunzo dama su nadiya sune amarori, shikuwa gogan mom ce tasawo shi agaba ta taso keyar sa suka taho tare, ba mom ba har shi daya kalli nana seda tabashi tausayi yadda takoma, sedai ji dakai yahanashi koda kulata mah, ana tashi bejira suba yabawa motar sa wuta yay gaba, hakanne yakara sawa zuciyan nana karaya takasa dena kuka seda safiyya ta rarrasheta sosai tukunna tasamu tadan sawa cikinta wani abu tasha magani saboda ciwon da kanta yakeyi.


Zukatan kowa cike yake da farin ciki da kauna a wannan gidan, murna da rawar kafa gurin angwayen biyu ba ah magana


WASHE GARI


Yau take lahadi! za ah mika meenal dakin mijinta tunda ta tashi takejin ta sukuku jikinta yayi sanyi sosai kiris take jira a zungureta tasoma kuka tawani lafewa safiyya ajiki, shikuwa muhammad tunda suka tashi mujaheed yasa shi a gaba da tsokana kan cewar yau yake ango.
Fuskar mom dauke da murmushi tasami meenal da mimi tana shaida musu cewar ay zarah itada iyayenta suna kan hanyar zuwa donma wani uzuri ya rikeso da tuni sun nan ana shagali dasu, bakaramin farin ciki mimi tayiba saboda tasaba da zarah sosai tanata zumudi,


Su muhammad sun tafi raka abokansu na nesa airport, 4 da 'yan mintuni kuma motar su zarah tayi parking a gidan na safiyya a time din kuma motocin Abban su mimi suka parker, yazo gidan domin yin sallama dasu yau ze wuce saboda uzurin da yake dashi,
Mahaifiyar zarah dince tafara fitowa acikin motan, hamshakiyar mata ce meji da kudi da class tasoma takunta cikin takama da izzah, se su zarah itada inty dasuka take mata baya yanzun, inty itace taje taho dasu gidan saboda basusan shiba, baban na zarah ne yafito daga karshe a mazau nin driver, abin mamaki koda suka zo shiga ciki securities din Abban su mimi, hanasu shiga sukayi hakanne yasa maman ta zarah juyowa tanawa Abban kallon mamaki, wanda shima hakanne take, cikin wani irin yanayi yake kallon su da matukar mamaki hannun sa har rawa yake ya daga waya yakira daddy awaya,
Batare da bata time bah daddy yafito, sedai koda ganin abinda yay arba dashi yasashi yin turus a tsaye yana wani irin yamutsa fuska kamar yaga kashi, zuwa wan nan lokacin maman zarah tasoma kufula cikin fushi tasoma tambayar daddy lpy ne meke faruwa? sedai sam be tanka mata bah illah iyaka ma hankalinshi yana kan mijinta bama jinta yake sosai bah, jawo kofan daddy yayi ya isa gabansa yana me yi masa wani irin kallo na kaskanci da rashin mutum ci, finger dinsa guda daya yasa ya nunasa ya ambaci sunan sa


" Imam!
Menene yakawo ka gidan nan? akan wani dalili mah zaka zomin gida taya yama!" daddy yana maganr ne cikin wani irin fushi da kunan zuciya, se a lokacin Abban ya karaso inda suke tsaye yace." Yazone domin yakara haddasa mana wata masifar a rayuwar mu, domin zuwan wan nan butulun gidanka sam ba alheri bane,"
" Inafa ze zama alheri!"
Daddy yay maganar yana kallon Abban, jikin imam a mugun sanyaye yace.


" Alhj Abubakar!" koda ya furta sunan daddy kukane yakwace masa yana me cewa." Tabbas kaine nashafe tsawon shekaru ina nemanka seyanzu Allah yahadani dakai, saboda nasan babu makawa kasan inda matata safiyya take....




TAKU A KULLUM NANA BMB


08147110349
[8/31, 3:39 PM] Nana BMB: ❣ RABON KWADO....!!


BOOK 3


NA NANA BMB


GARKUWA WRITTER'S ASSOCIATION
{ Marubuta masu garkuwa da alkalami domin fadakar da al'ummah }




page 41 - 42


Tassss! kakejin daddy ya kwadawa imam mari, cikin karaji yace." Wannan yazama nafarko kuma nakarshe dazaka kira safiyya matarka kagane koh!
Wani irin kallo imam yake watsawa daddy idonshi yakada yay jajir yace." Alhj mekake nufi dahakan?" Haba daddy kawai yake shafawa yama kasa cewa imam kala saboda takaici,
" Iman kayi gaggawar tattara iyalan ka kubar gidan nan! tunkan asan abinda yake faruwa mah,inkuma bahaka bah yanzu zansa bodyguards suyi waje daku"
Abbah cikin fushi shima yakewa imam maganar, kallon wulakanci imam yay masa yabudi baki zeyi magana, sega meenal da mimi sun bude kofa sun fito cikin farin ciki suka rungume zarah sam basusan abinda yake faruwa bah seyanzun dasuka kalli fuskan ko wannen su suka san ba lafiya ba, jikin meenal a sanyaye ta karasa inda su daddy suke tsaye tace." Daddy lpy kuwa muka ganku a tsaye haka meyasa basu shiga ciki bah," sam yarasa abinda ze cewa meenal mah, juwa tayi da kallonta kan imam wanda har seda ta tsorata da irin kallon da yake mata na kurillah, sauke ajiyan zuciya daddy yay yashafi kanta yace." Meenal kushiga ciki babu abinda yake faruwa yanzu zamu shigo muma" jinjina masa kanta tayi taname shirin juyawa tayi anyi ram da hannunta, hakanne yasa ta juyowa a tsorace tana kallon imam saboda irin rikon daya mata,


" 'Yata ina mahaifiyar ki take?"
Imam yay mata tambayar cikin wani yanayi kamar ze saka kuka gyara tsaiwar ta tayi kawai tana kallon shi da mamaki, ganin hakanne yasashi yimata murmushin karfin hali yace." Eh tabbas ke 'yata ce kuma ni mahaifin kine, koda kika kalli kwayar idona bakiga jinin kibah"
Murmushi meenal tayi tace." Wai bakai bane Abban zarah?" murmushin ya mayar mata yace." Niba mahaifin ta bane, mahaifiyar ta kawai na aura, ke kadai ce "yata a duniya"
Kasa motsi meenal tayi a gurin tanajin kalmar sa kamar an buga mata gudu ma akanta, jiki a sake ta juya tanama daddy wani irin kallo, cikin takaici daddy yadan ciji lips dinsa na kasa yaname lumshe ido saboda bakin ciki,bayyada ya iya dole ya kalleta yace." Meenal mahaifin kine shi yau Allah yakawo miki shi kada kiji mamaki ko shakku"
Sam meenal tama rasa awani hali take ciki yanzu ko hawayen ta nemesu ta rasa kallon imam kawai takeyi shikuwa matsowa yakarasa ze rungumeta cikin wani irin firgici tayi baya tana masa wani kaskan tancen kallo, cikin sanyin jiki yatsaya yana girgiza mata kai harda magiya
" Kiyi hakuri 'yata kada kiyimin haka kutemaki ni don Allah keda mahaifiyar ki ku kadaine farin ciki na wlh"
" Allah yasawa kah! koda wasa ko a mafarki bazamu taba zama farin cikin kaba kada ka kuma kirana da 'yarka domin ni bansan kaba, bansan waye kaibah duk duniya banida mahaifin da yawuce daddy nah wanda yasan fadi tashi nah a rayuwa saboda haka kada ka kara danganta kanka da mahaifiyata don tafi karfin kah, kakuma tafi kabar mana gidanmu! domin kai ba alheri bane a gun kowa!" meenal takarashe maganar cikin kuka!


A lokacin kuma su muhammad suka dawo gidan kasan cewar motocin Abban su mimi tacike parking space dinne yasa basusamu damar shigowa da tasu motanba sosai suna dai hangen abinda yake faruwa bude kofan motan mujaheed yay zefita muhammad ya riko masa hannu yana girgiza masa, yana cewa." Fara kiran mimi muji abinda yake faruwa naga meenal tana kuka" dawowa yayi yazauna mujaheed din yakira mimin, tsaki kawai muhammad yay yace ba lallai sun fito da waya bama kawai muje don bazan iya jurewa bah ganin meenal tana wan nan kukan" kafin ya rufe baki kuwa an daga wayan sedai be tantance muryan wayeba yace." Wai meyake faruwane awaje? suwaye sukazo?"
Ba ah bashi amsa bah yaji an yanke wayan, bebi takan hakan bah suka fita a motan suka karasa inda kowa yayi dako dako a tsaye, mujaheed ne ya tsaya gefen mimi yana tambayar ta lpy? sedai kanta bashi amsa mahaifiyar zarah ta karaso gaban imam fuskarta babu alamun annurin rahama tasoma sauke masa maruka dukda haka be isheta bah seda ta cakumi kwalar rigar sa tana huci tasoma magana cikin fusata!
"Tabbas yau nakara yarda da cewar kai butulu ne bakin muna fiki macuci! namaka dare dole kayimin rana, dama ance kaji tsoron wanda kafiya temakawa dayawa, ashe har mata ce dakai harda 'yah saboda muna fiki ne kai daya sa aka kamaka bacemin kayi harkallar kudi bace ta hadaku ashe karya kakeyi" Abban su mimi lokaci da yakama imam yasanar dashi yasaki safiyya.


Mari lafiyayye shima imam ya sauke mata wanda yasata kara gigicewa takara shake masa wuyan riga tana cewa." Wlh yau imam taka takare a duniya sekayi nadamar abinda ka aikata min rayuwar ka ma a gidan yari zaka karasa ta"
Fitowan safiyya kenan domin ganin abinda yake faruwa sabida itace ta daga wayan mujaheed,tayi mummu nan gani, ganinta da imam yayi ne yasashi dena jin abinda maman zara take cewa ma kallon ta kawai yake,
Girgiza kai kawai daddy yay cikin takaici yaje yakama hannun ta suka shige ciki, tsaki Abbah yayi yaname cewa." Ay kuma shike nan tunda haka yafaru gara komai yazo karshe yau, hajiya kisake shi yanzu dai dole mushiga ciki a kashe wan nan kurar data taso sabida haka idan kuntafi kwacigaba da rigimar ku kome zakiyi masa kimasa"
Dakyar imam yakwaci wuyan rigarsa a hannun ta se faman haki yakeyi don ya shaku kam ba karya rankayawa akayi parlour kuma kowa ya hallara, ummi tana ganin imam tasoma sallal lami tana cewa." Haba tunda naga daddyn ku ya haye sama da safiyya nasan ba lpy bah ashe bala ei ke kuma tunkarar mu"
Dakatar da ita Abbah yayi kan tayi shiru kada takara cewa kala, haka kuwa tai gum da bakinta se uwar harara datake antaya masa haka muhammad kallon sa kawai yake, dakyar Abbah yashawo kan daddy ya fito da safiyya aka zauna gaba daya kuka kawai take tamkar numfashin ta ze fita, bayani daddy yamasa kan cewar shida safiyya yanzu shikenan har abada domin matar sace a yanzun harda yaransu ma, 'yar sace meenal gata nan sedai bashida da iko da ita sam seyanzun hassan da usain dasukaji wan nan batu sukasan ma abinda yake faruwa, saboda kululun daya tsayawa imam hawaye kawai yafara yanajin kamar yahadiye zuciya ya mutu jiyake makar yashake daddy,


" Macucin banza da wofi dole mana dama kayi hawaye, mummu nan kaddara ce nima tasa na aure kah amma kasani yau taka takare bayan sakina dazakayi zakaga abinda zanyi maka"
Sam bebi takan taba yamike ya tsugunna a gaban safiyya yanajin kamar ya hadiye zuciya yace." Safiyya kiyi hakuri ki gafarceni kaddarar rayuwar muce ahaka mutum baya taba gujewa kaddarar sa arayuwa" tunda yafara magana kukan nata ya tsananta nan danan numfashinta ya canza, dafe kanshi daddy kawai yayi don yasan za ayi haka dama kafin yagama tunani kuwa sejinta yayi ta fado jikinsa a sume! cikin kidi ma kuwa ya rarumeta yana jijjigata yana ambaton sunan ta,
bodyguards Abbah yakira yace suzo su fitar da imam daga gidan domin anyi anyi yafita sam yaki hankalinshi nakan safiyya, su hudu suka shigo kuwa suka cukwi kwiyeshi kamar kayan wanki sukayi waje da shi, maman zarah tamike taname cewa " kusamin shi a mota mutafi kai tsaye police station zamu tafi yau duk kudina dayacimin seya biyani kuma yasakeni inba hakaba kuwa sena daureka imam"


Dr bello daddy yakira a waya cikin gaggawa kuwa ya iso yaduba yanayin jikin safiyya hankalin kowa a tashe yake ba

Please Login or Register in order to submit comment