Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

da maryam ke sallama da mama tana shirin ficewa daga tsakar gidansu zuwa soron jamila ta danno kai zuwa,ta cake ado cikin wata yar ubansun shadda dinkin riga da skert na rashib arziqi,qam rigar ta kamata har boobs dinta na yowa sama,babu zancan mayafi sam atattare da ita sai daurin zamanin nan da ake kira ture kaga tsiya,waya take tana taku cikin isa da qasaita tamkar wata diyar qaruna
''yanzun nan na fito daga gidan mu hadu kawai a ni'ima guest palace din,amma fa gaskiya wannan karon bazan kuna ba gida zan koma,ok sai na iso''daidai lokacib da ta kammala wayar,bangazar kafadar maryam din tayi sannan ta juyo a wulaqance ta qare mata kallo,wata mahaukaciyar dariya ta saki tana ci gaba da kallonta
''sannu adda maryam,ana nan ana fama ko,ko da yake dai....''ta fada tana kuma kallonta daga sama har qasa
''ba laifi naga kin dan canza,ko an fara bin kwalta ne?''
waniabu ne ya tokarewa maryam dim maqoshi,rainin hankalin ya fara isarta dukan ya mata yawa,tayi mata uwarta ta mata,batasan lokacin da ta daga hannu ta zabga mata mari ba,ba ita kadai ba hatta da hindatu tayi mamaki,tsawon shekarun da suka dauka bata taba gwada yiwa wata cikin maraina wayon ta haka ba
''kan can uba,kut,me nayi miki,ko ko tsabar baqin ciki da qyashi ne...''
''kika ci gaba da magana ina mai tabbatar miki zaki kwashi haqoranki a qasa,banza jahila dabba wadda batasan inda yake mata ciwo ba''
tsit tayi da bakinta don taga irin bacin ran da bata taba gani cikin idanun maryama ba,gaskiyar hausawa dake cewa wargi ma guri shika samu
daga haka bata dada ba ta mewayeta tayi wucewarta,dadi kam tamkar maryama ta taka rawa saboda farinciki,mama ma wannan karon bata ce uffan ba,don tsan yau da gobe tafi qarfin wasa,fitarta waje babu inda idanunta suka kai sai kan jabir dake zaune mazaunin direba,idanunshi qur bisa qofar gidan tamkar dama an sanar da shi maryam din na fitowa,mamaki da tausayi suka cika maryam,jabir ne wannan,jabir ne ya koma haka,ina gayu davtsaftar jabir suka tafi?,me yake faruwa da jabir me ya sameshi?,mamakinta bai sake daduwa ba sai da taga ya dauke kansa daga gareta tamkar ma bai taba saninta ba
cikin matuqar sanyin jiki take takawa har ta isa bakin titi ta tari napep tayi gida
lokacin da ta isa gidan tuni anyi sallar magariba duhu ya riga ya shigo,ba haka taso ba taso ne ta koma da wuri ta dora musu dinner din,saidai lokacin ya riga ya qwace mata,kitchen din ta nufa kai ysaye bata ko doshi dakinta ba,mami,ce gaban gas din tana ta hidimar hada abincin,yayin da kuna dan shagwabar nata ke tayata da dauko wannan dauko wancan
''idan banda rigimar abdallah don Allah ina kai ina girki?,nace ka...''sallamar maryam ta katseta
''sannu mami da gida,har kin dawo?''ta fada tana ahirin amsar aikin daga hannunta
''yauwa maryamu ya kika barosu?''
lafiya mami suna gaidaki?''
''kinga maruamu barmin nayi yau dai daya ki huta kema,nima na wasa qwaqwalwata ko?''mami ta fada tana hanata aikin da take qoqarib karba
''ayyah,mami da wuri ma naso na dawo lokaci ne ya qwace min''
tsaki abdallah ya ja hadi da barin miqo albasar da yakewa mami ya koma ya zauna
''ki bata mami aikinta ne,idan baki bata ba ma acikin albashinta na wani watan''
yau ranta abace yake tana jinta daidai da duk wanda ya taba tane,hakan ne yasa ta maida masa raddi
''babu damuwa,mami ina jinta ne tamkar mama na ne saboda haka babu ciniki tsakaninmu,ko ba kudi qimar shekarunta sun biya in mata aiki''
baki ya tabe kamar mace
''gaskiya ne naga kina amsar albashinki,ai da,sai kice kin yafe''
murmushi tayi cikin gatse,sanann cikin qasa da murya ta yadda mami da ta tafi sink wanke albasa ba zata ji ba
''kada ka manta haifata akayi yadda akayi yadda aka haifeka,aiki nake kamar yadda kake wa qasarka aiki da albashi ake biyanka,am not a servant,ciniki kuma ko tsakanin da,da uwa halas ne''
tofa baki yasan me zai fada tuni fuskar 'yan maza ta sake hadewa
a zafafe yayi niyyar maida raddi saidai isowar mami gun ya katse masa hanzarinsa,tilas ya hadiye abunda ya qunso
''zan zuba miki albasar maryamu kafin nan ki shiga daki kin ajjiye kayan hannunki kin sauya kaya ko?''
''to,mami na gode''maryam ta fadi gami da juyawa ta bar kitchen din,abdallah ya bita da kallon zaki san koni waye,yayin da ta daga kafadu alamun dake nuna masa am ready
*mrs muhammad ce*
[9/17, 12:52 PM] 80k: 💖💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺🌺
🌺💖🌺💖🌺
🌺💖🌺💖
🌺💖🌺
🌺💖
💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺
💖💖💖💖💖💖💖
*WRITTEN BY*
*SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
💖🌺💖🌺💖🌺
💖🌺💖🌺💖
💖🌺💖🌺
🌺💖🌺
🌺💖
🌺 ▶2⃣3⃣




*_an karbo daga abu hurairah Allah ya qara yadda da shi yace:manzon Allah tsira da amincin Allah su qara tabbata a gareshi yace: kalmomi guda biyu,masu sauqi akan harshe,mafiya soyuwa agurin ubangij,masu nauyi akan mizanin auna ayyuka SUBHANALLAHI WA BI HAMDIHI,SUBHANALLAHIL AZIM_*






su biyu cikin falon misalin qarfe goma na dare,mami na bisa computer dinta tana tsara wata saminer da zasu gabatar yayin da maryam ke zaune gefanta tana tayata hira
''abdallah shiru bai dawo ba,halan yau aiki ne ya tasaahi gaba''cewar mami lokacin da take ci gaba da typing
''da alama''maryam tace
mami tadan bar abunda take ta juyo da hanklainta ga maryam
''wai ni kam maryam meye matakin karatunki ne?''
murmushi ta danyi
''degre ce''
''ta daya ko ta biyu?''
dan bude baki tayi alamun mamaki
''a'ah mami,ta dayan dai''
''mai zai hana in maida ke makaranta ki samu wata degree din kan fannin kasuwanci?,na fuskanci kina da amfani matuqa atattare da mu,sa'annan ina buqatar mai kula da kamfanonin abdallah mai amana kamar ke,kamfanoni wadanda ya gada da kuma wadanda ya bude daga baya,ya kike gani maryam zaki iya?''


shiru ta danyi cikin shakku,bata son ta fiya zura kanta cikin harkokin masu hannu da shuni, tana gudun wulaqanci,duk da tayi amanna cewa mami sam ba haka take ba,ta yarda da karamci da kuma son jama'a irin nata,to amma shi uban tafiyar fa wanda sam tasu batazo daya ba?
''yaya ne maryam naji kinyi shiru ko baki da sha'awa?''
girgiza kanta tayi
''a'ah mami,duka abunda kika yanke mami dai dai ne,amma zanso na fara sanar da baba da mama naji me zasu ce akai''
''gaskiyarki,wannan dai dai ne,amma duk da haka ki fara hada min takardunki nasan bazasu qi ba,babu wanda zaiqi ilimi wa dansa,ina da qawa a jami'ar b u k sanate ce so insha Allau babu matsala''


''to mami na gode Allah ya saka da alkhairi ya qara girma''
''no maryam,diya ta nayiwa kinga babu buqatar godiya''gyada kai tayi fuskarta qunshe da murmushi
sallamar nene ce ta maida hankalinsu bakin qofar,nenen ce kiwa cikin doguwar riga mai zubin buba mai taushi saidai wannan nada hannaye gajeru da alamu shigar barci ce tayi
''maraba da nene''
''yauwa...mami''ta fada tana zama cikin daya daga cikin kujerun falon dake,daura da inda mami da maryam din ke zaune,a mutunce suka gaisa
''zuwa nayi na diba yarona abdallah kwana biyu banjin duriyarsa''nene ta fada tana murmushi


mami ta rufe computer tana cewa
''abdallah na nan qalau aiki ne ya sashi gaba,da wuri yake fita kuma bai shigowa da wuri,yanzun na zancanshi muka gama da maryam''
ta juya ta dubi maryam sai a lokacin ta gaidatakanta na sunkuye a qasa,sam batason kallon idanun natar,haka nan sai taji fargaba ta kamata,second talatin idanunta na kan maryam din tana saqa a kanta kafin ta dauke kabta ta maida ga mami
''lafiyanshi dai qalau ko?''
''lafiya qalau yake''mami ta bata amsa cikin jin dadin tambayar tata,wadda har ga Allah tayi tsammanin ta mata ita ne da zuciya daya


ta miqe tsaye tana cewa
''tiw,ni zan wuce dama abunda na shigo naki kenan,sai da safenku''
''Allah ya bamu alkhairi nene an gode ki gaidamin su zubaidan kwana biyu ma bata leqo min ba,zahariyya dama sai wani abun ya kawota''murmushin yaqe nenen tayi cijin zuciyarta tana cewa
''bintu ki guji ranar gamuwar mu dake,gamon mu dake bazai ma rayuwarki daidai ba''


''abdallah na bani kunya wlh,dubi yadda baiwar Allahn nan ke sonshi take damuwa da shi,amma shi bashi da abun wulaqantawa sai diyarta,idan baiyi wasa ba na kusa masa auren dole''
'yar qaramar dariya ce ta subucewa maryam
''ai mami ba'a yiwa namiji auren dole''
itama dariyar ta tayata
''to za'a fara kan abdallah''


mintina ashirin basu cika da fitar nene ba abdallan ya shigo,ya sauya shiga ba wadda ya fita da ita bace,indai mami taga hakan to a gajiye ya dawo ya fara shiga sashensa yayi wanka ne
kan table maryam ke serving nashi yayin da shi da mami ke hira jifa jifa,ta kammala tana shirin sauka ta basu guri taji yace
''ke...mene wannan din?''ya fada yana nuna abincin da ido,kafin ta bashi amsa mami ta karbe zancan
''dambun shinkafa ne mana''
ya bata fuska kamar yadda yara keyi ya dubi mami
''gaskiya mami ni bazanci wani abu dambu ba''maryam ta kalli farantin don sake gano aibun dake tattare da dambun da ta bata lokaci a kitchen tana girkawa,dambun shinkafa ne da aka masa hadin vegtables sosai saboda ta sonshi da son gayayyaki,cabbage ne carrot zogale green beans harda gyada da wadatacciyar albasa sai dafaffen nama data yankashi qananu ta zuba a ciki,mamaki tayi cikin zuciyarta duk da bata nuna ba kan fuskarta,ta lura tsirfar da ya tsuro da ita kenan cikin yan kwanakin nan


''amma kaifa dazun kace shi kake sha'awar ci ayi maka?''
''am sorry mami na,dambu ayanzu is too heavy na cishi na kwanta ai sai ya kashe miki ni''
dariya ma ya bata,bata zaci konai ba don yaune ya fara wa marya din a gaban idonta
''is ok,maryam yi haquri kinji taimaka ki sama mishi wani abun mai sauqi da sauri''
''no mami,ni zan zaba akwai abunda nake sha'awar ci''
''uhmm''ta fadi tana kallonshi
''sakwara nakeso miyan agushi''bata fuska mami tayi
''kai lokaci fa ya qure gaskiya ba zata girka ma sakwara a yanzu ba saidai ka barwa gobe''
''tunda kin roqa mata shikenan tamin jallop din supaghetti with serdine''bai qarasa ba ma ta sauka tayi kitchen


girki ba baqonta bane cikin minti ashirin ta kammala ta,tun kafin ta fito qamshi ya soma cika qofofin hancin abdallah amma sai ya dake
''mami,dazu munyi waya da abida,ta ce nan da kwana uku zata zo nijeria''
farinciki sosai maryam ta gani fuskar mami
''masha Allah,gaskiya ta kyauta qwarai kuwa da gaske,kaga ta baka kubya kai da kaqi zuwa''
''to mami me zanje na mata''
''any way dai tunda tace zata zo magaba ta qare,fata na idan tazo din wannan karon konai ya daidaita,canki cankar da kake tayi wa muta ne ta qare''
''haka nake fata,na soma gajiya da qulafucinsu naci da rashin zuciya,inason nima na huta mami na samu peace of mind''


kafadarshi mamin ta buga''ja'iri sai yanzu kasan da hakan...am maryam''
''na'am''
''insha Allahu nan da kwanaki uku zamuyi baquwa abida diyar ambassador muhammad mukhtar kuma idan tazo zata dan zauna da mu na wani dan lokaci,so ya kamata kinga na sanar miki haqqinki ne sa'an nan daura da dakinki zata zauna kinga ke zaki karbi baquncin,ina son kuma a sake tanadin sabbin girki,duk na san ban da matsala dake,ke din ba baya bace''ta qarashe maganar cikin sigar zolaya tana murmushi wa maryam din
murmushin ta maida mata
''insha Allahu mami babu damuwa''


''mami a maida abincin nan kawai kitchen nina qoshi ma''inji abdallah bayan ya gana jagulashi da cokali
harararshi tayi
''baki isa ba ko zaka ci kayi amanshi sai ka ci,maryam tafiyarki kije ki kwanta Allah ya bamu alkhairi,gobe insha Allahu zamu tattauna''sallama ta yi mata tayi shigewarta yayin da mamin ta ja plate din ta soma nado taliyar cikin pork tana cusawa abdallah,shikam ya bude ciki ya dinga diba,dama yana so kasuwa kawai yake kaiwa
''almiri ashe kana ci din kenan shegen girman kai yasa kace baka ci''mami ta fada tana dubanshi
dariya ya qyalqyale da ita ya kanne ido daya
''so nake dama mami ta bani da kanta nasan sai yafi dadi''
''Allah ya shirya min kai abdallah''ta fadi tana murmushi

🍂🍃🍂🍃🍂🍃

tafiya take bata ko ganin gabanta saboda takaici da baqinciki,wai sai yaushe ne burinsu zai cika kan abdallah?,sai yaushe zasu samu nasarar kau da abdallah daga doron duniya,da wannan tunani ta samu da qyar ta maida kanta bangarensu


adnan da zahariyya dake dakon zaman jiranta cike da buri da fatan jin daddadan labari suka taso
''yaya nene?,anyi nasara kuwa?,rashin ganin nashi nada nasaba da aikin mu kuwa?''saida ta fada jabar saman kujera kafin tace
''mun sake fadu wannan karon ma babu nasara,rashin nasarar kuma yafi na kowanne lokaci''
adnan ya sake matsowa gabanta
''yaci dinne bai mutu ba?''
''ina ma yakai ga cin,ai ko ci baiyi ba,kuma hakan baya rasa nasaba da wannan tsinanniyar mai girkin da na rasa inda bintu ta samota,yarinya sai shegen kwarjini''
''oh shit!''adnan ya fada bayan ya dunqule hannunshi ya daki tafin hannunsa,zahariyta kuwa kasa magana tayi face bin sahun uwarta da tayi ta fada saman kujera


a sukwane ya koma shina ya zauna bayan yayi qasa da muryarshi
''nene,nifa na gaji da wannan shirin kisan ta bayan fage,ki barni kawai na tari abdallah na kasheshi da hannuna''
''kai dalla gafara can''nene tayi hanzarin katseshi
''ashe baka da hankali?,waye ya gyamaka kashe mutum kamar abdalla abune da yaje da sauqi har haka?,ka manta matsayinshi?,ka manta wayeshi a nijeria,bama haka ba,ka mance qirar qarfin da abdallah ke da ita,wanda na tabbatar idan aka barka da shi naushi daya zai maka saidai mu dauki gawarka ba kai din ba''shiru adnan din yayi don yasan haka maganar maman tashi take


zahariyya ta furzar da wani rin huci
''tsinanne matsiyaci,ni da zai amince ya auri waccar yarinyar zubaida ai da kinga komai yazo mana da sauqi,mu kasheahi hankali kwance,idan da rabo ma har sai ta haihu kinga tuwo namu miya ma tamu,to amma shegen girman kai da jin ajinsa bazai barshi yaso zubaida ba,to amma nene mai zai hana mu nemi hadin akn ita kukun tashi ko zata amince kamar yadda na baya suka amince,idan yaso itama musa a mata daurin baki idan ta amshi kwangilar ta yadda koda lamari ya baci zata gaza ambato sunansu kamar wadancan kukun''


ajiyar zuciya nenen ta saki
''hmmm,yaro yaro ne,duka tunaninku babu wanda ya kwanta min,wannan yarinyar tasha banban da wadancan kukun nasu na baya kallo daya na mata jiki na ya gaya min haka,abunda zai faru shine ni da kaina nake so ku bani lokaci zanyi tunanin mafita,na rantse da Allah wannan karon ko bata hanyar guba ba *SAI NA SALWANTAR DA ABDALLAH*


_TOH FA_🤔



📚📚📚✍🏻✍🏻✍🏻
[9/17, 12:52 PM] 80k: *ABADAN*
*WRITTEN BY*
*SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
*_daga abu hurairah yardar Allah ta qara tabbata a gareshi yace:manzon Allah tsira da amincin Allah su qara tabbata a gareshi yace:ba zaku shiga aljanna ba har sai kunyi imani,ba zakuyi imani ba har sai kunso junanku,shin bana nuna muku abunda idan kuna aikatashi zaku so junanku ba?KU YADA SALLAMA A TSAKANINKU_*
cikin kwana ukun mami ta hana gidan sakat da shirye shiryen tarbar abida,ragowar daki biyun dake maqotaka da nata aka bude,kusan komai irin na nata dakin ne sai dan bambancin abunda ba'a rasa ba,ganin yadda mamin ta dauki zuwan abida da muhimmanci ya sanya maryam itama sake shirya kitchen
Ranar da zata iso din jirgin da yake sauka sha biyu na rana ne zai sauka da ita,tana jin mami na sanar da abdallah ya,haqura da fitar yau yaje a taro abidan da shi
''kai mami barta kawai,fita ta ta yau mai muhimmanci ce,driver yaje kawai ya daukota,ba dai tana gidan ba almost two to three months fa zatayi tare da mu''
qarfe sha daya maryam ta gama kintsa dining da kalolin abincin nijeria africa da kuma qasar da abidan ta baro wato turkiya,dakinta ta shige tayi wanka,don aikin bai barta tayi wankan ba,riga da zani ta zaba ta shirya cikinsu dukkansu normal dinki ne irin na riga da zani plain na asali,ba qaramin fidda sigarta yayi ba yanayin dakin akwai fidda shape din mu ba irin dinkin mu na yanzu ba mai tattara dake cika mace ya badda shape dinki,bata fito a dakin ba sai da ta jiyo surutu sama sama cikim parlour din mami qarfe daya saura kwata na rana
mutum uku ne cikin parlour din harda mami ta hudu,tashin farko zuciyarta ta bada abida cikin su ukun,sanye take da doguwar riga baqa mai azabar kyau da tsada irin mai robar nan dake bin jikin mutum,fara ce qal don har tafi maryam fari duk da dai akwai bambanci,farinta mai dau ne babu sirkin ja aciki ko kadan,zaka iya kiranta gajeriya don bata cika tsawo ba,tana da kyau kam ba laifi don kallon farko zaka kirata kyakkyawa,bata da qiba da yawa saidai jikinta acike yake babu lobawar rama
mami ce ta soma ganinta fitowarta
''yauwa maryam kin fito?''
''eh mami na fito baqin sun qaraso,sannunku da zuwa''
ta fada tana dubansu,daya ce kadai ta amsa sabanin biyun ciki harda abidar wadda ta dago kai ta dubeta,kamar ba zatayi magana ba sai kuma tace
''nidai kam ba baqiwa bace ina tsammanin kece baquwar''
murmusho maryam din ta danyi
''eh to,kusan haka dinne''ta bata amsa tana kallon fuskarta wanda take bisa screen din tsadaddar wayarta
''maryam kuje da ita ki nuna mata dakinta''
''to mami''ta fadi tana yin gaba
''wa zai daukar miki trolly din?''abida ta ce tana hakimce a zaune tamkar ba ita za'a nunawa dakin ba
bata ce komai ba ta dawo,ta dubi akwatinan da kallo,qwaya biyu ne masu azabar kyau wanda ko ba'a fadi maka ba kasan cewa ba na talaka bane,ta daga dogon sandan dake jikin akwatin wanda zai bata damar janshi akan tayoyinshi ta kwantar da ita ta jata zuwa ciki
ta sake dawowa don daukar dayar,saura mami da abidar kawai yanzun cikin falon still abidan na hakimce,nuni ta mata da handbag dinta big mama tace
''shigarmin da wannan ma''
''barshi,maryam bari baba uwani tazo zata shigar miki da su,aikin maryam a gidan nan girki ne kawai''mami tace da abida,sai ta bar abinda take yi din ta dubi maryam sannan ta dubi mami
''ok,ai duka daya ne mami,dan aiki dan aiki ne da mai girki da mai shara duka 'yan aiki ne''
''to kam anan gidan akwai banbanci,kowa matsayinshi daban''
dan tabe baki tayi sannan ta saki murmushi kana ta canza topic din
''gaskiya mami abdallah bai kyauta min ba,yaushe rabona da nijeria ammayau kawai ya gaza kashe aikin gabansa yaje ya dauko ni''
''kinsan dai halin abdallah sarai tun ba yau ba,aikinshi na da muhimmanci matuqa a gunshi,ba dan qaramin abu bane zai sanya shi qin fita aiki ranakun ayyuka ba''
maryam dake tsaye tana jiran tasowar abida duk ta qosa,ta dan gyara tsaiwarta
''mu qarasa na nuna miki dakin''
''jeki kawai gidan ba baqona bane''
bata kuma tanka ta ba tayi komawarta daki,saida da ta dqidaici lokacin da ya kamata tayi serving nasu sannan ta fito,saita taddasu tuni sunyi nisa da fara cin abincin,son haka ta qarsa ficewa daga bangaren gaba daya,boys quaters ta zagaya inda anan gidan baba uwani yake
da fara'a ta tarbeta
''maraba da maryamu,sai yau Allah yayi za'a zo mana''murmushi tayi har fararen jerarrun haqwaranta suka bayyana
ta gaida baba uwanin da baquwar da ta taras tayi
hirarsu suka sha sosai don bata baro bangaren ba sai da akayi sallar isha'i sukaci tuwon dawar da baban ta girka,don dama tana kewarsa matsalar su mutanen cikin gidan basa cinsa shi yasa ma bata girkashi
ita daya ta taho iskar damuna na kadata,cikin parking space ta jiyo motsi,ta dan juya kadan hisham ne abokin abdallah,a tunaninta basu ganta ba don haka ta kau da kai tayi gaba
''haba 'yan mata irin wannan shan qamshi haka?,a qalla dai ai ko gaisawa kya tsaya muyi ko?,duk da cewa ma zuwan don ke nayi shi''inji hisham wanda ya sha gabanta,qirjnta ne ya shiga dukan uku uku,fatan ta kada Allah yasa ya furta mata kalmar so,don ita tsoro ma take bata,ta jita daga bakunan maza da yawa saidai babu abunda ta tsinana mata
a qagauce ta ce masa
''ina wuni''
''lafiya qalau maryam diya na ya gida ya aiki?''
kai ta dago ta kalleshi jin ya ambaceta da sunan da schoolmate da classmate dinta zuwa friends ke kiranta da shi
''lafiya qalau,ina son ganinki amma bari idan mun gama da abdallah zan kiraki,da fatan ba zaki qi zuwa ba''
''Allah ya bani iko''ta fada da gaggawa tana wucewa don ganin abdallah na isowa gurin
duk da haka bata kasa jin abunda yake fada ba kasancewar sun biyota ne a baya
''hisham,wlh hisham ka fita a ido na,kai me yasa baka jin shawara sai shegen taurin kai?''dariya ya qyalqyale da ita
''kai kuma mai yasa kake da girman kai da kafiya,Allah bai haramtamin harinya ba na gani inaso to kuwa ba zaka hanani ba''
''ok haka kace?''ya fadi cikin huci yana dubanshi
''yes,haka nace,idan kuma kai ke sonta ai sai ka fada sai in janye maka''
a zafafe ya soma fadin
''na rantse hisham zaka jawo mu samu sabani mai girma da kai,in rasa inda zanyi ajiyar soyayyata sai gun house girl kuku?,ina da dukiyar da zata iya bani duk kalar macen da nake so na aura,ko 'yar wane kuma ko awanne qasa take,wanda nake tare da shi ma yafi qarfin auran house girl,indai ko zaka ci gaba kan qudirinka ka tabbatar cewa yana daidai ne da datse igiyar abotarmu''yayi gaba cikin hanzari abunka da qaqqarfan mutum
ko cikin parlour din ma dambarwar da suka dinga yi kenan sai da mami ta shiga maganar
''hisham ka qyale rigimar abdallah,maruam ta cika macen da za'a so,tana da dukkan halaye managarta,uwa uba kyau,don haka babu hujjar da abdalla yake da ita da zai hanaka neman maryama,ni na goyi bayanka saidai idan ita tace bata so''
''toh...nima haka na gani mami,nace masa ya fada idan yana so ne shima sai....''
''dakata hisham,don ina nema maka hanya mai bullewa kake cimin fuska?,to kayi na farko kayi na qarshe,duk lokacin da ka sake cewa inasn waccar abar wallahi sai na fasa bakinka''
ba hisham ba hatta mami abun ya bata dariya,abdallah mai rikicin gangan inji hisham,a haka abida tq fito ta taddaau,wannan karon ma cikin shigar doguwar riga take mai sulbi saidai armless ce,a mutunce suka gaisa da hisham don sunsan juna,ta juya ga abdallah
''soulmate,me yasa kamin haka don Allah,na diro naija da daukin ganinka sai kuna kayi tafiyarka aiki sai yanzu zan ganka?''
''da kika ganni yanzun ma ki godewa Allah,a tsare gobe ne haduwarmu,haka ne?''da sauri hisham ya shiga maganar ganin abdallah nason qarawa kwabar ruwa
''shareshi don Allah,kanshi ne ke hayaqi tun dazun''
tuni abida ta rudevta dawo kukerar da abdallan ke kai tana tambayar wa ya taba mata ruhinta,tsam mami ta miqe ta basu guri,banza ya bawa ajiyarta don haka kawai yake jin ransa na zafi
''wlh abdallah nan naki rigimamme ne sai kinyi da gaske,haka kawai ya haqiqance wai bazan auri maryam ba?''
''wace maryam?''ta tambaya tana duban abdallah
''mai shirya masa abinci kullum yana dirkewa''
ido ta,zubawa abdallan,lokaci guda wani kishin maruam din ya dirar mata,take taji ta tsaneta
''amma soul mate mene hujjarka na hana hi....''
a fusace ya miqe
''ke dakata min,kinsan banson titsiye ko?''yaja tsaki ya juya zai fice a sashen
kuka abida ta saki,wannan wane irin jaraba ce,daga dirarta a qasar ko kwana batayo ba abdallah ya aona bata mata rai,lallai abunda kake so shike wahalar da kai
kukanta bai dameshi ba ya juya ya fice,da sauri hisham yace
''kiyi haquri bari,na sameahi ranshi ne a bace''cikin hanzari ya bi bayanshi
amma da yake gwanin sauri ne tuni ya miqe balcony yayi sashensa
bai damu da hade girar sama da ta qasa da ya sakeyi ba duk don kada ya masa qorafin abunda ya yiwa abida ya hau masa fada tare da cewa yaje ya lallasheta
''wa?,ni?Allah ya tsareni,bani da lokacin lallaahin mace wallahi,ruwanta ta ci gaba da sona ruwanta tace ta haqura,amma babu lokacin rarrashin mace a rayuwata indai ba mahaifiyata ba''
karab cikin kunnen maryamu dake kwance saman gadonta don sun iso saitin window dinta,miqewa tayi ta zauna saman gadon,wani irin haushi da tsanar abdallah suka kamata
wanne irin nau'in mitum ne shi?
taqama da gadararsa sunyi yawa,dukiya?ita ke rudarshi ko kyawun da yake da shi?,haushi da takaici suka kamata tamkar da ita suke maganar,haushinsa ta dinga ji sosai,da tana da iko sai ta masa dukan tsiya ko zata samu sauqin abunda take ji
haushinsu abida ya kuma kamata
don me suna mata da Allah ya yiwa baiwa da ado da kunya su dinga watsi da baiwar,so hauka ne?,ta godewa Allah da bai dora mata wannan masifar ba,gwara da Allah ya bar zuciyarta wankakkiya kuma kubutacciya daga dukkan soyayyar wani
kusan awanni biyu da shigewarsu mami ta turo qofar dakin ta shigo fuskarta qunshe da murmushi
''maryamu diyata,jeki harabar gida hisham abokin abdallah na son magana da ke,duk abinda ya tambayeki kada kiyo nauyin baki ki sanar masa da gaskiya kinji ko?''
ba zata iya musu da mamin ba tilas ta amsa da to sannan ta fito
yana jingine jikin motarshi ta isa gareshi,da fara'arsa yake fadin
''barka da isowa,tun dazun nake jira har ma na fidda rai?''
''uhmmmm''kadai ta iya cewa taja bakinta tayi shiru tana sauraren bayanan hisham,ya rufe

Please Login or Register in order to submit comment