Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

gyaran da ake mata ba,tamkar ana shirin canza mata fata,ita kanta mai gyara ta yaba yadda gyaran ya karbi jikin maruym di sosai da sosai,baaba uwani kuwa zama take kawai tana kallon maryam din
''gaskiya meramu anya ba canza miki fata hajiyar nan me gyaran jiki take ba?''duk sanda ta fadi hakan dariya take basu ita da mami


Kusan tun ranar da sukayi waya da abdalla kan zuwanta gida basu sake samun kiranshi ba,ana gobe kwanaki bakwai din da ya diba zasu cika mami ta nemeshi don taji goben zai dawo,saidai ta nemi layin nasa yafi sau goma bata sameshi ba,har cikin dare tana iransa bata sameshi


da safe ma hakan ce ta faru,damuwarta ta kasa boyuwa ta tadda maryam a kitchen tana goge freezer tare da sake jera kayan ciki don mamin ta hanata yin kowanne aiki
''ni kam maryam kina samun abdallah a waya kuwa''maryam din ta waiwayo ta dubi mamin sai ta rasa amsar da zata bata,don ita kanta tasha kasa kunne cikin dare lo da rana taga ko zata samu koda texs nasa,Allah ya taimaketa tin kafin tace wani abu mamin tace
''sam ba'a samun wayanshi,na kira na kira duka akashe''
jikinta taki yayo sanyi gaba daya,gabanta ya dan fara faduwa kada kadan ta juyo gaba daya ga mamin tace
''to mami ni cewa nayi ko chargy ne babu a wayoyin nashi?''
kai ta girgiza
''bana jin haka,saboda ba cikin wani qauye bane cikin tsakiyar abuja ne fa,kusa da villa,kinga ta yaya za'a rasa chargy a wayoyi?''
sbiru ya sake ratsa tsakani,bayyanar damuwa kan fuskar maryam wadda ita kanta batasan ta bayyana bayasa mami riqe hannunta
''kada ki damu in sha Allah he is safe''
kai ta gyada asanyaye,sai ta kasa qarasa ci gaba da aikin ta biyo bayan mami ta fita a kitchen din ta koma dakinta ta kwanta


Maganganunshi na qarshe ta dinga tunawa
_''Allah ya qaddara saduwarmu,sai Allah ya dawo da ni,kimin addu'a don muhimmin aiki zan gabatar,wanda ko shine aiki na na qarshe da zan aiwatar in sha Allahu sai na gabatar da shi,ki sakani a addu'o'inki,idan kuma na mutu shikenan sai a darus salam''_


Wani irin juyi tayi cikin matsananciyar faduwar gaba ta tashi ta zauna sosai kan katifarta,sai taji kanta ya sara ta dafe goshinta da sauri kana ta maida jikinta fuskar gadon ta jingina
kusan wuni tayi sukuku zuciyarta ba dadi,duk motsin da tayi maganansu ya qarzhe a airport ke mata amsa kuwwa a kunnenta,ko falon bata sake fitowa ba saboda rashin kuzari,mami keta leqota don kada ta takure ranta ta sa damuwa,ta karanci wani kalarson abdallan mai qarfi cikin zuciyar maryam din,da taga ta leqo ta sai ta qirqiri murmushin dole,gaba daya walwalarta ta ragu,ta dinga kiran layin abdallah a jejjere kamar wadda aka bata aikin yi amma ko da wasa bata shiga ba is switched off computer keta faman gaya mata,



Cikin kwana biyu duk yadda taso hana kanta damuwa zuciyarta tace batasan wannan ba,bata taba jin damuwa irin ta wannan lokacin ba,bata taba jin ta damu da wani abu a rayuwarta ba kamar wannan lokacin


cikin kwana na uku ta gaza daurewa
fitowarta a wanka kenan wanda tun safe ta kasa yinsa sai kusan daya na rana ta samu tayi,mai kawai ta shafa ta fesa turare ta zira doguwar riga ta nade kanta da mayafinta,takalmanta plate ta jawo ta saka kana ta fito,babu kowa bangaren don mami ta fita asibiti don haka ta fito waiting parlour ta zauna tana kallon shigewa da ake tayi da sabbin furniture bangaren nene a da,bata cikin nutsuwarta batasan wa zai zauna anan ba bata kuma damu data sani din ba,abinda ke cunkushe kadai a ranta ya isheta jarraba


number din hisham ta laluba ta kirashi,daga yanayin yadda taji sun gaisa har yana zolayarta ta tsinke da lamarin,sai kawai ta fasa tambayarsa ta kashe kiran,lambar abdallah ta sake trying wanda ta maida kiran tamkar ibada a gareta saidai amsar daya ce kamar kullum is switched off,ita kanta ta fuskanci yanayin damuwa kan fuskar mamin duk da bata kai tata ba,jin zuciyarta take kamar ana hura mata wuta
son abdallah
kewar abdallah
duk su suka mata rubdugu,kalamansa na qarshe a gareta ke sake sanya mata karaya,kawai sai ta zame a gun ta kwanta rub da ciki,batasan ya akayi ba ta tsinci kanta ne kawai tana kuka tuquru,bakinta na fadin
''kada ka yimin haka abdallah,kada ka guje ni,kada ka tafi ka barni''take furtawa a hankali cikin kuka,Allah ya taimaka mutanen dake aikin kafa kayan furniture din sun kammala sun fice


Kuka tayi mai yawan gaske har yasa idanunta suka kumbura baya ga zafu da radadin da suke mata amm hakan baisa ta haqura ba,sai da bacci ya lallabo ta taimaketa ya saceta,bacci ne mara dadi wanda tana yinshi tana sayke ajiyar zuciya ma kukan da ta yi


Hannu taji kan wuyanta a hankali ta soma bude kumburarrun idanunta wanda hasken daya cika falon yasa ta gaza budeshi gaba daya,mami ta gani tsaye a kanta tana fadin
''bacci kuma a waiting parlour maryamu?''ta tambayeta ba tare data lura da yadda idanunta suka sauya kala ba
''tashi ki koma daki idan baki gama ba kiyi a can amma nan ai yayi waje''
sosai tayi qoqarin tashi amma ta kasa,ga zaton mamin magagin bacci ne don haka ta kama hannunta don tayata tashin,zafin da taji da hucin zazzabi ya sata furta
''subhanallahi,maryam me ya sameki haka?''sai a lokacin ta lura da yadda idonta ya suntume fuskarta tayi jawur
''ya salamu ya Allah,maryam''mamin ta fada a rude,zare wayar hannun maryam din tayi don ta miqar da ita,number din abdallah ta gani kan scrren din wayar,sai ta dubi maryam din
''abdallah dai maryam?duka a kanshi kika yiwa idanunki haka?,sai kace an ce miki ya mutu ne''kalmar mutuwa data ambata wa abdallan sai ta sake karyar mata da zuciya,take taji ko,mutuwar ma yayi ne tunda gashi mami ta fada?,sabbin hawaye suka soma tsiyayowa,sai mamin ta dafe kanta don ta fuskanci abinda ya sakata kukan
''babu abinda ya samu abdallah maryam,tashi maza mu shiga ciki ki je ki watsa ruwa ki karbi magani,zafin zazzabin nan yayi yawa kada ya zama wani abun kuma daban''


mamin ce ta taimaka mata har ta shiga toilet kana ta fita ta bar mata dakin ta haye samanta don tayi wanka,itama ta hada mata magungunan da zata sha da zai saukar mata da zazzabin,zuciyarta fal da fafinciki jinjinawa da yaba tsaftatacciya kuma ingattaciyar qauna kuma mai qarfi da ya samu daga gun matarshi,wanda tayi imanin koda bafa duniya zai samu kyakkaywan kulawa a rayuwarshi



Ta kammala watsa ruwan ta canza kaya,da qyar ta iya bada sallar azahar da la'asar da suka shigeta ta dawo ta nade a gado,har yanzu zazzabin tana jinsa cikin qashinta,a haka mami ta taras da ita


Sai data tilastata taci abincin da ta shigo da shi sannan ta bata maganin ta sha,tana nan a gurinta har bacci ya sake daukarta sanann ta fita dakin


Bata farka ba sai da wani amai mai zafi ya farkar da ita,da gudu ta miqe kanta na sarawa ta shiga bandakin ta dinga kwarashi,mami wadda ta idar da sallar magariba tana jiran isha ta dawo falin qasa ta zauna saboda maryam din ta fara jiyo kakarin amai,da hanzarinta ta shiga dakin,ita ta wanke gun data bata din ta maidata gado ta kwantar tana mata sannu,ta taba jikinta kana cikin damuwa tace
''maryam anya ba ciki gareki ba kuwa?''
duk da tana cikin ciwo sai da tambayar tq bata kunya,tayi qasa da idonta tana girgixa kai,sake matsowa mamin tayi tana lallabarta
''kada kiji kunyata idan shine ki gayan kada na yita baki magunguna muyi asararsa don Allah''
nan ma kai kadai ta iya girgiza mata ta kasa hada ido da ita
''to shikenan,allura dama zan miki naji zazzabin yaqi sauka''
sam bata qaunar allura,da kayi mata allura gwara ka zabga mata mari,ita ta sani ciwonta ba na magani ko allura bane,da sauri cikin murya ta marasa lafiya tace
''don Allah mami ba yanzu ba,a barshi sai anjima zai iya sauka''ta fahimci allurar ce bata so don haka ta qyaleta ta sake bata wasu magungunan


Ranar kam har kusan biyu na dare ana fama,qarshe dai allurar da bataso mamin ta mata,bayan tasha fama da ita kafin ta tsaya din,sai kusan uku saura na dare ta samu bacci ita kuma mamin ta koma dakinta

🍂🍃🍂🍃🍂🍃

A daddafe ta tashi tayi sallar asuba sakamakon baccin daya cika mata ido,duk da zazzabin ya sauka baki daya sai ciwon kai dake son matsanta mata kuma,da qyar ta gama sallar ta kwanta saman daddumar zuciyarta babu dadi,duk wani minti idan ya wuce sai taji kamar yana sake nesantata da abdallah ne


A hankali taji an turo qofar dakin,ta daga kai tana amsa sallamar da akeyi,mami ce cikin hijabinta da carbi a hannunta da alama idar da sallarta kenan itama,tayi qoqarin tashi zaune don gaisheta mamin tace a'ah yi kwanciyarki,a haka suka gaisa ta duba jikin taji babu zazzabin,shuru tayi bata ce mata kan nata na ciwo ba din kada ta daga mata hankali
''yanzu maryamu jinkirin dawowar abdallah yasa kika matsantawa kanki da damuwa haka har da ciwo?,lallai ba shakka gaba guduwa zaki dinga yi kibi mijinki kuna barina kenan?''ta fada cikin tsokana da zolaya,kunya ta kama maryam sosai,ita kanta batasan tana misbehaving har haka ba,batasan ya akayi abun ya hudata haka ba har yake bayyana kanshi da kanshi ba tare da ta sani ba.


''a'ah daina jin kunyata,ni hakan dadi ya yimin sosai,Allah ya qara hada kanku,aikin da yayi ne ya tsaudashi jiya kafin na kwanta saiga kiranshi,amma alhamdulillahi an samu nasara ya kama dukkan jama'ar daya shirya kamawar sai mu yiwa Allah godiya''
hakanan taji wani sanyi na sauka tun daga kanta har tafin qafarta,a gida ko a waje abdallah jarumi ne tabbas babu kokwanto,a hanakali cikin zuciyarta ta dinga fadin alhamdulillah
''sai ki kwanta kiyi naccinki sosai,kiyi bacci harda minshari ko''ta sake fada cikin zolaya,murmushi tayi tana sake sunkuyar da kanta mamin ra mata sallama ta fice


Ta lumshe idonta tana jin wani shauqi na kamata,duk da ciwon da kanta yake murmushi sai daya subuce mata,ta dan dafe kanta idanu a lumshe,a hankali bacci mai dadi ya sureta

🍃🍂🍃🍂🍃🍂

Sannu a hankali taji yanayin baccin nata na sauyawa,ta dinga bude idanunta a hankali har ta kammala budesu tas,yana zaune gefan gadon nata sanye da baqar jallabiya mai hula irin ta maza ya zuba mata idanu kamar wanda aka bashi aikin zana fuskarta,wani abu mai kama da farinciki taji ya ratsata
''welcome dear''ya fada a nutse
''an tashi lpy gimbiya?''ya tambayeta idanunsa har yanzu na kanta,kasa amsawa tayi sai cusa kanta da tayi cikin hijabinta,yayi maganar amma taqi dagiwa sabida haka ya tashi tsam ya koma gabanta yana qoqarkn dago fuskarta amma ta qiya,shima bai sakar mata qarfi ba ya qyaleta yana fadin
''kin daga min hankali da yawa baby,tun asuba na baro abuja duk sabida nazo na ganki amma kin min rowar fuskarki,shikenan na gode''ya fada yana miqewa zai fice a dakin,sai ta bude ido daya taba satar kallonshi tamkar ta tsaidashi tana kallo ya fice a dakin a hankali kamar wanda aka qididdigewa iya takun da zaiyi


Kunya da tsoro ranar suka hanata sakewa ko fitowa,sai taci gqba da kwanciyarta kan gado abinta mami na kulawa da ita a tsammaninta jikin da saura,tana son ta fito ko zata sake ganin fuskarshi amma kunya ta hanata,tana jiyo muryarshi a falo lokaci lokaci shida mami suna maganar bangaren nene da ta ga ana sawa sababbin furniture



_WASHEGARI_


Tas ta jita ta warke sosai,ko guntun ciwon kan ma babu shi,qarfe tara ta hada ruwa mai zafi tayi wanka,muradin ganin abdallah take,shi kuma kamar ya sani tun jiyan bai sake leqota ba duk da ya turo mata guntun sms
_sorry dear na zama busy kan wani abu,see u later_,iya abinda ya turo kenan



Ta shirya cikin atamfa riga normal da zani rafa,tayi lite make up kana ta feshe jikinta da turaruka masu dadi,ta daura dankwalinta bayab ta gyara gashinta kai azabar santsi ta hadeshi da ribbom madaidaici,haka nan ta tsinci kanta da yin kwalliyar,ba qarya ta mata kyau matuqa,muryarshi da jiyo a parlour ta haifar mata da fargaba,sai ta koma bakin gado ta zauna ta fasa yunqurin fitar da takeyi,ta dauki wayarta ta fara danne danne kanta a qasa



Raliya take turawa tex don taga missed call dinta na kiran data mata tana bacci


A hankali taji ana taba qofar kana aka turota,cikin qananun sakanni tattausan qamshi ya buwayi hancinta,qamshi ne mai kwantar da rai tamkad zai saka bacci a nata bangaren wani shauqi ya qara mata,kallo daya ta masa ta sauke idanunta qasa,kunya take ji sosai,ga wani maganadisu dake fisgarta cikin idanunshi,wani kyau na musamman taga an qara masa,gani take kamar mami ta gaya masa sirrinta,nauyin hada ido take da shi,yayi kyai sosai cikin light blue din shadda,babbar riga da yar ciki da wando,fadan irin kyawun da shaddar ta masa ma bata baki ne,shadda ce yar ubansu sai maiqo take tasha bugu,a hannunshi riqe da hularse,a gogone baqi a hannunshi na fata na kamfanin armani sai takalminsa half cover irin na maza,sai ya tashi sak dan kano don ba baya bane su wajen iya wankan shadda suna sahun gaba,ba qaramin amsarsa shigar tayi ba,do da wuya ya sanya kaya komai rashin kyawunsu suqi amsarsa ,fuskarsa cike da murmushi mai bayyana sirrin kyawunshi
''amincin Allah ya tabbata a gare ki baby,ina fata kin wayi gari cikin qoshin lafiya,af kice ma anko mukayi''ya fada cikin zolaya,sai a sannann ta dubi kalar atamfar da ta saka blue ce da baqi,duk da blue din ya dan dara nashi turuwa da kadan
qarasowa yayi bakin gadon ya tsugunna kana ya dafa cinyoyinta,abinda taji a jikinta shima shi yaji,sai tayi saurin zame hannun nasa,dauke hannun yayi yayi murmushi yana yiwa hular hannunshi kari ba tare da ya dubeta ba
''am too busy jiya naso inzo in sake tozali dake,ina daya bangaren can ana jeran amaryata''
sai tayi dumm ta rasa yadda zara fassara maganarshi


Ya miqe ya isa gaban madubinta ya daidaita hular bisa kanshi kana ya sake dawowa inda take
''wanne saqo kike da shi gun imna wuro,qauyen ni'ima zamu je,yau idan Allah ya nufa zan zama angon mero''
batasan lokacin da ta daga kanta ba,ta yi masa wani birkitaccen kallo ido cikin ido,wani irin zazzafan kishi baqinciki da takaici ya lullubeta
''naga kina duba na maryam idan da magana kiyi''ya fada yana sake matsowa kusa da ita tare da riqo hannayenta ya sanyasu tsakiyar tattausan tafin hannunsa,a zafafe ta fusge hannun nata kana cikin tsananin fushi da bacin rai da kuma masifa tace...........




*mrs muhammad ce*👑



📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽
[4:28pm, 10/10/2017] Huguma👑: [3:31pm, 10/10/2017] Huguma👑: 💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺
💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
💖🌺💖🌺
💖🌺💖
🌺💖
💖

*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
🌺💖🌺💖🌺💖
🌺💖🌺💖
🌺💖🌺
💖🌺
💖
© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡
*_home of expert and perfect writers_*

▶6⃣1⃣




*An karbo daga Anas dan maalik R A yace: Manzan Allah S A W yace''dukkan dan adam mai kuskure ne,mafi alkhairin masu kuskure sune wadanda suke tuba(idan sun aikata kuskuren kuma bazasu sake komawa ba)''*





Tace cikin wata iriyar murya mai dauke da tashin hankali
''jeka.....jeka nace,kaje tunda ka fadi abinda kake son gaya min lallai saqonka ya isa''tayi maganar cikin zafi da juyewar kalar qwayoyin idanunta
ya sake matsota yana fadin
''to kima me nayi don Allah maryam,ina cewa ke kika bada damarcda,zan qaro auren ko?,tunda na baki dama na ganin canji kafin dawowata saidai har naje na dawo din banga wani canki ba,it means abdallah jeka auri ero ko?''


Idanunta cikin nashi tana dubanshi kuka takeson tayi saidai ta kasa
''dama kana sonta din abdallah na dade da sanin hakan,toma meye donta ka aureta,hakan na nufin yankewar numfashin maryam da qarewar rayuwarta aduniya?''ya fuskanci ta fara ficewa daga saitinta,don haka sai ya miqe yana sake saba babbar rigarsa yana shirin ficewa tare da cewa ''Allah ya kyautq,Allah ya baki haquri,sai mun dawo''
tsintarta kawai yaui a gabansa tana tura qofar hadi da jingina jikinta da qofar,hawayen da bataso su fita su suka soma turereniya kan kuncinta.


Ta jingina kanta da bango kana ta saki kuka,muryarta a shaqe cikin raahin sanin me yake fitowa daga bakinta tace
''idan kana so ka tafi kaje,amma banu inda zaka fita abdallah sai ka tsaga qirjina ka cire zuciyata ka tafi da ita,wananna wanne irin so ne?,wanne irin horo ne wanan?,na gaji.....na gaji abdallah da irin wanann horon,me yasa kake ma zuciuata irin wanann hukuncin?,me yasa ka kasa gane qirjin maryam cike yake da so da kuma qaunarka?,kasan matsayinka a cikinta kuwa?''


Kasa tsayuwa yayi har sai da ya qarasa inda take tsayen yasa hannayenahi duka biuun ya dafe shima qofar ya yiwa maryam din rumfa,numfashinsa na fita da sauri,wani irin nau'in farinciki da baiyi tsammanin akwai irinsa cikin duniya ba ya mamaye ilahirin jiki jini tsoka da zuciyarsa yace
''abdallah ya dade da sanin ya dasa qauna cikin zuciyar maryamunshi,irin qaunar da ko mutuwa kayi bata barin zuciya ta huta,abu daya abdallah yake da muradon ji daga bakin mace qwaya daya tal aduniya shine *NIMA INA SONKA ABDALLAH KWATANKWACIN YADDA KAKE SONA K......*


*NIMA INA SONKA ABDALLAH FIYE DA YADDA KAKE SONA,FIYE DA YADDA KAKE TSAMMANI KO HASAAHE CIKIN ZUCIYARKA*,ta fada cikin tare numfashinsa ba tare da ta barshi ua kammala fadar abinda zaima fada din ba,kasa daurewa yayi sai da ya ji duminta ajikinsa,sai da yaji hucin numfashinsu na gauraya guri guda,gaba daya ta narke a qirjin nasa tana sake cusa kanta cikin qirjin nasa,tsaiwa ce ta gagaresu ya jata gefan gadon suka zauna,bai janata kuka na don shi kansa badon kada ya nada yammazqn ba dira kanshi zaiyi a kafadarya ya sha kukanshi saboda tsabar farin cikin da yaji yana kewaye duniyar subhana da shi


A hankali kukan ya soma jan baya sai ta janye jikinta ta dubeshi da brown oily eyes dinta da a yau suka sauya kama
''abdallah......mero fa?''ta tambayeshi tana jan majina,dariya taso qwace masa dik da haka sai da murmushi ya wadaci fuskarsa,ta tsareshi da ido sosai da alama kishi ne ya bude fagenshi cikin zuciyarta,sai da ya lakuce mata hanci kana yace
''gaki nan,ai kece *MERO NA*kuma kece *MAIRAMU* hakanan kece *DIYANA* duka''
kunya ta kamata,wai haka abdallah ya qware wajen buga game ne?,bata tsammaci a fili tayi maganar na sai da taji yace
''yes abdallah good player ne,sanna kuma winner ne,yau nayi winning,the game is OVER today''shigewa jikinsa tayi yama boye kanta aqirjonsa murmushi kwance kan fuskarta,hannunahi duka ya sanya ya marabceta zuwa jikinsa yana fadi cikin dariya dariya
''ashe haka kike da kishi maryam?,amma fa kin danji kunya kadan,kishi da 'yar qauye?,ya akahi kika aminta abdallah zai iya duban wata mace dina ma burgewa ma balle a kai ga batun so,macen ma irin mero,kin manta da su abida salma saddiqa zubaida da sauransu,basu isheni kallo ba sai mero?''


Kuma fa haka me,but ya akayi ta kasa tunanin hakan kishi duk yabi ya rufe mata ido ,ba shakka taji kunya,sake duqunqunewa tayi a jikinsa
''amma fa ta bangare guda kin burgeni haka nan kin gama biyana''ya fada yana lalubar kunnenta son so yake maganar ta koma ta sirri tsakaninsu
''yadda kika nuna kishi na na tabbatar cewa ni din ba qaramin dan gata bane''



Tayi har da ido duk da bai ganinta,can qasa muryarta tace
''amma daurin auren wa zaku a ni'ima,kuma waye zai zauna a bangaren nene na da''
''daurin auren mero,amma fa meron qauye,kuma a ni'ima din sannan bangaren nene na da anan zata zauna nata ne''
sai ta miqe daga jikinsa,hawayen ta na som dawowa
''abdallah ya zaka yimin haka,dai da zuciyata ta gama kamuwa da qaunarka zaka qara aure,bazan iya ba....bazan iya sharing wata da kai ba Allah,ina kishinka fiye da yadda kake zato''ta fada tana girgiza kanta tare da yunqurin sauka daga gadon,wayyo farinciki ya kamashi kamar yayi adungure,tuni ya riqota yana girgiza kai shima ya birkitota ta fada jikinsa ya rungumeta tsam


''Allah na gode maka da ka bani mai kishi na,nasan ba komai ya jawo hakan ba face tsatsar qauna,calm down madam,maro zata auri labaran ne nata nacan qauye na daukota ta zauna nan ne tare da mami ta dinga tayata da aikace aikace da kula da gida,tunda mamin tace tana sonmu tana son zama da mu amma ta rantse gidan mu zamu tafi,ba zata zauna tare da mu ba gudun shiga haqqinmu,labaran kuma na bashi aiki cikin kamfanoni na na nan kano,kuma banyi qarya ba *YAU ANGON MERO NAKE AMMA MERO DIYA NA* don na tabbatar yau ba zaki tsallake tarkona ba saikin fallasa min da bakinki qaunar da kike son binneta cikin ranki bayan akwai mamallakinta,shi yasa nayi miki adon angwayen don nima ango ne,haka daga yau ba zaki sake kwana gidan mami ba sai cikin gidanmu,gidan da na fara ginashi tun daga sanda na fara tizali dake a rayuwata,don ke dama na ginashi na dana jeshi dalili kenan da yasa a china na muku shigar sauri na zabi *gadon amarcinmu* don ni kadai nasan wanda zaifi dacewa da gidan,a lokacin mami na ganin na miki shishshigi batasan tanadi na yiwa kaina ba''


''wato abdallah mugun dan duniya ne?,ya iya buga qwallo son ranshi cikin hikima kuma ya saka ta cikin raga ba tare da golan ya sani ba''maryam ke gulmarsa cikin ranta bayan tayi luf a qirjinsa,tashi yayi ua fidda babbar rigar jikinsa ya dorata saman madubi bayan ya je ya sakawa dakin key,ya cire yar cikin ma daga shi saura farar vest dinshi qal da dogon wandon shaddar,gadon ya dawo ya haye yana fadin
''yau kam nima zan more soyayya mai 'yanci''sai ya kuma bata kunya ta cusa kanta tsakani cinyoyinta,sam ta kasa hada udo da shi,kowanne sakon kunya yake sata turata ciki,anan ya lalace yana gaya mata yadda take da tasiri cikin zuciyarsairin girman matsayinta,da irin yadda yake ji game da ita,yadda sonta ya dade da illata zuciyarsa,duk inda ta duqa sai ya hanata,yace ta barshi yau ya bararraje ya fidda duk wani feelings da yake ji game da ita,daga qarshe tallafe kumatunta tayi tana kallonshi,tayi imanin ya zauce cikin so kamar yadda ita ta zauce,saidai tsakanin shi da ita batasan wanda yafi wani ba,sau biyar hisham yana kiransa yana katsewa,qarshe ma ya daga yana fadin
''kaga malam idan zaka kama hanyarka ka wakilceni shikenan,nikam a inda nake yanzu ko mami,nasan zata min uziri''da yaga yaqi daina kiran nasa sai ya kashe wayar baki daya ya jawo bedside ya wullasu ciki yana jan tsaki ya sake dawowa sukayi zaman dirshan saman gadon suna kallon junansu cike da shauqim bege da qauna


Itama mamin ba ta nemi ko daya daga cikinsu ba kamar tasan tsiyar da abdallah ya qulla,cikin dakin sukayi sallar azahar har ma da la'asar,babu wanda yayi tunanin wani abu waishi abinci a cikinsu,wani irin shauqi ke dawainiya da su wanda gaba dayansu basu taba zaton akwai irinshi ba,a haka ma maryam na doddojewa saboda tsoro da gudun kada a tafka abun kunya cikin gidan suruka,ya qaraci fitinarsa sau biyu yana wanka tana kallonsa,


Sai da suka idar da la'asar maryam tace
''ya kamata ka tafi haka,kaga kada mami taga rashin,hankalinmu''kamar ma ba da shi take ba sai ua dira kansa saman cinyarta yayi kwamciyarsa yana fadin
''babu rashin hankali,tsakanin miji da mata sai Allah ita kanta mamin ya sani,nasam ta mana uziri,uziri kam dole ne ayi mana musamman ni Allah sarki da na jima ina faman rainon soyayyarki tun kima qwaila''ya qarshe maganar cikin salon zolaya
ta fara tura bakinta tana qoqarin tureshi
''ni daga ni,nikam ba qwaila bace ko a da dinma''yadda ta turo bakin ba qaramin sha'awa ya bashi ba,bai iya haqura ba sai da tsotseshi tas,abdallah na haukata ta iya yau da salon soyayyarshi tana zaton na gaba sawa zaiyi ta manta kowa da komai


cikin haka sukaji ana knocking,aka rasa mai magana tsakaninsu,murya qasa qasa tana zare ido tace
''mami ce fa''
kafada ya daga ya ware hannunshi kana ya miqe ya nufi qofar,ido ta sake zarowa ta biyoshi da sauri tana roqonsa qasa qasa saitin kunnanshi kada ya bude sai yasa rigarsa
''sai na cire wanann ma na zauna da boxer ki da kanta ma idan mami ce anjima zata kaimu gidanmu''kunu tasha tana miqo masa rigarsa kana ta fece bandaki ta saka maqulli ta buya,bai kuwa saka rigar ba ya budewa mamin,ita kanta sai da taji kunya ta kamata,ta kautar da kanta sanan tace
''ba kai nake nema ba diyata nake nema,kasan bata gama warkewa ba akwai sauran magungunanta da zata sh''
shima sai ya hau sosa kai don ya gama fuskantar inda mamin ta dosa
''mami ki

Please Login or Register in order to submit comment