Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

nasara*?''
sai da tadan shiga tunani sannan tace
''eh ina jin sunanshi mama''
''yauwa,kinga sanannen mutum ne kuma fitace tun kafin rasuwarshi,yaro daya Allah ya basu wato *Abdallah*duk da cewa yana da wata matar amma Allah abi bata haihuwa da shi ba,saidai ya riqe mata nata uaran da ta taba haifa awani gidan mata ne su biyu da nimiji daya yanzu haka duka suna tare a gidan duk da rasuwan shi alhj abdulkareem din hakan baisa sun raba mazauni ba,mamanshi na matuqar sonshi da kaffa kaffa da lamuranshi,duk da haka ana farautar rayuwarsa don kusan sau biyu kenan ana zuba poising abincinshi,ta rasa daga ina matsalar take,kuma duk lokacin da hakan ya faru idan aka tashi binncike sai a samu da hannun kukunshi,hakan yasa take canza masa kuku kala kala,amma har yau babu wanda hankalinta ya kwanta da shi


abdallah shine shugaban jami'an tsaro na farin kaya wato *S S*na nijeria gaba daya,wanda aikinsa kansa na buqatar ya zamo cikin kulawa da tsaro na musamman


bata da lokacin zama agida kasancewarta cikakkiyar likita kan fannin matsalolin da suka shafi mata,wannan ne yasa ta bayar da cigiyar amintacce ko amintacciya wanda ya qware kota qware afannin girki,to qawarta aminiya ta ce hakan ne yasa ta bani cigiya ni kuma naga ke kika fi cancanta da wanna aikin maryam,ina fatan kin fahimceni abunda kuma ya shige miki duhu kina iya tambaya ta''


shiru tayi domin tana jin abun da kamar wuya,sam bata ji ya kwanta mata ba aikin,tamkar aikatau zata tayi,kenan tunda aikin dafa abinci zata gidan wasu?,anya kuwa zata iya amsar tayin maman,amma tana jin nauyinta ,ba zatq kallon tsabar qwayar idonta tace mata a'a kai tsaye ba,kusan minti biyi sannan ta ajjiye numfashi
''ina ganin mama zanje na sanar da maga batana tukun,idan yaso duk abinda suka yanke akai zan sanar miki''
''yayi kyau,hakan dai dai ne maryam,wannan shike dada nunamin hankalinki da kaifin tunaninki,amma ina fatan bazaki watsa min qasa a ido ba''
''insha Allahu''
ta fada ka a qasa''
a haka sula rqbu bayan ta baiwa hindatu dubu daya tace ta siyi kayan kwalliya


cikin mota hindatu ta isheta da karadin wallahi yaya maryam ki amshi aikin nan
murmushi kawai tayi
''yarin ya ce ke hindatu har yau baki da hangen nesa''
''to,ya maryam meye aibu a ciki?''
bata amsa mata ba sakamakon jin ringing din wayarta da tayi ta soma kiciniyar cirota dqga aljihun jakar,raliya ce mai kiran
''hello ummin fadil''
''na'am mommyn fadil kina ina ne?''
''kin ganni a hanya na dawo ne a wata unguwa''
''yauwa don Allah ina son ganin ki ne ya za'ayi?''
''babu damuwa bari kawai na qaraso''
''yauwa ta gurina''
dariya ta bata tace ''sai na qaraso''ta maida wayar jaka sannan ta yiwa mai adaidaita bayanin inda zai juya da su''

🎄🌲🎄🌲🎄🌲

''daga ina kuke da yammacin nan ne?''raliya ta tambayi maryam sanda take dire musu drinks
''hmmm,wallahi kinga haj atika ce tayi kira na,wai ta samamin aiki gidan marigayi abdul kareem mai nasara''
sai taga fuskar raliyan ta sauya ta dan tsuketa
''ba zaki koma wani aiki ba,aure zakiyi maryam''ta gada kai tsaye tana kallon maryam din
ba tare,da kawo komai cikin zuciyarta ba tayi murmushi
''banda abinki qawata ba sai Allah ya kawo mijin ba?''ta fada cikin rashin kulawa
''Allah ya kawomiki miji maryam''sai da taji qirjinta ya wani irin buga
''miji?,wa ya gaya miki,qarya ne ni babu mijin da na samu''
matsowa tayi sosai ta kama hannayen ta
''maryam kin amince da ni kin kuma yarda da amincin dake tsakaninmu?''
''me ya kawo wannan tambayar kuma raliya?''ta tambayeta cikin yanayi na shiga duhu
''maryam so nake ki auri nasir mijina''


a hagunce take kallon raliyan,jo tayi lamar ta doka mata guduma atsakiyar ka,gani take kamar ba'a hayyacinta take ba''raliya,me kika sha yau,ko baki da lafiya?''
murmushi tayi
''nasan zaki fadi haka maryam,amma ras nake,kuma nasan me nake,cewa nayi mijina nake so ki aura nasir''
''shi ya aiko ki lo ke kika aiko kanki?''ta tambaueta tana mata kallon ba a hayyacinta take ba
''ni na aiko kaina tare da amincewarsa''
zame hannayenta tayi ta miqe
''idan kin warke kya kirani muyi maganar da kika rani domin ita,don dai wannan ban daukeshi da muhimmanci ba''
kamo hannunta tayi
''zauna maryam,wallahi a hayyacina nake,kuma lafiyata lau''


wani kallo ta watsa mata''sake ni raliya,ni 'yar halak ce kuma nasan halacci na kuma yi imani da akwaishi,idan haka kike to ni ba haka nake ba,idan kuma nasir din ne ya saka ki to ki gaya masa ni maryam 'yar halak ce''ta zame hannuwanta ta fice yayin da raliya ta bita tana qwala mata kira amma ko waiwayota bata yi ba,hindatu dake farfajiyar gidan tana waya itama wucewar maryam din ta gani sai binta tayi a baya


kuka zata yi ne ko ihu?me kuma yake shirin faruwa da ita?me yasa guguwar rayuwa ke walagigi da ita?,yau wai amiyarta ke gaya mata ta auri mijinta,ta ina ta yaya ma zata iya auren mijin raliya ko su biyu ne suka rage a duniya,ko da suka ke gida mama kasa gane kanta tayi,don tunda ta shigo gidan dakinta ta wuce kai tsaye,cikin damuwa maman ke tambauar hindatu me ya faru da maryam din
''ni dai mama da mukaje gidan hajiya lafiya lau muka fito,kuma iki ta samar mata gida alhj abdulkareem mai nasara,amma dai mun biya gidan anty raliya,to nidaiina waje bansan me suka tattauna ba naga dai ta fito da sauri ma biyo bayanta''
''alhj abdulkareem mai nasara?''mama ta maimata sunan don ba boyayyen mutum bane,mai arziqi ne na gani a fada wanda akayi qiyason duka nigeria babu wanda ya kama qafarshi


''to Allah ya kayuta,indai raliyance ai ba'a ashiga tsakaninsu,idan kuma aikin ne ma zamuji,qyaleta hindatu,nasqn zata min maganar da kanta''don shaquwar dake tsakaninsu yasa maryam bata boyema maman tata duka damuwarta




*mrs muhammad ce*👑



📚📚📚✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻
[9/17, 12:50 PM] 80k: 💖💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺🌺
💖💖💖💖💖💖💖
🌺💖🌺💖🌺
🌺💖🌺💖
🌺💖🌺
🌺💖
💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺
💖💖💖💖💖💖💖
*WRITTEN BY*
*SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
🌺💖🌺💖🌺💖🌺
💖🌺💖🌺💖🌺
💖🌺💖🌺💖
💖🌺💖🌺
🌺💖🌺
🌺💖
🌺


▶9⃣




kwana guda da yini daya bata ce da maman tata komai ba,itama zuba mata idon tayi bata tambayeta ba


kwana na biyun ne qarfe uku taji sallamar raliya,tana kwanve can cikin dakinsu saman katifarta,don yanzu zaman daki da kwanciya kuma ta aira wanda hakan baya rasa nasaba da yawan tunanin da take fama da shi,sai da gabanta ya fadi lokacin da tqji suna gaisawa da mama ta fadi mata tana cikin dakin


jawo dankwalinta tayi tana dauraqa tare da qoqarin yashi duka a lokaci daya,raliya ta iso bakin katifar ta zauna bayan ta shimfide fadil dake sharar bacci a gefanta
''na gode diyana,na gode''
''ai ni ke da godiya''ta fadi tana sake matse fuska
''wai ni zan ta kiranki maruam amma kiqi dagawa?''
''kadan ma kika gani matuqar kina kan qudirinki,nan da dan qanqanin lokaci zansa almakashi na datse igiyar mu'amala ta dake,tunda ba son Allah da annabi kuke min ba,so kuke ku cutar da ni''
dafe bakinta raliya tayi tana kallon maryam din kamar yau ta fara ganinta,ta sani babu shakka ba qaramin baci ran maryam din yayi ba tunda har ta iya furta mata haka,tafi kowa sanin halinta na rashin son fada da tashin hankali


''sonki muke kuwa maryam,saidai ke dake ahirin juya manufarmu ta alkhairi ki maisheta ta sharri,meyw aobu cikin aurenki da nasir maryam?''kafeta tayi da ido cikin bacin rai tace
''baki bar maganar,nan ba kenan ko raliya?''
''ta yaya kikeso nabar alkhairin da na hango miki ha wofanta kenan a banza?''
''lallai babu shakka kin gaji da hulda da ni.....ina zuwa''sai ta yunqura ta miqe kana ta fice


mintina kadan sai gata sun shigo tare da mama
''wai me ya hadaku ne da raliyan?''maman ta tambaya tana daga tsaye ba tare da ta zauna ba
''mama kinji abunda raliya ke fada kuwa,ba shakka ina tsammanin ta haukace ne,wai mama na auri nasir mijinta fa take cewa''
ba shiri mama ta nemi giri ta zauna,ta dubi raliya sosai
''da gaskene abunda maryama ke fadi?''
cike da tabbatarwa ta girgiza kai
''eh mama haka ne,ni a ganina ni da maryam mun zama daya,na yadda da ita na kuma aminta da kyawawan halaye da dabi'unta,na tabbata ba zata cuce ni ba,to mama laofi ne don na gayyatota tazo mu zauna qarqashin inuwa guda?''


azafafe maryam tace
''kinjifa mama irin abunda take cewa,ro billahil azim indai raliya bata sauka daga kan bakanta ba na miki rantsuwa mama har da Allah daga yau babu ni babu ita har abada''
tsot dakin yayi son su kansu aun sani matuqar maryam ta rantse akan abu to sai ta aiwatar,kuma alamu duka sun nuna irin yadda batun ke taba mata zuciya ba qarami bane,maman ce ta soma magana
''koda maryamu ta amince da maganar ma ni bazan amince ba,haba raliya aisai duniya ta zagemu,jama'a su saka mu a tadinsu,idan banda abunki ma raliya kwata kwata shekarunku nawa da yin auren,banda quruciya haka kawai kuna zamanku gwanin sha'awa ki dinga kira ma kanki kishiya uhm raliya?,na roqeki nima ki bar maganar haka nan kinji?''
qwalla ta cika mata ido ta tausayin maryam don qaunar da take mata ta fisabilillah
''shikenan mama,koda baki roqeni ba zan bar zancen ko don kada na rasa aminiya irin maryam,saidai....maryam na gode,na gode da kika nuna min iyaka ta''
duk da taji rashin dadin batawa raliyan da tayi amma sai taji kamar an tafiyar mata da wani qullutu da ya tokare mata wuya,sai taji damuwarta ta rage farashi zuwa kaso tamanin


durqusawa tayi bayan ta miqe tana qoqarin daukar fadil tace da mama
''mama ni zan wuce''
''kinga malama ajjiye fadil din ni zan daukeshi,tunda ba ke kadai bace ai uwarshi ba''cewar maruam tana yafagyalenta don yi mata rakiya,don ta fuskanci tafiya,zata yi,ta san halin raliya ciki da bai tasan fushinta koda ta tsaidata ma ba hirar atziqi zasu yi ba
''ni kadai ce mana uwarsa tunda kinqi ubansa''ta maida mat martani tana qoqarin ficewa,murmushi kawai maryam din tayi ta saba fadil din ta biyo bayanta


''halan driver ne ya kawoki?''
''ban sani ba,idonki ya baki amsa''tave da maryam din lokacin da auka fito tana gaba ita na binta abaya,mirmuahin dai ta kuma yi har beuty points dinta suka loba
''Allah ya baki haquri,yau kam ai akan gwiwa kike sai lallabe''
''a'ah,akan haba nake''
amsar da ta bata ta sanya maryam tuntsirewa da dariya har itama raliyan ta dan murmusa don fushinta da maryam ba ya wani tasiri
suna isa gaban motar ta ganshi zaune,shi ya kawota kenan,raliya ta bude ta shiga yayin da maryam ta galla masa harar lokacin da suka hada ido,dariya ya tuntsure da ita yana kallon raliya da tayi kicin kicin
''kada kice komai,don babu ruwan nasiru,kinga kanwar nan''
''babu wani nan,waye baisan halinku maza ba,to wllahi bari kaji,idan ka sake ka yiwa aminiya ta kishiya ban yafe ba koda wace ce kuwa,ke kuma kici gaba da nema masa aire kinji ko solobiyo''ta fada harda dan kama kunnen raliyan
dariya abun nata ya basu
''ni don Allah sake min kunne,tunda kin gujemu dai ba shikenan ba''
''indai irin wannan gudun ne raliya am sorry to say....zanta gudunku har abada''ta dan ja da baya ta rue musu qofar tana murmushi sanna ta dan sara mata shigen yadda sojoji suke
''Allah ya huci zuciyar ranki shi dade,oya kai kuma kaja mini aminiya ta ahankali''
''oho dai abanza tinda yau gaku a rana''ya fadi yana yiwa motar key tare da cillawa raliya gwalo
''wlh a inuwa ka ganmu,kuma duk qwaqwqwafinka ba zaka taba ganinmu a rana ba,ku sauka lafiya,sister am sorry,sai munyi waya''


koda ta koma gidan cikin al'ajabi suke tattauna zqncan da mama,maman ta kuma yabwa qwarai da irin qaunar dake tsakanin maryam din da raliya,ta musu addu'ar Allah ya dorar har tsufansu
sai a san nan ne maryam ta samu sukunin yiwa maman zancan aikin da hajiya atika ta samar mata,shiru maman tayi kamar yadda maryamun tayi tana jirqn cewa maman,shudewar mintina kusan biyu kafin tace
''ke me kike gani game da aikin,tunda kinga azahjrin gaskiya zamanki babu aikin babu dadi,tunda kin riga kin saba,hakanan zai debe miki kewa,baya ga haka harkar makarantar hindatu wa zqi ci gaba da daukar nauyinta idan har kika daina?,amma ke me kike gani mene ra'ayinki?''
''aini mama banida wami zabi sai abunda kika ce''



''kina da zabi mana maryamu zan tauye miki haqqinki ne?,amma dai abinda yafi kawai shine kici gaba da addu'a,Allah yayi miki zabi mafi alkhairi''
''ameen mama''
da haka suka saki maganar suka shiga kuma wani batun daban kuma,haka rayuwarsu take su uku suke yinta,su kashe su binne abinsu babu maiji,hakan ne ke qara haushinsu,cikin zukatan al'ummar gidan


sati guda da maganarsu da haj atika amma har yau ta kasa yanke komai a kai,kwana bakwai daidai da azahar tana sharar tsakar gida ta jiyo sallamarta,cike da mamaki ta yi mata sannu da zuwa sannan tayi mata jagora zuwa dakinsu


ruwan sanyi na pure water da alalen da sukayi ta ajjiye mata sannan ta zauna suka gaisa
''baki da kirki maryamu''haj atika ta fada tana dubanta
murmushi tayi ta dan sunkuyar da kai
''kiyi haquri mama''
''tashi kike abunki da mamanki ma zanyi magana,ko abbanki yana nan?''
''eh,bari na dubo miki''ta fadi tana miqewa,
taci sa'a kuwa yana niyyan fita ta tadda shi,ta sanar da shi sannan ta zura mayafinta ta fita gidan maman fatima maqociyarsu


mintina talatin suna cikin hira isyaku ya shigo yana zumbure zumbure
''ke kije bana yana kiranki''ya juya ya fice abinsa,maman fatima tace
''oh ni Allah,Allah ya kyauta''
''hmmmm,ameen bari naje maman fati sai anjima''maryamu tayi mata sallama ta fice


bata tarad da haj atika ba,sai babanta da mama dake zaune
''baba gani''ya fada bayan ta samu guri gefe da su ta zauna
''maryam''
''na'am baba''
''ki shirya gobe idan Allah ya kaimu ki hada duka abunda kike da buqata hajiya zata zo zaki tafi gidan nan da kukayi magana da ita ta samar miki aiki''
cikin rashin fahimta ta dubeshi
''amma baba ni ina ganin koda zanyi aikin ma ai bani da buqatar tafiya da kaya na,tunda ba wani garin bane ko?''
''ke,bani son sakarcin banza,na riga da na gaya miki,ki hada kayanki,suna da buqatar zamanki ne a can gidan,yo idan kin zauna anan din me zaki tsinana min,illa inyita ganinki baqinciki na ci gaba da damu na?,kije kawai banason kuna sauran qorafi kinji ko?''


kai ta gyada hawaye na layi bisa kuncinta,wannan sam bai dadashi da qasa ba ya miqe ya fice abinsa,kai ta hada da gwiwa ta rushe da kuka,duk yadda taso daurewa zuciyarta ta kasa
''wai me yasa baba baya sona ne mama,me nayi masa?''ta tambaya cikin kuka
''kul maryam,kada na sake jin wannan mummunar maganar a bakinki,mahaifinki ya isa da ke,saboda haka nima bana buqatar wani qorafi kibi umarninshi kawai''
bata iya cewa konai ba face miqewa da tayi ta shige dakinsu zuciyarta na zafi tare da jin tsanar wannan sabon aikin,aikin da zai nisanta ta da mahaifiyarta,zai nisan tata da 'yar uwarta,mama binta tayi da kallo tana jin tausayin diyar tata sosai na sauka cikin zuciyarta,addu'a kawai take mata cikib ranta Allah ya yanke mata wahala,ya kawo lokacin da zata zauna ta huta cikin dakin mijinta

🎄🌲🎄🌲🎄

jikinta duka a sanyaye take shirya kayanta cikin sabon dan trolly dinta mai kyau pink wato ruwan hoda,hindatu ce ta rufe mata sannan ta jawo mata shi cikin parlour don bata da kuzarin da zata iya janshi


tsaye tayi cikin falon ta kasa cewa maman nata komai,don hawaye ne fal cikin idanunta da suya da zuciyarta ke mata,ji take kamar ta bar gida kenan,tana jin tamkar ta bar mamanta kenan,sai maman ce tace
''kuje hindatu jiranta suke,Allah ya bada sa'a,abu guda zan fada miki,ki riqe mutuncinki a duk inda kike,ki tsarw ksnki maryam ki kuma ji tsoron Allah,don babu wani abu da zan iya yi miki a lahira,iya kacin amfani na a duniya ne wajen tunatar da ke bin hanyar Allah,ki riqe amsna ki zauna da kowa lafiya''
kuka ta saki ta fada jikin mama,sai da taci kukanta sannan a sabule ta fice hindatu tabi bayanta da akwatin


sam basu lura da su ba sai shewa suka ji,inna hadiza nw da binta har da tafawa kamar sa'annin juna
''haka dai za'a qare a boyi boyi''inji inna hadizar,hindatu na shirin maida mata martani maryam ta damqe hannunta ta jata suka fice ba tare da ta bata damar tsayawa sun taya yinsu ba



*mrs muhammad ce*👑



📚📚📚✍🏻✍🏻✍🏻
[9/17, 12:50 PM] 80k: 💖💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺🌺
💖💖💖💖💖💖💖
🌺💖🌺💖🌺
🌺💖🌺💖
🌺💖🌺
🌺💖
💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺
💖💖💖💖💖💖💖
*WRITTEN BY*
*SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
🌺💖🌺💖🌺💖🌺
💖🌺💖🌺💖🌺
💖🌺💖🌺💖
💖🌺💖🌺
🌺💖🌺
🌺💖
🌺




▶🔟




shiru tayi cikin motar tana maida ajiyar zuciya,zugi take jo tana yi mata
har ga Allah da tana da iko ba zatayi aikinnan ba,sam bai kwanta mata ba ko kadan a rai
''maryam,kiyi haquri kinji,na fuskanci baki son aikin nan,amma ni mai sonki ce maryam,na yadda da tarbiyyarkk,ke yarinyace mai hankali da nitsuwa,idan da nasan zaki cutu a gidan wlh bazan gaba kaiki ba,ki kwantar da hankalinki na tabbatar zaki samu nutsuwa da jin dadi cikin gidan *haj hasiya*na da dadin mu'amala,insha Allahu ba zaki samu matsala ba,ki cire damuwa a ranki don Allah kinji maryamu''


ta sake sakin ajiyar zuciyar a bayyane ''to msma insha Allah''ita kanta tasan ta fada ne kawai amma Allah ne kadai yasan ranar daina damuwarta,bata taba rabiwa da maman nata ba sai yau


tafiyar mintina kimanin talatin suka iso unguwar,tun daga farkon unguwar zaka gane cewa ba qananan muta ne ke zaune cikinta ba,daga get din farko allo ne mai dan girma dauke da rubutu kamar haka
*welcome to millonier quaters*


sannu a hankali suke ratsa layukan,layuka ne tsararru tamkar a qasar waje,shuke shuke ne jere reras qofar kowanne gida,hakan sai ya yiwa layin ado ya zamo cike da furanni,layin ya burgeta sosai,duk,da uadda,zuciyarta ke mata babu dadi


qofar wani gida suka ja suka tsaya,dauke yake da madaukakiyar katanga da get mai tsawo da girma,horn tayi har kusan uku kafin wata qaramar qofa ta bude
kallo daya zaka masa ka tabbatar cewa qaqqarfan mutum ne,sanye cikin kaya riga da wando ruwan bula wanda ke alamta unifoarm ne a jikinsa


fuska a hade yake tambayarsu cikin karyayyen turancinsa na brooking
''wa kuke nema?''
haj atika ce ta amsa masa''gurin hajiya muka zo,ta san kuma da zuwan mu''ya sake tambayarta mene sunanta ta gaya mishi
bai sake cewa komai ba ya wangale mamakeken get din motarsu ta fada ciki


gurin parking ne wanda yake cike da motoci na alfarma a qalla guda goma,haj atika ta raba tata gefe kana suka fito,sunyi tafiya ta kusan minti biyar kafin su cimma dogon valcony din dake fuskantarsu wanda lullube yake da nau'in furanni kala kala masu qamshi da kyawun kaloli,qofa ce mai fadi cikin valcony din wanda suna shiga ta kaisu ga tafkeken falo wanda ya lamushe rukunin kujeru har set biyar saboda girmanshi


iya qawatuwa an qawata falon iya ganin mai kallo,saidai kawai na barwa mai karatu ya siffanta shi iya yadda zai iya,shiru falon yake sai qamshin freshner da ya gauraye falon da na a.c




_kuyi haquri da wannan don Allah,ku bini bashi gobe uxiri ya riqeni_



*mrs muhammad ce*👑



📚📚📚✍🏻✍🏻✍🏻
[9/17, 12:50 PM] 80k: 💖💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺🌺
💖💖💖💖💖💖💖
🌺💖🌺💖🌺
🌺💖🌺💖
🌺💖🌺
🌺💖
💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺
💖💖💖💖💖💖💖
*WRITTEN BY*
*SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
🌺💖🌺💖🌺💖🌺
💖🌺💖🌺💖🌺
💖🌺💖🌺💖
💖🌺💖🌺
🌺💖🌺
🌺💖
🌺 ▶1⃣1⃣



tsit falon yake tamkar babu kowa cikin gidan,da ido suke kallon falon tare da yin sallama koda zasu samu wani a akusa ya amsa musu,saidai har yanzu babu motsin kowa
qofar dake hannun hagu suka ji an murda an bude,duk da 'yar tazarar dake tsakaninsu suna iya jiyo dariyar su,su biyu ne daya a gaba daya abaya
matashiya ce 'yar kimanin shekara ashirin da biyar sai wata agefenta wadda zata iya bata shekaru uku


basu kula da su maryam ba dake tsaye a tsakiyan katafaren falon ba har sai da suka zo daf da su,ta gaban ce mai kimanin shekaru ashirin da biyar din ce ta soma qare musu kallo,kallo ne na qurilla da saka tsarguwa,sai da ta gama tace
''mu je ko jidda na taka miki''ta fada tana kallonsu sama da qasa
har zasu gota haj atika tace
''ji mana''ba tare data dawo ba ta waiwayo tana jirqn me zasu ce
''don Allah ko zaki mana magana da haj bintu?''


cikin halin ko in kula tace''ku zauna ku jirayi fitowarta,may be yanzu zata fito''daga haka tayi gaba abinta tare da jan hannun wadda suke tafiyar tare,haj atika tace ''zauna maryam,bari na kira hajiyar''
maganar second uku fayi da ita ta kashe wayar,cikin minti biyar katafariyar qofar dake hannun dama ta bude,kyakkyawar mace ce 'yar kimanin shekara talatin amma a zahiri ta kai shekara hamsin da uku,kyawun jiki iya ado da kwalliya hade da tsafta ne suka wawashe ragowar shekarun suka boyesu


sanye take da swiss lace ruwan toka da adon orange,sai labcoat da ta dora fara tas a sama,takalmin qafarta hill ne shima fari ne qaf kamar ranar ta fara sashi,ta nade wuyanta da mayafi orange,fuskarta qunshe da yalwataccen murmushi
''sannu hajiya,maimakon ku shigo sai kuma ku zauna anan,ku taso don Allah''ta fada tana nuna masu qofar,gaba tayi suka bita abaya


abun mamaki sai gasu a wani gurin,guri ne mai kama da gurin shan iska,saidai dauke yake da tyles fari qal illa tsakiyar gurin da aka yiwa shafe din cycle aka cika shi da 'yan shuke shuke masu furanni dake fidda qamshi
qofa ce ta glass wanda na waje baya iya ganin na ciki bayan sun shiga ciki ta fahimci hakan,falo ne shima mai dauke da kujeru set biyu,gini ne sama da qasa wato mai bene,wanda matattakalar na acikin falon,tsarinshi abun sha'awa ne matuqa duk iya iya tsarinka sai ya burge ka,komai na cikin falon fari ne da milk,babu alamun qura ko dauda a tattare da shi sai kace yanzu aka bare komai aledarsa aka sanya


''bismillah''hajiya bintu tace musu tana shirin zama
''hajiya ga maryam na kawo miki,kuma bani da haufi a kanta,ke kanki,nasan zaki ji dadin aiki da maryam insha Allahu''haj atika ta fada bayan sun gama gaisawa
murmushi ta sake yi
''ina fatan haka,maryam sannu,ina fata hajiya ta gaya miki komai,girki ne kadai nake so ki dinga yiwa yaro na,kada kiji a ranki cewa wai aiki kika zo,kisa aranki taimako na kika zo yi,ki dauki kanki tamkar diyata,domin dama ina cike da kewar rashin yarinya mace,to ina ji a raina yau Allah ya bani,abu daya kawai nake buqata daga gareki,ki riqe amana don Allah,ki kula ki kuma yi taka tsantsan da abincin yarona,nasan kinsan komai game da abubuwan da ya faru a kanshi,ina son *abdallah* don Allah ki kula min da shi,na rasa babanshi bana son in rasa shi''ta qarashe maganar muryarta na bayyana raunin da zuciyarta tayi


duk sai taji tausayin su ya kamata,sai take jin ina ma ita ta samu wanna gatan,ina ma ita ke da gata har kamar haka
''insha Allahu haj na miki alqawarin ba zaki samu wani abu mai kama da cin amana ba daga gareni''
hakan data fada dukansu yayi masu dadi har haj bintan na murmusawa
''idan kika min haka kuwa maryam kin gama min komaibani da abinda,zan saka miki da shi,gyara guda daya,indai kina son insinga jinki kamar diyar tawa da gaske to kada ki sake kira na hajiya,ki kirani da *mami* kamar yadda *Abdallah na* ke kirana''
sai a lokacin maryam tayi murmushi karo na farko,harga Allah taji dadin karramawar da tayi mata''to,mami''
''yauwa,na gode,hajiya atika na gode qwarai da gaske,bazan iya manta wannan taimakon da kika yimin ba''
''babu komai haj bintu,ai abdallah kamar da yake a gurina,ni zan wuce,maryam.....''
hajiyan ta fada tana miqewa


har waiting parlour haj bintu ta taka mata sannan ta dawo,da murmuahin dai nata ta dubi maryam
''taso,maryam na nuna miki daki,don fita zanyi asibiti ina da C S har mutum uku,Allah ne ma yayi ba zamu samu sabani ba''ta gaya mata lokacin da tayo gaba ta bita abaya,wani labule mai kyawun tsari ta daga daga sashen hagu na falon,saiga gajeran corridor ya bayyana,dakuna uku ne a gun,ta tura daki na uku ya bude tace
''bismillah maryam,ga dakinki,ni,zan fita ki zauna ki huta kafin na dawo mu shirya yadda lamuran zasu kasance,yau dai babu aiki,don Abdallan ma baya gari,amma gobe zai dawo''
''to,mami sai kin dawo''ta fada cikin girmamawa


tabi dakin da kallo bayan mami ta fita,daki ne wadatacce shimfide da carfet mai taushi,sai gado cupboard ta jikin bando da madubi hadi da dressing chair,curtains,dukkaninsu pink da fari,cikin dakin akwai

Please Login or Register in order to submit comment