Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

fiddo da wani foodflask daga cikin kwalinshi
''mata su dinga biyo maza gida suna neman aurensu?''
''kamar yaya baaba?''
''hmmm,yaran nan mana dake son yaron gurin hajiya abdullahi,dazu daya yarinyar nan itama tazo da kayanta na satittika,ummm.......salamatu,mu a da ba sai an kaiki daki ba ma kike sanin waye mijin?,idan ma kuwa har kinsan waye shi din kafin a daura aurenku to ko hanyar da yabi baki iya bi saboda kunya,idan kuwa tsautsayi ysda kuka hada hanya to sai kinkusa qamewa a tsaye vaki iya motsi har sai ya wuce''


dariya ce ta kubcewa maryam
''baaba kin iya bata suna,salma ake cewa ba salamatu ba''
''kome me take ne barta,abun nasu sai addu'a,ko kunyar hajiya basa ji,ko fada ne ya kama yi suke a gabanta,abunda mu ko abinci baka iya ci gaban suruka,wannan zamani wannan zamani yazo qarshe,fatan Allah yasa mu gama lafiya''
''ameen''maryam din ta amsa mata da shi,daga haka bata ce komai ba,ita kanta mamaki take,saidai babu ruwanta don bata shiga shirgin da ba nata ba


ana kiran sallar magariba suka kammala aikin duk girman kitchen din yayi kyau ya sake haske,lallai sabon abu akwai kyau inji baaba uwani,ita kanta mamin ba qaramin mamaki tayi ba,ta sallami sauran ma'aikatan tana yabawa qoqarinsu


dakinta ta kuma komawa sanda tafito daga kitchen din abida ce zaune gaban makekiyar t.v plasma tana kallo sanye da matsattsun riga da wando,kusan duka shigarta kenan ta fidda tiraici ko doguwar riga zata sanya sai ta samu mai tighting jiki,wanka tayi ta sauya kayan jikinta,ta daura alwala tayi sallah,tana saman dadsuma tana lazumi ta tuna zata kira fa hindatu,ta laluba wayar bata jita ba hakan ya bata tabbacin ta manto ta a kitchen,ta gyara zaman ijabin jikinta ta fice ta nufi kitchen


su uku ta tadda yanzu a falon abida salma da abdallah da suka saka atsakiya,kallo daya zaka musu ka tabbatar daga abidan har salman ba jin dadin zaman suke ba,shi kuwa hakimin na tsakiya zaune yana ta aikin amsa waya,bisa dukan alamu wani aiki yake shiryawa don taji bada order din yayi yawa cikin fada da fushi


ilai kuwa cikin sabuwan kitchen wear din ta ganta,missed call goma ta taras,hudu na hindatu hudu na abdur rahim daya na raliya,murmushi tayi don dama ta sani bata da masu kiran nata sai su,sai ta rasa wanda zata soma kira a cikinsun,cikin haka kiran mami ya shigo
''kina ina ne maryamu,na shiga dakinki ban tadda ki ba''
''mami ina kitchen''
''baki gajiya ne maryam aiki sai kace inji,already baaba uwani tayi abinci ki huta haka nan don Allah''
tana jin dadin qaunar da mami ke nuna mata qwarai da gaske
''wayata na manta ma nazo in dauka''
''ok,ki sameni a parlour na''
''to''ta amsa mata ta cire wayar daga kunnenta ta fita daga kitchin din


''ke mero''taji an fada lokacin da take qoqarin hawa matattakalar benan
kamar kada ta juyo sai kuma ta waiwayo din don ganin mai mata kiran,abida ce
''meye kika tsatstsareni da idanuwankin nan kamar na?,shawarma nake sonci,ki shiga kitchen yanzun kimin idan kin iya''
rausayar da kai maryam tayi
''batun iyawa na dade da wuce babinshi,saidai lokacin aiki ya qare,zaki iya barwa gobw idan Allah ya kaimu,tunda majority utensils din duka sabbi ne bamu bude su ba''


cikin izza isa da gadara tace
''ke,wai mai kike taqama da shi ne,ki fadi nawa ne albashinki duka a nunka miki bama iya kudin aikin yau ba,ban mance ba rannan haka kika mana wani abu tuwo sunanshi ko me?nace kimin wani kalar girkin kika ban banzan answear irin wannan,kinsan wace ni kuwa?''


sakin makarin silver din da maryam din ta riqe tayi ta juyo ga abidan sosai
''ni ba kowa bace kuma bana taqama da kowa face Allah,kudi kuma ba zaki bani yanke talauci ba har abada,matsayin da Allah ya ajjiyeni ya gamsar da ni sosai na kuma gode masa,gaskiyata na fada tsarin siki na kenan cikin gidan nan,baquwa ce ke ina zato shi yssa kike mantawa,sannan ke din ma ba kowa bace face baiwar ubangiji kamar yadda nike kowa kuma yake''


a hankali abdallah ya dago kanshi daga kallon wrestling a tashar mbc action da yake ya dubeta,sai yaji amsarta ta burgeshi,babu hayaniya cikin raddinta,cikin calmnesses and cool voice,sai ya dan tsaida abunda yake yaga yadda za'a qare
tuni fuskar abida ta canza,cikin bacin rai ta dubi abdallah
''mu sugar kana gani da jin abunda yarinyar nan ke gaya min ko''ta fadatana nuna maryam wadda tuni har ta kusa kaiwa qarshen benan


murmushi ya saki mai hade da yar dariya
''duk bakery din dake garin kano kin raina,kin rasa inda zaki ci shawarma ne?''
''zaka iya kaini ne?'
''a lissafin lukuta na babu wannan,idan kina so akwai direbobi sai wani daga ciki ya kaiki ya dauko''sai ta sake tunzura,ya yrfata gaban salma kenan?,abunda madyam din ta mata ya hadu da wanda abdallah ya mata ya zamar mata zafi biyu
a zafafe ta miqe tana cewa
''tunda kai bazaka iya daukan matakin komai ba to ni zan daukarwa kaina,bazan zauna talaka 'yar talaka wulaqantacciya ta dinga taba mutuncina ba''


wani murmushin ya kuma saki ya kima kashingida
''eh kuma fa,gaskiyarki nima na goyi bayanki,kamarki diyar ambassador guda bai kamata a dinga samun iein haka ba,jeki dauki mataki''
sai ya kuma tunzurata don ta fuskanci kamar gatse yake mata ko kuma jirwaye mai kamar wanka,a haukace ta haye saman


kujera ta samu ta zauna tana fadin
''gani mami''
''yauwa maryam....cewa nayi''maganar mamin ta katse sakamon kiran da ya shigo wayar maryam din,screen din ta duba,sunan abdur rahim ya bayyana,sai ta maidata silent taqi dagawa
''ki daga mana maryamu''inji mami
murmushi tayi ta dan sadda kanta
''um um mami,ina jinki''
cikin murmushin da salon zolaya tace
''kodai suruki na ne maryam?''


sai kunya duk ta kamata tayi qasa da kanta tana murmushi
,ganin tayi shiru yasa mami cewa
''Allah ya tabbatar mana da alkhairinsa,shawarata gareki ki riqe mutuncinki,ka kame kanki,mutuncin mace kunya da kamun kai,duk da nasan duka halayenki ne,idan na samu lokaci zan miki magana yazo inganshi mu gaisa''cikin jin dadi da gamsuwa da maganganun mamin take gyada kai,sai ta kuma tsokanarta
''bari nayi sauri na sallameki kada surukin nawa ya qosa da jirankin ko''sai ta sake bawa maryam din kunya


''kaya ne wadanda aka fitar da kayan firniture da za'a fitar gobe nake son ki zazzabi dukka abunda kike so ki kaiwa mamnki ko zatayi amfani da wasu wadanda bata so ta bada''
tayi mamakin yadda mamin ta bada kayqn,don kaya ne da babu abunda aukayi tamkar yau aka zuba su espicially kayan furniture din,ta wani fannin kuma ba abun mamaki bane saboda halayen mamin ne *karamci* da *kyauta*
sabanin wasu masu hannu da shunin da sun gwammace su saida kayan maimakon 'yan uwanau su amfana furniture ne ko kayan sawa,ko me zasuyi da kudin oho,bayan Allah ya wadata su ya basu arziqin amma suna maida kansu baya


''na gode mami qwarai,Allah ya qara girma''
murmushi mamin tayi
''bakin maryamu ya saba da godiya,nasha fadi miki ba haka tsakani na da ke''
kafin tace wani abu an banko qofar an shigo,abida ce kanta tsaye ta tafi gurin mami
''mami,ki shiga tsakanina da house girl din nan,hala bata san koni wace ba,ta raina ni matuqa,wallahi idan bata kama kanta ba zanyi sanadiyyar qulle danginta kaf babu wanda ya isa ya fito da su,batasan ba'a raina ni ba,bana daukar raini?''
kama kai mami tayi tana kallon abida
''qara kika kawomin ko mataki kika zo dauka?''cikin rashin iya magana tace
''duka mami''
ta riga da tasan abida rainon tabara ce,ta san ita har zuciyarta magana ta fada mai kyau,ta bar ta tata ta juya ga maryam ta tambayeta mai ya faru,a nutse ta gaya mata
''tashi kije maryam,sai da safe Allah ya bamu alkahairi''
''ameen mami''ta fada tana ficewa,yunqurowa abida tayi gurin maryam mami ta dakatar da ita


mamaki ne ya ishi maryam,tana shiga daki kiran abdur rahim ya shigo wayarta,murmushi ta saki ta isa gefan gadonta ta zauna sannan ta daga





*mrs muhammad ce*👑



📚📚📚✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻
[9/17, 12:53 PM] 80k: 💖💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺🌺
🌺💖🌺💖🌺
🌺💖🌺💖
🌺💖🌺
🌺💖
💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺
💖💖💖💖💖💖💖
*WRITTEN BY*
*SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
💖🌺💖🌺💖🌺
💖🌺💖🌺💖
💖🌺💖🌺
🌺💖🌺
🌺💖
🌺 ▶2⃣9⃣


*_HASKE WRITERS ASSOCIATION_*💡
*_home of expert and perfect writers_*







Kimanin awanni biyu suka shafe kan layi ita da abdur rahim din,ta fuskanci ya dan san wasu abubuwa game da ita wanda hakan ke qara mata amanna da qaunar da yake iqirarin yana mata din,tuni ta yanke ma ranta abdur rahim na daya daga cikin batutuwan da zasu tattauna a gobe ita da mamanta,bai barta ba har sai da ya fuskanci ta soma jin bacci tukunna ya mata sallama cike da qauna da bege mai yawa

🍂🍃🍂🍃🍂🍃

Abu na farko da ta fara cin karo da ahi cikin gidan nasu bayan yin sallamarta shine dambe tsakanin huwaila da haduza abinda zata iya cewa bata taba gani ba,daga gefan huwaila lubabatu ce da binta ke zuga uwarsu,yayin da kuna gefan hadizar kuma shamsiyya da yasira ne suma ke nasu aikin sai jamila dake zaune bisa dakalin qofar dakin mahaifiyar tata da uban akwati a gaba,idanu jajir wanda ke nuna bisa dukkan alamu kuka take sharba ko kuma take kan sharba din,mamanta ta hango na shirin fitowa daga dakinta hannunta ruqe da dankwalinta tana mai qoqarin daurawa hindatu na biye da ita tana fadin
''don Allah mama ki barsu''


Da sauri maryam ta taya hindatu tarar maman nata
''mama wanna ba sabgarki bace,kin taba ganin suna dambe?,to ki qyalesun kamar yadda hindatu tace Allah ne yasan me ya hadosu,babu ruwanki mamana tunda koma mene lokacin da zasu qulla basu nemi shawararki ba,kiyi addu'a kawai Allah ya warware musu ita ta ruwan sanyi''


da dadin baki suka sanyata a tsakiya suka koma cikin dakin abinsu,har aka gama shigowa da kayan suna bala'i basu sani ba
''amma maryama gini irin wannan namun ai bai cancanci kayan gado na alfarma irin wannan ba''
dariya ma maman ta baiwa maryam
''haba mama,tunda Allah ya baki sun cancanta din kenan,yanzu aikin kawai zamu shiga yi har kitchen din''
hindatu dake tsaye wadda farinciki duka yabi ya cikata tace
''yauwa adda maryam,kinga zuwa gobe mun gama zama 'yan gayu,babu raini wallahi,don duk cikin gidannan babu mai arziqin siyan irin wadan nsn kayan''
dadiya duka ta basu don har yau hindatu shirmen auta bai saketa ba


sai da suka soma fidda na dakin maman suna shigar da wadancan sannan suka ankara,lubabatu ce ta fara gani ta zunguri uwarta dake riqe da habar zaninta daketa kwancewa saboda azabar bala'i tana qoqarin daurawa


''huwaila tayani gani,kinga su kuma wadan nan ina suka samo kayan alfarma haka''
da sauri ta juyo don ganin abunda lubabatun ke nuna mata,idanunta suka sauka kan kayan fadon da buhun shinkafa catoon na taliya mscaroni da couse couse wabda mami ta hada mata da su irin kayan da Abdallah ke rabo na musamman duk azumi sadaka ga mahaifinsa mafigayi alh abdul kareem mai nasara


''kinga inda ake abu,kare ya san ana abu a gidansu,tunda gashi yana gani a qasa''
wannna zancan ne ya dauko hankalin hadiza kan kayan
''mtswew,aikin banza aikin wofi,kayam haram din da aka samu ta hanyar haram har wani abun fariya da alfahari ne?,kwadayi dai ai mabudin wahala ne Allah na tuba nawa akayi''
''kamar ku kenan da ruwan ya qarewa dan kada ko?'' wani irin ashar hadiza ta lailayo ta narkawa huwaila
''ai wallahi qaryarki tasha qarya,tuni na gama fahimtarki dama huwaila,sai kima kinsan cewa ba'a ja da masu kudi''
tsaki ta ja kana ta turo daurin dankwalinta gaba
''yo Allah na tuba ina abun yake,ina qudan yake ballantana romonsa?,game ce anyita kuma yau anzo game over din,sai kusa haquri masu rano su dara daga inda kuka tsaya'ta antaya qeyar yaranta daki ta bar hadiza abakin qofar tana ci gaba da zage zage kamar zata tada jinnu,ta gama da huwaila ta kalli qofar dakin mama ta yi nata,ita kadai ita da yaran nata tamkar wasu sababbun tabi


hindatu kam babu abunda take sai sheqa dariya cikin dakin suna aikinsu maryam ta dan dubeta kana ta kau da kai ta ci gaba da ahimfida zanin gadon dake hannunta kan sabon gadon maman
''ko kema shirin bin sahun nasu kike irin wannan dariya haka''dariyar na ci gaba da cinta tace
''ai wallahi adda maryam ki gode Allah,kinsan wannan bala'in tun jiya ake zuba shi cikin gidan nan''
''amma ina baaba,bai tsawatar ba?''
''ya tafi gaya duba inna gwaggon baba,kuma ko yana nan ma ma zai tsawatar din akai?,mowarshi aka taba fa,jamila ce ta dawo gida jiya wujiga wujiga''


sai da gaban maryam ya fadi,a hanzarce cikin fuskar mamaki ta kalli hindatu
''garin yaya?''
''to yaya jabir yace baya yi ta taho gida har dactakardar sakinta kyawawa guda uku,a kuma karbe duka wani abu na dukiya ko kadara da ya mallaka mata,amma in fada miki baaba hadiza da yake jahila ce ba ilimi a take suka hau dan sahu ta maidata wai zata bashi haquri a daidaita,wallahi in taqaice miki ko zama bata yi ba bayan dawowarta sai ga jamilar ta biyo sahunta,da duka ya koro ta daga cikin gidan da qyar ta qwaci kanta,to kuma bala'i sai ya koma kan inna huwaila wai itace sila tunda dama ta taba cin alwashin sai ta wargaza komai''
hindatu ta sake qasa qasa da muryarta kada mama ta jiyota
''in taqaice miki adda maryam jiya dai har gun bokan da sukaje ya raba tsakaninsku da ya jabir sai da suka tona abinsu,cikin hargagin fadansu''


sai jikin maryam yayi sanyi,ta bar abinda take yin din tayi zaune gefan gadon,tabbas tasan ba'a yi mata adalci ba,saidai rabuwar aure ai ba dadi gareta ba,espicially yaran gidansu da dukkaninsu babu wani mai qwarin gwiwa kan aurenshi kullum cikin jeka ka dawo suke,to ga wata kuma sabuwata samu
''kinga ya maryam,kada kice fa zqki wani damu,sakayya ce Allah ya miki ita da gaggawa haka''ta fadi ita tana ci gaba da dame gadon aikin da maryam din ta saki


''a'ah,maryamu kin gaji ne,idan ba dama sai na aika hindatu ta kiramin laure ta tayamu''
girgiza kanta tayi alamun a'a
''mama haka abu ya faru da jamila kuma dai?''
''uwar asugwi din ta fesa miki din kenan ko''maman ta fada tana qarasowa cikin dakin,ta kama kunnen hindatu ta dan murde har sai da ta saki aiririyar qara tana dafe hannun maman
''don Allah mama kunne na,zaki tsinke kunnen autar taki fa ki rage mata kudin sadaki''
''ai gwara in tsinke kunnen tunda ya iya jiyo gulma ya fadawa addarshi''
da qyar hindatu ta zame a hannun maman


jikinta babu qwari haka suka dinga aikin,har ga Allah bata ji dadin mutuwar auren ba,tunda yau babu wanda,zaiso ace nashi ne kullum a bazawara,sai magariba uka kammala aikin komai yayi neat da shi,ta cire kaya jikinta ta daura zani da hijabi tq fito bandakin tsakar gidansu tayi wanka,tsakar gidan shuru da shi qwal kowa yana daka da mugun abinshi a zuciya,girgiza kai kawai tayi cikin zuciyarta tana fadin Allah ya gyara,sam rayuwar gidan nasu a karkace take kowa da inda ya dasa tasa alqiblar


tana cikin sallar isha'i kiran abdur rahim ya dinga shigowa wayarta,hindatu ce zqune kan kujerar dq wayar ke kai don haka ta daga,bata ankare ba taji sun shiga hira da hindatu,dama gata gwanar surutu,sai da ta idar sannan ta miqa mata wayar,kasa dagawa tqyi saboda kunyar ama dake gurin,itama maman na ankare da ita amma tayi kamar batq gani ba,dn tasan maryq din ba boye mata zata yi ba,cikin zuciyarta take addu'ar Allah yasa mijin aure ne diyartata ta samu


su ukun cikin kwano daya kamar ko yaushe suka ci tuwonsu na masara miyar busashshiyar kubewa,santi kawai maryam ke ti wa mama don tayi missing girkin maman sosai,mama gwana ce ba baya bace gun tsara girki musamman namu na gargajiya


zumudi yasa hindatu ta kasa shiru jin addar tata taqi tada zancan mutumin da ya kira din dazun
''wai adda maryam abdur rahim din dazun fa yace saurqyinki ne,kuma naji shiru baki ce komai ba''
hara rarta tayi
''wannan baki naki hindatu kamar ba'a gasa miki shi ba?''
dariya suka sa su dukka ukun,tilas yanzun ta yiwa mama maganarshin tunda tun ajiyan yake jadda da mata aure yake son yayi bada wasa ya zo ba,a kunyace ta yiwa maman bayani,farinciki fal zuciyar maman
''Allah ya tabbatar mana da alkhairinsa,ya kade dukkan sharri da fitintinu,addu'a ce yanzu kawai abunyi gareki maryam''
''insha Allahu mama,sai a tayamu muma da ddu'ar''ta fada cikin karyewar murya wanda ke nuna raunin zuciyarta,tausayinta ya kama maman


''addu'a ta zama dole akan musulmi,ballantana uwa ga 'ya'yanta,wacce garkuwa kike da ita da zaki basu wadda ta zarce addu'ar,uwar ma irina mai yara mata da take musu fatan samu mazaje na gari nagartattu,babu sallar da zan idar da ita maryama ban muku addu'a ba,ku kadai nake da su fa''
wata iriyar qauna hade da tausayin mahaifiyar tasu suka lullubeta,haqiqa uwa ba wasa bace,wata ni'ima ce daga ubangiji,cikin zuciyarta take fata insha Allahu wannan karon zuciyar mqhqifiyar tasu zata wanke daga dukan wani quncin rashin auren nata,hawayen da suka tqru suka fara sauka a idanunt cikin dabara take sharewa don kada maman ta gqni hankalinta ya tashi


kiran abdur rahim ne ya sake shigowa,wannan karon ba tare da jinkiri ba ta daga don so take ta kaucewa idon amman kada tqyo tozali da hawayen da takeyi
''ranki ya dade lafiya kike kuwa?''ya tambaya a sanyaye
''lafiya nake me kaji?''
''muryarki ce naji tamin kama da ta masu kuka''
duk da yanayi da take ciki sai da murmuahi ya subuce mata
''idan banda abun abdul har yaushe kasan muryata da zaka tantance kuka nake yi?''
murmushi ya saki har tana iya jiyo sautinshi
''na dade da sanin muyarki maryam,ke dince baki sani ba,kina gidanku ko?''ya qarashe maganar da tambaya,cikin mamaki da sigar tambaya itama ta maida masa amsa
''wa ya gaya maka?''maryam,kina shakka cikin son da nake miki ko.....any way....naje gidanku ance min baki nan kina gun mamanki''


a wani mamakin ya kuma sakata,son iya saninta babu mai shigowa gidan su mamin ta sauqi
''ya akayi kasan gidan da nake zama taya kuma ka iya shiga da sauqi irin haka?''
''maryam,duka abdul ba mai daukar abunda yake so da sauqi bane,yana bashi muhimmanci ne afili da boye,ina fata kin fahimceni?''
''jinjina ga irin wanna son da abdul yake min''
''jinjina ga zuciyar data sadaukar min da kanta''sai duka suka yi murmushi


''ina fata zuwa yanzu mutanen gida sun san da zama na?''
''tun yanzu abdul,duka duka jiya fa muka hadu''
''ke kika hadu da ni jiya,nikam ba tun jiya ba kika zama wani bangare daga jikin zuciya ta,so inason asan da ni maryam,aure nake so nayi da,wuri idan da ina da iko ma cikin watan nan banqi ki zama tawa ba''
tilas abdur rahim ya bawa maryam dariya
''gaskiya na baka sarkin zumudi na duk duniya''
''na amsa tunda sonki ne ya ja min''


cikin qanqanin lokaci ya cika zuciyarya da farinciki ta mance duka abinda take ciki,ba dadewa da gama wayar tasu bacci yayi awon gaba da ita don tuni mami ta yarje mata tayi kwananta a gida washegari taa dawo

🎄🌲🎄🌲🎄

qarfe tara na safe ta gama shirinta tas,a falo ta taradda hindatu na shirya musu abun kari kan center table daya daga cikin abunda jiya ya zama mallakinsu
cikin girmamawa hindatun ta gaidata ta amsa mata tana tambayarta mama
''mama na gurin baaba''
''ya dawo ne?''
''eh ya dawo dazu da sassafe,kin sanshi da tafiyar asubanci,yauwa tace idan kin tashi ki shiga ku gaisa''
''yanzu kuwa''ta fada tana ciro wayarta dake tsuwwar shigowar saqo tana dubawa
saqon barka da asuba ne aga abdur rahim,zaqaqan kalmomi da suka sanyata mirmushi ita daya tamkar wata zautacciya,tana mamakin yadda zuciyarta ta nutsu wa abdur rahim lokaci guda,sai da ta kammala karantawa ta masa reply sannan ta koma bedroom ta ciro dubu goma cikin kudin da mami ta bita kyautasu jiya dubu goma sha biyar


mamanta inna haule baaba hadiza sai lubabatu jamila da shamsiyya su ta tarar cikin dakin,kallo banza uka suka bita da shi,gefan binta ta matsa zata zauna,cikin rashin mutunci bintan ta janye jikinta tana wani harare harare da kumbure kumbure
gaida su ,bata da isar da zasu amsa mata har gara inna haule ta ama din sama sama,cikin girmamawa ta gaida baaban nata,ba laifi a sake ya amsa mata har yana tambayarta gun aikin nata,shiru ne ya biyo baya na wasu mintina sanan baaban ya dubi jamila
''inatambayarki tun dazu kun min shiru,yaro yace shi baisan lokacin da ya aureki ba,to inason in san ta yaya akayi ya aurekin,tunda shi ya rantse ya mayq bai san ke matarsa bace kuma bazai dawo dake ba''
cikin fitsara da rashin tarbiyya ta zumburo baki
''toni baba....ka tamvayi hadiza mana''
ya juya ga inna hadizan
''to kimin bayani tunda tace a tambayeki''
cikin borin kunya da haqiqancewa tace
''haba malam,wannan wane irin abu ne,ya zaka zo kasuwa ka dinga kwance min zani,sai da ka tara min idon duniya ni da diyata zaka hau bin qwaqwafinmu''


''ke hadiza dubanni nan da kyau,na gaji da iskanci da rashin mutuncin yaran nan,jiya tunda naje qauye fita ta daya na gaza fita,zance na ake ko ina,ance na kasa kula da yaya matan da Allah ya bani,dukkansu babu mai zaman aure ko wacce rabi aure rabi zaman gida,ga wasu kuma sun kasa auruwa''
zuciyar mafuam ta kada don tasan maganar qarshen tata ce
''to wallahi ya isheni haka,kun gama mai da ni mutumin banza ko,baku isa ba wanna karon na gaji ko masu auri suyo zaman auresu marasa aure suyi aure ko inci uban yarinya wallahi''
ba inna hadiza kawai ba hatta da su maama sunyi mamaki,yau baane ke ja in ja da inna hadizar?,lallai a dade anayi sai gaskiya,komai yayi farko qarahensa na zuwa babu shakka,a bangaren inna hadiza kuwa ta gama qullatar huwaila ne dadi bisa dari kan dukkan bala'in da taga ya afko,mata babu shakka ita ta qulla zuwanshi


qasa mama tayi da kanta tana fadin
''Allah ya huci zuciuarka malam,a yi mana afuwa''
sai yaji zuciyarahi ta dan rage zqfihar ya juya ya dan dubi maman,sannan ya maida idonsa gasu hadiza wadanda sjka zuba masa iddo qir babu mai cewa komai,baba hadiza na huci tana jiran ya gaya mata cuta ta fada masa mutuwa
''ke jamila ki tsaida hankqlinki,mahaifinki ne wanna,ki fada masa ya aayi hakan ta kasane don,samun bakin zaren,so ake a gyara lamarin ki koma gidanki kuci gaba da zama,mutuwar aure gun diya mace ai faduwar daraja ne,saidai kuma idan na qaddara ne''cewar mama


jin an sako maganar komawarta gidan jabir ya,sanyata cikin rawar jiki ta bude baki zata yi bayani a wautarta da jahilcinta za'a maidata din,don a yadda ta dandana zaman daula bata jin zata iya zaman gidan nasu kona wata daya ne bare na dindin din
tuni inna hadiza ta katsi numfashin jamilar
''uban me zaki gaya musu,cin fuska yaso yi miki kawai,ya aureki da kansa sanna yace baisan ya aureki ba,kujimin da,ke kuma aminatu banason munafurci da gilma,ina ruwanki?,ina cewa dai jamila bake kika haifa min ita ba,ai na dade da sanin cewa abunda kike nema kenan saboda har yau baqincikin qin aurar diyarki da baiyi ba yana nan cikin zuciyarki,to ahir dinki ki fita sabgata data yara na''
tsawa baban ya daka mata ya kuma ce ta ta shi ta fice masa adaki,koda ta ficen da yake ta riga da ta rainashi sai tayi tsaye abakin window tana eqa dakin tare da kallon jamila tana mata gargadi





*mrs muhammad ce*👑



📚📚📚✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻
[9/17, 12:53 PM] 80k: 💖💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺🌺
🌺💖🌺💖🌺
🌺💖🌺💖
🌺💖🌺
🌺💖
💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺
💖💖💖💖💖💖💖
*WRITTEN BY*
*SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
💖🌺💖🌺💖🌺
💖🌺💖🌺💖
💖🌺💖🌺
🌺💖🌺
🌺💖
🌺 ▶3⃣0⃣


*_HASKE WRITERS ASSOCIATION_*💡
*_home of expert and perfect writers_*






dauke kanta tayi tamkar bata ga gargadin nata ba,domin burinta kawai a maidata ga gidan jabir,don ba jabir dinne ma yafi damunta ba tunda bashi daman take aure ba dukiyarshi take aure,tana da abokanan holewarta a waje
a take ta warware musu yadda tayi amfani da sihirtaccen kwalli da turare har sau biyu ta dauke hankalin jabir ya aureta cikin gushewar hayyaci


gumi ne kawai ke ketsatstsafowa maryam,bata sake jin tsananin tausayin jabir ba sai a lokacin,shikam baban nasu shiru yayi ya kasa furta komai,kimanin mintina biyar sanna ya dubi su binta yace su fita adakin,sumi sumi suka fice ya dubi huwaila da tayi tsamo tsamo
''duk abinda kukayi huwaila don kanku,amma ku sani dole ne ku nemi yafiyar maryama don an zalunceta''
ya waiwaya ga inna hadiza dake labe yace
''kije Allah ya isa tsakani na dake,tarbiyyar yara da kika bata min,haqqin maryam kuma ke da ita,kya sake samowa jamilar wani mijin,ku taahi dukkanku ku bani guri''


dama a qagauce suke saboda kunya da nauyi tuni suka fice,saura maryam da mama,miqewa itama maryam din tayi ta ajjiye masa kudin hannunta
''ba wanna babu yawa amana addu'a,kuma kayi haquri Allah ya huci zuciyarka,insha Allahu zamu gyara dukkan abinda

Please Login or Register in order to submit comment