Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

a lahira,irin mu muna nan da yawa Allah ya ajjiyemu saboda ire irenku,haka gaba dayq mu da ku kuma sai munje lahira za'a hukunta mu baki daya,ni dama na riga na sani bani da rabo a lahira,kunga ai gwara naci nawa tun anan''ya juya ya fice yana sheqa dariyarsa.


Hada kai sukayi suka fashe da kuka kowacce da irin tata nadamar,sun qi Allah bayan ya musu ni'ima,idanunsu ya rufe basu ganin baiwar da yayi musu da tarin ni'imominshi a garesu sai yanzu da ya karbe abinsa,dama ya fada cikin littafinsa mai tsarki''idan kuka gode min zan qara muku,idan kuma kuka kafirce to haqiqa azabata mai tsanani ce'',sun yarda sun dauki hudubar shaidan,wanda dama bashi da burin da ya wuce batar bayan dama ya sani cewa tun can dama shi batacce ne,kuma dama yayi wa Allah alqawari sai ya batar dq bayinsa kamar yadda yazo cikin wasu surori na qur'ani lokqcin da Allah yace ya fita daga aljanna la'ananne ne shi
''kuma la'anata tana tare da kai har zuwa ranar qarshe''
sai shaidan din yace
''ya ubangiji ka jinkirta min izuwa ranar qiyama''sai Allah yace an jirka maka,har uzuwa rana da lokaci sananne,sai shqidan yqce da ubangiji
''na rantse da isarka da buwayarka sai na batar da su gaba daya,saidai bayinka daga cikinsu tsarkakakku''sai Allah yace da shi
''haqiqa bayina baka da wani iko a kansu sai wadanda suka bika dagq cikin batattu,kuma haqiqa jahannama ce makomarsu gaba dayansu,tana da qofofi guda bakwai''a wani gurin kuma shaidan din yace
''zanzo musu ta tsakaninsu data damansu data hagunsu mafi yawansu zaka samesu marasa godiya''
haka ya sake fada a wani gurin cewa
''sai na batar da su,sai na sanya musu buri sai na umarcesu su canza halittar Allah(kamar bleeching yana daya daga ciki)
shi yasa Allah da kansa yake fada mana
''haqiqa shaidan abokin gabarku ne ku ruqe shi abokin gaba'',muna mantawa ne da ranar mutuwa ranar tonon asiri ranar hisabi,ranar da duk wata rai saita bi ta saman siradi ta wuce wanda qarqashinsa wutar jahannama ce,aikinka mai kyau gaskiyarka zumunci da ruqon amana ne kawai zai qetarar da kai cikin salama


Son zuciya ya mana yawa,muna biyewa soye soyen zuciyoyinmu baka iya hana zuciyarka aikata mummuna wanda hakan ke kaimu ga halaka,Annabi muhammad S A W yana cewa''an lullube aljanna da abinda rai baya so(kamar salla azumi zakka,zumunci,da sauran ayyukan alkahairi da bamu son yi ko muke jin wuya gun aikata shi)an kuma lullube wuta da sha'awe sha'awe(kamar zina,caca,cin dukiyar marayu,annamimanci,sata da sauran abubuwa da rai kejin dadi yayin aikashi)''

Allah ya sake cewa ba don falarlarsa da rahamarsa ba da duka munbi shaidan face 'yan kadan
Allah kasa mu dace duniya da lahira


Sun jima cikin alhini da jimantawa kansu kafin habiba tace
''zahariyya nifa na gaji,anya ba kashe malam zamuyi ba?''duk da yadda taso ga neman mafita amma sai da shawara ta tsoratata,don bata manta ba irin wannan kuskuren taso aikatawa ya kawota ga wannan matsayin da take ciki yanzu
''habiba,in sake yunqurin aikata wani kuskuren kenan?''
''kashe malam,zahariyyq rage mugun iri ne cikin al'umma,bakiji abinda yace babe,malam fa bazai taba shiryuwa ba,shin kin san shi mutum nawa ya kashe cikin wannan qazamar harkar tasa?(hmmm,sai yanzu data ritsa da su suka san qazama ce)''
cikin rashin gamsuwa ta girgiza kai
''wannan shi da Allahnsa amma mu dq muke neman kubuta kuma inamu ina kisa,shawara daya ce kawai tunda mu bamu tsaya munyi karatun addini ba boko muka sa a gaba,ba wasu addu'o'i garemu ba kawai kullum mu dinga karanta masa fatiha ba adadi,ai Allah yana jinmu,kuma nasan da yardaraa wata rana zamu kubuta''
take ta yarda da shawarar zahariyyan don tafi tata fidda maslaha




*mrs muhammd ce*


πŸ“šπŸ“šπŸ“šβœπŸ½βœπŸ½βœπŸ½
πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺
πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
πŸ’–πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊ
πŸ’–πŸŒΊπŸ’–
πŸŒΊπŸ’–
πŸ’–

*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’–
πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’–
πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊ
πŸ’–πŸŒΊ
πŸ’–
Β© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*πŸ’‘
*_home of expert and perfect writers_*

β–Ά5⃣9⃣


*An karbo daga Abdullahi dan amru dan Aas Allah ya yarda dasu baki daya,haqiqa Manzan Allah S A W yace''yana daga cikin manya manyan zunubai mutum ya zagi iyayensa(uwa da uba)'',sai sahabbai suka ce ''shin mutum zai iya zagin iyayensa?'',sai Manzo S A W yace''eh,a zagi mahaifin mutum,mutum(wanda aka zaga) shima ya zagi mahaifinsa(mahaifin wanda ya zageshi din),ya zagi mahaifiyarsa shima(ya rama) ya zagi tasa(wanda ya zageshin)''*

_ruwayar bukhari da muslim ne_







Itakanta ko ba'a gaya mata ba tasan ta canza,wani santsi da qamahi fatarta ke fitarwa na musamman,wani lokaci har shanshana kanta takeyi kota tsaya kallon kanta a madubi,magani masu kyau mamin ke bata na ainihin 'ya'yan itatuwa ba gamje gamjen bature ba,tana jin naiyinta da kunyarta haka zata karba ta sha tana rufe ido,mamin takanyi murmushi tace
''babu kunya tsakaninmu maryam diyata ce ke kamar yadda nasha fada,namiji kuwa dan son gyara ne bashi da kunya ta wanann bangaren,balle abdallah da ina kula da rawan kanshi,idan kika zaune kara zube cikin lokaci qanqani zaki wargaje fes babu kunya zai dauko miki wata,shi yasa har yau ina alfahari da lambar yabo da na karba agun daddyn abdallah har ya mutu yana yabamin,so haka nakeso ki zama gurin abdallah koma kifi haka,koda akwai wata ma kisha gabanta''


kunya ta kuma kamata duk da maganar ta taqarshe ta dan haifar mata da fargaba

πŸƒπŸ‚πŸƒπŸ‚πŸƒπŸ‚

Tun ranar bai kima kiranta ba,har ta dinga zaton ko fishi yayi,cikin ranta take jin ba dadi idan fushin kuwa yayi,can qasan ranta ake tsinkularta ta kirashi taji muryars amma da zarar tayi kamar ta kira din sai kunya da nauyi su hanata


Kusan tara na dare ne suna zaune ita da mami da baaba uwani,baaban ce ta musu sallama ta wuce bangarenta mami ta duba agogon kana ta miqe ta haura sama bayan ta ce da maryam tana zuwa,kallo take amma batasan ya akayi idanunta suka kai kan hotkn abdallah window size dake kafe a can kusurwar falon ba,sai ta kafe hoton da ido,a hankali wani abu ya dinga motsa zuciyarta,ta miqa hannunta ta duba call history inda num dinsa take wadda ko serving bata yi ba,ta shiga canki camkin ta kira ko a'a,kamar wadda aka tankwabi hannunta ta danna kiran gakin ya soma tafiya sai ta qyaleshi.


Daidai lokacin da yake cikin dakin hotel din da suka sauka,shi da manyan yaransa ne guda biyu,a gaggauce yake shiryawa cikin wadansu baqaqen kaya samfurin kayan jami'an tsor,duk da kqyqn qiki ne amma ba qaramin kyau suka yi masa ba,yana cikin daura belt dinsa bayan ya sanya bindigarsa a aljihun wandon na baya yaga shigowar kiran,bai lura ba sosaj ya dauke kai yaci gaba da sanya boot a qafarshi baqi don muhimmin aiki ne a gabanshi bai saba qa'idar lokaci komai nasa a tsare yake


Tana dab da tsinkewa ya kai hannu da niyyar dauke wayoyin nashi ya kashesu don bazai fita dasu ba,ba dasu zaiyi amfani ba already ya gama maqala na'urar da zasu dinga communicating da abokan aikin nasa a jikinsa,mamaki ya kamashi ganin sunan *honey sweet* bisa screen dinshi,katse kiran yayi kana ya kirata
sai da gabata ya dinga bugawa kafin ta amsa kiran,a kasalance ta kara wayar a kunnenta hade da yin sallama,duk da kuzarin da yake da shi sai da yaji an zare masa shi tas,shi da yake ta shiryawa a gaggauce yana basu order din baison bata lokaci sai gashi yana shirin kwanciya saman gado,yaran nashi suka kalli junansu da lamar tambayar ya haka?a tsakaninsu saidai babu damar furtawa oga suka ja bakinsu suka tsuke,alama ya musu da su fita su jirashi a qofar dakin yana tsoron kada ya tafka abun kunya a gabansu,don tunda yaji muryarta komai ya kwance masa.



Shima dai a kasalance ya amsa mata sallamar,daga nata bangaren ma wani dafin ya kuma zuba mata,shiru ne ya ratsa tsakaninsu tana jiyo saukar numfashinsa,ya shiryawa sata tayi magana koda bata so,ya santa da qin yarda da gaskiya ta wannnan bangaren,saida yayi dariya ciki ciki sannan yace
''Allah sarki baby,kafin kice komai nasan kewata ke damunki kika kira kiji sweet voice nawa ko?''
gabanta ya dan fadi ta zaro ido kamar tana a gabansa ne,sai data cire wayar daga kunnenta ta sake dubawa shidin ta kira sanann ta maida kunnenta


''sai kace wata kai,niba wannan yasa na kira ba,dole ce ma ta sani kiranka''
murmushi ya saki mai sauti wanda ya kusa wucewa da imaninta
''attitude naki din nan yana burgeni,kina da jarumta da yawa,aiki ne ya cushe min shi ya hanani kiranki my suger''wani sanyi taji yana ratsata har sai data cure gu daya,rake idea din yadda zata bagarar da shi yazo mata
''hmmmm,gida nakeson naje naga mama''
shiru ya danyi kana ya sake sanyaya muryarsa
''nima zanso kije ki ganta din,amma sorry baby,gaskiyq ina kishinki da yawa,na tabbatar idan zaki din saidai driver ya kaiki fa,kinga kun kadaice daga ke sai shi cikin motar....har zuciyata ta fara zafi ma wallahi da tuna hakan da nayi''
ta hade rai don gaskiya tana matuqar son ganin maman


''amma fa ka sani yaushe rabona da mama,tun ranar da kasa aka fiddani a gidan''ta fada cikin shagwabar da batasan tayi ba ma,shikam tuni taso sauya masa lissafi don sai da yayi ajiyar numfashi kana yace
''shine kuma sai kin illatani da muryarki?''
''me kuma nayi?''
''kinfi kowa sani,gaskiya my kiyi haquri idan Allah ya dawo dani na miki alqawarin kaiki da kaina ki wuni har dare sai nazo na daukeki kinji?''
hawaye taji kawai na silmiyo mata,don haskiya ta qagu taga mamanta,tayi kewarta sosai,sai kuma yqce sai ya dawo sanann zata je,bayan shi kullum sai yaga tashi maman saidai idan baya gari,kasa magana tayi shima shiru yayi yana saurarenta,can qasa ya jiyo kamar sautin kuka,da hanzari ya miqe ya zquna yana fadin
''ya salam,maryam me yasa kika maida hawayenki masu araha irin haka?,daga cewa sai na dawo zaki je?''


''eh,ai baka kyauta ba,banson rashin adalci fa abdallah ka san halina sarai''cewar mami data amshi wayar bayan ta maidata handsfree,sam maryam bata san ma ta iso ba sai da ta qaraso gabanta
kanshi ya dafe
''shikenan mami nikam abdallah bawan Allah,naga ta kaina an hade min kai''
''har hanci da goshi ma zamu hade maka indai zaka dinga matsantawa irin haka''
''mami ina da kishi sosai kin sani,dole idan zata je mami driver ne fa zai kaita,mami banason wallahi yani ya kalleta''
''oh abdallah,halin naka dai yana nan,to zuwa kam sai tajeshi haka kawai,wake raba da da uwa,yaushe rabon da tq gansu,haba abdallah''
''shikenan mami na yarda mata taje,amma ba kwana ba,yauwa......baaba sule ne zai kaita,kuma don Allah ta saka hijabi don Allah''ya fada a sanyaye,wani mugun kishinta yake ji yana yi kamar yasan gyaran jiki ake mata dan ubansu
kama bakinta mamin itama tayi kana tace
''iyeee,sannu fa ubana''marairaicewa yayi
''mami pleaseeeeee.......''
''ya isa''tayi saurin tsaida shi
''taji zata saka,ince ko shikenan?''
''i love u my mommy''ya fada cikin murmushi
''me too my son''ta fada itama,tana shirin katse wayar yace
''yauwa mami.....i need your prayer mami zami fita aiki kan mutumin nan kimin addu'a mami kamar kika saba,i know ita ke kaini ga yin kowacce iriyar nasara''maryam dake gefe duk dai taji ba dadi wani kewa da karayar zuciya na son kamata
addu'a tayi masa sosai y
hannayensa a sama kamar suna tare ta gama suka shafa su duka,sai yaji wata nutsuwa da dukka qarfinsa sun dawo.


Miqawa maryam wayar tayi dom suyi sallama
''baby....ki kulamin da kaina''
''kanka kuma?''
''eh i mean you,nine ke kamar yadda kece ni,byee love u much more''ya fada ya katse wayar sai ya barta da waya a kunne,a sanyaye ta cire wayar bayan ta sauke ajiyar zuciya

πŸ‚πŸƒπŸ‚πŸƒπŸ‚πŸƒ

Cikin atamfa excellent ta shirya pure cotton,duk da mai qaramin kudi ce amma ta matuqar amsarta,kalar blue black dark blue and navy blue da sea green ce,sai ta samu kanta tana aiwatar da umarnknsa duk da ba'a tuna mata ba,hijabi ta sanya blur black wanda ya rufe ilahirin jikinta,mai hannu ne hakanan yayi matching sosai da atamfar ta,ita kanta data kalli madubi sai taga tayi masifar yin kyau,hakanan tana jinta compertable sabanin mayafi,duk da cewa dama ita gwanar hijabince musamman sanda tana gida
baaba sule dinne kuwa tana fitowa suka gaisa da kanshi ya bude mata motad duk da bata so kunya ce take rufeta,don aqalla ya kusa sa'an abbanta


Ta dinga kallon unguwar tasu,babu shakka gida akwai dadi,baka gane hakan sai randa aure ya daukeki daga cikinsa ya kaiki wani gu,komai rashin sukuni na gidanku randa ka barshi sai kaji kana kewa da begensa,ta samu gidan auren da ya ninka gidansu nesa ba kusa ba amma bata daina kewar gidansun ba,may b home is nothing but two arms holding you tight when you are at your worst


Cike da zumudi ta saka kai cikin gidan da saurinta saboda yadda jama'ar unguwa keta binta da kallo,suna ganin ta sake zama ta daban,wata ma yaranta ke kai mata gulmar maryam tazo sai a hau leqe saboda ta tsaya suna magana da baaba sule ashe mami ta cika boot da kaya bata sani ba sai yanzu yace ta turo yara su kwashe


Farinciki ya cika,zuciyarta ganin gidan qal a share sabanin da da iyakacin tsaftar qofar dakinsu ne zuwa,cikin dakin nasu,lubabatu ce kan tabarma zaune da qananun qannensu wadanda suke daki daya da da qatuwar farar takarda ta shimfideta kan tabarma ta zana alifun ba'un har zuwa ya'un manya manya da alamu tana koya musu ne shi yasa ko sallamarta basu ji ba,kafin ta sake maimaita sallamar ta hango isyaku ya fito daga dakin uwarsa kanshi tsaye yabi takan takardar ya take rubutun kana yayo hanyar waje,lubabatun ce ta yunquro da sauri ta cafko wuyanshi ta baya
''wannan iskancin naka isyaku ya isheni wallahi yau sai jikinka ya gaya maka''


Da sauri maryam ta qarasa don kada abun ya kwabe tana banbare hanunta daga wuyan isyaku wanda keta kici kicin qwace kansa cike da rashin kunya
''sakeshi lubabatu kinji sakeshi''sai a lokacin taga maryam din ba musu ta sakeshin ya kuwa fice abinsa da gudu,ta saki fuskarta daga daurewar da tayi tana fadin
''sannu da zuwa adda maryam''
''yauwa lubabatu,karatu ake yi ne?''ta dubi yaran kana tace
''eh,makarantar dare suke zuwa malaminsu yace su tabbata sun iya zuwa anjima zasu je kuma naga basu iya ba''farinciki ya kama maryam ganin an fara samun ci gaba a harkar karatun yaran
''da kyau kin kyauta kuwa lubabatu''
yaran suka zuba mata ido suna shakkad zuwa gurinta,ko dama can ita ba mafadaciya bace bata dai shiga shirginsu ne saboda gudun rashin kunya irin tasu,su kuma suna ganin a yanzu ta zama yar gayu kada ta makesu idan suka matso gurinta tunda haka jamila ke musu sanda tana aure gidan jabir
sai ta bude hannayenta tana fadin
''kamar baku ga yayarku bane,ku taso mu gaisa mana asiya''
ai kuwa har rige rigen zuwa suka dinga yi,sai taji farinciki ya rufeta,zaman lafiya babu abinda ua kasihi dadi haka dan uwa,baka da kamarshi cikin duniya,hamsin hamsin ta fidda ta raba musu su biyar tace su sayi alawa


Ganin har suka gama budurinsu,aka gama shigowa da kayan da mama ta hadota da su samfurin kayan masarufi babu wanda ya leqo daga matan gidan ya sanyata tambayar lubanatu wadda gaba daya maryam ta karanci nutsuwa sosai a tattare da ita
''ina wai matan gidan ne?''
''au...''ta fada tana murmushi tare da dafe bakinta
''na manta ban gaya miki ba,sun fara zuwa makarantar matan aure qarfe tara na safe zuwa daya na rana mamata da maman hindatu(maman maryam din)ke zuwa,ya hindatu ce ta sanyasu''
cike da nuna kara tace
''inna hadiza fa?''
sai da ta kalki qofar dakin nata kana ta tabe baki
''tana ciki tana bacci,tata makarantar kenan''ta fada tana bushewa da dariya,daquwa maryam ta mata
''mamarki ce itama''daki lubabatu ta shiga ta daukowa maryam maqullin dakin maman tace
''adda ga key din ko''ta karba kana ta budr dakin maman ta shiga


ta bi dakin da kallo ya sake kyau ya canza,cike yake da tsafta da qamshi,wani kewar dakin ta kamata,sai ta cilla mayafinta da jakarta saman kujera,kai tsaye ra shige dakin maman ta fada gadonta data yi kewarsa matuqa



Tana son gadon umman nata tana jin dadin kwanciya a kai,gadon da tasha dabdalar quruciyarta a kai har yanzu katifarshi ce a kai,duk da canza kayan daki da taga umman nata tayi amma bata canza abarta ba,ta sake juyawa tana tuna rayuwarta cikin gidan quruciyarta zaqi da madaci kala kala,a haka bacci yazo ya sureta.


Can cikin barcinta taji kamar ana kiran sunanta,a hankali ta dinga bude idonta har ta budesu tarwai kan fuskar mamanta,farinciki ya kamata,yaushe rabon data ganta,tana tsaye cikin unifaorm ash colour doguwar riga da hijabi,sun mata kyau kuwa unifaorm din sosai
''ki tashi kiyi sallah kina ta bacci har anyi azahar''sai ta miqe tana mutstsuka ido
''ashe har kun dawo mama''
''eh kina ta bacci har girki akayi aka gama baki sani ba,halan bacci kika koyo''murmushi tayi ta miqe zata fice a dakin tace
''sannunku da dawowa''
''yauwa''maman ta amsa tana rataye jakar makarantar ta data daukota daga falo gami da cire hijabinta ta linke ta saka a sif


Duk inda tayi maman kallonta take,godiya take wa Allah cikin zuciyarta,farinciki fal ranta,lallai addu'a bata faduwa qasa banza,duk wanda ya kalli maryam din koda makaho ya shafata yasan ba a wahala take ba,babu shakka Allah ya share mata hawayenta na shekara da shekaru wanda ya jima yana zuba,hirarsu suke gwanin sha'awa da maman bayan baaba huwaila ta aiko mata da abincin rana don girkinta ne,bata zauna ba sai data shiga dakin baba huwailan suka gaisa,kayan dakin mama datq cire ne jere a dakin nata,ba laifi sunyi kyau kam,cike da sanyin kiki da nadama ta dubi maryam
''na godewa Allah da ya ganar da ni gaskiya tun lokaci bai qure min ba ni da yarana,maryam na cutar da ke a baya na kuma so na sake cutar da ke amma da yake ALHERI ne cikin zuciyarki sai Allah ya kareki ya kuma sanya kika mana zarrah a rayuwa,maryam don girman Allah ki yafe min ni da yara na gaba daya''
sam magiyar da take mata bata yi matq dadi ba,ko da can baya ta sani cewa shedan ke rudarsu da duhun kai,bata taba riqar baaba huwailan ba
''baaba,tamkar mahaifiya kike a gurina,nikam dama ban riqe ki ba,na yafe miki Allah ya yafemu baki daya''


Data zo cin abinci duka qannenta ne kewaye da ita suna hirarsu abinda bai taba faruwa ba tsakaninta da su ba tarihin rayuwarta,nan take jin duka baaban su ya maidasu makaranta,sosqi taji dadi don babu gatan da zaka yiwa yaro da ya wuce ka bashi ilimi(har kullum haka iyayenmu ke gaya mana,burinsu kenan (rabbirham huma kama rabbayani sagirah)


maryam ta dubi mama''ni ka ban ma ga baaban ba''
kubrah tayi caraf tace''baaba yana kasuwa,sai shida zai dawo''ta juya ta kalli mama
''kasuwa kuma mama''
''eh,kin manta da shagonsa da abdallah ya bude masa cikin kwari?''
''abdallah,a cikin kwari?,yaushe abdallahn yayi haka ba ta taba sani ba,koda mami bata taba mata magana makamanciyar wannan ba''cikin zuciyarta tayi maganar amma a fili sai tace
''au na manta fa''
''ai kullum malam sai ya yiwa yaron nan addu'a,yanzu kam qlhmdlh malam ya dauje duk wani,nauyi na gidansa da a da baya iya daukeshi,abdallah kam ba baya ba wajen alkhairi,abu daya zaki mana maryam ki wanke mu kiyi zaman aure mai cike da biyayyar miji,duk yadda kika zauna da mijinki kina nuna masa irin kalar tarbiyyar da kika samu kenan,kibi mijinki maryam ki riqe abdallah hannu biyu,bawai don arziqin da yake da shi ba,a'ah ko daya,kinfi kowa sanin cewa ba wannan ne gabanmu ba,nagartattun halayen abdallah kadai sun isa su sama masa kowacce kalar mace ta gari,ina fata kin fahimceni''kanta ta gyada
''na fahimta mama''
''Allah ya albarkaceku ke da shi baki daya''
''ameen ameen mama''ta fada cike dda jin dadin addu'o'inta


kafin ta rafi sai data tambayi yan qannenta me suke so ta saya musu kowa ya fadi abinda yakeso wanda bai wuce sabon unifoarm,jakar makaranta da lunch boxs,excercise book,lubabatu ce mai registration na placemen da sauran tarkacen kayan karatu,bata bar gidan ba sai data hadasu da lubabatun da kulu sukaje aka siyo,murna da tsalle kam sun sha shi,ko idon inna hadiza bata gani ba bare jamila ko binta,tana tsammanin ma basa gidan don idan banda isyaku data gani dazun da take shigowa gidan babu wanda ta gani cikinsu





*mrs muhammad ce*


πŸ“šπŸ“šπŸ“šβœπŸ½βœπŸ½βœπŸ½
[8:18pm, 10/9/2017] HugumaπŸ‘‘: πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺
πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
πŸ’–πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊ
πŸ’–πŸŒΊπŸ’–
πŸŒΊπŸ’–
πŸ’–

*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’–
πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’–
πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊ
πŸ’–πŸŒΊ
πŸ’–
Β© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*πŸ’‘
*_home of expert and perfect writers_*

β–Ά6⃣0⃣





*Daga abi musa al asha'ari R.A yace:Manzan Allah S A W yace da ni''ya Abdullahi dan qais,shin bana nuna maka wata taska daga cikin taskokin aljanna ba?LA HAULA WALA QUWWATA ILLA BILLAH''a ruwayar nisa'i ya qara da ''LA MALJA'A MINALLAHI ILLA ILAIHI''*

*Daga abu hurairah R.A yace: Manzan Allah S A W yace ''duk wanda ya fadi SUBHANALLAHI WA BI HAMDIHI sau dari za'a kankare masa zunubansa koda sun kai yawan kumfar kogi''*

_ruwayar bukhari da muslim_




Bata bar gidan ba har baaban ya dawo,a tsaitsaye suka gaisa saboda an soma kiran sallar magariba ya daura alwala ya fice yace yana dawowa,itama alwalar tayi ta shiga dakinsu tayi sallah,tana idarwa kiran hindatu ya shigo,a dokance take cewa
''Allah yasa adda baki tafi ba,gamu nan ni da jabir''
''da daddaren nan''
''wlh,daga asibiti muke kuma akace kina gida''
''ina nan ban tafi ba baaba nake jira,sai kun iso''ta fada sanan kowacce ta kashe wayarta


Tana dakin baaban ita da shi bayan baaba huwaila ta ajjiye masa kwanukan abinci ta fice,hira suke yi abinau gwanin dadi,abin ya faranta ranta sosai,ashe akwai lokackn da zata ga rana irin wannan?,lallai komai yayk farko zaiyi qarshe,basu damu da yadda inna hadiza keta kai kawo bakin qofar dakin ba,baaban ya dubeta bayan ya ajjiye carbin hannunshi
''maryam,ina fata zaki yafemin,na dade ina daukan haqqinki,na yi watsi da duk wani haqqi naki da Allah ya doramin,tun kina mitsitsiyarki na watsar da duk wani haqqi naki da Allah ya dora min,gashi daga qarshe ta inuwarki muke samun rufin asiri,ki yafemin maryamu,haqiqa na dau darasi a rayuwata,na qiku don kuna 'ya'ya mata,ina neman dq namimi,ido rufe,sai gashi yarin yana daf da lalacewa,Allah ya sa baiyi girma mai yawa ba,duk da haka har yau na kasa saitashi kan hanya madaidaiciya saboda na riga da na batashi na nuna masa gata,duk da haka na godewa Allah da ya ganar da ni gaskiya tun da wuri,a yanzu ne nake ganin budi cikin harkokina da nake yalwatawa iyalina nake daukan duk wani nauyinsu bakin gwagwado,kimin afuwa maryam''


Itakam bata jin dadin yadda mahaifinta wanda yayi sanadiyyar zuwanta duniya ke faman roqonta haka
''nikam baaba wallahi abunda kamin bazan taba iya biyanka ba,banga wani da zaka yimin ba na riqeka,komai qaddara ne kuma nasan haka lah ya qaddara dama zanyi rayuwata''
''duk da haka,na sani maryamu ki yafe min''
''na yafe maka baaba har abada duniya da lahira''
''na gide madyamu na gode,Allah ya albarkci rayuwarki,ki sake yimin godiya gurin yaron nan abdullahi,babu shakka babu abinda zamu iya cewa da shi,tsakaninmu da shi fatan alkahairi ne''
har yanzu mamamin abdallah bai saketa ba,yaushe ya shiga jikin yan gidansu ne wai haka?,yaushe suka saba soaai har yake musu alkhairai bai taba nuna mata ba ko sau daya


Suna cikin dakin suka jiyo shigowar hindatu,shigowarta ne ya tunowa da baba sabon babur da jabir din ya siya masa ya dinga zuwa kasuw ko wata guda ba'a rufa ba yace maryam din ta tayashi godiya


Nan cikin dakin itama ta ahigo bayan sun gama gaisawa da mama suka sha hirarsu da baban,har kusan qarfe tamwas da rabi suna tare,tuni ta kira baaba sule tace ba sai yazk daukarta ba don hindatu tace su zasu maidata
har soro suka rakosu baaba huwaila da yan qannesu,a tsakar gida sukayi sallama da baaba,suna kallo su jamila da binta na leqensu ta window


cikin mota suka tadda jabir din,hannunsa ya dunqule yana mata jinjina irin ta sarakai''Allah yaja da ran antinmu,Allah ya taimakeki uwar gidan abdallah mai nasara''dariya ya bata ba kadan ba
''haba jabir,ka mance cewa ka girmeni irin wanan gaisuwa haka?''
''ai yanzu kece babba,ko kin mance kin bani 'yar qanwa,gimbiya hindatu,wadda ba qaramin yabawa da zaben da nayi nake ba har yau''dariya ya bas gaba dayansu har suka fara taciya suna hira abinsu


sai da suka fara biyawa ya yiwa hindatu siyayya ya hada harda maryam din kana suka ajjiyeta a gida sannan suka nufi nasu gidan

πŸƒπŸ‚πŸƒπŸ‚πŸƒπŸ‚

kwana bakwai mami bata bari an dakayar da

Please Login or Register in order to submit comment