Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

awoyin man iya ka kadai wadan nan abubuwan kika rubuta?,sunyi kadan''tace tana sake qarewa takardar kallo tana girgiza kai''
kararki tayi yawa dama nasan ba iyawa zakiyi ba,jeki kawai,zanyi amfani da wannan din da kuma wadanda na rubuta''
tana murmushi ta juya ya shige dakin ta barsu nan suna ci gaba da lissafe lissafensu

πŸŒ²πŸŽ„πŸŒ²πŸŽ„πŸŒ²πŸŽ„

ta riga su tashi kamar yadda ta rigasu kwanciya su sai yanzu suke nasu baccin gajiyar,kafin su farka harta kammala breakfast taci nata,sai tayi zaune a parlour tana kallo abinta cikin riga da wando na pakistan orange da baqi,ya mata kyau kuwa sosai


takun da taji shi ya ja hankallinta abdallah ne ke fitowa sanye da riga armless da wando three quater,fuskar an ahade kirtif ya qarasa gaban freezer ha ciro fresh milk da ta hada sanyi ya balle robar ya soma sha,baifi rabi ba ya ajiye saman freezer din ya nufi kitchen sai gashi da plate da cup,mamaki tayi yau da kanshi ya zuba baiko nemi ta zuba masa ba lallai da alamu tunwa ce ta koroshi ma,zaya zo yana wani ciccin magani kamar wanda wani ya zageshi


can gefe guda ya samu ya zauna kan ya fara break din,duk sai taji kamar ya cika falon,zaman ya daina mata dadi,neman dalilin da zaisa ta tabar falon kawai takeyi,don bata buqatar ko qanqani zama inuwa daya ya dinga hadata da shi ko naminti dayane idan ba lalura ba
''ke''taji yace sai tayi banza da shi kamar bata jishi ba,ta fuskanci wani jan bala'i gake nema da ita tunda suka taho,ita kuwa kodan daraja da kunyar mami bazata bari su raba abun fada ba


''bakiji kashein da na miki jiya ba kenan sai da kika kira wani da phone dina ko,to ki gayawa rubabben saurayinkin kada ya kuma kiran numberta don ba sa'anshi bane ni''ya miqe yana dauke cup din tea tare da bari plate din a gun,bai kai ga shiga corridor din ba sukayi kacibus da mami tana fitowa da hijabi jikinta qafarta sanye da silifas
''mami ina zaki?''
''zan sauka ne floor na qasa mu gaisa da maman farida,jiya kaga ban samu na ahiga ba saboda gajiya''
''pls mami ki taimakeni kada ki cewa zeenah tare muke,wallahi kika bari ta sani tofa na banu kafin mubar qasar nan nacinta sai yasa na rame,ango kuma da rama ami ai babu kanta kada ta koro miki ni tace na mata rama da yawa''
dariya ma ya bata gani irin marairaicewar da yayi
''ka maida ni kakarka Allah abdallah,kakannin naka ma ka shafa musu lpy a kaina abun yake qarewa,ni dai Allah ya kusa rabani da alaqaqai gwara kayi auren ko kunnuwa da idanuna zasu huta da ganin yammata,ka shirya kafin na dawo mu fita da wuri so nake a yau a gama siyayyar baki daya''


tayi gaba suka gaisa da maryam ta fita,tayi zaton ya shige dakinsa tana zuwa sukayi kacibus bakib qofa,tana mura handle din dakin da qoqarin shigewa ciki taji yace
''kika sake mami ta miki tayin fita kika ce zaki bimu wata siyayya sai na qarasa targaden da na miki jiya''wuf ta shig dakin ta saka maqulli tadan daga murya
''to baaba na'' sanna taja tsaki,gado ta fada cikin jin haushinsa,dama ita bata sha'awar zuwan ma sam,dadai ba da si din zasu je ba shine,amma indai da shine zamanta a gida ya fiye mata dadi,qofar ya tsaya yana kallo,dan qaramin murmushi irin na gefan baki ya subuce masa ya cije lebansa na qasa kadan kana ya tura qofar nashi dakin ya shige ya cire kayan jikinshi ya fada wanka






*Mrs muhammad ce*πŸ‘‘

πŸ“šπŸ“šπŸ“šβœπŸ½βœπŸ½βœπŸ½βœπŸ½
[9/17, 12:54 PM] 80k: *ABADAN*36
*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
Β© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*
*_home of expert and perfect writers_*
*_annabi muhammad s a w ya tambayi sahabbansa_*
*_''shin ko kunsan waye matsiyaci?''_*
*_sai sahabbai suka ce''matsiyaci shine wanda bashi sa dirhami ko dirane''ma'ana bashi da cin yau bare na gobe_*
*_sai annabi yace musu''matsiyaci shine wanda zaizo ranar qiyama,yayi azumi yayi sallah yayi sadaka yayi zakka yayi hajji saidai kuma ya cuci wancan ya zalunci wancan ya zagi wancan yaci dukiyar wancan,sai Allah ya dinga dibanadan wadancan ayyuka na alkhairin da yayi ya dinga rabawa yana biyan wadanda ya zaluntar har sai ya tashi bashi da komai cikin aikin ladansa,ga ragowar wadanda ya zalunta ba'a gama biyansu ba,sai Allah ya dinga diban zunubinsu yana bashi da haka da haka har sai ya tashi bashi da komai face kayan zunubi sai Allah ya jefa shi a wuta''_*
*ya ubangiji kayi mana tsari don isarka*
Har mami ta dawo daga gidan maman farida ta shirya bai gama nashi shirin ba,sai da ta leqa ta masa magana,ta leqa dakin maryam ta taddatakwance
''ya kike a kwance mu da zamu fita?''
sai ta miqe zaune
''bana jin dadi sosai mami''
''ashsha,Allah ya sawwaqe,ki kwanta ki huta qila gajiyar tafiyar ce bata sake ki ba,Allah ya qara sauqi ma fita gobe ba damuwa,ungo wannan ajjiye min''ta miqa mata baqar leda,kayan bacci ne masu azabar kyau guda hudu
''maman farida ce ta bani su,nikam ina ni ina saka wadan nan qannnan tsirarar ai sai ku''
kunya ce ta kama maryam ta karbi kayan fana sunne kai,sanann ta tashi tayiwa mamin rakiya zuwa falo,sgi din ma ya fito sanye da qananun kaya,t shirt ce mai gajeran hannu baqa wanda a gaban rigar akayi rubutu gwara gwara kamara haka *we all have story to tell*,sai baqin trouser da ya saka,sun masa kyau aoaai kasancewarsa fari sai suka haskashi,qofan ta maida ta rufe ami tace sai sun dawo
kusan wuni sukayi ranar a waje har maryam ta qosa da zaman kadaitakar,duk da cewa ko a gida ma idan duka suka fice kusan haka ne amma acan wani okaci takan fice gidan baaba uwani susha hirarsu,da zaman shirun ya isheta sai ta fito valcony din gaban floor dinsu tayi zamanta tana qarewa unguwar tasu kallo
basu suka dawo gida ba sai da suka kammala siyayyar lefe kaf baki daya,hatta da akwatunan basu bari ba,daga can kuwa gurin da zasu dora kayansu a jirgi suka zarce basu ko dawo gidan ba,sun zabi zuwan kayan ta iska wato ta jirgin sama don shine mafi sauri,tunda kafin su koma za'a kai kayan suna sa ran kuma idan ta jirgin saman ne bazaya wuce kwana hudu zuwa biyar ba yaje sabanin ta jirgin ruwa da,zaya dauki watanni
sai da mami ta tabbatar komai ya kammala sannan ta karbi wayar abdallah ta kira qanwarta hajiya ruqayya ta mata bayanin kaya sun taho,tayi qoqari don Allah da sunzo a shirya komai yadda ya kamata aje a kai lokaci yana qurewa
a mugun gajiye suka dawo don haka suna dawowa wanka sallah da cin abinci kawai sukayi,cikin qanqanin lokaci gidan ya sake zamowa shiru saboda yau babu zaman hirar daki kowa ya shiga ya kwanta
Washegari dukkansu su ukun suka fita kai tsaye kamfanin sarrafa kayan gado suka shiga,katafaren kamfani ne da suka qware wajen qera da sarrafa kayan daki da suka hada da gadaje sif madubi zuwaafiyayyun kujeru iri iri,inda suke ajjiyesun bayan sun gama sarafa su aka shiga da su,mami ta bawa maruam dama ta zabi irin wanda takeao,duk sai ta duburbuce ta kasa zabar kowanne daga ciki
sun kusa shafe awa guda saboda girman gun ba tare sa ta iya zabar koda kala daya ba daga ciki
abdallah ne ya ja tsaki
''yarinyar nan fa wahal da mu kawai take yi mqmi,kawai ki fidda mata wanda kika ga ke ya miki''
''meye naka a ciki dakina ko naka ko kuma dakinta ita zata zabi abinta''
''Allah ya baku haquri''ya fadi yana kewayesu ya barsu a gun ya nufi inda ma'aikatan ke zaune
ma'aikata biyu da leburorin gurin guda biyar suka qaraso inda suke tsaye ita da mamin,daya daa cikin su yace da mami cikin harshen nasara
''madam,ku zaku yi signing a nan za'a fitar da kayan,motocin kamfaninmu zasu kaimuku har inda kuke buqata suna wajen kamfanin suna jira''ya fada yana miqa mata wata yar matsakaiciyar takarda,ta amsa ta duba kana ta kalleshi cikin arahen nasaran itama ta maida masa
''ai bamu kai ga zabar wadanda mukeso din ba ai''
''yallabai ya riga ya zaba har ma ya biya kudaden''yayi maganar yana nuna wasu tsadaddu kuma tsararrun kayan gado dake gefan hannun damansu,kala biyu ne kujeru sif gado da madubi curtains,dressing chair da bedside sai abun maqale jakankuna dukkan kalolinsu light and dark purple ne sai wasu set din kamar haka amma su blue black ne da light blue
ba qaramin burge mami kalolin sukayi ba har ta tsaya kallinsu saboda kyawun da sukayi mata,abdallah ya iya zabe kamar mace,ta daga kai sai ta hangoshi can sama wata kujera mai siffar kwano mai azabar tsawo a zaune hannunshi riqe da cup din glass yana shan lemo,kashe mata ido yayi ya langwabar da kai alamun bada haquri tare da nuna mata agogo lokaci na tafiya kenan kana ya mata alama da hannu na kayan sunyi?,dariya ma ya bata sai ta daga masa girarta alamar eh,hannunshi ya sake dagawa ya mata alamar i love u,murmushi ta kuma yi ta girgiza kai kana ta samu gefe ta zauna tana fara signing din paper din zuciyarta cike da tunanin mahaifin abdallah,wani lokaci idan hayi wani abun sai taga ya koma mata alh abdulkareem sak,barewa batayi gusu danta ya rarrafa ba ta fada cikin zuciyarta
duka cikin kamfanin suka nufi bangaren kayan kitchen anan kam dama kawai ta basu nasu hada mata duk wani abu da yake,da amfani cikin kitchen,cikin lokaci qanqani sai gasu da,kaya bila adadin sukayi total ta biya,yawan kudin da maryam taga mamin ta kashe mata shi ya sake raunata mata zuciya sanyata kuka,kuka sosai ta saka har ta kasa magana ma,hatta da abdallahn dan garari tsayawa yayi yana kallonta,karo na farko da ta bashi tausayi,jawota mamin tayi jikinta sai ta ora kanta a kafadarta,hawaye naci gaba da zuba,itama mamin kasa magna tayi sai bayan maryam din da take dan bubbugawa a hankali cikin sigar lallashi,har cikin zuciyarta tanq jin ciwon rabuwa da maryam din,idan banda aure batq jin akwai abinda zata lamunce ya tsinke zamansu mai dadi da suka fara
washe gari ma baccinsu suka sha sai yamma sanan mamin tace su shirya su fita maryam ta danga gari,kada tazo ta kuma koma bata san ya garin yake ba
babu musu ta shirya cikin doguwar riga dark blue da adon golden din duwatsu saqar india ce,ta haskata qwarai,saidai kasala da rashin dadin zuciya da take ji ya rage walwalarta qwarai,wanna fargabar ta aure sai yqnzu taji ta fara shigarta daga lokacin da tayi tozali da kayan dakin aurenta,Allah ya sani ba zata yiwa Allah butulci ba amma tilas amatsayinta na budurwa taji fargabar aure kamar yadda kusan kowacce soya mace take ji a auren farinta a rayuwa
da qafa suka dinga tattakin suna taba hira kadan kadan cikin sassanyar la'asar din,yanayin garin ami kyau ne,babu ruwan wani da harkar wani,kusan hirar dake gudana jefi jefi tsakanin mami ne da abdallah,bata ankara ba sai da taji shirun na maryam yayi yawa,a hankali ta juyo ta dubi maryama dake hannun hagunta
''maryam''
da sauri ta juyo tamkar mutumin dake cikin tunani aka katse masa,nazarinta tayi na yan sakanni kafin tace
''lafiya kike kuwa,daga jiya zuwa yau naga duka kin canza,ko bakijin dadi ne?''kai kawai ta iya girgizawa tayi qas da kan nata tana qoqarin mayar da qwallar data cika mata idanu,hannunta mamin ta kama ta jata kan kujerar dake girke daura da su yayin da abdallah yayi tsaye hannayenshi harde a qirjinsa yana kallonsu,bai iya jin me suke fada amma yana iya ganin me ke gudana,motsawar bakin mami da gyada kan maryam,a hankali ta dinga share hawayen idanunta qarshe ta buge da murmushi kana suka taso suka iske shi
mami ta dubeshi ya wani hade rai yayi kitchen kitchen,ta dan ranqwashi qeyarsa
''kai kuma da wa mai aljanun sauyin yanayi''dariya taso qwacewa maryam har sautinta ya dan fita,tayi gaggawar gumtse bakinta ganin yadda ya zuba mata harara cikin shan mur
''nifa mami gaskiya ina da kishi,don me za'a tafi ni a barni ni kadai a tsaye kamar maye bayan da can ba haka kike min ba,kawai don an samu wasu''
''maganarmu ce ra mata bai kuma cancan ci kaji ba ehe,ciwon 'ya mace na 'ya mace ne,sannan wasun ma da ka kafawa qahon zuqa suka tsole maka idanu sun kusa tafiya su baka sararin gurin kaga qarewarta sai ka koma shan nono kace ma ko yaye ka banyi ba''sosai mami ta bashi dariya har sai da ya dara yana fadin
''ni na isa,amma dai nasan tattalin da ake min irin na da zai dawo,kinga na zama dab lelen murum biyu,ga na my dear ga naki,thank god''
Da daddare suka hada dukkan wasu kayayyakinsu washegari jirgi ya debesu sai qasa mai tsarki,washegarin ranar da suka je suka sauke faralin ibadarsu ta umara,hakan bai sanyasu shiga wasu sabgogin ba sai da suka kwashe kwana biyar basu rabo da masallaci wanka ko cin abinci ke fiddasu,har gwara mami wani lokacin ta dan koma ta runtsa,maryam kuwa bata bawa kanta wannan hutun ba,tun mami na mata mita kan ta huta harta gaji ta barta,cikin kwana biyar din nan sai da tayi saukar alqur'ani biyu,dukkan alkhairi babu wanda bata roqawa mami mamanta raliya hindatu da ita kanta ba
kwana uku sukayi a madina ziyara,daga nan suka hada ya nasu ya nasu,mami tace itafa sai ta sauka a sudan tukun,cikin alamun tuburewa yace
''me zamuyi kuma a sudan mami,dear fa ta matsanta tana da buqatar gani na,i have alort to do mami a gida,inaga tafiya zanyi nikam sai kin taho''
''wa salaam wa kitabi,nima na huta da qorafi kama gabanka Allah ya miyaye hanya sai mun taho''anan suka raba jaha da shi,maryam batasan me zasuyi a sudan ba sai da suka je,unguwar tamkar tana cikin qasarta haka ta gani,sai dai 'yan bambance banbance da ba'a rasa ba na suturu abinci da al'adu.
kallo daya zaka yiwa matar ka tabbatar da 'yar sudance gabanta da bayanta,saidai mamakin da maryam tayi yadda hausa radam ta kama bakinta yanayin karyewar hatshen bw kawai zai nuba maka ba yarenta bane ara tayi ta yafa,ba abun mamaki bane jin yaren gausa bisa harsukan wasu al'umma ko qabilun da ba ahalin hausa ba,saboda yaren hausa yare ne sha kundum da ya fantsama lungu da saqo na fadin duniya,kusan a yanzu shine yare na biyu ko na uku da akafi amfani da shi,babu inda zaka tsoma qafarka a duniya ka rasa wanda ya iya ko yakejin yaren
gida ne babba mai bangare biyu bangare daya na matar ne daya bangaren kuwa harkar sana'arta kawai take gudanarwa,gyaran jiki gyaran gashi lalle ne kayan gyaran jikin na mata turaruka na ruwa dana ice da humra na tsuguno harda na wanka,kai hatta da kitso idan kana da buqata akwai mai yi maka,yadda maryam taji suna hira da matar tana tambayar mamin bayan saduwa ya fahimtar da ita lallai sun san juna dama can da mami,tunda har taji tana tambayar matar wata najwa tace taje daarfur sai gobe zata dawo,hajiya laila ita kewa mami irin wadan nan gyararrki zamanin alh abdulkareem mai nasara nada rai,gayu kam da gyaran kai mami ta yishi lokacin da mijin nata ke raye shi yasa ta zama ta gaban goshinsa,duk da a yanzun ma bata saki gayunta ba saidai ta daina wasu abubuwan tunda babu mijin
cikin kwana uku matar ta fara tsuma maryam,gyara take mata bana wasa ba tunda ta san haj bintu akwai sakin hannu idan harka ta hadaku,wani irin daddadan qamshi ta zaunar a jikinta wanda ko zama tayi a gu sai qamshin ya nasheka,farar fatarta ta canza yanayi farin nata ya saje armashi kyau gami da daukan hankali,sati guda ana mata gyararrkun taki wanne b'angare kafin suyo gida nijeria bayan haj laila ta hada muta wasu hade haden da zata ci gaba da amfani da su koda bayan bikin ne
bayan sun koma boyonta mami ta dinga yi,tuni ta daina komai a cewarta bataso nan da kwanakin da suka rage biki wani abu na gyaran da akayi mata ya samu naqasu,baaba uwani ita ta goyi bayan mami tayi uwa tayi makarbiya take komai
sunyi waya da mama da hindatu,mama cewa tayi sai tazo godiya don sam bai canci ta yiwa mami godiya iya ta waya kadai ba,amma da maryam ta sanar da mamin sai tace sam wallahi kada tazo,idan kuwa tazo din to ta nuna ba ita ta haifi,maryam ba,karamci da mutuncin mamin sunyi yawa har suka sa mama ta rasa ma me zata ce ko ta saka mata da shi?,hindatu amarya kam babu zama,ita da qawayenta ke gudanar da komai,don hatta da rabon kati su suka dinga yi,saboda mami ta riqe maryam tace babu yawon rabon iv da zata ta bata jikinta,ganin komai take tamkar a mafarki,wai tau ita maryam ce ake kira da sunan *amarya*,lallai babu wani abu da yake tabbatace sai mulkin ubangiji
bata fidda ran ganin irin wanan lokacin ba saidai koda wasa bata taba kawoshi nan kusa ba haka,dukka kayan da zata saka raliya ta fidda takai dinki,duk wata sabga da ya zamto ita zatayi raliya ta tsaya kan komai ita keyi kan jiki kan qarfi kamar a itace maryam din,kyakkyawan amincin da aka gina shi bisa turbar gaskiya da amana kenan,yakan iya kai ku zama qasan inuwar al'arshin ubangiji ranar da babu wata inuwa sai taahi
Biki ya rage saura kwana uku da daddare tana gurin baba uwani ta kai mata wasu kaya da take son bata ita da yan jikokinta kiran hindatu ya shigo wayarta
''kinyi tsada adda maryam,mami ta tsaya miki''inji hindatu cikin salon tsokana
''kema mama ta tsaya miki ai ya akayi ya gidan''
ajiyar zuciya tayi
''lpy lau,gida alhmdlh don har wasu daga 'yan gaya sun fara sauka,saidai ta wani bangaren ba lafiya lu ake ba''sai da gaban maryam din ua tsinke ya fadi,cikin sakonni zuciyarta ta fara raya mata faruwar abubuwa marasa dadi masu yawan gaske kuma duka akanta,muryarta na rawa t tambayeta mai ya faru
dariya hindatun ta qyalqyale da ita
''kwantar da hankalinki adda mana,na gaya miki mu lpy muke alhmdlh,bangaren da babu lafiyar su inna huwaila ne da baaba hadiza,kinsan watan baqincikinsu ya kama,yanzu haka jamila na daki ita da sauran yan uwanta anata mata ruqiyyar banza da wofi ta tada aljanun qarya,wai wlh indai na auri jabir sai ta kashe kanta,ni kuwa nace shashasha ki kashe kan naki mana kanki da uwarki kika yiwa asara,ita kuwa inna huwaila sai zirga zirga take ta fita aje ta dawo ta kasa zaune ta kasa tsaye,zuwa dare saiga aminiyarta uwani sai ji mukayi tsakiyar tsakar gida tana cewa,ke kika kawo kanki kikace na kaiki gun bokan nan bani na jawoki ba,don aiki bai ci ba kuma zak nemi tijara ni gaban kishiya?,to ai ramuwar gayya tafi ta gayya zafi shi yasa na biyoki ayita mai kankat kema kowa yaji,mugun qullin da kika so qullawa,ta fayyace duk abinda suka qulla din sannan ta dora da fadin,bola kuma na bogi ne kudi kuma muni babu yadda kika iya,aminad da kuke baqinciki da ita daga ke har hadizan ai ta fiku,yanzu gashi data miqawa Allah kukanta ta jadiye baqicikinta na shekara da shekaru Allah ya yaye mata damuwarta ba tare da tayi hasarar sisin kwabonta ba,ku kuwa haihuwar asara babu kudi babu biyan buqata ga asarar imani,sallolin kwana arba'in a ajejere kun rasa ta kusan kwana dari bakwai,amina Allah ya sanya alkhairi ya tsone idon maqiya,kuma wallahi ni da ku dukanku ke da hadizar shege ka fasa,naci uwar mace a iya tijara da ramuwar gayya,duk kuma wadda take jin ta haifu da jini uwarta ta haifeta ta fito ta tanka
wai in gaya miki adda saiga inna huwaila ta fito da borin kunyarta waisai sun daky wallahi bugu daya uwale rayi mata sai gata tayi plate a qasa''hindatu ta fada tana sheqa dariya
''wai kuma ta sumewa mutane jadiza tayo kanta wai huwaila kinci amanata ta hau dukanta,lubabat
u kuwa itama tayo kan,hadizar ke in taqaice miki labari kowa sai ya ahigarwa uwarsa gida ya zama na wrestling,ina ta laluben wayata in miki vedieo don,kada ayi babu ke saiga babamu nan ya shigo shi ya raba cakwakiyar,kowacce da dogon bakinta ta taho zungi zungi zata yi masa bayani don ya bata gaskiya yadda suka saba yace babu wadda zai saurara,wanna ya ishesu ishara,mama ce......''
''haba aku mai vakin magana,sai kace na kunna freedom?''inji maryam tana murmushi bayan ta katse hindatu
''kefa adda ba'a miki abun arziqi''
''to ai wanna ba baun arziqi bane''
''wallahi nikam abun arziqi ne tunda na gano tashin hankalinsu ranar kawo lefenki,da farko da suka ga anfara shigowa da qananun akwatuna har sun fara yada habaici,da suka ga dai shigowara ke sai suka fara lissafi suna tabe baki,qarshe da suka lissafi akwati ashirin da hudu cif manya da qananu sai aka nemesu aka rasa,inna hadiza na quryar daki suna safa da marwa huwaila kuwa anyi tsamo tsamo an rasa na kamawa,ana cikin haka saiga nawa lefen akwati sha uku,qarshe saiga inna hadiza na dora hannu aka tana xunduma ihu huwaila a taya ta da sharbe hawaye da fyace majina,a gaban idon mutane fa abin mamaki da dariya,ko kunya babu''ta sake qyalqyalewa da daria don tuna abun da tayi
''Allah ya rufa asiri,yanzu ya abubuwa suke tafiya?''
''komai na tafiya daidai,amma wlh adda kizo ki kalli lefanki''
''kai hindatu,me kike ci na baka na zuba,abinda za a ajjiye maka su a dakinka wataran har sai ka gaji da su''
''to ai shikenan,dazu yaya abdur rahim yazo ya kawo kudin dinkunanki,dazu naje gidan adda raliyan na kai mata,har ta fara karbo wasu ma ta bayar an goge miki,gaskiya adda raliya tayi wallahi,akwai zumunci tayi qoqari''
''gaskiya ne Allah ya bar zumunci ya saka mata alkhairi''
''ameen''
nan take aya mata kayan gadonsu da aka siya duka an hada mata sun zama biyu kenan har kayan kitchen dinsu,madyam din tace yayi babu laiciya zama dakin baqi kenan da naki dakin tunda kince shima jabir din ya zuba naahi furniture din,jibi insha Allah nima zan taho gidan gaba daya ai,ki gaida mama''
''Allah ya kaimu,zata ji insha Allah''
daga haka dukkaninsu suka katse wayar
*mrs muhammad ce*
[9/17, 12:54 PM] 80k: πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺
πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
πŸ’–πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊ
πŸ’–πŸŒΊπŸ’–
πŸŒΊπŸ’–
πŸ’–

*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’–
πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’–
πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊ
πŸ’–πŸŒΊ
πŸ’–
Β© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*πŸ’‘
*_home of expert and perfect writers_*


β–Ά3⃣7⃣


*_ina so nayi amfani da wannan 'yar damar wajen miqa jinjinar ban girma tare da ddu'o'i na fatan alkahairi wajen jajirtaccen dan kishin qasa da al'ummarsa BARRISTER ABDU BULAMA BAKARTI duk da cewa ban masa sanin ido da ido ba saidai tarin gaskiya amana taimakonsa da jajircewa kan qasarshi da garinsa ya kewaye kunnuwanmu,ina tare da duk wani jajirtacce mai gaskiya da amana dan kishin qasa da al'ummarsa,ubangiji yayi maka jagora ya tsare gabanka da bayanka,ya qara yawaita mana irinku cikin wannan alumma tamu dake fagamniya cikin wani irin hali,Allah yayi ruqo da hannayenka ya dorar da kai kan gaskiya har abada ameen suma ameen_*







Kanta bisa kafadar mamin tana rabza kuka tamkar wadda zasuyi rabuwar har *ABADA*,sai yanzu take kuma jin zugin rabuwa da mamin,tabbas sabo turken wawa ne,ita kata mamin zuciyarta a karye take ta kasa cewa komai,tanajin zatayi asarar diyarta ne guda zata rabu da ita,da qyar tayi,conrtolling kanta kafin,su tsaya suyi sallama
''naso a gudanar da komai da ni maryam,saidai ga yadda lamarin Allah ya kasance,date din bikinku da abdallah yazo daya,kinga ma ko a yanzun gidan ya fara cika da mutane wasu ma rabonsu da gidan nan an jima,kinga bazan iya tsallakesu ba na fita wani guri ba,amma nayi miki alqawarin bayan komai ya lafa wuni guda zanzo nayi a gidanki,hakanan zan dinga dubaki akai akai da yardar Allah''


kafin tace komai muryar abdallah ta ratso falon yana kiran mamin
''gani nan abdallah''
da azamarsa ya shigo hannunshi daya riqe da leda baqa mai kauri mai dauke da tambarin wani gurin saida kayan maza na ado,daya hannun kuma rafar yan dubu dubu ce dauri biyu,cikin shigar qana nan kaya yake,sai ya sake wani dan banzan kyau,farar fatar nan tayi luf da ita tamkar rainon larabawa,ko dama can yafi yanayi da su din sam sai ka rantse babu abinda ya hadashi da nijeria ,sai ya danyi turus yna dubansu
''qaraso mana abdallah,ya ake ciki?''
ya qaraso ya zauna gefanta
''mami duka guest house din guda biyu sunyi kadan,yanzun dai hisham ya samar ma ragowar mutanen hotel''
''yayi kyau hakan,sai ayi total abiya kudin kwanakin da zasuyi da abincin da zasu ci basai an yi jigilar kai musu daga nan ba''
'to''yace

Please Login or Register in order to submit comment