Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

muhimmanci a muhallin daya dace ba, amma mubari zuwa weekend sai muyi zamana musamman akan maganar”. Cikin gamsuwa Aliyu yace, “Shikenan ALLAH ya kaimu”. Fitowar Jay daga bayi fuskarsa jiƙe da ruwa ya sakasu yin shiru, babu wanda yace dashi komai yazo ya zauna a kujerarsa, Hafiz ne ya fara miƙewa yana faɗin, “Bara muje zuwa anjima ma dawo muyi maganar idan ka samu lokaci”. Kai kawai jay ya ɗaga amma baice uffanba.

      Fitar su Aliyu babu jimawa Dad ya iso station ɗin su Jawaad, ba'a bashi damar shigaba saida ya kira Jawaad a waya, tamkarma Jawaad bazai ɗauka wayarba sai wani tunani yazo masa a rai, hakan yasa bayan wayar ta katse yabi bayan kiran Dad shi ya kirashi. Koda ya sanarmasa yana gate sosai mamaki ya kasheshi, amma sai yabama securitys ɗin umarnin a rako Dad office ɗinsa, shaf ya manta da Bilkisu dake kwance tana barci.
        Bai nunama Dad komaiba yay masa tarba ta mutuntawa, bayan sun gaisa ya bashi ruwa Dad ya fara magana cikin karyar da murya. “Jawaad”. Yanda ya kira sunansane ya sakashi ɗaga kai ya kallesa, ya amsa da “Na'am”. “Jawaad wajenka nazo gwiwoyina a ƙasa da tarin magiya da roƙon da idan kamawa tai na duƙa a gabanka zanyi hakan. Dan ALLAH ka tausayama Mamana ka dubi al'amarinta, bazan musamaka ba akan ita mai laifice damu kanmu, sai dai ince dan ALLAH mu manta da baya domin ta shuɗe, wlhy ina mai tabbatar maka duk wautar dake kan Mamana a yanzu babu ita, dan ta gurzu da horonka, ka tausayamin kodan ciwon dake tare da ita na hawan jini da likita ya sanar mana, badan tanada sauran shan ruwaba faɗuwar da tai jiya a gidanku likita ya tabbatar mana da sai ta kamu da paralysis, wlhy yarinyarnan tana sonka fiye da yanda kake zato ko tsammani........” Jawaad da kansa ke ƙasa yace, “Kayi haƙuri Dad ban katsekaba, da Huda na min irin wannan son da bazata guji haɗa zuri'a daniba, yakamata mu fahimci Hudah ta huce sahun ƙuruciya yanzun, bai kamata ace duk abinda yazo zuciyarta tai tunanin aikatashi shine mafi dai-dai a rayuwarta ba, sannan kuma abinda takeso ace dole saita samesa, dolene duk inda akwai take wataran za'a samu babu. batason haihuwa yanzun miyasa ta yarda tai aure? Bata shirya zama kamar kowacce macen aureba miyasa ta zaɓi muyi aure? A ganina da sai ta bari sai lokacin da duk ta shirya waɗan nan, Dady ni bahaushene, uwata bahaushiyace, mahaifina bahaushene, dukkanin dangina hausawane sai fulani, addinina shine musulunci, addinin iyayena da dangina duk musuluncine, tayaya Hudah take tunanin zan biye mata na ajiye dokokin UBANGIJINA na ɗauki son zuciyarta?, tayaya take tunani zan ajiye al'adun yarena dana tashi

cikinsu na ɗauki ra'ayinta data aro a wajen wasu?, ai duk duniyar da zan shiga dady ina alfahari da abubuwannan guda biyu, YARENA ADDININAH, banajin kunyar nuna kaina a gaban kowanne mahaluki da tambari kasancewata musulmi, dan rahamace babba a gareni da wofantar da ita babbar asarace da bata da madadi duniya da lahira, a duk duniyar dana shiga zan kira kaina bahaushe, koda wanda nake tare dashi baitaɓa jin sunan yaren hausa ba ma zan tabbatar masa da yaren ya fara saninsa a lokacin kuma nai masa AlFAHARI dashi saboda yarena ne, shine harshen da UBANGIJINA yafi ganin ya cancanta na fito a ciki ya zama abin maganata, to mizaisa na ƙyamacesa saboda yaren wasu da ko za'a kashesuma basusan nawa ba, wlhy Dady idan ka cire LARABCI daya kasance yaren MANZON ALLAH (S.A.W) to babu wani yare da yakai muhimmancin dazan fifitashi sama da yarena na HAUSA, duk yaren da kaji yafita a harshena saɓanin LARABCI da HAUSA to inayinsane saboda lalurar mu'amulla da mutane badan ina kallonsa a saman nawaba. Kayi haƙuri Dad mubar wannan maganar kawai, ku tayamu addu'ar ALLAH ya bama kowa dai-dai da ra'ayinsa ni da ita, dan nikam Hudah tafi ƙarfina”.
          Jikin Dad duk yayi sanyi da maganganun Jawaad, dan kuwa dukkan abinda ya lissafa matsalace mai tushe da shima yanada kaso mafi yawa wajen ƙirƙirarta ga ahalinsa, to amma yanzu bata wannan akeba, matsalar mamansa itace gaba da komai. Ya nisa cikin girgiza kai da raunana murya fiye da farko yace, “A karo na babu adadi Jawaad zan kuma cewa kayi haƙuri, ina mai tabbatar maka a yanzu zaka sami mamana a yanda kakeso kuma kake buƙata”.
            Shiru Jawaad yay yana mai kallon Dad cike da tausayi, dan yasan shine ginshiƙin ruguza gidansa wajen sakaci, gashi a yanzu abinda ya raina yayi gawurtar da al'amarinsa yafi ƙarfinsa amma shi baima fahimtaba, cike da girmamawa yace, “Kayi haƙuri Dad zanzo gida na sameka idan na tashi aiki insha ALLAH, wannan maganar bata nan baceba, ALLAH ya zaɓa mana abinda yafi alkairi”. Shiru Dad yay ya kasa tashi, dan gani yake tamkar Jay yawo da hankali zai masa, saboda yasan taurin kan yaron da kafiya idan ya juyama abu baya, tun yana yaro ya fahimci wannan shegiyar halayyar tattare dashi, shiko buƙatar ƴaƴansa bai haɗata da komai a wannan duniyar ba. A bazata Jawaad kawai sai yaga Dad tsuggunne gabansa yana faɗin, “Jawaad dan girman ALLAH karka wofantar da maganar n....” da sauri Jawaad ya miƙe jikinsa har rawa yake ya tanƙwaɓe wayarsa dake kan desk ɗinsa ta faɗi ƙasa, baibi takantaba ya kama hannun Dad yana faɗin, “Ya ilahi, Dad dan ALLAH ka tashi, minene kakeyi haka? Wlhy na tabbatar maka zanzo muyi magana a gida” da ƙyar Jawaad ya samu Dad ya tashi tsaye, gaba ɗaya al'amarin yana neman birkita masa ƙwaƙwalwa, wane irin ubane Dad? Wane irin kalar mugun so ne wannan yakema ƴaƴansa? Abin yayi yawa matuƙa, kowanne iyaye nason ƴaƴansu amma na Dad yana neman wuce hankali. Shidai Jawaad sai ya koma lallashin Dad ɗin ya samu suka fita yay masa rakkiya ya tafi, gaba ɗaya kansa a cinkushe yake, harma ya fara masa wani masiffen ciwo tacan ciki.

        Koda ya dawo office da shashshekar kukan Bilkisu ya fara cin karo, tun shigowar Dad ta farka, dukkan maganganun da Dad sukai da Jawaad kaf ta jisu, takuma fahimci kaso mafi yawa na dangane da matsalar data raba aunty Shahudah da mijinta, Dad ya bata tausayi matuƙa gaya yau, babban mutum kamarsa da ya haifi ɗan da yafi Jawaad amma yake tsugunawa a gabansa domin kawai farin cikin ƴarsa, wanne irin makahon so ne haka Uncle ɗin nata kema zuri'arsa?, a ganinta lokaci yayi da zata bada gudunmawarta ga Dad ko ƴar kaɗance......
      Jawaad tsaye yay a ƙofa hannunsa duka biyu cikin aljihun wandonsa ya zuba mata ido, ransa a dagule yake, sannan ita kuma baisan ma'anar kukan nataba balle inda ya dosa, hakanne ya sakashi jan wani shegen tsaki ya cigaba da takowa cikin office ɗin batare daya sake kallonta ba. Har cikin zuciya da ruhi tsakinsa ya taɓa Bily, hakan ya sake jawo gudun ruwan hawayenta babu ƙaƙƙautawa, ta cigaba da kukanta na tsawon wasu mintuna shi kuma yana cigaba da aikinsa tamkarma baisan da zamanta a office ɗinba. Dan

kanta taji kukan ya isheta ta share hawayenta ta tashi ɗauke da rigarsa a hannu ta nufesa. A tsorace zuciyarta take, amma wani sashe na bata ƙwarin gwiwa akan abinda take shirin yi. Gaban Jawaad taje ta durƙusa kanta a ƙasa. Jawaad da yaƙi ɗagowa ya kalleta dukda yanajin motsinta ya cigaba da aikinsa.
         Karan farko a rayuwar Bilkisu data shirya ambaton sunan Jay a harshenta harma da ƙarfin halin furtawa a gabansa, sai dai tayi imanin bazata iya ambaton sunansa da kallonsaba a yau, dan haka ta duƙar da kanta tana durƙushe akan gwiwoyinta, rigarsa riƙe a hannunta ajiye akan cinya, tace, “Yah Jawaad!.…….”
     Cak Jay dake rubutu a wasu takardu ya tsaya tamkar wanda aka tsaida da remote, shi bai kalleta ba, kuma bai cigaba da abinda yakeba, saima lumshe idanunsa da yay yana sauraren sarawar da kansa ke masa da harbawar jijiyoyinsa harma da gudun jininsa daya tsinke a lokaci ɗaya. Bilkisu daba kallonsa takeba ta cigaba da faɗin “Dan girman ALLAH Yah Jawaad kayi haƙuri karka wofantar da magiyar Dadynmu, wlhy ni shaidace aunty Shahudah na matuƙar sonka, duk da bansan ainahin matsalarkuba inada yaƙinin zaka iya amfani da son da take maka ka canjata, matsalar da duk kake ganinta da ita ƙirƙirarriyar matsalace dakeda tushe a gareta tun tana tsumman haihuwa, ba laifinta bane ita kaɗai haka ta tashi taga kanta itama, bata isa banbance baƙi ko fariba a buƙatar jin zafi saboda an nuna mata hakan shine dai-dai da rayuwarta kuma nasararta, Mahaifina yasha faɗamin, {Bilkisu, aduk lokacin da zama ya haɗaki da mutane ki fara nutsuwa ki fuskanci halayyarsu da tsarin rayuwar da suka rayu, dan babu wata zuciya dake gogayya da ƴar uwarta akan hallayya iri ɗaya, lokacin da k tarbiyyarki ta baki dai-dai a wajen wani shi kuskurene, abinda yake kuskure a yaƙininki a wajen wani dai-dai ne, idan har kika kasance cikin mutane masu fahimtar ilimin duniya ina mai tabbatar miki zaki zama nasararki sama data kowa koda ace ke kaɗai kike kallon kanki a wannan nasarar,  daga lokacinda ilimin sanin hallayar ɗan adam ya dawo tafin hannunki inada yaƙinin zaki gyara ɓarna da yawa, domin zakibi mutum da halinsa ki ɗorashi akan hanyarki mai nagarta batare dashi yasan ya afkaba ma, munzo zamanin da halin ɗan adam dashi ake cinsa da yaƙi bada takobiba, zauna dame ƙinki da zuciya ɗaya, ƙyautata masa kuma da yaƙinin neman sakamo wajen mai badawa ba ga shiba, koda shi a kullum zai kasance mai bibiyar bayanki da sharri, karki zama mai damuwa da zama gwana a duniya, dan wani lokacin nasarar duniya faɗuwace gamai ita, koda idanun duniya na kallonsa a saman kowa, mai kuma sa'a fiye da kowa}, Yah Jawaad ba soyayyarka kawai aunty Shahudah ke buƙataba, a yanzu tafi buƙatar ka jingina da soyayyar tata ka ɗorata a hanyar tsira domin kaikaɗaine zata iya saurara, saboda girmamaka a matsayin gwaninta, na yarda dakai ta kowanne fanni koda banida ilimin sanin ɓoyayyun halayenka, ina sake roƙonka a matsayin Yaya ba shugabana a wajen aikiba, dan ALLAH ka ceto rayukan bayin da zukatansu suke a rufe ruf akan sanin gaskiya da makomar bin hanyarta, yahudanci da nasaranci duhune, wannan duhun kuma shike mamaye da jama'ar gidanmu, sai dai hasken ruɗani da gushewar banbance mai tsafta ya hana ijiyarsu ganin kowanne tsani sai wanda suka hau, kullum fatana ALLAH ya kawo musu drivern dazai fidda rayukansu a kwale-kwale saboda ni nayi ƙanƙanta ƙarancin matsayin yin wannan jagorancin, kaiko inada yaƙinin zaka iya, domin son da sukema aunty Shahudah gyaruwarta tamkar gyaruwar kaso mafi yawane daga ahalin gidan, ciki kuwa harda Dad da tuni ya fahimci gaskiya, sai dai ƙarfin riƙonta a garesa da tafi ya hanashi nunawa ko a fuska, ya gwammaci ya haɗiyeta a rai yacigaba da rainon ƴaƴansa tamkar ƴaƴan agwagi da basa bin uwa sai dai ita ta bisu” na ɗago kai a karo na farko tunda na fara maganar na kallesa, sai dai a mamakinna shi ba ni yake kalloba, gashi yayi kicin-kicin da fuska irin yanda ban taɓa ganiba a tun sanina dashi, na raya a raina saitna dire abinda na fara, dan haka nace, “Dan ALLAH Yaya Jawaad ka yarda a maida aurenku da aunty Shahudah a karo na b....i...y...u.”
         A yanda y

a juyo ya sauke rikitattun idanunsa a kainane yay masifar hargitsani na ƙarasa kalmar ƙarshe da ɗai-ɗai.............✍

Tab wlhy badaniba nayi nan, idan ya huce na dawo na ƙarasa muku yanda aka ƙare🚴🏼🚴🏼🚴🏼🚴🏼🚴🏼kuma bily addu'ar fitowa lafiya itama, dan inaga ba'a taɓa karyata ba😂🤣.

Barkanmu da dawowa, inafatan kowa yayi weekend cikin ƙoshin lafiya?.😍😍[12/1/2020, 12:26 PM] HASNA✍🏻: Bilyn Abdull 📚:
Telegram link group ɗinmu kenan, dan wasu sunata tambaya cewa ya zasu shiga, indai kana tele to kawai ka antaya MASARAUTAR BILYN ABDULL tanan.

https://t.me/joinchat/TIsXYRvhtri2kQ9E4x7w6g


Page 19

................Idanunsa sunyi masifar kaɗawa sunyi jajur, batare da yace dani komaiba yaymin nuni da ƙofa alamar in fita, kasa koda motsi nayi, sai hawaye dake cigaba da ambaliya a kumatuna tamkar an buɗe fanfo.
          Cikin matuƙar kaushin murya da tsawa na tsinkayi furucinsa cikin kunnuwana, “Miemaa! niɗin sa'anki ne ko?!”. Da sauri na shiga girgiza masa kai jikina na rawa saboda harga ALLAH na matuƙar tsorata da yanayinsa. Ya sake faɗin, “Tashi kifita a office ɗinan kafin naimiki duk abinda yazomin kai, Yanzunan har idonki yakai tsaurin kallona ki faɗamin abinda ya dace dani?!, ki fitar min anan kona sauya miki kamanni!!”. Kuka na sake fashewa dashi ina saurin jan jikina nai baya gudun karya makeni, dan harga ALLAH tausayin Dad na tsaga dukkan jijiyoyin jikina harda aunty Shahudah, na tabbatar samun boss ga aunty Shahudah shine farin cikin gidanmu, Hawayen dake ziraromin na share tare da faɗin “Kayi haƙuri dan ALLAH, bazan sakeba”. Cikin faɗan dana rasa abinda ya fusatashi irin haka yace..... “Baki jiniba ko?!” yay maganar a hasale yana tasowa kaina, Baya na shiga jan gwiwoyina batare dana tashiba, matsanancin fushin dana gani akan fuskarsa ya bani tsoro matuƙa, bantaɓa tunanin yanada zafin zuciya irin hakaba, ya nunani da ɗanyatsa yana faɗin, “Badai kece kika buƙata da kanki ba, to duk abinda ya biyo baya kiyi kuka da kanki ba daniba Miemaa, zan aureta tamkar yanda kike buƙata, amma wlhy ko sau ɗaya kikai ƙorafin hakan wataran saina hukuntaki da mafi girman hukunci, indai Hudah ce gaki ga tanan shashashar banza”. Ya ƙare maganar yana ranƙwafowa kaina ya fisge rigarsa dake hannuna ya fice daga office ɗin”.
          Ɗif naji komai na ya ɗauke wuta yabar aiki, sam narasa awane mizani zan ɗora ruɗaɗɗun kalamansa marasa tushe balle makama, man kaina gaba ɗaya ya tsiyaye, babu wata jijiya dake ɗaukar saƙon ƙwaƙwalwa zuwa zuciya dake aiki a jikina har tsahon wasu mintuna da naji saukar abu mai ɗumi a jikina. Zumbur na miƙe domin samun dawowar hankalina daya gushe na wucin gadi. Ban sami damar gama tattaro abinda ya shuɗeba idona ya sauka akan Oga Jabeer dake bakin ƙofa a tsaye yana kallona. murmushi yaymin kafin ya ƙarasa shigowa office ɗin, “Tashi ki shiga toilet ki wanke fuskarki kinji” Ya faɗa yanamin nuni da hannu. Ban musa masaba na miƙe, dan koba komai ina buƙatar duba halin da nake a ciki.
             Bani da isashen lokacin fashin baƙi akan ruɗaɗɗun kalamansa, dan kaina tsaye ina dangantasune kawai da rufewar ido ga mamallakin furtasu, to danmima zuciyata kesan rikitani da hasashen abinda bazai taɓa zama hakaba, na ƙurama kaina ido a madubin dake cikin toilet ɗin ina mai tariyo kalaman dallah-dallah yanda zasu bani fassarar da nake buƙata, “{Duk abinda ya biyo baya kiyi kuka da kanki badaniba Miemaa, zan aureta tamkar yanda kike buƙata, amma wlhy ko sau ɗaya kikai ƙorafin hakan wataran saina hukuntaki da mafi girman hukunci, indai Hudah ce gaki ga tanan shashashar banza}”. ‘Kenan yana nufin inhar aunty Shahudah ta sake koma masa da halinta na baya akwai hannuna wajen cutar dashi? Kuma nizai kuhunta ba itaba? To miyasa? Miyasa zan zama laifi akan ƙoƙarin ganin na inganta auren sunna, na haɗa zukata biyu masu ƙaunar junansu, na tabbata shima yana sonta kawai halayyarta yake ƙyamata, to miyasa ni laifin zai tattara a kaina kuma?’ “Saboda kalamanki ne suka tursasashi yarda ta koma” wata zuciya ta ayyanamin daga can ƙasan rai, ‘To miyasa zai amince da abinda bai zama wajibiba? Ni shawara na bashi da nuna masa ƙwaɗayin samun lada ai ba tilasba, sannan na ceto zuciyar Dad daga ɓacin ran tashin hankalin gudan jininsa, kenan hakan yana nufin kuskure nayi?, ni wacece da har zai amshi roƙona ya wajabtama kansa?, nasake tambayar kaina hawaye na silalomin. Nima kaina sai yanzu naga ƙarfin halina da wautata akan taryarsa, banyi tsammanin zan iya hakanba koda a cikin mafarkine kuwa, zan cigaba da roƙon ALLAH ya hana faruwar mat

salar da yake hangowar, insha ALLAHU lafiya zasu zauna abinsu. Haƙura nai da tunanin na kimtsa jikina da tissue ɗin dana gani a toilet ɗin dan inada tabbacin zai riƙeni har zuwa a tashi insha ALLAHU, na sake ɗauraye fuskata na fito. Zaune na iske oga Jabeer, yana ganina yay ƙaramar dariya da faɗin, “Anya maman nan tamu ba raguwa baceba?” murmushin da ban niyyaba ya suɓucemin, na girgiza masa kai ina faɗin “a'a sir”. Dariyar ya sakeyi da cewar, “To ALLAH yasa, yanzu daga nan sai ina kuma?”. Nace, “Zan koma Office ne, akwai aikin da boss ma ya sani tun ranar waccan monday ɗin ban kammalaba”. Ya miƙe yana faɗin, “To masha ALLAH, nima bara na koma office, amma daga yau idan kikaga Jay a irin wannan matsanancin fushin ki daina masa naci akan koma wane irin maganace, dan idan yay fushi irin haka akwai matsala, ALLAH ne ya taimakeki ya zaɓi ya fita yabar miki office ɗin, amma dabai fitanba ke kuma kika cigaba da taurinkan kin fita komai zai iya biyo baya, ki kiyaye kinji, boss ya wuce duk yanda kike zatonsa, mutumne murɗaɗɗe mai wahalar sha'ani matuƙa, idan yaso kaji dadinsa baka taɓa fahimtar tsaurinsa, idan baiso hakanba wahala zakasha ta gaske”.
       Nace,  “Insha Allah zan kiyaye nagode sosai”.
      “Hakan shine dai-dai, ALLAH ya kiyaye gaba”.
     Tare muka fita, shi ya nufi office nikuma na sauka ƙasa, harna fara tafiya sai naji ina buƙatar ganin yah Qaseem, dan tunda mukazo yau ban gansaba kuma bai nemeniba, ko a waya.
       Nayi knocking kusan sau uku babu amsa, hakan yasani tura ƙofar office ɗin a hankali na shiga, zaune na sameshi a kujerarsa, ya kwantar da bayansa jikinta idanunsa a lumshe, na sake maimaita sallamar tawa idona kafe a kansa. A hankali ya buɗe idonu yana kallona, sai kuma ya tsashi zaune sosai yana murmushi damin alamar nazo da hannu. Takawa nai a hankali zuwa garesa, na zauna a ɗaya daga kujerar gaban tebirinsa idona har yanzu a kansa. Wani murmushin ya sakemin, kafin ya buɗe baki a hankali cikin sanyin murya yace, “Har yanzu jikin dai bilkisu?”. “A'a Yah Qaseem naji sauƙi, mike damunka? Tunda muka baro gida baka da walwala, gashi har yanzu ina ganinta a saman fuskarka kuma, mike faruwane?”.
       “Humm” ya faɗa yana cije baki, kafin yace, “Babu komai, kawai dai banajin ƙarfin jikinane”. Numfashi na sauke a hankali fuskata na nuna tausayinsa, nace, “To ko zamu tafi gida kaga likita”. Nanma kansa ya girgiza mani, cikin kauda maganar yace, “Kinci abinci ko?”. Kaina kawai na iya ɗaga masa, dan jinai dukna damu da halin da yake a ciki, shiru mukai na wasu mintuna kafin na miƙe nace, “bara na wuce dama leƙoka nayi dan naji shiru”.
      Baice komaiba saida na doshi hanyar fita daga office ɗin, “Ki ƙoƙarin gama abinda kikeyi, da anyi la'asar zamu wuce dan yanzu Mom ta kirani jikin Shahudah ya sake rikicewa”. Sosai naji gabana ya faɗi, na kaɗa masa kai kawai ina haɗiye ƙwallar data cika mani ido, “ALLAH ya bata lafiya” “Amin”. ya amsa mini akan laɓɓa.

★★★★★★★

               A ɓangaren Jay kuwa gaba ɗaya yarasa gane kansa, haka kawai ya tsinci zuciyarsa da fushi mai tsanani, koda ya fita daga station rasa ina zai dosa yayi, yata zagaye gari daga wannan titi zuwa wannan har ƙarfe biyar na yamma, sallar la'asar kawai ya tsaya yayi da lokacinta yayi, ganin yamma tayi saiya juya kan motar Jabeer daya ɗakko daga office ya nufi gidan Alhaji baba kakansa.
       A ƙofar gida ya iske Alhaji baba da tsaaffin anguwar a bishiyar dalbejiyar dake ƙofar gidansa, inda yake zama duk yamma yasha iska koda hantsi, sai yazam tsaffin dake anguwa sukanzo suma su zauna suyita hira, a kusa dasu yay parking, yaja kusan mintuna uku bai fito a motarba, tsoffin nata magana akan wanene? Amma bai tankaba balle ya fita, shiko Alhaji baba bai tankaba, dan yaji a ransa Jawaad ne dukda yasan ba motarsa bace, kuma glass ɗin motar nada duhu ba'a ganin na ciki.
      Sai da ya mula dan kansa ya buɗe ya fito. Alhaji Baba ya bisa da kallo kawai batare da yace komaiba. Jawaad ya rissina ya gaida tsoffin kafin ya miƙe ya nufi hanyar gate ɗin gidan batare da yacema Alhaji baba komaiba. A falo ya zube saman doguwar kujera ko takalmi bai cir

eba, ya lumshe idanunsa yana maijin kewar iyayensa na tsarga masa da zafi-zafi, a yau babu abinda yake tsananin buƙata sama da ɗumin mahaifiyarsa, burinsa kawai ya ɗora kansa a cinyarta tana shafawa da tambayar damuwarsa, shiko ya juye mata duk abinda ke ransa ta bashi shawara da masa addu'a. Sai dai kuma gashi ƙaddara ta daɗe da hana hakan a jerin farin cikin rayuwarsa, ƙilama tuna tabar masa duniyar bai saniba, kokuma ta fita hayyacinta fiye da yanda zata iya tuna ita wacecema balle abinda shi ta haifa, amma duk yanda take yanason abinsa, zaiyi farin ciki da maraba da ganinta a duk yanda take.
           Buɗe idanunsa yay saboda saukar hannun Alhaji baba a saman fuskarsa yana share masa ƙwalla, Alhaji baba yay murmushi cikin zolaya yace, “Kullum kai saika kwaso ragwantakarka ka kawomin gida, ina namijin dake filin daga ina kuka Muhammadu”. Murmushi Jay yayi tareda lumshe ido yana rungume hannun kakan nasa a cikin wuyansa, baidaice komaiba, hakan yasa Alhaji baba ɗaga kansa ya zauna sannan ya maida kan saman cinyarsa ya ɗora, ahankali ya shiga shafa kan Jay dake cinyar tasa, hannunsa ɗaya kuma na shafa fuskarsa da ƙananun gashin saje da bai askeba ke kwance a jiki. Shiru sukai gaba ɗaya, Jawaad yay lamo a jikin kakansa yana sauke numfashi a hankali, tuni kaso mafi yawa na damuwarsa yaji ya gudu, tsahon lokaci suka ɗauka a haka babu wanda yay magana, ganin lokacin salla ya gabato Alhaji baba ya shafa fuskar Jay yana faɗin, “Muhammadu tashi kaje kai wanka kayo alwala muje masallaci”. Buɗe idanu Jawaad yay a hankali, sun ƙanƙance sosai alamar yanajin barci, tashi yay ya nufi ɗakin kakansa dan baida matsalar kaya tunda yana ajiyewa anan. Cike da tausayawa Alhaji baba ya bisa da kallo, yana tsananin son jikan nasa tilo namiji da tausayinsa matuƙa, a kullum baya gazawa da yimasa addu'ar kariya daga dukkanin abin ƙi da maƙiya.
 
             Ana ƙoƙarin shiga sallah Jawaad ya fito a gaggauce cikin jallabiya ruwan siminti, sai ƙamshin turaren kakansa yake mai sanyin daɗi, tare suka tafi massalaci dan Alhaji Baba yayi alwala a toilet ɗin falo. Koda aka idar sai sukai zamansu acan har isha'i, bayan sun fitone Alhaji baba yay sallama da mutane da neman gafara ga wanda ya ɓatamawa bisaga al'adarsa, dan acewarsa bai zama lallai yana cikin jerin masu tashi suga safiyar gobe ba, shiyyasa duk bayan kowacce sallar isha'i yakanyi sallama da maƙwaftansa da neman gafararsu kafin ya shige gida. Sun iske Nabeelah ta kawo masa abinci kamar kullum, tunda ta gaida Jay sau ɗaya ya amsa yay kwanciyarsa a doguwar kujera, sai hira suke ita da Alhaji Baba, zuwa takwas da rabi tai musu sallama ta tafi dan tare suke da driver dama. Tana fita Jawaad ya sakko ya shiga buɗe kulolin da aka jero cikin kwandon mai ƙyau daga gidan Ummah, tuwone kamar kullum dare da Alhaji baba ya wajabtama kansa, jay ya miƙe zuwa kicin ya ɗakko filet da cokali, tuwon alkamar ya dawo ya ɗiba da miyar ɗanyar kuɓewa, shidai Alhaji baba nata tsokanarsa da gwauro kafi tuzuru. Wani ya tanka wani yay shiru, sai kuma a hankali ya saki jikinsa sukai hira sosai kamar yanda Alhaji baba ya buƙata, cikin hikima kuma yake masa nasiha, sai wajen sha ɗaya suka kwanta, dan Jay yace anan zai kwana yau, da yayi sallar asuba sai ya wuce gida.

★★★★★★

             Ƙarfe huɗu da rabi muka bar office, daga nan asibiti muka nufa, mun iske jikin aunty Shahudah kan babu daɗi, dan yanzunma dai saida tasha allurar barci. Anan muka zauna har magriba saboda kowa yana nan sannan muka tafi kamar yanda Dad ya bamu umarni. Har zuwa yanzun

Please Login or Register in order to submit comment