Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

tsawon shekaru kuma."
Kwaffa tayi cikin baƙar zuciya tace.
"Uhum ki jirani bafullatanar daji tabbas zan biyo ta kanki".
Tafaɗa tana wani irin shu'umin murmushi.

A can Part ɗin Lamiɗo kuwa.
Sheykh ne zaune a parlour'n Gimbiya Aminatu su Lamiɗo da Abba'n sa da Galadima duk suna zazaune can gefen ɗaya falon.

Gimbiya Aminatu ce ta fito daga cikin ɗakinta tare da wata ƴar karamar ƙwarya takaraso gaban Sheykh tamiƙa masa tana faɗin
"Ungo karɓi ka kaiwa Aishatu kasan masu ciki sai da ɗan kayan marmari musamman maiɗan tsami-tsami kaivmata tasha nasan zataji daɗin bakinta".
A bazata maganar tazowasu Lamiɗo cikin tsananin farin cikin jin cewa Shatu na da ciki Lamiɗo yadafa kan Sheykh yace
"Masha Allah Slhamdullah godiya ta tabbata ga Allah munji daɗin samin wannan babban Al'bishir kami ƙamin gaisuwata gun Aishatu".
Murmushi Abba yake cike da jin daɗin hakama Galadima.
Shiko Sheykh kansa ya ɗan kawar tare da karɓar ƙwaryar da Gimbiya Aminatu take mika masa.
Murya can ƙasa cikin maƙoshinsa yace.
"Koma menene ni zanci tun da nike laulayin ba itaba".
Yayi maganar a saman lips ɗin sa,
Da sauri Abba ya zuba masa ido cike da mamaki, kenan Jabeer gadonsa yayi shikeyiwa matarsa laulayi, murmushi yayi sanin yayi maganar ne batare da yasan tafito ba.
Shiko Sheykh mikewa yayi rike da ƙwaryar yanufi kofa yana cewa
"Sai anjima"
cikin ɗan ɗaga murya Galadima yace.
"A miƙa mana gaisuwa gun ta".
Shidai baice komai yafita dan a zatonsa basuma ji mgnar da yayi ba.

A parlour yasameta zaune ita ɗaya Ummi na kitchen.
A hankali ya ƙaraso gareta.
Hannunshi kawai yasa ya kamo mata.
Ba musu ta miƙe, hannunta yaja suka nufi falonshi.

Bisa kujera ya ajiyeta, kana ya zauma kusa da ita kallonsa tayi tare da kallo ƙwaryar dake hannunsa sai ta daɗa matsowa jikinsa sosai tace
"Menene wannan ɗin?".
gyara rike ƙwaryar yayi tare da cewa.
"Gimbiya Aminatu ce tabani wai in kawo miki irin wai ke mai ciki al'halin nine ma nake miki laulayin.
Dan yanzu dai koma menene ni zan cinye tun da nike laulayin".
Ya karasa faɗa yana ɗage faifayin da a ka rufe ƙwaryar da shi, kindar ne fari sol sai ɗan mai kon yelo a saman sa, yawun da ya cikin mata baki ta haɗiye tana miko hannu tana faɗin
"Bani tunda ni tace ka kawowa".
ƴar karamar ludayin duma dake ɗaure kan fefayin yaɗauka yaɗibi kindar mai sanyi da shi,
kana yace
"Sai dai kijira idan na koshi nabaki sauran".
Ya ƙarashe mgnar yana ɗago ludayin yakai bakinsa, lumshe ido yayi jin garɗin daɗi da sanyi da ɗan tsami-tsami ya gauwaye bakinsa, sosai yaji daɗin yadda yaji ɗan tsamin a bakinsa.
Zumbura baki tayi tare da cewa.
"Ni dai ka bani".
A hankali ya kamo hannunta ya ɗagota ya ɗaurata kan cinyarshi yasa ƙwaryar a tsakiyarsu,
Ido ya lumshe tare da sa hannunshi ya tallabo haɓarta bakinsu ya haɗe, a hankali ta buɗe bakinta.
Shi kuwa cikin sanyi ya lasa mata kidar ɗin.
Kusan a tare suka lalumi tong ɗin juna,
jin yadda ta mishi riƙon lollypop ne ya sashi janye bakinsa da ƙarfi tare da cewa.
"Wash Mamey zata cinye min harshe".
Da sauri ta riƙo hannunsa dake rike da ludayin takarkatashi takawo bakin ta takurɓa, harshenta ta fidda talaso sauran ragowar dake cikin ludayin.
Hannunsa ta sake tana gyara zamanta da kyau ta ce
"Yah Sheykh shanyewa zakayi gaskiya ni dai kabani kayana".
Da sauri ya ɗan zaro idansa tare da cewa.
"Kuma tun yazu kike so in baki."
ido ta rufe kana ta buɗe tana kallonsa.
Sai kuma yasaki wani murmushi da har sai da jerarrun fararen hakoransa suka bayyana,
yatsar sa ya miƙa kan kumatunta yalakaci kindar daya shafu mata a gefen kumatu yaɗa go yatsar, kana yanuna mata, fuska takwaɓe tare da turo baki gaba tace
"Bakai bane".
ludayin yakuma maiwa da cikin ƙwaryar yaɗiba yakai bakinsa yakurɓa tare da mai da ludayin cikin ƙwaryar kana yace
"Danayi mefa?".
baki takuma turawa tace
"Ka hanani a buna".
ido ya kuma zarowa yace.
"Ni Muhammad na isa in hanaki abunki da Allah ywce in baki.
Taso muje ɗaki nabaki abin naki yanzu nan".
Ya ƙarashe mgnar yana mata dariyar wasa kafaɗa ta maƙe gane abin da yake nufin, tace. "Nidai a'a wanna nakeso". ta ƙarashe
tana nuna ƙwaryar. mikewa yy yariko hannunta yace.
"Zomuje duka zan baki ai da wannan ɗin da Jabeer ɗin".
yana rike da hannunta ɗaya hannunsa na rike da ƙwaryar suka nufi bedroom ɗin shi.


Rayuwa kenan. Haka rayuwa tacigaba da tafi kwanaki suna juyawa i zuwa makonni, makonni na shuɗewa i zuwa watanni.

Alhamdullah cikin ikon Allah da buyawansa yanzu cikin Shatu wata shida kenan kuma har yau magauta basu san da shiba dan bata fiye fita kuma cikin baida wani girma.
Tana zuwa makaranta tana karatunta hankali konce.
Tana waya da Ummeynta.
Alhamdullah yanzu zazzaɓin daren da Sheykh yakeyin nan yazamo tarihi yawarke tsaf abinshi,suna rainon cikinsu cikin kula da tarai raya da ɗonkin ganin ranar zuwan Baby.

Zaune suke a parlour Ummi na saman kujera Shatu kuma na zaune a kasan carpet ta mimmike sawunta ta tasa ɗan madaidacin cikinta a gaba,
tana ɗan kurɓar kunun tsamiya da Ummi ta dama mata,
Ummi ta ɗan kalleta tare da cewa.
"Ikon Allah kinga na sha a fa ɗazu Juwairiyya ke cemin Gimbiya Aminatu ba lafiya tana zazzaɓin mura".
A jeyi cup ɗin kunun tayi tana cewa.
"Allah sarki shiyasa tun jiya bata turomin haɗin furan nan ba Ummi muje mudubata tunda ba abinda mukeyi". Ta ƙare mgnar tana miƙe cafal kamar ba mai cikiba.
Cikin fari kenan.
A hankali ta shiga ɗaki taɗauki ɗan ma dai-dai-cin hijabi tasaka a kanta tafito,nan tasami Ummi rike da mayafin ta.
Tare suka nufi sashin Gimbiya Aminatu.

Da sallama suka shiga parlour'n Gimbiya Aminatu.
Ummi na gaba Shatu na biye da ita.
Hajiya Mama da Gimbiya Saudatu duk suna zaune cikin parlour'n.

wani irin mikewa Gimbiya Saudatu da Hajiya Mama sukayi cikin tsananin
kaɗuwa da zallar mamaki suke kallon cikin da basusan farkon saba sai daya baiyana kansa yau rana tsaka suka ganshi,
Cikin wani irin tashin hankali da baƙin cikin Hajiya Mama ta juya cikin wani irin kiɗima tafice a parlour'n gaba ɗaya idanunta sun wani fiffito sun zazzaro waje saboda sabar firgici da baƙin cikin wannan cikin data gani.

Tana fita hanyar part ɗin ta tanufa hankali tashe, ɗago wayarta tayi tana tafiya tana daddanna shi tana sharar ƙwanar part ɗin ta takai wayar kunne,
Tana wani irin huci na tashin hankali,daga cikin wayar kuwa ringing biyu zuwa uku a ka ɗaga me biye da kiran

yace.
"Hajiya bar".
Da sauri cikin ɗaga murya tace.
"Dakata Boka gilmau bana bukatar gaisuwarka! haka mukayi da kai wani irin makudan kuɗine ban zubda makaba k".
Cikin dakiya boka GILMAU ya katse ta.
"Da kata Hajiya ki daina min ihu akunne dan ba fahimtarki zanyiba."
Bokan yadakatar da ita kafin takarass faɗar kalmar k. data furta.
Itako cikin musifar tashin hankalin da take ciki tace
"Gani nan zuwa gurin ka yanzu dan wlh bazai yuwuba dole a sake sabon shiri".
Tana kaiwa nan takashe wayar tashiga ciki taɗau mayafin ta da makullin mota da da wasu kuɗaɗe masu yawa a ɗaure bandir-bandir tafita tanufi in da mota yake tashiga taja da mugun gudu tafi tanufi gidan Boka.

Cikin rawan jiki take tuƙi hannunta ɗaya riƙe da waya ta kara a kunne wanda ta kira Jahan.
Shi kuwa Sheykh (Jahan) kenan yana zaune a Office nashi yaga kira da layinsa na sirri a yar ƙaramar wayar da ko inganta a garƙame yake.
Murmushi yayi ganin 3 bala'i da haka ya seba number.
Wani murmushi iya salon taku yayi kana ya amsa kiran tare da ƙara wayar a kunne ya sauya muryarsa tare da cewa.
"Hajia Mama Uwar Sheykh meke faru".
Cikin faɗa tace.
"Oouxubillahi subahanallahi Jahan kada ka sake cemin uwar Sheykh kai kasan duk duniya babu wanda yasa irin zallar tsanar da nakeyiwa wannan shegen yaron da sihiri baya cinsa data daɗi wlh yau ji nakeyi zan iya zubawa Part ɗinshi Dana ƙannenshi wuta su ƙone su mutu kowama ya huta".
Wata iriyar ja'irar dariya yayi tare da cewa.
"A a to yau kuma me kika gani a kansu ɗaya tada miki hankali ne haka".
Cikin tafasan zuciya tace.
"Dariya ma na haka kenan, to bari kaji wannan shegiyar matar tasace, naga cikine da ita cikima mai girma kuwa".
Da sauri yace.
"To dan ganin cikin ne hankalinki ya tashi".
Cikin tsantsar tsana tace.
"Wlh tallahi sai na zubda cikin nan wlh babu wanda zai ƙara haihuwa cikin ahlin A'isha nida nake son on ɓaddasu a masarautar Joɗa ya zanyi in barsu suyi ta haihuwa wlh zan zubda cikin in Kuma ya fito duniya tabbas zan kashe ɗan".
Wani irin miƙewa tsaye yayi lokacin ɗaya zufa mai zafi ta karyo mishi gaba ɗaya jikinsa rawa yake, cikin saisaita nitsuwarsa yace.
"Eh lallai wannan batun babbane bari anjima zanzo muyi shawarar yadda zamuyi".
Yana faɗin haka ya katse kiran.
Yatsarsa manuniya yasa ya sharce zufan daya feso masa a goshi.
Kana sai kuma yayi murmushi tare da cewa.
"Innalillahi wa innailaihi rajiun. Hasbunallahiwani'imanwakil."
Yayi ta maimaitawa kana ya koma ya zauna ya dafe kanshi tare da cewa.
"Uhmmmm Hajia Halima kenan rashin sani ya saki kina shuka a idon makorwa.
Wai ni Muhammad Jabeer mena tsare miki nada yan uwan da mahaifiyarmu da kike so ganin baya mu, me cikin matata ya miki, meyasa zaki so cutarmi da Aish da ɗan...!




By
*GARKUWAR FULANI*GARKUWA




PAGE 25

"Da Mamaki kwallo a maƙabarta.
Wato dai haka za a cigaba da gwara kawunan mutanen. Masarautar Joɗa ana mayar da su marasa tunani?".
Gimbiya Saudatu Ta faɗa tana ya mutsa fuska don ta kasa kallon ƙwayar idon Sheykh.
Banza ya yi da ita duk da ya waiwayo ya kalleta, ya so tanka mata, amman sai ya share yaci gaba da takunshi cikin nitsuwa yana tafe yana tasbihi.
A hankali ya isa falon.

Kanshi ya ɗan juyo ya kalli tsakiyar falon.
Sam bai hango Shatu da Ummi ba dake zaune a falon.
A nitse ya maida kanshi ga inda ya nufa ya juya zai shiga corridor'n da zai sadashi da falonshi. "Ba ka ji me nace bane? Dutse ne kai ko waliy? Wata da watanni a kawo maka mace a ce sai yau ake bada kyautar budurci dan rainin wayo tuntuni kallon hoto kake mata ko me.
Ba ma wannan ba, wanne irin munafurci ne ya sa aka bada kyautar dawakai amarya da ango? Duk yana cikin sahun munafurcin da boye-boyen.."
Cikin tsawa ya dakatar da ita da cewa.
"Bana son shirme fa! Fitar min a gida tunda ba wancan tsohon ne ya gina min shiba".
Da sauri tace.
"Zan fice ba sai ka koreni ba."
Ta ƙarashe mgnar cikin tsananin takaicin tsawar da ya yi mata don sai da hantar cikinta ta kaɗa.
A dake ta jujjuya idanuwanta tare da cewa.
"To wai ɗaga Muryar na meye ne? Tambaya fa kawai nayi nake son amsa.
Wannan sarƙar kuma ta mece ce? Ta asalince wacce ta ɓace ɓat ko in ce ta yi ɓatan-dabo, ko kuma wata ce ta dabam aka ƙirƙiro, don nasan waccer dai bata kai labari ba, daga wuyan waccer ts..."
Bai bari ta cigaba ba ya tare ta da muryarsa a nutse cikin iya sarrafa harshe, ya lumshe idonshi kana ya buɗesu a hankali yace.
"Dakata, tsaya kiji."
Da sauri tace.
"Uhum ina jinka".
Rausayar da kanshi yayi kana a hankali yace.
"Kyauta ce ta girmamawa, wacce ba kowacce mahaluƙiya ce take katari da irinta ba a cikin Masarautar Joɗa, duk da kyautar ta yi kaɗan a wajen wacce ta cancanci ninkin hakan, bana ji akwai abinda za a iya biyan macen ƙwarai da abun duniya ba ko da kuwa za a bata kujerar masarautar Joda wanda wasu wayayan mazaunan cikinta ke wawasun nema ba. Darajarta da kimar kyautar data bada yafi ƙarfin tukuicin da masararutar Joɗa ke badawa, ita ba irinku bace ta wuce hakan".

Shiru Ummi tayi tana mai jin kalamanshi tare da yin wani sassanyan murmushi.

Ita kuwa Aysha a hankali ta lumshe idonunta tanajin kalamanshi masu sanyi da sanyaya zuciya.

Gimbiya Saudatu kuwa. Wani irin baƙin ciki ne ya turniƙe ta, da kyar ta iya saita numfashinta cikin karkarwar jiki da rasa abin cewa ta ce, "Wannan wanne irin yabo ne haka har sai ka haɗa da sarautar gidan nan?"
Yanayin ta ya kalla ya yi Murmushi, wanda ya ƙara tunzirata kana a nitse yace.
"Dan na tabbatar miki da ƙimarta da darajarta ne, ina son kuma hakan ya zauna a cikin ƙoƙon ranki har illa masha Allah..."
Cikin takaici tace.
"Wannan kuma ka yi kaɗan ka sani adana shi a raina"
Kallon da yake mata ne ya hana ta ƙarasa zancen, don daga inda take tana iya jiyo sautin hucin da yake, muddin ta ƙara sa maganarta tsab zai iya wanka mata marin da zai sa ta rasa jinta na awanni.
Da hannu ya nuna mata ƙofa alamar ta fice mishi a gida.
Kamar munafuka ta wuce simi-simi tana gunguni.

Juyowa yayi ya nufi cikin, sai kuma ya ɗan juyo ya kalli cikin falon jin alamun akwai mutun a ciki.
Juyowa yayi cikin falo.
Cikin nitsuwa ya kalli Ummi da Shatu.
Da alamun Ummi lallaɓata take taci abinci,
Idonshi ya ɗan lumshe, haka nan yaji wani irin sanyi har cikin ransa yake jin daɗi.

Wani ɗan guntun Murmushi yayi bayan ya kalli fuskar Shatun data ke kwaɓe har da turo baki.
Wayar Ummi ce ta fara suwa juyowa tayi ta ɗan jawo wayar,
tana dubawa taga Umayma cikin farin ciki ta ɗaga, tare da karawa a kunne kana tace.
"Assalamu alaikum, Umaymah Sheykh."
Cikin tarin jin daɗi Umaymah tace
"Wa alaikassalam Ummin Sheykh ina yaran naki? Ya jikin ɗiyar tawa"!".
Murmushi Ummi tayi kana tace.
"Alhamdulillah suna lfy, ɗiyarki jiki da sauƙi gatasu ma kusa dani".
Cikin kula tace.
"Bata wayar".
To Ummi tace kana ta miƙawa Aysha wayar.
Tare da cewa.
"Ga Umaymah".
Amsa Aysha ta yi ciken jin sanyi tace.
"Assalamu alaikum Umayma barka da rana."
Cikin tsananin kulawa Umaymah tace.
"Waalaikumus salam Habibty, sannu Aysha Addana, Allah ya yi miki albarka, Allah ya saka miki da al'khairi, na ji daɗi sosai, in sha Allah al'khairi da haske yanzu zai bayyana, sannu kin ji my dear, ki kula da kanki sosai, ki dinka shiga ruwan dumi akai akai, sannan kada ki yi wasa da kunun nan da Ummi take miki, kin ji ƴata ki yawaita cin gashin naman da zatanayi miki da shan kunun har na tsawon kwana uku kinji ko Aysha."
Wata azababbiyar kunya ne ta rufeta.
A kunyace tasa ɗayan hannunta ta rufe fuska tana jin inama ƙasa ta tsage ta shige cikinta.
Da ƙyar ta iya ce wa,
"To Umayma."
Jin Muryarta ya sa Umayma yin dariya don tasan kunyace irin na ƴaƴan Fulani ne yasa ta yin shiru.
Cikin murya mai baiyana jin daɗin da take ciki tace.
"Yauwa Aysha, Allah ya yi miki al'barka."
Cikin sanyi da jin daɗi tace.
"Amin Umaymah".
Kana daga nan
Suka yi sallama ta kashe.

Sunkuyar da kanta tayi tare da mikawa Ummi waya, don izuwa yanzu kunya ta gama jiƙeta, kallonta Ummi ta yi tana jin dadi aranta tana kuma addu'ar Allah ya nuna musu ranar da ƙwai zai fasha, don ga alamun nan suna ta tabbata.
Shi kuwa Sheykh ajiyan zuciya mai sanyi ya sauke kana ya juya ya nufi falonshi.

Ummi kuwa Kitchen ta wuce da tray'n a hannunta.


Ita kuwa Aysha Anan falon ta zauna tana tunani kala-kala musamman akan masarautar sam ta kasa gane mata.
A kullum da kalar surƙullen da zai bayyanar mata, ko meye ma'anar zantukan da suke yawan yi wanda bata gane masa ba?.
Dazu tajiyo Gimbiya Saudatau da Sheikh maganganunta sun bata mamaki, lallai akwai wani babban al'amari a cikin gidan nan, wanda da sannu zata fahimci menene wannan abu.
Kuma zata tambayi Ummi wani abu ko zata gaya mata, ko ta samu sauƙin Tsarkakkiyar dakw cinnzuciyarta.
Tana nan zaune har aka kira sallar la'asar ta tashi daƙyar don har yanzun bata jin dadin jikinta.
Bedroom ɗin ta ta wuce.
Kai tsaye Bathroom ta nufa.

Al'wala ta ɗauro don har masallacin masarautar sun tada kabbara.

A hankali take taku sabida har yanzu tanajin jikinta na mata zafin rabuwa da budurci.
Sallaya ta shimfiɗa kana itama ta tada kabbara.

Bayan ta idar da sallah ne,
ta kuma miƙewa a hankali ta fito falo, sabida ta gaji da baccin kwanciya tayi bisa kujera da wayarta a hannunta, tana mgna da Junaidu.

Ummi kuwa tana kitchen.

Murmushi ta ɗanyi jin Junaidun na cewa.
"Dan Allah Adda Shatu kicewa su Bappa su dawo haka nan, zamansu a waccar ƙasar ya isa.
Ina kewar Junainah, Rugar Bani gaba ɗaya muna kewarsu dan Allah su dawo".
Gyara konciyarta tayi tare da cewa.
"To Junaidu in sha Allah zan gaya musu, su dawo maka da masoyiyarka dan nima nayi kewar Junnu ina kewar Ummey na".


Ummu dake kitchin ne ta ɗan tsagaita daga motsa naman da take fasawa Aysha
Sabida jiyo sallamar Hajiya Mama da Aunty Zuwairiyya.
Haka yasa ta fito tai musu barka da zuwa kana suka gaisa tare.
Sannan tace su isa Aysha na ciki.

To Juwairiyya tace kana tai gaba Hajia Mama na biye da ita a baya.

Ita kuma Ummi ta koma Kitchen dan kawo musu ruwa.

Ba a jima ba sosai Ummi ta debo drinks ta fito da nufin kai musu.
Sai kuma sukayi kiciɓis a bakin ƙofar falon Ayshan. Sun fito falon Shatu fuskarsu a murtuke, da alamun ransu a ɓace, suka wuce ta.
A hankali ta bisu da ido, tare da tambayarsu.
"Har kun fito ko ruwa baku shaba".
Dukansu babu wacce ta kulata suka fice.
Ajiyan zuciya ta ja ciki da mamaki, sai kuma ta juya ta nufi falon Ayshan.
Tana gab da shiga falon ta ji sautin muryar Aysha na faɗa da ɗan ɗaga murya take cewa. "Mitssssss munafukan banza masu fuska biyu mugaye masu baƙaƙen zuciya. In sha Allah sai Allah ya toni asirinku!".
Da sauri Ummi ta ƙaraso gareta tare da ajiye tray'n hannnunta bisa stoll cikin kula tace.
"Lafiya dai Shatu Meya faru?".
Girgiza kai Shatun ta yi cikin jin haushi ta ce
"Ummi nace bana son su, bana son ganin sun shiga rayuwata, bana son su rinƙa zuwa inda nake saboda na tsani mu'amala da mai fuska biyu."
Ajiyar zuciya Ummi ta yi tana jujjuya zancen Shatun, da kuma tsananin mamakin takun sakar dake tsakanin Aysha da Hajiya Mama.
Numfashin ta ɗan fesar tare da dafa kafaɗarta kana a hankali tace.
"Shike nan ki yi hakuri yanzu ai sun fita."
Ƙwafa Aysha ta yi tare da kishingiɗa sosai tana mamakin yanda mutanen gidan suka kasa fahimtar komai tana matuƙar mmkin in ance wai Hajia Mama itace Mamansu Sheykh kuma ita har yau bata yardaba bata kuma jin zata yarda har gaban abadan.


Bayan ta idar da sallar isha har yanzun jikinta ba kwari haka tana jin ciwo a gabanta musamman in ta miƙe tana tattakawa, miƙewa ta yi a ciccije, "Wash Allah na!".
Ta faɗa haɗe da miƙewar ta fara tafiya tana gwale-gwale kamar ƴar kaciya, kallonta Ummi ta yi tana nazarinta, bayan ta shige ɗaki ta tashi ta bita ɗakin.

A tsaye ta sameta gaban drower'nta.
Juyowa tayi ta kalli Ummin dake matsowa kusa da ita tare da cewa.
"Aysha kin sake shiga ruwan ɗumi kuwa?".
Kai ta jujjuya mata a hankali tace.
"Ɗazu da yamma dai na shiga".
Kai Ummi ta jinjina kana tace.
"Yauwa to kije yanzuma ki shiga ruwan ɗumi zakiji sauƙin abin sosai."
Ya mutsa fuska ta yi irin na mai jin ba daɗi kana cikin sanyi tsce.
"Ummi bana jin daɗi kwata-kwata."
Kusa da ita ta matso cikkn kula tace.
"Na sani, amma shiga ruwan ɗumin zai tai maka kwarai wajen jin daɗinki, don zaki sake sosai, duk wannan ciwo-ciwon zaki daina ji." Kwafe fuska ta yi kamar zata yi kuka.
Yanayinta Ummi ta kalla, ta so yin dariya sai dai kuma danne tare da cewa.
"Yi haƙuri kin ji Ayshs, daure kada ki zama raguwa mana."
"Uhmm".
kawai tace ta miƙe ta shige cikin bathroom.

Ita kuma Ummi ta wuce kitchen tare da ɗauko haɗaɗɗen kunun gero wanda ake yinsa na musamman kuma shi ake bawa amaren masarautar haɗe da farfesun farararen tattabaru, wanda shi ma wani haɗi ne na sirri mai tsuma mace, da yajin da ake barbaɗawa akan tattabarun wanda yake ƙarawa mace wani ɗanɗano na musamman.

Ita kuwa Aysha ta daɗe cikin ruwan ɗumin tana jin wani irin daɗi na ratsa ta, lumshe ido ta yi, tare da miƙewa tayi wanko fes kana ta fito.

Tana buɗe toilet ɗin ta ji ɗakin na ƙamshin wannan gashin tattabarun da Ummi ta kawo mata su har ɗaki.
A hankali ta matso gefen Ummi dake cewa.
"Yauwa kin fito ko Aysha?".
Kai ta gyaɗa mata tare da cewa.
"Eh Ummi".

"To yanzu ya kikaji jikin naki?".
Ummi ta kuma tambayarta.
A kunyace tace.
"Alhamdulillah naji sauƙin".
Cikin gamsuwa Ummi tace.
"Toh zo ki zauna ga wannan kici duk za su ƙara miki ƙwarin jiki." Girgiza kai tayi alamar bazata ciba.

"Yi haƙuri ki daure kici." Ummi ta daɗi mata cikin lallami.
Zama Ummi tayi tare da janyo flask ɗin ta zuba mata mai ɗan yawa.
Kana ta turo mata plate ɗin gabanta, kunu ta tsiyaya mata a cup mai ɗan girma ta miƙa mata tare da cewa.
"Yauwa maza kici zakiji daɗin jikinki".
A hankali ta gyaɗa mata kai, dan bacci ya fara kashe mata jiki.
Cikin lumshe ido ta fara sawa a bakinta.
Jin wani irin ɗanɗano mai daɗi ya ziyarce harshenta ne yasata, lumshe ido tare da haɗiye tsinkekken yawun bakinta ta cigaba da taunawa tana haɗiyewa tare da korawa da kunun geron.

Ummi kuwa tana ganin ta faraci ne ta wuce ta fita.

Bayan ta gama ta shanye kunun don shi ma ya yi mata daɗi sosai.

Cike da bacci ta ɗaura plate ɗin kan kofin ta turasu gefe kana a kasalance.
Ta wonke hannunta.
hamma mai sanyi tayi kana ta kwanta nan bacci ya yayi awon gaba da ita.

Shi kuwa Sheikh yana dawowa daga sallar isha ɓangarensa ya wuce kai tsaye.
Yana shiga bedroom ɗin sa ya zare al,kyabbarsa tare ta ajiye hirami gefen gadonsa ya zauna, yana ajiyar zuciya tare da lumshe idonsa.
Wayarsa ce ta yi suwa,
Ido ya zubawa wayar yana kallon mai kiran, kamar ba zai ɗaga ba,
Sai kuma dai ya janyota hade da murza screen ɗin wayar.
Da sallama ya amsa. Cikin zolaya Haroon ya ce.
"Barka da dare angon Shatu."
Wani ɗan guntun Murmushi Sheikh ya yi, haka nan yaji sunan yamishi raɗau yayi masa a kunne a zahiri kuwa ɗan gajeren tsaki yaja tare da cewa.
"Bana son surutu fa." Cikin Murmushi shi ma Haroon yace.
"Kasan dai ba ƙarya na yi ba, balle ka fara yi min wa'azi."
Gyada kansa yayi tare da cewa.
"To ina jinka menene zaka kirani da daren nan?".
Murmushi nan Haroon ya cigaba da tsokanarshi har ya gaji ya katse kiran.

Dai-dai lokacin kuma ya ya fara jin yunwa haɗe da zazzabi mai zafin gaske wanda ya jisa atake.
A hankali ya miƙe yana jin zazzaɓin tamkar wanda ake ƙarawa tun daga kan yatsansa har zuwa saman kansa, cikin tafiya a hankali ya fito daga bedroom ɗin zazzaɓin na cigaba da fisgarsa da ƙyar ya kai tsaƙiyar falon ya zauna kan kujerun dake falon, a hankali ya kwantar da kansa jikin kujerar yana furzar da numfashi mai zafi, lumshe ido ya yi, saboda ƙugin yunwa da cikinsa ke yi, zaman da ya yi, so yake ya ji dama-dama ya ci abincin ya kwanta, tun yana iya jujjuya jikinsa har ya gagara yin hakan saboda ilahirin gaɓoɓinsa sun amsa da zazzafan zazzaɓin ji yakeyi gaba ɗaya gabban jikinsa kamar allurai ake sokawa mushi, yana nan kwance har wajen ƙarfe ɗaya na dare jikinsa na karkarwa.
Cikin rawan sanyi daƙyar ya lallaɓa ya samu ya shiga bedroom ya kwanta a kan gadon a gicciye, hannunsa na rawar ɗari ya janyo blanket ya rufe dukkan jikinsa, shi kansa yana jiyo hucin numfashinsa da zafi, yana yi yana ɗan nishin azaba ƙadan,
a haka ya samu yayi baccin wahala mai cike da rikitaccen mafarki mara kan gado.

Kiran sallan farko ne ya tashe shi, cikin yanayi wanda bai saba tsintar kansa ciki ba ya miƙe, kasala-kasala gajiya-gajiya, ga mamakinsa zazzaɓin ya sauka, don yana ga ɗumin da jikinsa ya fitar da gumi alamun sauƙan zazzaɓi duk da akwai sanyi ac, addu'a ya yi ya miƙe a hankali ya shige toilet sai

Please Login or Register in order to submit comment