Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

dole ya faru tunda ban san gaibuba bare in banbane abunda ke ɓoye, sai iya abinda Allah yaso in sani ya sanar dani ya nuna min cikin hikimarsa".
Cikin sanyi da rauni Aunty Juwairiyya tace.
"Uhummm Shatu kenan ba komai.".
Tayi mgnar hawaye na zubo mata.
Da sauri Shatu tace.
"Dan Allah kiyi haƙuri".
Kai ta jinjina hawaye na zuba murya na rawa tace.
"Nayi kuka a lokuta da dama, na rasa wa zan gayawa damuwata ya fahimceni, kin nuna kina zargin zan cutar dake da kuma ƴan uwana.
Mahayarfiyarsu Yah Jafar da mahaifina uwa ɗaya uba daya suke.
Bani da kowa sama dasu a Masarautar Joɗa, sune ƴan uwana sune farin cikina rana ɗaya na fahimci kina zargin zan cutar dasu nayi kuka mai ƙuna a raina naji tsoron in gayawa Umaymah kada itama ta zargeni.
Ta yaya zanyi haka, ƴan uwana na jinina.
Ta ya zan cutar dasu.
Bayan tarin son da nakewa Yah Jafar wanda yasa duk da halin da yake ciki a haka na dage akayi mana aure wanda a lokacin su Sitti sun so a fasa aurena dashi.
Ina son Sheykh a raina tamkar yadda nake son Ibrahim ɗin mu".
Sosai take kuka alamun ƙuna a ranta.

Cikin sanyi da zubda hawaye Shatu ta riƙo hannunta a hankali tace.
"Aunty Juwairiyya, akwai dalilin nuna rashin yardarta.
Amman yanzu na gano ta ina matsalar take.
Ina neman al'farmar ki sallami Huwaila mai tayaki aiki.
tana cutar dake da yaranki da ingiza cutar Yah Jafar ita ke ƙara sa mishi abinda ke hanashi mgn, nanma Allah yayi yana yawan zama da al'wala da yawan karatu.
Ba dan hakaba da tuni sun kaudashi a masarautar Joɗa sun medashi kan juji.
Ki kuma kula kisa lura.
In babu halin ki sallameta kuma to ki cireta a masu tayaki aikin girki".
Cike da mamaki da tsoro Aunty Juwairiyya tace.
"Innalillahi wa innailaihi rajiun".
Cikin nitsuwa.
"Tace no kada ki tada anhlalinki ki lura zaki gane abinda nake nufi.
Kiyi kwana bakwai kacal ba tare da kin bawa Yah Jafar abinci da Huwaila ke dafawa ba, zakisha mamaki".
Cikin gamsuwa da shawarar Shatu tace.
"In sha Allah kuwa zan gwada da izinin ubangiji".
Daga nan sukaci gaba da hirarsu.
Yah Sheykh kuwa jin shiru-shiru bata zo bane.
Yasa ya fito.
Ya tambayi Ummi da ita kuma a zatonta suna can tare.
Ganin bata ɗakinta ne Ummi ta kirata a waya.
Cikin murmushi tace.
"Ummi ina wurin Aunty Juwairiyya ne".
Jin hakane yasa Sheykh yace.
Ba matsala a barta.
Daga nan ya juya ya fita, kai tsaye gidan Malam Abubakar ya nufa.
Inda suka ƙara tattauna batun Sulaiman.

Ita kuwa Shatu tun jiyan gudunshi takeyi.

Wayewar garin yau kuma sun tashi da aiyukan tarban su Umaymah.

Shi kuwa Sheykh wunin yau duk yana tare da Lamiɗo da Galadima suna tattauna wa.


A ɓangaren su
Aysha ƙarfe 3 suka shiga kitchen
girki na musamman suka fara ƙoƙarin shiryawa baƙin nasu,
Cikin kula Ummi ta kalli Sara da yanzu shigowar ta tace
"Yauwa Sara ƙaraso ki yankamin waɗan nan".
Tafaɗi tana nuna Mata Karas da green beans da kabejin data rigada ta wankesu ta tsane cikin kwando
"To". Sara tace tare da karasowa tad'au wuka ta fara yankan kamar yadda aka umurceta.

Shatu kuwa gaban tukunyar data ɗaura.
Kan gas taje tabuɗe tuni shin kafar da tazuba ciki yatafasu yadda take so irin tafsaa ɗaya zuwa uku'nna,
sauƙewa tayi kana tatsaneshi cikin kwando,
Wata tukunyar ta ɗaura tasulala Mai a ciki tare da wasa yankakken al'basa a ciki
Al'basar tana soyuwa Ummi tamiƙo mata jajjagegen kayan miyar da ta jajjaga bawani mai yawa bane tazuba cikin man,
shin kafar data tsane ta ɗauko tarika zubawa cikin man tana mosawa sai da tajuyeshi Kaf, kana takalli Ummi tace
"Ummi karasa wanna". Tafaɗa tare da Mika Mata ludayin dake hannunta wanda take motsa shinkafar dashi,
amsa Ummi tayi ita kuma tamatsa can gefe.

Ɗan ma dai-dai-cin roba taɗauka ta nufi in da fridge yake tabuɗe taɗebi hanta mai yawa sai jan nama ɗan dai-dai.
Wanke hantar da naman da taɗebo cikin roban tayi tazubashi cikin tukunya kana ta kunna wuta,
Citta da kanumfari da tafarnuwa tazuba a ciki sannan tazuba thym da curry da Maggi sai ɗan gishiri ɗan dai-dai, kana ta ɗauki al'basa ta yankashi mai ɗan yawa
ta wasa a ciki kana ta rufe tukunyar.

Attaruhu da al'basa ta ɗiba tawanke ta jajjagasu.

Tuni Naman ya dahu har ruwan cikin sa ya kafe yayi dai-dai yadda takeso
Sai wani tashin daddaɗan kamshi na namusamman yake,
A nitse tasauke tukunyar taɗan barshi yahuce,
Sannan taraba hantar da Jan namar ko wanne tacire shi daban,
hantar tajuye cikin madaki ta dakeshi yaɗanyi laushi, kana tazuba cikin wani roba Mai d'an faɗi.


Attahuru da albasan da ta jajjaga tazuba cikin dakekkeyer hantarna, sannan tafasa kwai guda15 takaɗa tajuye ciki,
tazuba curry da Maggi da gishiri daɗan garin citta kad'an tayanka al'basa tazuba ta ɗibi Karas acikin wan da Sara ta yanka ta haɗa da ɗan
Ƴaƴan green beans tazuba ciki,
kana ta ɗan zuba mai me ɗan yawa ba sosai ba
sokokim naman nan ta yayyanka shi kanana tatajuye ciki, motsashi tayi sosai, kana taɗaki laida tafara ƙullawa.

Matsowa kusa da ita Sara tayi kasan cewar tagama aikin da Ummi tasa ta,
idan Shatu tazuba haɗin cikin laida saita amsa ta ƙulla, a haka har suka gama ƙullashi kamar ƙullin alale,
A tukunya tajuye
Tazuba ruwa taɗaura kan wuta.

Ummi kuwa tuni tagama shirya lafiyayyen Friend Rice wan da yaji wadataccen nama da sauran kayan haɗi.

Wani haɗɗen foodflaks mai kyan gaske mai ɗan girma Ummi ta ɗauka tazuba a bincin, kana taɗau wata karamar kula tazuba ragowar abincin a ciki.

Shatu kuwa matsowa tayi jikin tukunyar ganin yanda yataso, har yana ɗaga murfin tukunyar murmushi tayi lokacin data buɗe murfin ganin Yadda yahaɗa jikin sa yayi wani tip-tip dashi gwanin sha'awa,
Laida ɗaya taciro taɗaki plate tasa a ciki kana ta yaga laidar da fork sabo da tirriin da yake bazata iya sa hannunta cikiba,
Wani hamshakin kamshine yabigi hancinta nan take kamshin yagauraye ilahirin cikin kitchen ɗin, kamshin ta zuko tare da lumshe idanunta kana
tayan koshi takai baki Kai ta gyad'a alamar gamsuwa,

Murmushi Ummi tayi kana tamasota ganin yanda take gyaɗa kai har tana wani lumshe idanu,
Murmushi tayi tare da cewa.
"To zauna kici Mana Aysha da ma ai bakici wani abun kirkiba tun safiya".

Idanunta tabuɗe tare da faɗin
"Mugama tukun zamuci da su Umaymah nasan ma yanzu haka suna can suna shiri ".
Ta ƙarshe mgnar tana sauƙe tukunyar.

Wata haɗeɗɗiyar kula Ummi tamiko mata nan suka fara cire haɗin hanta da nama da kwan nan wanda yajuye yadawo alale suka rinƙa cireshi cikin laidar suna sakawa cikin kula,
Sara kuwa in da suka ɓata tafara tsaftacewa, suna gama cirewa Shatu tamaida kular gefe batare da ta rufe kular ba,sotake yaɗan huce kafin ta rufeshi dan kada zufa ya ɓatashi.

Karfe shida da Rabi suka gama shirya komai kan dinning area.

Jamil ne yashigo cikin parlour'n daɗan sauri kallon Shatu dake tsaye saman dinning area tana gyara zaman kayakin dasuke kai yayi.
Tare da cewa.
"Aunty Shatu wanna kamshin fa yau kuma me a kayi mana wata ƙil dai yau da naman ɗawisu a ka haɗa girkin nan ko?".
Murmushi Ummi dake tsaye cikin parlour'n tayi
Kana tace,

"Kai Jamil tun bakaci ba har kafara sanni".

Cikin yin kasa da murya yace
"Allah dai yasa yau bason kai za akuma nuna mana ba, shi kibashi mai daɗi mu a barmu da na tsakar gida, nidai ko kaɗan ne a ɗibamin a cikin na Hamma Jabeer in dan..."

Saurin haɗeye sauran ragowar maganar yayi, ganin Sheykh yafito daga parlour'n sa, yanufo parlour'n cikin shigarsa ta Kamala kamar na yau da kullum sai baza kamshi yake.

Aysha ko murmushi tabi Jamil da shi ganin yanda ya rusunar da kai kamar bashinr yayi maganar ba,
Karasowa yayi inda Jamil ke tsaye a hankali yaɗan talli ƙeyarsa kana yace
"Wuce muje magananne kawai".
Hannu yakai bayan keyar nasa in da Sheykh yaɗan talleshi ya ɗan sosa wurin yace.
"Afwan Hamma Sheykh".

Shiko kuwa Yah Shekara wani irin juya kwayar idanunsa yayi yanayiwa Shatun sa kallon kasa-kasa wani irin mayataccen kallo yake binta dashi takasan ido.
Da sauri ya janye idonshi ya juyo jin Ummi nacewa
"Am Sheykh fita zakuyi ne?".
Kai ya gyaɗa kana yace
"Eh Ummi zamuje ɗauko su Umaymah ne".
Kai Ummi ta jinjina cike da farin ciki tace.
"Masha Allah Allah ya iso dasu lfy".
"Amin Amin". yace.
Shatu kuwa da sauri ta
sauko daga saman dinning area da farin cikin jin sa sun kusa su iso.

Ita kuwa Ummi cikin yanayi gajiya tajuya tashige ɗaki.
Dan so taje taɗan watsa ruwa kafin su iso,
Jamil kuwa tuni yafita Yana can waje yana jiran Hamman nashi dan tare zasu tafi tarar su Umaymah'n a airport,

Shi kuwa Sheykh a hankali yabi bayan Ummi da ido ganin tashige ɗaki ne da sauri ya juyo.
Jin ta rungumeshi tabaya tasakalo hannun ta a kugun sa tasauke wuyan ta kan kafaɗarsa,
wani sassanyan numfashi yafesar a hankali yaɗaura hannunshi kan nata dake saƙale a gugunsa, tare da fara murza fatar hannun ta,
sai kuma yayi kasa da hannun ta ƙasa kaɗan dai-dai kan jikinsa yaɗaura hannun nata yahaɗa da jikinsa din ya matse wan da tuni yafara motsi Jin abin cinsa kusa da shi.

Sai Kuma yayi saurin ciro hannu nata yaɗan waiga gefe da gefen sa tuno ashefa a babban parlour suke,
Juyo da ita tagaban sa yayi yamannan mata kiss a goshi kana yayi ƙasa da bakin sa dai-dai saitin kunnen ta cikin yin ƙasa da murya yace
"Sheykh fa na fushi kinyi Mlmasa laifi tun shekaran jiya kike gudu nai".
Wani irin yarr taji sigar jikin ta yatashi, saboda kalar tsigar yadda yayi maganar cike da wani irin salo da sai da yasa ta lumshe ido,
Batare da tabuɗe idanunta ba tace
"Kabashi hakuri".
Iska yahura mata cikin kunne kana yace.
"Yaƙi hakura so yake kibashi da kanki".
Ware manyan idanunta tayi kan fuskarsa jin yasauke hannun sa Kan kirjin ta.

Da ɗan sauri tamatsa da baya langwaɓar da kai tayi tace.
"Ummi zata fitofa".
Tayi maganar tana kallon hanyar dakin ta,
Hular kansa yacire yashafa lallausan gashin kansa dake shinfiɗe sai tashi da sassanyan kamshi yake,
Sassayan iska ya ɗan furzar daga bakin sa cikin tsareta da idansa dasuka fara canza kala yace
"Kece ai".
Idon talumshe tare da kuma buɗesu tace
"Da nayi me?".
Hularsa yamaida ya dai-dai-ta zamanta, lumshe mata idanunsa yayi kana yace
"Dakika sokano shi mana".

Murmushi tayi kana tajuya tana faɗin.
"Nidai Babu ruwana".
Tattausan tafin hannunshi yasa ya shafa gefen fuskarsa ya shafa Yana binta da wani irin mayataccen kallo
Har tashige bedroom.
shikuwa ajiyan zuciya mai nauyi ya sauƙw kana ya juya yanufi hanyar fita zuciyar sa cike tab da farin ciki.

Tana shiga bedroom rage kayan jikin ta tafaɗa bathroom wanka tafesa mai rai da lfy kana taɗauro al'wala tafito, lokacin kuma masallacin Jod'a suka kira sallah.

Shin fiɗa sallaya tayi tazura babban hijab tafiskanci al'kebla ta tada sallah,
Tana idar wa tayi duk kanin addu'o'i.
Kana ta miƙe tazo gaban mirror nan tafara lailaye jikin ta da mayukan ta masu sanyin kamshi.

A ɓangaren Sheykh kuwa yana fita direct masallaci yanufa Jamil yarufa masa baya,
Kamar koda yaushe sahun gaba yashiga
Suka gabatar da sallar magriba,
Koda a ka idar a gogo yakalla ganin da ɗan sauran mintuna sai yacigaba da tasbihin sa har lokacin sallar Isha yayi.

Ana idarwa yafito da ɗan sauri,
acikin mota yasami Jamil zaune a mazaunin driver yana zaman jiransa,
Gefen mai zaman banza yabuɗe yashiga yana dai-dai ta zaman sa yakalli tsadadden a gogon dake ɗaure a tsinsiyar hannusa.

"Yisauri mutafi lokaci ya tafi".
Yafaɗa tare da maida idanunsa kan hanya,
"To". Jamil yace kana yywa motar key suka fice cikin masarautar,

Direct airport suka
nufa har acan ciki inda ake isa dan tarban manyan mutane Jamil yayi parking
ganin fasinjoji na fitowa suke hakanne
yatabbatarwa Sheykh jirgin yasauka kafin isowar su,
Dasauri ya buɗe
marfin motar hangosu Umaymah
da yayi sun fito suna gaba
(hadiman) masarautar Jod'a
wad'an da Lamid'o
ne da kansa yaturosu domin tararsu, suna biye
dasu riƙe da jakukkunan su.

Murmushi mai fad'i Umaymah tayi lokacin data hangoshi yana
tahowa garesu Jamil na biye dashi, a baya a haka suka iso garesu, ko wannen su zuciyoyin sa.
Cike da farin ciki fuskokin duk ɗaukeda yelwataccin murmushi
sannu da hanya su Sheykh suka yimusu.
Ishma dake rike hannun Aunty Rahama ne tajanye hannun ta taje ta rungume Sheykh tana faɗin.
"Oyoyo Hamma Jabeer".
Murmushi yayi yana masa hannu kan ta yace "Kunzo lfy ya gajiyar hanya".
Kai ta gyad'a tare da cewa.
"Lfy".,
sai Kuma tasakeshi takoma jikin Jamil tana masa Oyoyo.

Umaymah kuwa cikin tsananin kula ta zuba mishi ido mishi kallon kula duk da al'kyabbar dake jikinsa bai hanata gano ƴar ramar dayayiba


Fuska ɗaukeda murmushi haɗe da ƴar zolaya
Aunty Rahama tace.
"Sannu ɗan al'barka Ina ɗiyar tawa ko ba tare kuka zoba?".

Murmushi Momma tayi ganin yadda Sheykh ya tsare gira wai dan Aunty Rahama tace mishi ɗanta.

Cikin girmamawa ya juya ya kalli Umaymah tare da cewa.
"Mujen ko Umaymah".
Cikin sakin fuska tace to.
Kana suka raka'a suka nufi mota.

Aunty Rahama da Umaymah da Momma Ishma baya suka shiga Jamil na mazaunin driver shikuma yana mazau ninsa naɗazu.
Kayansu Kuma Yana can motar da Lamid'o yaturo domin tararsu,
nan suka nufi masarautar Jod'a.

Shatu tsaye gaban mirror tana feshe jikinta da turare sai wani kyalle da d'aukar Ido take
tsanye take da wani dogon rigar atamfa ɗinkin yazauna ajikin ta yayi ɗamas dashi,
Jin hayaniya cikin parlour yasa ta aje kwalbar turaren tanufi kofa da sauri, tana kutsa kanta cikin parlour'n tahangi su Umaymah da yanzu shigowar su Ummi nayi musu sannu da zuwa.
Cikeda farin ciki da murnar ganinsu takaraso cikin parlour'n da sassarfa ta rungume Umaymah data juyo tana mata murmushi.

Cikin farin ciki da kula Umaymah ta kalleta tare da cewa.
"Kai Masha Allah ɗiyata haka kika zama kincanza sosai, kodai abin da muka dad'e muna hasashen sa ne Allah ya ai komana shi".

Cikin sanani jin kunya tasaki Umaymah tarungume Momma da Aunty Rahama suma rungume ta sukayi suna mai jin sananin kaunarta cikin ransu,
Umaymah kam sosai tabita da kallo tana nazartar yanayin ta na sauyin data gani tattare da ita.

Sakesu tayi tariko hannun Ishma
Tana mai faɗin.
"Oyoyo my Ishma".

Dariya Ishma tayi wan da yasa Shatu zuba mata Ido, ji tayi zuciyar ta naɗan harbawa da sauri-sauri ya ilahi wannan kamar tayi yawa hatta dariyarta iri d'ayane da na Junaina sam ta kasa sabawa da ganin wannan kamacceniyar tasu dake sa ƙirjinta harbawa.
Rass takuma jin kirjinta yabuga jiyo muryar Aunty Rahama lumshe idanunta tayi.
"Yasalam".
Tafurta acikin zuciyar ta, muryar Aunty Rahama Babu banbanci data Ummey'n ta.

Kamshin turarensa ne yasata bud'e idanunta tazubasu kanshi,
Cikin yanayin zazzab'in daya fara rufeshi yakaraso cikin parlourn, al'kyabbar sa yaketa d'an bud'awa yana haɗeshi saboda wani masi faffen sanyin da yake ji,
Direct parlour'n sa yanufa cikin mawuyacin hali kai tsaye bedroom nasa yashiga yafaɗa kan gado.
Yaja blanket yarufe jikinsa duka har kansa, kar-kar-kar haka jikinsa ke rawa.


Da ido Umaymah ta rakashi har yaɓacewa ganin ta, sosai tayi mamakin ƴarramar da yayi.
Taso ta binshi ɗakinshi to mutanen da suke ta shigowa suna yimusu barka da zuwane ya hanata bin bayanshi.

Bayan ƴan gaishe-gaishe sakanin su sai kuma sukayi salla kana.
Suka hau hira wane kamar waɗanda sukayi shekara cur rabonsu da juna.
Sosai Aunty Juwairiyya tasake cikin su ganin yanda Aysha tasaki jiki da ita, ganin hirar nasu bazata kare nan kusa ba yasa Ummi cewa
"Muje kuci abinci tukun a dawo aciga".
Nan suka mimmiƙe suka nufi dinning area Ishma na makale da Shatu,
Bayan sun gama cin abin cin ne suka kuma dawowa cikin parlour'n sai wajen karfe 12 da Rabi kowa yanufi
makwan cinsa.

Aunty Rahama da Ishma ɗakin Shatu suka shiga,
Anan zasu kwana,
Aunty Juwairiyya tatafi part in ita da Mamma,
Ummi da Umaymah Kuma ɗakin Ummi suka shiga in da nanne da ma masaukin Umaymah.

A hankali Shatu taɗauki Ishma wacce tayi bacci tuntuni tasaɓata a kafaɗa tayi tanufi ɗakin ta da ita a tsakiyar gado ta shimfi ɗata, yazamo tana gaban Aunty Rahama.
Ita Aunty Rahama tana can jikin bango ita kuwa Isham tana tsakiya.
Kyara mata kwanciya tayi taɗan sa pillow ta tokareta dashi tabaya,
Ido Aunty Rahma ta zuba mata ganin yadda taketa yimata komai a sannu kamar jaririyar goye,
Cikin jin sonta tace
"Aysha kenan sai wani lallaɓata kikeyi sai kace wata jaririya".
Murmushi tayi lokacin data gama gyara Mata pillow'n tamike tasauka kasa,
Gyara kwan ciya Aunty Rahama tayi
Kana tace.
"Ai kam saita tasaki ciwon baya tun d'azu tana jikinki tana bacci madadin kitasota da kafarta tazo Amma kika saɓota a kafaɗa.
Ishma kuwa uwar ƴan son jikine in kika bi ta nata kuwa sai ta saki ciwon jiki".

Murmushi takumayi kana tace
"Ai bako mai bazata sani ciwon jiki ba ai batada nauyi".
Tafaɗa tana shigewa bathroom rike da hijab a hannunta.

Tana shiga ta rataye hijab ɗin kana ta tuɓe kayan jikin ta ruwa ta cika cikin bath tashige cikinm
Kana ta ɗauki soso da sabulunta mai matukar kamshi tashiga wanke lungu da sako najikin ta.
Tana gamawa tajanyo towel taɗaura a kirjin ta
Kana taɗau hijab ɗin data tashigo dashi tazura sannan tafito,
Lokacin har bacci yafara ɗaukar Aunty Rahama sai dai tana ɗan jiyo motsin ta sama-sama kasan cewar baccin nata baiyi nisaba.

Gaban mirror tazauna batare da tacire hijab ɗin ba tashafa mai kana tamurza humra ta kowani lungu da sako najikin ta,
Tamike taje tabuɗe wardrobe wata rigar bacci mai santsi kalar pick mai siririn hannu da gidan bra taciro, taɗaki pant Shima kalar rigar,
Bathroom takoma tasaka kayan kana ta maida hijab ɗin ganin rigar da kaɗan ya shige guiwar ta.
A hankali ta fito,
Tazauna bakin gadon ta gaban Isham wacce tuni ta matso bakin gadon. pillow ta gyara tare da kwan ciya ta kasan kusa da Ishma.
Matsawa tayi taɗan daɗa gyara kwan ciyar ta dan tayi baki-bakin gadon da yawa taɗanyi baya da hannunta tana gyara hijabin jikinta, nan hannun ta yaɗan bigi ƙafar Aunty Rahma,
Ita kuwa Aunty Rahma da baccin nata baiyi wani nisaba, buɗe idanu tayi zatonta ma Ishma ce uwar birgimar yakawota kusa da isa da ɗan sauri tamike dan ta tarota kada tafaɗi.
Ido taware cike da mamakin ganin Shatu ce kwance a gun,mussuke Ido tayi cikin muryar bacci tace
"Ke Aysha me kike jira Anan da Baki tafi ɗakin mijin kiba jika kwanta Anan?".

Gyara kwanciya tayi kana tace
"Aunty Rahma anan zan kwana kusa da Ishma na".
Ido Rahma taɗa waro tace.
"A'a Aysha tashi maza kitafi ɗakin mijinki."
Shiru tayi bata kuma cewa komai ba ganin haka yasa Aunty Rahma fahim tar kunyace ko rashin sabo da zuwa gareshin ke ɗawai niya da ita,
Muskutawa tayi cikin dabara tace
"To ai kinga nan ɗin ma gadon yakasa mana bazai ɗaukemu dukaba ga Ishma da birgima zamu kwana a takure ke kije can.
Kinga den bazamu takuraba maza tashi kinji, ki kula da mijinki kada kiyi yaji haushina yace nina riƙe masa mata, kinga dama ya rainani".
Ta ƙarashe mgnar cikin sigar raha.
"Toh". tace a hankali tamike tasauko daga Kan gadon,
Ita kuwa Aunty Rahma gyara kwanciyarta tayi tace.
"Yauwa in kin fita ki jamana kofar".
Namma to ɗin takuma cewa kana ta fita tare da ja musu kofar.
A hankali tanufi parlour'n shi.


A ɓangaren su Umaymah kuwa suna shiga ɗaki Ummi bathroom tashiga taɗan watsa ruwa dan taji daɗin jikinta, bayan ta fitone tayi shirin bacci Nan ta tadda Ummi harta kwanta Amma batayi bacci ba idonta biyu, Zama tayi bakin gado ta fuskanci Ummi da kyau cikin sauƙe numfashi tace.
"Niko Ummin Jabeer anya ɗiyarnan taki ba cikine gareta ba kuwa?".
Da sauri Ummi ta mike zaune tana cewa
"Kai Anya kuwa?".
Gyara zama da kyau Umaymah tayi tare dayin murmushi tace
"Nikam dai naga kamar akwai abu tattare da ita. Amma dai sai da safe in Allah yakaimu zan ƙara zuba ido in dubata da kyau in ƙoƙƙofo mana".
Ciki da jin daɗi da fatan Allah yasa akwai ɗin Ummi tace.
"Allah yakai mu".
Kana sukaa ta kwanta suna mai fatan hakan yazamo gaskiya.

Shatu kuwa a hankali ta kutsa kanta cikin parlour'n da sallama ɗauke a bakin ta,
Shiru parlour'n babu motsin komai sai karar A/C da wani sassanyan ƙamshin dake tashi.
A hankali tanufi kofar bedroom ɗin shi.
Tura ƙofar tayi a hankali tashiga da sallama kana ta ta mai da kofar tarufe, juyowa tayi cikin ɗan kin cikin nitsuwa da ɗan yanayin bacci.
Can ta hangoshi kan gado.
A dukunkune cikin blanket sai karkarwa yaka.
Cikin sauri haɗida sassarfa tanufi inda yake,
cikin tashin hankali ta hayo kan gadon.
Da sauri tasa hannu tayaye blanket ɗin,
Da sauri ta kuma matsoshi ganin yadda jikinsa yake wani irin karkarwa, cikin sananin tashin hankali da tausayi ganin halin da yake ciki takai hannu saman kafaɗar shi tana faɗin
"Innalillahi Yah Sheykh meya sameka! dama baka da lfy ne!?.
"Innalillahi wa'inna'ilaihirraji'un!!".
Ta kuma haɗi da karfi lokacin da tasauke hannunta saman kafaɗarsa jin wani irin zafin da jikinsa yayi.
Shi kuwa Sheykh kanshi ya ɗago cikin mawuyacin hali yaɗaura kanshi bisa cinyar ta, cusa kanshi ya farayi cikin jikinta cikin sananin zazzafan zazzaɓin da yarufeshi yace
"Aish sanyi, sanyi nakeji".
Yayi maganar cikin mawuyacin hali yana daɗa cusa kansa cikin jikinta,
Wani irin sahihin runguma tayi mishi gam-gam tana ƙara mannashi da jikin nata.
Da sauri cire hijabin jikinta.
Tare ƙara tallafe kansa tamanna da ƙirjinta ganin Yadda yaketa manna jikinshi da nata yana bin ɗumin jikinta,
Wasu irin hawayene suka fara sassafo Mata
Murya narawa cike da tausaya mishi tace
"Yah Sheykh da ma haka zazzaɓin yake maka?".
Kai kawai ya iya gyaɗa mata alamar Eh
Hannunsa yaɗago da kyar yasauke kan ƙirjinta yacusa cikin bra'n rigar baccin dake jikinta yaciro Cab'b'ulenta duka biyu fuskarsa yacusa sakan kaninsu wani irin numfashi yasauke wanda yasanya Shatu rumtse idanunta jin ɗumin numfashin sa a kirjinta,
Hannunta ta ɗaura kansa a hankali tariƙa shafa sumar kanshi yayin da gudun hawayenta suka d karuwa,
wani irin masifaffen tausayin sane yarufeta,
lamo sukayi a jikin juna. Sun jima sosai a haka.
Kana ta ɗan ronƙofo suka kwanta manne da juna dan ta fahimci ɗumin jikinta yake bi.

Daren ranar dai Shatu taga tashin hankali Danko haka suka kwana basuyi bacci,
Sai can wajen kiran sallar farko zazzab'in yafara tafiya nanne yasamu bacci yaɗan ɗaukeshi.

Nan itama tasamu tad'an gyangyaɗa kaɗan.
Kiran sallar asuba kuwa a kunnen shi.
A hankali ya buɗe idanunshi tare da addu'a a bikinshi,
ido yatsurawa fuskarta ta kanainayeshi tayi lup a jikinsa tana fidda numfashi a hankali,
wani irin tausayinta ne yakamashi, tuno halin suka kwana jiya yadda baiyi bacci ba haka itama bata runtsaba.
Zame jikinsa yayi a hankali ya miƙe zaune.
Numfashin ya ɗan fesar kana ya sauƙo kan gadon.
Cikin lumshe ido ya nufi bathroom.
Yana mai mamakin yadda zazzaɓin nan yasakeshi watsai kamar ba shiba.
Wanka yayi tare da d'auro Al'awala kana yafito.
Farar jallabiya yazura tare da fesa turare mai sanyin ƙashi sannan ya murza hula bisa sumar kanshi.
Kana yaɗan maso bakin gadon da sauri jin ana kokarin tada ikama.
Ragowar ruwan hannunsa ya ɗan shafa nata a fuska tare da cewa.
"Aish tashi kije kiyi sallah".
A hankali tayi miƙa tare da buɗe idanunta kana tace.
"Toh, ya jikin naka?".
Murmushi yayi mai cike da jin daɗi cikin lumshe ido yace.
"Alhamdulillah da sauƙin tashi kiyi salla ko Boɗɗon Ummey".
Miƙewa zaune tayi.
Kana shikuma yafita.

Wayewar garin ranar kuma.
Shatu Ummi Sara suka shirya lafiyayyen breakfast suka jerashi kan dinning area dake cikin babban parlour.
Abinci kuwa takowani sashi yana fitowa zuwa wannan sashi.
Tuni Aunty Juwairiyya ta iso da nata lafiyayyen breakfast ɗin.
Bayan sunyi breakfast suka dawo cikin babban parlour nan suka buɗe sabon hira.

Shatu kuwa tun da sukayi breakfast ɗin takama hannun Ishma suka koma ɗakinta, wanka tayi sannan tayiwa Ishma.

Bayan tafiyar ta ba jimawa Sheykh yashigo parlour'n.
Cike da jin daɗin ganin ƙannen mahaifiyar tasu da aminta ciyar Jakadiyarsu mai kamar uwa.
Ya isa tsakiyar.
Suma cike da jin daɗi suke kallonshi.
A hankalu ya zauna kan kujerar dake fuskantar Umaymah.
Yayi wasai da shi kamar bashine jiya ya kwana da zazzafan zazzaɓi ba.

Hira sosai suka buɗe sunayi ana dariya da raha.
Shi kuwa Sheykh murmushi yake ɗanyi kanshi a sunkuye kan wayarsa da yake ɗan lasawa.
Umaymah kuwa gaba ɗaya ta maida hankalin ta kanshi, sosai hankalin ta yatashi dan yau tafi ganin ramar tasa da yawa fiye da jiya,
cike da kulawa ta tsare fuskarsa da ido tare da cewa.
"Jazlaan."
A hankali ya ɗago kwayar idanunshi ya kalleta cikin maida hankalinshi kanta yace.
"Na'am Umaymah".
Gyara zamanta tayi ta fuskanceshi da kyau cikin sanyi tace.
"Jazlaan meke damun ka baka da lfy ne wannan ramar duka ta mecece?".
Tajero mashi tambayoyin cikin alamun tashin hankalin.
Mamma da Ummi da Aunty Rahma da Juwairiyya kuwa shiru sukayi suna kallonsu.
Shi kuwa Sheykh a hankali ya ɗan sa hannunshi ya shafi sajenshi.
Wayar hannun sa ya ajiye bisa hannun kujera da yake zaune.
Ɗan gyara zamanshi yayi

Please Login or Register in order to submit comment