Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

wata ƙil jininka bazai juri 1+ ɗin ma zai wahal da kai.
Gashi dama na biya Pharmacy na amso allurar bari inyi maka kawai muga zuwa gobe ya abun zaiyi".
Cikin gamsuwa da hakan yace.
"To".
Hannunshin ya kuma kamowa ya tsira mishi allurar.
Kana ya bashi wasu magunguna a take a nan ya shasu.

Nan sukayi sallama ya tafi gida.

A gida kuwa tuni su Shatu sun shiga dan basu dawo da wuriba shiyasa suna dawowa basu tsaya hiraba.

Shiru ya samu falon babu kowa.
A hankali ya wuce Side ɗinsa.
Dan wani irin masifeffen karkarwa da jikinsa ya fara.
Ga wani irin tsuka da zazzaɓin ke mishi.
Da kyar ya rage kayan jikinshi.
A daddafe ya shiga yayi fitsari yayi al'walan kwanciya bacci.
Yana fitowa ya kwanta.

Kar-kar haka yake rawan sanyin masifeffen zazzaɓin nan kamar zai ɗauke ransa.
Allurar tamkar ƙara mishi ciwon tayi.

Haka ya kwana wannan ranar da masifeffen zazzaɓin.

Ana kiran sallan forko, yaji zufa na karyo mishi alamun zazzaɓin zai ɗan sauƙa kamar yadda yake mishi kullum.
Ai kuwa lokaci ɗaya zufa ta jiƙashi.
Jikin sanyi ya tashi AC ya kunna kana ya dawo bakin gadon ya zauna yana maida numfashin jin daɗin sanyin ac lokacin ɗaya kuma ya jishi garau kamar bashi ba, ƙamshin turaren jikinshi da sanyin ac yasashi jin wani irin sassanyan yanayi yana rufeshi.

Kusan 5 minute yayi kana ya miƙa ya shiga Bathroom.
Allah ya sani da Shatu na kusa dashi zai raɓeta ko zaiji daɗin rayuwarshi.

Ruwan sanyi ya watsa kana ya fito. Da al'walan sa.
Nafila ya fara. Kana ɗaya sallame ya fara karatu.

Jin anyi asslatune ya sashi fita ya nufi Masallacin masarautar Joɗa.

Ƙarfe bakwai dai-dai ya turo ƙofar falon jiki a mace. Wani fitinenne yanayi nata ɗawainiya dashi.

Yana zuwa tsakiyar falon Ummi na fitowa cikin kitchen.
Da sauri ya sunkuyar da kansa cike da kunya.
Domin tun randa Ummi ta ritsashi ya fito ɗakin Shatu bai sake yarda sun haɗa idoba sai yanzu.
Cike da kunya yace.
"Uhmm Barka da safiya Ummi".
Cikin kula da mamaki, ramarsa ita kuma Ummi ta bishi da kallo tare da cewa.
"Barka dai Sheykh lfy kuwa, meke damunka".
Murmushi yayi cike da kunya yace.
"Uhum Ummi me kika gani?".
Cikin tausayawa tace.
"Sheykh kaga yadda ka rame kuwa, anya kanada lfy kuwa?".
Kanshi ya ɗan juyo ya kalleta kana a hankali yace.
"Lfy ta lau Ummi kawai dai ɗan zazzaɓin dare ne ke yawan damuna, in gari ya waye kuma sai inji sauƙi".
Da sauri tace.
"Ina kuwa sauƙi Sheykh nadai lura sam baka son cin abinci.
gashi gaba ɗaya ka faɗa".
Ci gaba yayi da tafiya tare da cewa.
"Ina ci fa".
Da sauri tace.
"To kaje kaga likita ne?".
Kai ya gyaɗa mata tare da cewa.
"Eh naje. Jiya da dare".
Cikin sanyi tace.
"To Allah ya sauwaƙa".
Amin yace kana ya wuce.
Ita kuwa Ummi sosai taji ba daɗin ganin yadda ya ɗan faɗa.


Suna cikin yin aikin breakfast ita da Shatu.
Huwaila ta shigo kamar yadda Sara take zuwa tayasu aikin.
Kai Shatu ta jinjina kana ta nuna mata Arsh tace.
"Fere minshi in kin gama kije kawai sai anjima kizo yanzu mun gama".
Cikin kallon ƙasa-ƙasa Huwaila tace to.

Bayan sun gama komai na aikin breakfast sun shiryashi a Dinning table ta kalli Shatu data nufi ɗauki ta.
"Zo ki kaiwa Sheykh abincinsa kinga ba lfy ce da shiba".
Cikin gajiya tace.
"Ayyah Ummi to bari inje in watsa ruwa wlh zafi nakeji.
Watsawa kawai zanyi yanzu zan fito".
Kai kawai Ummi ta gyaɗa mata.

Bayan tayi wonka, mai kawai ta shafa ta fesa turare.
Ta zura doguwar riga ko bra bata saba.
Jin Ummi na kiranta
tana fitowa ta samu Jalal, Jamil, Affan, Sulaiman Imran duk suna yin karin kumallo su.
Tray'n da Ummi ta miƙa mata ta amsa kana ta wuce falonshi.

A hankali tayi sallama tare da kutsa kanta cikin falon.
Shiru babu motsin komai sai na A/C, bisa Dinning table ta ajiye tray'n kana a hankali ta juyo ta ɗan tsaya tsakiyar falon.
Ido ta ɗan zubawa ƙofar ɗakinshi.
har kamar zata shiga sai kuma ta juya da nufin fita.
da sauri ta ɗan ja da baya ganinshi tsaye a gabanta ya tankwara kanshi bisa kafaɗarsa, a hankali ya ƙara matsota.
Batayi yunƙurin matsawa ba, saima idonta data ɗan lumshe.
a hankali ta buɗe idonta jin ya kamo hannunta ya riƙe cikin nasa a hankali yace.
"Tafiya zakiyi bazaki duba lfyata bako?".
Cikin kula tace.
"A a nayi tunanin ko kana baccine kada in shiga in tada kai".
Murmushin gefen baki yayi kana yace.
"Zo in baki saƙonki to".
"Toh". Tace mishi kana tabi bayanshi.
Har ya nufi Bedroom ɗinsa, sai ya kuma juyo a hankali ya fuskanci ƙofar nan da zata sadashi da Garden ɗin Masarautar Joɗa.
Ita dai Shatu ido ta zuba mishi tare da bin bayanshi.
Hannunshi yasa ya tura ƙofar tare da juyowa ya ɗan kalleta a hankali yace.
"Muje kiga yadda tsuntsayema ke nunawa juna kula".
Murmushi tayi tare da cewa.
"Yakai rabin kular da nake nuna maka ne".
Yatsarshi yasa ya ɗan lakaci tsinin hancinta tare da cewa.
"Muje dai kiga yadda sukeyi, ke zaki yanke hukuncin irin kular da kike bani".
Wani irin sassanyan numfashi suka sauƙe a tare dai-dai lokacin da suka shigo cikin filin, sanyin iskar da ƙamshi ya'yan itatuwa da kukan tsuntsaye yasasu jin wani irin masifeffen shauƙi na musamman.
Ido ta fara jujjuya tana kallon tsarin wurin da kyanshi, sai kuma ta ɗan juyo ta kalli ƙofar da suka shigo ɗin wanda bata taɓa sanin da zamanshi ba, tsawon watanni kusan bakwai da take gidan.
Cikin lumshe ido ta juyo ta kalleshi.
kanta ta ɗan manna a ƙafaɗarsa, jin haka yasa hannunshi ya ɗan shafi haɓarta, ido ya zuba mata jin tana cewa.
"Uhummm Yah Sheykh kenan".
Cikin yin sassayan numfashi yace.
"Me nayi?".
A hankali tace.
"Uhumm naga ƙofofin dake sade ɗin kane kamar basu da adadi, ashe shiyasa wasu lokutan kake ɓacewa."
Murmushi yayi tare da cewa.
"Ɓacewa kuma kamar wani al'jani".
Cikin sanyi tace.
"Ɗan baiwa dai, dan tabbas dai kam kana ɓacewa tunda dai a Bedroom naka dai kam naga babu wata ƙofo to amman ina gani ka shiga a take in shiga in nemaka in rasa, to gashi kuma yau dai naga wata ƙofar da ban san da itaba."
Wani irin ɓoyeyyen murmushi gefen baki yayi tare da ɗan manna mata kiss a goshinta, kana a hankali yace.
"Wato bincike kike min a ɗaki".
Dai dai lokacin kuma suka iso cikin fagen da tsuntsayen suke, gyaran murya yayi a hankali ai kuwa a take sai ga tsuntsayen wurin kab sun nufoshi.
Wani irin narkekken murmushi tayi tare da ƙara manna kanta a damtsen hannunshi a hankali tace.
"Ni ɗakin mijina nake bincika".
Wani irin yalwataccen murmushi yayi dai-dai lokacin kuma.
Ɗawisun nan na tarin masarautar Joɗa ta iso gabanshi.
Wani irin taku yakeyi cikin rigima, ya iso garesu a hankali ya fara zagayasu.
"Wow masha Allah".
Tace dai-dai lokacin daya gama zagayasu kana ya dawo gabansu ya ɗaga binɗinsa sama ya buɗa fikafikinsa, ya baza a gabansu.
Wanda ya iso har kan fuskarta shi kuwa Sheykh zuwa kan ƙirjinsa.
Wani irin murmushi Sheykh yayi tare da cewa.
"Kekkyawar tsuntsa a gaban kekkyawar sarauniya, kiyi haƙuri karon farko dai na kawo miki sarauniyar data fiki kyau, sabida na halittar bani Adam amman dai a cikin tsuntsaye har gobe babu ya kai".
Wani irin juyowa tsuntsuwar tayi, ƙuntunta mai cikar blue color ya manna bisa saman rumfar sawun Shatu.
Murmushi tayi kana ta sunkuyo ta shafata tare da cewa.
"Masha Allah da kekyawar halinta".
A hankali ta juya ta fara tafiya cikin rigima.
Da sauri Shatu ta ɗago kanta ta kalli sama ganin yadda suntsaye masu masifar kyau sukayi musu ƙawanya suna kukansu mai daɗin ji.
Murmushi tayi ta kalli Sheykh dake musu kirarin zaƙin muryarsu.

Ruggumeshi tayi ta bayanshi tare da lumshe idonta lalacin daya nuna mata tattabarun daketa yiwa juna ƙoto kana suna kusantar juna.
Cikin murmushi da shauƙi yace.
"Lallai ke ta musamman ce, kalli ɗawisun nan batama jira na gabatar mata da keba, to ko-dai-ko dai".
Da sauri tace.
"Ko-dai-ko-dai mefa?".
Ido ya lumshe tare da kamo hannun ta ya manna a habarshi tare da cewa.
"Kodai jinin masarautar Joɗa ya gauraye da nakine, wanda ba sai an gabatar da keba".
Ya ƙarashe mgnar yana sa tafin hannunshi yana shafa lafeffen cikinta".
Cikin lumshe ido tace.
"Kamar ya".
Sunkuyowa ya ɗan yi bisa kunnenta ya kai bakinshi a hankali yace.
"Kamar ko mun samu ƙaruwar akwai shigar cikin Muhammad jikin Shatu".
Da sauri ta manna kanta da ƙirjinshi dai-dai lokacin kuma suka iso bakin ruwan nan inda agwagin ruwa ke cike murya can ƙasa tace.
"A a kam ba wani ƙaruwa".
Ƙara jawota jikinshi yayi tare da matseta murya can ƙasa yace.
"To muje muyi fatauci Allah yasa muyi dace da katarin ƙaruwa, mu samowa Mamey jikoki masu kama dake in ta dawo ta samu masuyi mata surutu."
Da sauri ta ɗan kalleshi dai-dai lokacin kuma ya juyo da ita suka nufi hanyar komawa falonshi murya a nitse tace.
"Wacece Mamey Ina take? Yaushe zata dawo".
Cikin sanyi ya ɗan kalleta a hankali yace.
"Da gaske Aish ina son haihuwa matuƙa gaya, inason inga jinina ina son samawa Mamey na jikoki".
Ya kauda zancen tambayar da tayi mishi.
Da wannan batun yana kuma mai kai hannunshi kan cikinta.
Dai-dai lokacin kuma suka shigo falon.
Meda ƙofofin yayi ya rufe kana a hankali yace.
"To muje in baki saƙonki".
Cikin nazarta zantukanshi tace. "To". daga nan suka nufi bedroom ɗinsa.

A hankali suka shiga bedroom ɗinsa,
Komai kimtse sai ƙamshi turarukanshi da suka kama ɗakin.

A hankali ya iso da ita bisa, carpet zama yayi kana itama ya ajiyeta.
Suna fuskantar juna, kwaren da ke gefen gadonshin ya jawo ya ajiyesu tsakiyarsu.

Cikin nitsuwa ya janye fefeyin saman.
ya ɗaura matashi bisa cinyarta, wasu dandatsa-dandatsan al'kyabba na matan sarakuna ya fidda masu masifar kyau guda uku ya ɗaura mata kan fefeyin dake bisa cinyarta.
kanshi a sunkuye yace.
"Wannan kyautar tukuicin budurci ne daga tambarin Masarautar Joɗa."
Ya ƙarashe mgnar yana fito da wasu takalma da linzamin dawakai biyu, ya ɗora bisa rigunan.
kanshi ya ɗan ɗago ya kalleta ido cikin ido.
Idonshi ya ɗan lumshe mata ganin yadda take kallon sajenshi.
cikin tsokana yace.
"Ya dai kin ƙyatsa ne?".
cike da kunya tayi murmushi tare da cewa.
"Nida abuna."
Wani yalwataccen murmushi, sai kuma ya tsareta da ido jin tana cewa.
"Ngd matuƙa Allah ya saka da al'khairi".
"Amin Amin". yace kana ya jawo ƴar ƙaramar ƙwaryar dake gefen babbar, a hankali ya buɗe hannunshi yasa ya ɗauki wata iriyar fitinenneyar sarƙar ɗanyen gol mai ɗan karen kyau da masifar sheƙi na ɗaukar idanun mutun.
da sauri ta waro idanunta woje cikin tsananin mamaki da al'ajabi take kallon sarƙar.
Shi kuwa Sheykh miƙo mata sarƙar yayi tare da cewa.
"Ga kyautar da ko wacce matar masarautar Joɗa ke harin ya kasance a sashinta.
sai dai banda Mamey na, ita batayi harinshi ba, kuma Allah ya ƙaddara aka batashi, wanda kuma batashi bai zame mana al'khairi ba. Tsawon shekaru babu wanda ya sake ganin makamancinsa, sai kuma gashi a karo na biyu ya shigo cikin ahlinta a hannunki."
Ya ƙarashe mgnar yana jawota jikinshi.
Ba musu ta kwanta cikin ƙirjinsa sabida ƙamshin jikinsa da take son shaƙa.
Sarƙar daya saƙala mata a wuyan nata ta kalla, cikin al'ajabi da mamakin ganin irin sarƙar Ummeynta ce.
Dan komai nasu iri ɗaya harta tambarin jikin sarƙar to sai dai wannan tafi sabunta da sheƙi.

Wannan banbanci na saraƙunan da kuma jin abinda yake matane yasa tayi shiru.
Ta gaza cewa komai, ido ta lumshe jin ya manna bakinshi bisa wuyanta, harshensa yasa yana ɗan lasar fatan wuyan nata a hankali.
Kana hannunshi na zuge zib ɗin rigarta.
batayi yunƙurin hanashi ba, jin yadda yake jan wasu tagwayen numfarfashi masu nauyi.

Ido ta ɗan lumshe ta faɗa jikinsa, lokacin daya gama zare mata rigar tata.
Jingina bayanshi yayi da jikin gado, kana a hankali yasa hannunshin ya jawo jallabiyar jikinshi daga ƙasa yayi sama da ita, ya cireta ya rage dagashi sai gajeren wondon iya guiwa wanda ƙasan shi kuma akwai boxes.

Ita kuwa Shatu manne jikinta tayi da nashi kana tasa hannun ta zagayo bayanshi tayi lib a jikinshi.

Ƙugunta ya zubawa ido cikin tsananin Feeling dake ɗawainiya dashi, yasa yatsunshi biyu ya kama bakin robar gajeren wondon dake jikinta wanda yayi cib da jikinta.
da sauri ta mirgino kanshi tare da tashi zaune bisa cinyarshi ya zama suna fuskantar juna,
hannayenta ta meda ta saƙale wuyanshi, tare da kai bakinta kusa da kunnenshi a hankali tace.
"Na gode Yah Sheykh, Allah ya cika maka burinka Allah ya kare min kai da kariyarsa yayi maka rahama da rahamominsa, ya albarkaci ahlinka da albarkarsa yasa ka gama da duniya lfy".
Hannunshi yasa ya mata wani irin masifeffen rugguma ya matse Caɓɓullenta da ƙirjinshi murya can ƙasa yace.
"Amin Amin. Ameeeeeeen ya rabbil izzati. Yah Aish Mar'atussaliha."
Sai kuma yasa hannunshi ya tallabo kanta ya haɗe goshinsu,
tsinin hancinsa ya goga kan nata,
a hankali kuma yasa harshensa ya fara lasar lips ɗinta kamar mai lasar askirim.
ido ta lumshe jin wani irin masifeffen abu ɗaya taso mata daga ƙan babbar yatsar ƙafarta har zuwa maɗigan kanta.
sabida yadda ya cusa harshensa a bakinta ya kamo nata, yanayi mata sahihin kiss mai lankwasa tunanin.

Yatsunta ta cusa cikin sumar kanshi tana yamutsawa wanda hakan ya zuzuta fitinar dake cinsa.
Hannunshi yasa ya murza gajeren wondon dake guguunshi yayi ƙasa dashi ya rage dagashi sai boxes.
Cikin rawan jiki yasa hannunshi yayi ƙasa ya ɗan nata.
Cikin ɗimuwar daya sata.
ta ruggumeshi gam-gam a jikinta tamkar zata game jikinsu.
da sauri ya yunƙura ya miƙe tsaye da ita.
taku biyu yayi da ita zuwa uku yasa hannunshi ya ɗauki al'kyabbar shi dake gefen gado.
Wore al'kyabbar yayi ya rufesu gaba ɗaya.
Kana ya juyo ruggume da ita sukazo bakin ƙofar.
Rufe ƙofar yayi kana yasa hannunshi ya kashe wutan ɗakin gaba ɗaya.
Duhu ya gama ɗakin,
Kasancewar duk labulayen wondons ɗin a rufe suke.
Ga yanayin ɗan hadarin.

Bakin gadon ya dawo da ita.
zama yayi kana ya jawota gareshi.
wani irin maraitaccen sauti ya sake lokacin da yaji ta fara mishi zazzafan darasin daya koya mata.
"Hyyyuu, Aishhh".
wani irin fitinenne salo mai gigitarwa ta fara mishi wanda yasa gaba ɗaya jikinshi karkarwa da amsa amon aiken da takeyi mishi.
Hannunshi yasa bisa kanta yana mai ɗan shafa kanta da ɗan marin kumatunta a hankali da sauri-sauri.

Da sauri ta janye kanta jin yadda ya saki wani irin sauti da ɗan ƙarfi.
"Ohh yess, Na'am Yah Subahanallah Alhamdulillah".
jawota yayi ta faɗa jikinsa bakinsu ya haɗe, ya fara yi mata wani irin tsadajjen kiss mai wuyar samu.
hannunshi na yawo a jikinta, yanayi mata wani irin sahihin murza mai cike da kwarewa.
cikin rawan jiki take shafa dukkanin sasan jikinsa gaba ɗaya da son nuna mishi kulawarta da tsantsar farin cikin kyautukan daya damƙa mata.
a hankali ya zame bakinshi daga nata.
yana mai laso fatarta yakeyin ƙasa, har zuwa ƙirjinta nan ya ƙara susucewa.
da ɗan ƙarfi tace.
"Shhhhhhhhwhhhh".
gaba ɗaya jikinshi da nata karkarwa sukeyi.
wani irin gigitaccen abu yayi mata mai wuyar a dannewa, kar-kar haka jikinta ya fara karkarwa cikin gigicewa ta yunƙuro ta tashi zaune.
hannunta tasa bisa kanshi.
Murya na rawa alamun kuka takeyi tace.
"Washhhhh Shyyyyyyyyyah Yah Sheykhhhh hyyyyhhhh".
sai kuma ta miƙe tsaye tare da ɗora hannun ta saman kanta, ji takeyi kamar tayi ta surfa ihu sabida wani fitinenne tsotsan da yasata jin tamkar shauƙi zai kasheta, da sauri shima ya miƙe tsaye, stiil al'kyabbarshi na jikinsa.
ganin yadda jikinta ke karkarwar ne, ya ruggumeta gam-gam ta bayanta.
A hankali ya sunkuyar da ita, ta dafa jikin gadon, shi kuwa ya matso kusa da ita ta bayanta.
Ware al'kyabbar yayi ya rufesu da kyau tana sunkuyen yana tsaye.

Kanta ta cusa cikin gadon tare da jawo blanket ta cusa bakinta ciki lokacin da ta amshi baƙoncinsa.
Sabida tabbas in ta bar bakinta a buɗe ji take in numfashin in ya fita bazai dawoba.

Wani irin masifeffen karkarwa yakeyi tamkar mazari hannunshi ɗaya dafe da ƙugunshi ɗaya kuma yasa ya danne nata ƙugugun.
wasu irin gigitattun hawaye yaji suna silalo mishi murya na rawa yake wasu irin gigitattun surutai da yaruka mabanbanta.
"Yah Salam Yah Subahanallah Alhamdulillah. Wayyo Y.M.D.G belɗum. Oh yessss my dear so sweet. Na'am yah Aishhhhhhhh laisa limisluki abadan. Aish! Aish!! Allah ya miki al'barka ya saka miki da jannatul fiedausi ya jiƙan iyayenki yasa ki gama da duniya lfy."
Wani irin kukane ya kubce musu Dukansu biyu. Ita tana kukan farin cikin addu'o'in da al'barkar da yake sakamata tabbacin ta bashi dukkan jin daɗi da farin cikin duniya.
wanda duk mace ta gari takeso ta bawa mijinta.
Shi kuwa Yah Sheykh yarukan da yake gwamutsawa.
Fullanci, hausa, larabci, turanci, Indianci harda barbarci."
Sosai yake yin abunda yakega zai iya sama mishi nitsuwar juye fitinar manyan tunzura dake cinsa.

Wani irin maraitaccen sauti yayi tare da matsawa gareta.
Ya faɗa kan gado.
kana yasa hannunshi ya jawota jikinshi ya ɗaurata kan ruwan cikinsa.
Ya ruggumeta gam-gam a jikinshi yana maida wani dogon numfashi cikin fizgo numfashin da mgnar yace.
"Jazakallahu khairan *Mar'atussaliha*".
Kanta ya fara shafawa jin har yanzu kuka takeyi a hankali yace.
"Kiyi haƙuri Mar'atussaliha dena kuka kinji ko? Kin samu lada mai tarin yawa. Allah ya miki al'barka kinji Nana Aysha Allah miki al'barka yasa ki gama da duniya lfy."
Cikin rauni da gajiya murya na rawa tace.
"Ahhuhh Amin ya Allah". Ya sani dole ta gaji kuma taji jiki dan sam bai bita a hankali ba, dan ta gama gigitashi.
gashi duk jikinta yayi laƙwas sabida dole akwai rashin sabo tunda du-du yaune karonta dashi na uku".
Sunkuyowa yayi tare da kunna hasken wayarshi daya ɗauka ƙasan pillow'nshi fuskarta ya haska, sosai idonta suka ɗan kumbura sukayi jazir.
tafin hannunshi yasa ya share mata hawayenta, kana ya miƙe zaune ya jingina da kan gadon.
Jawota jikinshi ya kumayi cikin sanyi da tausasawa da lallashi yace.
"I'm very sorry Aish, kiyi haƙuri daga yau bazaki sake jin wahala ba.
kiyi haƙuri gaya min me kike son inyi miki?".
Gyara kwanciyarta tayi a jikinshi murya can ƙasa tace.
"Kayi ta samin al'barka, kana roƙa min Allah ya azurtani da aljanna ya bamu ƴaƴa nagari salihan bayi da musulunci zaiyi alfahari dasu kamar yadda musulmai ke alfahari da kai Abbansu".
Da sauri ya rufe mata bakinta da hannunshi tare da cewa.
"Wannan ai na dade ina miki ita kuma in sha Allah har gaban abadan zanyi ta miki ita dan ko a aljanna kece' kece' kece! uwar gidan Yah Sheykh.
gaya min wani abun da kike so?".
Wani irin murmushi na jin daɗi tayi kana a hankali tace.
"Ka dena zuwa part ɗin Hajia Mama, in ta baka abu ko menene kada kaci kazo ka gaya min ni zan maka abun".
Cusa kanshi yayi a wuyanta.
Ya sani ya yarda yanzu dai Shatu ta zama wani sashi na jikinsa yasan irin duk abunda takeyi dan lfyarsa da farin cikinsa hankali yace.
"Me ma zata bani Aish? Ai babu wata mace da takeda abunda zata bani sai ke".
Da sauri tace.
"Ka cemin bazaka sake ciba kuma ka dena yarda da ita kawai".
Murmushi yayi tare da cewa.
"To Bazan sake ciba shike nan ko yarda kuma ai dama bbushi".
Da sauri tace.
"Yauwa Noor Hayat"..
A hankali ya miƙe tsaye al'kyabbar jikinshi ya gyara kana a hankali ya jawo blanket ya rufe mata jikinta.
Wonka yaje yayi kana, ya fito yace itama taje tayi.
Bayan ta fitone.
ya zura mata wata tattausar jallabiyarsa.
kana ya kamo hannunta suka fito falo.
Tare sukaci abinci kana ya jata suka koma ɗaki sukayi baccin liƙe da juna.

A hankali a haka dai rayuwa tayi ta tafiya, lokacin nata shuɗewa.

Zazzaɓin dare kuwa kullum Sheykh kwana yakeyi dashi, asuban fari ya worke.
Shatu na kawo mishi breakfast zai tsareta da salonshi mai gigitarwa.
Sai ya zama in ma bai sameta da safe ba.
Tofa bayan azahar sai ya ritsata.
Zuwa yanzu ya dena bata mamaki sai al'ajabi yake bata sabida ta lura in dai akan wannan fanninne to malamine mai zaman kanshi kullum da salon darussan da yake koyar da ita.

Ya ɗan rame alamun baida cikekkiyar lfy ga kuma aikin fatauci.

Zuwa yanzu kuwa Shatu ta gama gane cewa Huwaila munafukar Hajia Mama ce.
Ita takeyiwa aiki ta gano sam Aunty Juwairiyya Bata san komaiba zagon ƙasa akeyi mata.

Yanzu kusan wata biyu kenan Da Sheykh yake fama da wannan zazzaɓin da yasha mishi mgnin ya binciki kansa har ya gaji bai gano meke damunsa ba.


Yau jumma'a ne, bayan an taso sallan Jumma'a ne yana kwance a ƙasa bisa carpet.
Ita kuwa Aisha tana kwance gabanshi.

A hankali ya kamo hannunta ya manna da bakinshi kiss ya sake mata a hankali yace.
"Gobe Umaymah da Aunty Hafsat da Rahma zasu zo, jirgin magriba zasu biyo."
Cikin jin daɗi tace.
"Eh haka Umaymah tace min, zasu zo da Ishma ko?."
Cikin wani irin sauri.
Ya Tashi zaune y da sauri ya kamo hannunta tafin hannun nata ya zubawa ido cikin mamaki ya ɗago idanunshi ya kalleta cike da al'ajabi da kaɗuwa ya kuma kallon tafin hannunta na hagu.
Ita kuwa ido ta zuba mishi ganin yadda yake kallonta.
Cikin son tabbatarwa yace.
"Aish cik...!?




Littafin GARKUWA na kuɗine Special Group 1k zaki turo ta 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa.
Sai kiyi screenshort na shaidar biyanki ki turo min ta whatsapp 09097853276. In normal group kikeso na 300 ma ta nan zaki turo, in baki da damar turawa ta ac kuma to nayi miki uzuri ki sayi katin Mtn na ɗari uku kacal ki copy numbers ɗin ki turo min ta whatsapp 09097853276 bana son VTU KADA KIYI min bana so.



By
*GARKUWAR FULANI*Cikin wani irin tarin farin ciki mai wuyar misaltuwa jiki na kermam farin ciki da annashuwa ya jawota ta faɗa jikinshi.
Ture system ɗinshi dake gabanshi yayi ya ruggumeta tsam cikin jikinshi wasu irin hawayen farin ciki ne suka zubo mishi tamkar ƙaramin yaro.
Sai ya kuma ɗago kanta cikin tsoro da mamakin ganin hawaye na kwaranyo mishi murya na rawa tace.
"Innalillahi Yah Sheykh me nayi maka".
Da sauri ya kuma ruggumeta gam-gam cikin wani irin tsantsar farin ciki murya na rawa yace.
"Alhamdulillah Aish, Alhamdulillah meyasa baki gaya minba, kina da cikiba, meyasa zaki ɓoye min wannan abin farin cikin?".

Cikin wani irin yanayi ta faɗa jikinshi ta rungume gam a jikinta murya can ƙasa tace.
"Ciki kuma Yah Sheykh?".
Da sauri yace.
"Yes ciki mana Aish".
Da sauri tace.
"A a ni kam bani da wani ciki bayan na cin abinci".
Da sauri ya ɗagota har lau hawayen farin ciki na zubo mishi babu ƙaƙƙautawa cikin ruɗani yace.
"No kada kice min haka. Kada ki cemin baki da ciki ga nan alamomi duk sun baiyana.
Kina da cikina mana Aish, ya zaki cemin baki da ciki".
Cikin tura baki da son ɓoye mishi batun tana da cikin tace.
"Ni dai bani da ciki".
A kiɗime ya miƙe tsaye, tare da cewa.
"Ok tashi, tashi mu tafi Valli muje in duba".
Da sauri ta maƙe kafaɗarta tare da cewa.
"Ni dai bani da ciki".
Ta ƙarashe mgnar tana sa hannunta cikin boxes ɗin sa.
da sauri yace.
"Ni kada ki cemin haka muje in gwada in ga Zahiri".
Da sauri ya dawo ya zauna jin yadda take mishi wani salo.
Murya a mace tace.
"Sai dai in yanzu zaka bani cikin".
Ta ƙarashe mgnar da sigar yaudara da mantar dashi batun cikin da tasan yanzu watanninsa biyu harda kwanaki, a jikinta.
Ruggume ta yayi da ƙarfi tare da cewa.
"Tun tuni ai na baki ciki Aish, wlh kina da ciki.
Ya za'ayi ina Dr ki musa min".
Bakinsu ta haɗe wuri ɗaya tare da fara mishi wasu abubuwan da dole ya haɗiye regowar mgnarshi.
Yayinda zuciyarshi ke cike fal da farin ciki.

Kiran sallan la'asar ne yasa suka sahirtawa juna.
Ganin lokacin sallan yayine yasashi yin wanka a gaggauce ya tafi masallaci.

Ita kuwa Shatu.
Ajiyan zuciya ta sauƙe tare da sa hannunta ta shafa ɗan lafeffen cikinta.
Lokacin da take wonka.
murmushi tayi tare da cewa.
"Abbanka yana cikin tarin farin cikin gano alamun kana jikina, duk da ɓoye mishi da nakeyi.
sabida ina gudun kada ya gaza ɓoye farin cikin sa har magautansa su gano da kai su rabani da kai."

Sai kuma ta lumshe idonta.
Tana ganin yadda jikin Sheykh yayita rawa yana fidda hawayen dake bayyana tsantsar jin daɗinsa ziryan.
A hankali tace.
"Abbanka yana sonka so mai tarin yawa, wanda har ya kaishi da zubda hawaye.
Ina sonka so mai yawa wanda ya zame min dole in sirrantaka, dan ɗanyen mamlngoro buya yake sai ya nuna ya baiyana. Ina soron magautan Abbanka su dawo gareka".
A haka tana surutai taje tayi salla.

Tana idarwa tajoshi a falo yana cewa Ummi.
"Ummi ina Aish?".

"Tana ɗakinta, tana salla".
Ta bashi amsa,
Kai ya gyaɗa tare da cewa.
"In ta idar tazo".
Yana faɗin haka yayi cikin falonshi.
Ita kuma Ummi to tace kana ta shigo ta gayawa A'isha.

Ita kuwa to kawai tace tana fita.
Ta nufi sashin Aunty Juwairiyya sabida tasan in taje mgnar su tafi asibiti zai mata.

A falo ta samu Aunty Juwairiyya gefenta ta zauna.
Hannun tasa ta kamo hannun Mimi ɗiyar Aunty Juwairiyya kana a hankali tace.
"Yah Jafar fa".
Cike da mamakin sauyawar da Aishan tayi mata a ya kwanakin nan tace.
"Bai dawo masallaci ba".
Kai ta jinjina kana a hankali ta juyo ta kalli Aunty Juwairiyya cikin sanyi tace.
"Dan Allah Aunty Juwairiyya kiyi haƙuri da wasu abubuwan dake faruwa a wasu ma banbanta lokuta.
Abune da

Please Login or Register in order to submit comment