Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ta fita.
Ajiyan zuciya ta sauƙe tare dasa hannun ta ɗauki wayar.

Jujjuya wayar tayi tare da miƙewa ta nufi bedroom ɗinta.
Number Bappa ta saka, kana kirashi.
tare da kara wayar a kunne mugu ɗaya ana biyu, aka amsa kiran.
Wani irin murmushi tayi jin muryar Junainah tana cewa.
"Bappa! Bappa ga wayarka ana kiranka".
Da sauri tace.
"Ƙanwaliya".
Cikin wani irin mamaki da jin daɗin Junainah tace.
"Laaaaah Adda Shatu, kece? Ina kike? Adda Rafi'a tazo jiya wai tana neman wayarki baya shiga, Bappa yace mata ai anyi miki aure, taita kuka tace to ya batun karatunki,
Bappa ma ya nemi number ki baya shiga.
Ina kika ajiye wayar ne to Adda Shatu".
Cikin sanyi tace.
"Wayar ta ɓata ne Junainah".
Cikin tura baki tace.
"To mijinki ya saya miki mana".
Ido ta lumshe tare da cewa.
"Ina Ummey na? Ya jikinta?".
Cikin sauri tace.
"Ummey tana na Kitchen, yanzu jikinta da sauƙi tana mgna kaɗan-kaɗan, ko ɗazuma itace tace.
"Bappa ya kira mata ke!."
Cikin tsananin jin daɗi tace.
"Alhamdulillah, kai mata wayar".
Da sauri ya juya ta nufi kitchen tana cewa.
"Ummey! Ummey ga Adda Shatuna".
Da sauri Ummey ta fito, ta amshi wayar.
Cikin murya mai cike da sanyi tace.
"Aysha na!".
"Wasu zafafan hawayene, suka zubo mata,
Cikin rawan murya tace.
"Na'am Ummey na! Ya jikinki?".
Ajiyan zuciya ta sauƙe tare da cewa.
"Jiki da sauƙi, Shatu yaushe zaki zo?".

Bappa da yanzu ya iso daga rakiyar da yayiwa Rafi'a ne, yayi murmushi tare da cewa.
"Bani wayar nan".
A hankali cikin girmamawa ta miƙa mishi wayar.
Shi kuwa amsa yayi tare da karawa a kunne.
jin muryar bappa yanayi mata sallama ne yasata jin sabbin hawaye masu masifar ɗumi, sabida tausayinshi.
Duk da tsufanshi mugayen ƙabilar ɓachama basu barshiba, sun kashe mishi babban ɗan shi.
Kana sun tafi da uku, sun barshi cikin zulumin suna raye ne ko sun mutu? A ina suke? Me akayi musu? Me sukeyi? Sannan itama data rage anyi mata wani irin bahagon auren da yafi kama da na mulkin mallaka.
Muryarsace ta katse mata mgnar zuci da takeyi da cewa.
"Shatu kina Lfy ko?".
Murya na rawa tace.
"Lfy lau Bappa, amman bana jin daɗin gidan, ina kewarku, ya jikin Ummey na? Ya lbrinsu su Ya Gaini an samu wani lbrin ko har yanzu shiru? Ya Ba'ana bai muku komai bako? Ya tafi ne ko yana nan?".
Murmushi yayi tare da cewa.
"To Shatu wacce tamɓaya ɗaya zan amsa miki'.
Tana kuka tace.
"Duka".
Cikin hikima da jinƙai irin na iyaye yace.
"To sai kinyi shiru kin dena kuka".
Da sauri tasa hannu ta share hawayenta tare da cewa.
"Na bari".
Taku biyu yayi zuwa uku kana yace mata.
"Ba'ana bai mana komaiba! Ya gudu ya bar ƙasar ma baki ɗaya! Jikin Ummey ki da sauƙi sosai! Su ya Giɗi munata addu'a in Sha Allah, in Allah ya yarda zasu baiyana garemu da izinin ubangiji.
Kafuran nan kuma mun rigada mun karya ƙarfi su yanzu bazasu sake samun damar cutar da muba, in Sha Allah munfi ƙarfi su."
Sai kuma ya ɗan tsagaita jin, tana murmushi mai ɗan sauti alamun jin daɗi,
a hankali yaci gaba da cewa.
"Rafi'a tazo, nayi mata bayanin komai, kuma in ta dawo zata zo, in an barta zata shigo".
Da sauri tace.
"Zan gayawa Ummi ta sanarwa sarkin ƙofa in tazo a barta ta shigo".
Cikin danne ainihin tarin ƙunar watsewar gidanshi yace.
"Yauwa to haka zakiyi.
Sannan in sunƙi yarda kada ki damu.
Umarnine gareki, kibi dukkan umarnin mijinki, kiyi mishi biyayya a cikin dukkan lamuranshi nasan bazai saki mugun abuba, kada ki saɓawa umarninshi.
Kada kiyi komai saida amincewarsa.
Ki kasance mai kula da lamuran rayuwarsa kada ki bar wani abun cutarwa tare dashi.
Yanzu shine gatanki. Shine madadin Giɗi, Ganin, Seyo, Lado, ƙannenshi mata ki kallesu tamkar Junainah, mahaifiyarshi ki kalleta kamar Ummeynki, yan uwan mahaifiyarshi ki kallesu kamar yadda kike kallon innarku, yanzu sune ƴan uwanki.
Domin naki basa kusa Ki zama GARKUWAR sa".
Shiru yayi jin kuka na son kubce mishi.
Ita kuwa tuni hawaye na kwaranya daga cikin manyan idanunta.
Cikin sanyi yace.
"Gobe zamu tafi, lardinmu, zamu koma can na wani lokaci".
Wani irin tsananin razana da tsoro ta zaro ido tare da cewa.
"Bappa zaku tafi Kardi kuma!? Ni ku barni a nan ba kowa nawa!?".
Cikin sanyi yace.
"Zamu dawo Shatu. Donke zamu dawo.
Dole muje, in sanarwa iyayen innarku abinda ya faru da ita da yaranta.
In kuma gayawa yan uwana halin da nake ciki a kan ɓatan yayunki, bayan salla zamu dawo. Can zamuyi azumi. Bakiga yanzu a nan ko tinkiya ba'a bar manaba".
Cikin gamsuwa da zancen Bappa ta ɗan danne shessheƙan kuka tare da cewa.
"Allah ya kaiku lfy ya dawo daku lfy. Amman Bappa ku barmin Junainah mana, a kawo min ita mana in samu iƴar uwa kusa dani".
Cikin tausasamata zuciya yace.
"Kada ki damu, su nan bazasu barki da maraiciba.
Sai mun dawo zan kawo miki Junainah da kaina".
Kit kiran ya ƙatse sabida kuɗin sun ƙare.
Hibba da tun ɗazu ta shigo tana gefenta ne,
ta ɗan kalleta cikin sanyi tace.
"Aunty Shatu, meyasa kikace bakya jin daɗin zama a gidan nan? Munayi miki wani abune?".
Cikin zubda hawaye ta jujjuya mata kai.
Hibba bazata fahimci halin da take ciki ba, bazata gane matsalar rayuwarta ba.
Ita kuwa Hibba cikin sanyi tace.
"Aunty Shatu nima ƙanwarki ce, duk abinda zakisa Junainah tayi miki nima kisani zan miki kinji ko".
Cikin share hawayenta tace.
"To Hibba ngd".
Murmushi Hibba tayi tare da cewa.
"Yauwa kuma Umaymah ta aika Ya Jamil ya sayo miki sabuwar waya iPhone".
Cikin sanyi da son tsaida hawayenta tace.
"Ngd".


Haka yammacin ranar ta yishi a bedroom ɗin ta.
Sai Hibba dake ɗebe mata kewa ne.
Da Umaymah taga basu fito bane itama taje.


Washe Gari yau Jumma'a, kuma yaune ta cika sati ɗaya cib a gida.
Kuma tunda yazo gidan sau uku taga Sheykh Jabeer, tun randa ya wucesu, suna batun abinci bata sake ganinshi ba, koda a gilme ne.
Yanzu ta saba da Umaymah Sosai hakama Ummi
Ita da Hibba kuwa shaƙuwa ta fara ƙarfi a tsakaninsu.
Tana jin Hibba kamar Junainah.
Jamil da Jalal Haroon suna ɗan zama asha hira dasu.
Yau ne kuma Haroon zai tafi Leddi julɓe, sabida yayi masifar kewan Jannart ɗin shi, wacce taƙe ƙanwace ga Aunty Juwairiyya, kuma ƙawance ga Ibrahim.

Ƙarfe ɗaya dai-dai, Sheykh Jabeer, ne tsaye gaban dreesing mirror yana fesa turare bayan ya gama shirin jummarsa tsab.
Yau shigar baƙar Al'kebbar da farar jallabiya yayi.
Yayi wani irin kyau mai cike da sheƙi.
Kusan a tare suka jero da Haroon wanda yake cikin shigar ƙananan kaya.

Su kuwa suna falon suna, zaune.

Jamil da Jalal da Ya Jafar kuwa suna tsaye alamun fitowar Sheykh suke jira.

A hankali Shatu ta ɗan ɗago kanta jin wani irin masifeffen ƙamshi mai daɗin shaƙa.

Da sauri ta janye ƙwayar idanunta,
Sabida idonta da suka faɗa cikin ƙwayar idanunshi.
Wanda shi kuwa Jalal yake kallo ganin wani shegen wondo wai shi crezi ne ko meye ne oho, duk yana ɓuɓɓule har kana iya ganin farar fatar cinyarsa.
ga saɓulellen wonɗo ga kafurin aski.
fuskarshi ya tsuke tare da jan gajeren tsaki wanda shiyasa Jalal juyawa, ya nufi hanyar fita yana cewa.
"To Ni banifa da manyan kayan nan, yanzu bari inje in duba ko inada jallabiya sai in saka a kai zan biyoku daga baya."
Da ido suka bishi. Haroon da Jamil kuwa murmushi sukayi.
A haka suka fita suka tafi. Har sunje bakin ƙofar fita ba tare da ya juyoba yace.
"Umaymah ku tashi lokacin salla yayi". Ya ƙarishe mgnar suna fita
To tace.

Kana suma su Ummi suka nufi ɗakinsu.
Aunty Juwairiyya kuma ta wuce Side ɗinta.

Ita kuwa Shatu da Hibba suka tafi ɗalinta.
Hibba ce ta fara shiga tayi al'wala.
Sannan itama Shatu ta shiga.

Tana fitowa daga bathroom ɗin tayi wani irin....!




Uhummmmmm tuni mun gama shimfiɗan lbrin GARKUWA yanzu dai muna cikene dumu-dumu .

By
*GARKUWAR FULANI*Tsayuwa tare da kasa kunnuwanta.
Tana jin sautin zazzaƙar muryashi.
Yana kudba.
Akan laduban fuskantar watan Ramadan wanda zuwa yanzu kwanaki ne suka rage.

A hankali ta fara taku tana
Nufo inda Hibba ta shimfiɗa musu sallaya.
Ita kuwa Hibba ido ta zuba mata ganin yadda ta kasa kunne.
Cikin murmushin tace.
"Aunty Aysha me kikeji".
A hankali tace.
"Wannan me sunan malamin da yake huduban nan. Kamar inada wa'zuzzukanshi amman kuma, ban san sunanshi ba, kamar dai kam nasan wannan Muryar".
Murmushi Hibba tayi tare da cewa.
"Lallai ma kam Aunty Aysha wai muryar Hamma Jabeer ɗin ne ma kike cewa kamar kin santa, kamafa kikace, lallai kam my Aunty".
Da sauri ta kalli Hibba domin zuwa yanzu ta gane waye suke cewa Hamma Jabeer, Ko Sheykh, ko Jazlaan, ko Muhammad wani lokacin Umaymah na kiranshi haka.
Ta kuma fahimci wai shine mijin da aka aura mata.
Ta kuma gane sun taɓa haɗuwa sau biyu kafin yau.
ganin tayi nisa a tunnine yasa Hibba cewa.
"Aunty Aysha".
Murmushi ta ɗan yi tare Dasa hannun ta amshi hijabin da Hibba ke miƙo mata.
Cikin ranta take mgnar zuci.
"Uhumm mutun duk rayuwarsa tana cike da ƙalubale da matsaloli Magauta sun sashi a tsakiya kota ina ya juya suna tare dashi.
Amman bauɗewa ta hanashi ganewa, sai anyi mgn yace wai anayi mishi ihu a kai.
ko shi kunnen macijine dashi da yafi kowa jin sauti.
sai iya lillibka ɗika-ɗikan al'kyabbar yanata ɓoye jiki kamar wani mace".
Mitsss ta ɗanja gajeren tsaki tare daci gaba da zancen zuci.
"Yana nan jiki duk matsaloli ya bari mutun yaga iya inda abunda ke kan yatsunshi ma, ya gagara, shine kullum cikin al'kyabba har ƙasa uwa shine limamin harami.
Sai an kasheshi a banza yasa ƙannenshi da iyayenshi a matsala.
Danni matsalar rashin yayuna har huɗuma ya isheni damuwar duniya bazan ƙarawa kaina damuwar waniba".
Da sauri ta juyo ta matso kan sallayar sabida jin har masallacin sun sallame sallar, sabida ta daɗe a tsaye tana zancen zuci.

Nan dai sukayi salla, kana Hibba ta miƙa ta fita
Ita kuwa Shatu, sabuwar wayarda aka saya mata jiya da sabon layi aka haɗa mata komai ne, tasa hannunta,
ta jawo.
tare da komawa ta kwanta bisa sallayar.
Layin Bappa tasa kana ta kira.
Jin bata shiga bane yasata gane, sun tafi kenan.
Cikin sanyi ta kira ɗaya layin na wancan ƙasar tasu.
Cikin sa'a kuwa ya shiga sai dai ba'a ɗagawa.

Sau uku ta kira jin ba'a ɗaga ba, ta haƙura.
Number Rafi'a tasaka ta kira.
Tana ɗagawa tace.
"Rafi'a Garkuwa ce".
Cikin tsananin jin daɗi Rafi'a tace.
"Alhamdulillah Garkuwa ya kike? Ina kike? Ashe kuma abinda ya faru kenan.
Alhamdulillah mun rabu da matsalar Ba'ana, jiya naje Rugar Bani, wai yau su Bappa zasu tafi Lardi".
Cikin murmushi tace.
"Kai Rafi'a kimin mgna da ɗaɗɗaya mana zanfi ganewa".
Cikin dariya tace.
"Eh kyace haka mana kinyi bulunbuƙui a masarautar Joɗa".
Cikin sanyin jiki taja numfashin tare da cewa.
"MASARAUTAR Joɗa ko matsala, komai a bai-bai yake Rafi'a, bana fahimtar komai, tunda nazo cikin wannan masifeffen masarauta kaina a juye yake. Jina nake kamar a rami".
Cikin rauni tace.
"Rafi'a abubuwan sunmin yawa, da wanne zanji.
Tabbas nayi farin cikin tsira daga tarkon ya Ba'ana, to amman ƙaddara batayi min adalciba data kawoni wannan wurin.
Kin sani Allah ya sani ina son Ya Salmanu".
Da Sauri Rafi'a ta katseta da cewa.
"Kice Astagafirullaha kada ki mance da auren wani a kanki kike cewa kina son wani".
Hawayen da suka cika mata ido ta share tare da cewa.
"Bana sonshi! Bana ko son ganinshi, kuma shima hakane baya sona baya son ganina. sauƙina ɗaya da shima ba sona zaiyiba, kowa zaiyi rayuwarshi babu ruwanshi da wani shiyasa hankalina bai tashi sosaima, sai dai ina cikin tarin damuwa Rafi'a, babu Ya Giɗi,Gaini, Seyo, Lado, Inna. Sannan Junainah,Ummey da bappa da nake gani inji sanyinma wai sun tafi Lardi,
ya zanyi inji farin ciki, ga wannan gida mai mutantani daban-daban wasuma naga tsanar shi wancan mai jajayen kunnuwan zasu ɗora a kaina, ko uwar meye haɗina dashi, da magautanshi zasu haɗa dani a ƙiyayyarsa, suji dashi mana, tunda bansan meya shuka musuba, dan shima na lura ba kanwar lasa bane bakine dashi, kan ace ɗirin yake ce musu konɗi, rashin tsoronshi na bani tsoro."
Murmushi Rafi'a tayi tare da cewa.
"Yanzu dai ya batun karatunki?".
Cikin sauƙe numfashi tace.
"Zan gayawa Umaymah".
Cikin shaƙuwarsu Rafi'a tace.
"To sai na shigo, dan mgnar bazata ƙare a wayaba".
Da sauri tace yaushe zakizo?".
Cikin sauƙe numfashi tace.
"In sha Allah dai kafin azumi zan shigo".
Cikin sauri tace.
"Kafin azumi kuma azuminfa da ɗan saura bama kice gobe ko jibiba, Rafi'a in bakizo minba wa nake dashi da zai zomin?".
Ta ƙarishe mgnar cikin rauni,
Cikin tausayin Rafi'a tace.
"To gobe ko jibi in sha Allah".
Cikin jin daɗi tace.
"To sai kinzo."
Daga nan sukayi sallama.

A ranar da yamma Haroon ya wuce jiharsu Jannart inda nanne masarautar sarkin musulmai take.

A hankali dai kwanakin sukayi ta gungurawa suna cuɗewa Ramadan nata ƙara gaba towa.
Yayinda duk al'ummar Annabi suketa shirye-shiryen tarban watan Ramadan.

Yau dudu saura kwana bakwai ne ake zaton za'a fara azumi, in bai cikaba ma kwana shida.
Tuni Umaymah nata shirin komawa Jihar Tsinako sabida Abban Haroon ya matsa ta dawo sabida shirye-shiryen Ramadan.

Ita kuwa Umaymah tana jiran kayan auren data aika a haɗo mata a Dubai su isone.
wanda ƙawarta ce ta bawa aikin kuma ƴar nan cikin jihar Ɓadamaya ne!

Yau Lahadi ne, ta kama ranar bautar al'jihun baya ne.
Wannan yasa duk manya-manyan Coci na cikin garin Ɓadamaya ya cika maƙil da mabiya bayan addinin Kirista ci.


A hankali motocinsu suka fara fitowa cikin masarautar Joɗa, suna kama babban hanyar da zata sadasu da asibitin taraiya na jihar wato Genaral Hospital Ɓadawaya.
Kamar kullum haka tawagar take, Lamiɗo zaije kai ziyarar dubiyar marasa lfy kamar yadda ya saba duk ƙarshen mako.
A ƙalla motocin sun kai goma.
Suna tafiya a jere a jere.
Har suka iso yankin da asibitin yake, inda nan babbar hanyar hada-hadan cikin garin ne, wanda babbar kasuwar jiharma take kan titin.

Wani tabkeken cocine mai zaman kashi a bakin babban titin LCCN, yana ta hannun hagu.
Kana ta hannun dama kuma wani tsabtaceccen masallacin juma'a ne mai ɗan karen girma, haka ya zama suna fuskantar juna masallacin da cocin.
Kana sai an wuce ta gabansu za'a ratsa konar shiga asibitin.

To kasan cewar duk ranar jumma'a ƴan agaji na toshe hanyoyin daga ƙarfe sha biyu da rabi zuwa kan a idar da sallan jumma'a su buɗe,
sai kafuran nan suma suka tsiri duk ranar Lahadi tun shida na safe zasu,
Toshe hanyoyin nan, sai shida na yamma.
Wanda hakan ke jawo cinkoson ababen hawa ata yankin wuri. Sai ya zama duk masu son yin salla a wannan masallacin jumma'a to ranar a sai tsare musu hanya,
sai dai masu zuwa da ƙafa.

Wannan abun ya damu musulmai, koda aka kai ƙorafi ga gwamnatin jihar sai cewa tayi.
"Ita bata son fitina, a bar kowa yayi addininshi salin alum".
Haka musulmai suka haƙura dan a zauna lfy. To masarautar Joɗa bata da wannan lbrin sai yau da suka fito ranar lahadi da yake kullum asabar suke zuwa.

A jere a jere motocin ke tafi kasan cewar da sanyin safiya ne,
lokacin sun gama rufe hanyoyin kana sunata tsastsafowa gabas da yamma kudu da Arewa.
Cikin Mamaki motar su Lamiɗo da saura duk suka tsaya, sabida ganin motocin gaba sun tsaya.
da sauri Sallama ya fita, tare da dawowa baya.
zuwa gaban motar Lamiɗo yayinda Motar Sheykh Jabeer kuwa take can bayansu, shi sauri yake zaije Valli Hospital dan yiwa wata mata aiki.

Rusunawa Sallama yayi tare da cewa.
("Allah rene halkaleru en mabɓi labi mai".) Allah rene kafurai sun rufe hanyoyin".
Da sauri sarkin ƙofa ya fito yazo ya buɗewa Lamiɗo marfin yadda zasuji juna da kyau.
Cikin mamaki Lamiɗo yace.
"Lfy meya faru zasu rufe hanyoyin".
Da sauri dubagari yace.
"Ai haka sukeyi duk ranar Lahadi, su hana mutane sakewa su rufeshi tun safe sai yamma".
Cike da Mamaki Galadima da yanzu ya iso wurin yace.
"To duk hakan na menene?".
Cikin sauri Duba gari ya ɗan rusuna tare da cewa.
"Wai sabida musulmai na rufe hanyar duk ranar jumma'a sabida bada tsaro wai suma shine suka tsiri, hakan ankai mgnar wa gwamnatin kuma ta goyi bayansu".
Cikin ta ajjudi suka kalli juna,
kana cikin bada umarni Lamiɗo yace kaje kace, su buɗe hanyar yanzu nan.
Kuje da sarkin aike".
Nan take suka juya suka nufi can inda yaransu ƙananan ke tsaye su kakkafa Road closed and stop.
Suna zuwa jim kaɗan suka dawo.
Tare da cewa ai yaran sunƙi sabida sunce Gwamnatin jihar ta amince musu da haka.
Wannan mgnar yayi masifar tasa zuciyar Lamiɗo.
Cikin ɓacin rai ya zaro wayarshi ya danna mai girma Gwamnan kira.

Inda yace maza, ya bawa kafuran nan damar buɗe waɗannan hanyoyin da suka rufe.
Ba kunya gwamnan yace, to ai. Dokace Allah rene da kunbi wata hanyar ai yafi ko."

Cikin tsananin tarin takaici Lamiɗo yace.
"Muje duk ku shiga mota, mu canza hanya."

Sun shishiga kenan sai kuma sukaji.
matasa irin wanda suke gefen wurin suna cewa.
"Jahan! Jahan!! Jahan!!!".
Da Sauri Duk suka fara leƙawa suna kallon wanda ake kira da Jahan, ɗan jarida mai zaman kanshi wanda jihar Ɓadamaya da kewaye ke alfahari dashi. Duk da ya kasance Musulmi mai sunaga ba nasu bane, kafurai kuma suna alfahari dashi a matsayin nasune.

Cikin isa da karsashi yake taku cikin wasu irin zafafan ƙananan kaya masu masifar kyau. Jahan kekyawane aji ƙarshe a kyau, fari ne ƙal hanci har baki shiyasa da yawa kance shi iyamurune, idanunshi farare ƙal-ƙal gashin kansa gwanin kyau sai dai kafurin askin dake kanshi.

Yaran suna hangoshi suka matsa.
Shi kuwa Jahan da kanshi ya buɗe hanyoyin gaba ɗaya.
Kana ya nufi motar fadawa dake gaba.
Haɗe hannunshi yayi wuri ɗaya tare da.
Musu alamar suyi haƙuri kana ya musu alamar su wuce.
Daga nan motar Waziri ya nufa, suma ya basu haƙuri. Haka yayi tayi har gaban motarsu Lamiɗo,
cikin sanyi ya rusuna gaban marfin motar, tare da jinjinawa Lamiɗo kana yace.
"Tuba muke Lamiɗo, ga hanya an buɗe".
Wani irin sanyi da daɗi Lamiɗo yaji, gashi duk da Gwamnatin ta kasance ta musulmi siyasa ta hanashi adalci.
Gashi wanda ba nasu ba ya zantar da adalci".
Haka ya rinƙa bawa mutanen cikin motocin haƙuri suna wuce.
a haka har yaje mota ta ƙarshe,
Yana isa yasa hannu ya buɗe marfin motar.
Wani irin kallo mai cike da ma'anoni yakeyi mishi.
sai kuma yayi wani munafukin murmushi.
Ganin hakane ya ja motarshi ya tafi.



Washe gari ranar Litinin. Da hantsi Hajia Kubra aminiyar Umaymah ta iso.
da yan rakiyanta.

Kai tsaye har bakin part ɗin Sheykh Jabeer sukayi parking.
Kana ta shiga cikin

Cikin farin ciki suka ruggume juna ita da Umaymah cikin dariya Umaymah tace.
"Hajia Kubra amman kin shamma ceni".
Murmushi tayi tare da cewa.
"Ato ai naga kin zaƙu kina son ki koma Tsinako ne nace bari dai in hamzarta indawo".
Ta ƙarishe mgnar tana zama tare da miƙa Jalal car key ɗin ta tace.
"Yauwa Jalal Jamil ku shigo da kayayyakin."
To sukace kana suka amshi key ɗin suka fita.

Nan suka buɗe motoci biyun wanda tazo a ciki da wanda drever'nta yazo a ciki.
Nan suka rinƙa kwatsar akwatunan suna shigarwa.
Set biyune masu fasifar kyau da tsadan gaske.

Umaymah kuwa tuni tasa Juwairiyya ta cika Hajia Kubra kayan kwalam a gabanta.

Robar Inabi ta ɗauka tana buɗewa ta kalli Umaymah cikin raha tace.
"Hajia Khadijah ina ɗiyar tamu".
Cikin murmushin Umaymah ta ɗan juyo ta kalli ƙofar falon Shatu tare da cewa.

"Hibba! Hibba!!".

"Na'am".

Hibba ta amsa tana miƙewa tsaye
Kizo keda Aysha ga Mommy Kubra tazo".
Cikin jin daɗi Hibba ta miƙe tare da cewa Shatu.
"Wayyo Aunty Aysha tashi muje".
Cikin nitsuwa ta miƙe tsaye,
mayafin Arabian gawd ɗin dake jikinta ta gyara.
Kasan cewar shi guntu yasa bai ida rufe mata jelan gashin kanta data tubkeba.

Suna fitowa Hibba ta faɗa jikin Hajia Kubra tare da cewa.
"Oyoyo Mommy Kubra".
Ruggume Hibba tayi tare da cewa.
"Oyoyo My Muhibbat".
Sai ta kuma kalli Shatu dake ƙoƙarin rusunawa.
da sauri ta riƙo hannunta tare da cewa.
"Zo nan kusa dani kema ɗiyata ce, bakya ganin yadda Hibba tayiin".
Murmushi tayi sabida fara'ar matar ya burgeta cikin sanyi yace.
"Mommy Ina wuni".

"Lfya lau ɗiyata ya gida ya baƙun ta?".
Cikin girmamawa tace.
"Alhamdulillah".
Hibba ce ta zamo daga jikinta tare da cewa.
"Mommy wannan kayanfa?".
Murmushi Hajia Kubra tayi tare da cewa.
"Na Aunty Shatu ne".
Da sauri ta zamo tare dasa hannunta zata buɗe akwatin dake gabanta, cikin haɗe fuska Umaymah tace.
"To uwar azarbaɓin, waya saki. Tashi kije ki kira min yar uwata kice mata ga saƙon sun iso".
Da sauri ta miƙe tare da cewa.
"Aunty Aysha zo muje Side ɗin Hajia Mama mu kirata".
Da sauri ta jujjuya kanta tare da cewa.
"A a sai kin dawo".
Tana faɗin haka ta miƙe ta koma falonta.
Ummi Aunty Juwairiyya da Umaymah kuwa kallon junansu sukayi.
Hajia Kubra ce tace
"Kunya ko". Murmushi Umaymah tayi tare da badda zancen da haka.

Ita kuwa Hibba da sauri taje ta kira Hajia Mama, aiko kusan tare suka taho, da Botool.

Koda sukaje Umaymah ta aika Ummi a matsayin ta na Jakadiyarsu take ta sanarwa Gimbiya Aminatu tazo taga kayan auren da ta haɗa amryar Jazlaan ɗin ta.

Bayan duk sun zone, Suka bubbuɗe akwatunan, goma sha biyun nan duk cike suke maƙil da kayayyakin bukatar amare.
Abun sai wanda ya gani.
Lokacin da aka buɗe akwatunan turaruka gaba ɗaya Side ɗin ya cika da ƙamshi tako ina.
Manyan akwati biyu aka cika da dogayen riguna masu masifar kyau da tsada da taushi.
Sai kuma biyu da aka cikasu da atampopi da shadda da lace.

Sai kuma babba daya da aka cikashi maƙil da laffaya masu azabar kyau da tsada, babu kalan da babu a ƙalla sun kai kala ashirin da huɗu.

Sai biyu daga ciki ƙananan kayane birjik

Sai wani babban bakko, da aka cikashi da takalma a ƙalla kala goma sha biyar, bakwai daga ciki sunada hand bang, hudu daga ciki pase garesu.
hudu kuma masu siffan sayyadane masu kyau.

Sai kuma kayan tarkacen mayuka da sabulai na jiki da kai.

Kai abun dai masha ALLAH.

Da sauri Hibba ta zari takalma uku daga ciki takalmomin ta nufi bedroom ɗin ta da sassarfa tana cewa.
"Aunty Aysha bari inzo ki gwada takalman nan, Ni dai sai inga kamar zasuyi miki kaɗan.".
Tana shiga ta ajiye mata takalman a gabanta tare da cewa.
"Gwada mu gani".
Sosai takalman sukayi mata kyau, haka yasa ta zura ƴar kekyawar farar ƙafarta.
Ai kuwa tayi mata cib-cib cikin dariya Hibba tace.
"Ashe dai zai miki dai-dai".
Murmushi tayi tare da gyaɗa tare da cewa.
"Uhumm ba kin raina ƙafar tawaba".

Daga nan ta juya, ta koma falo, nan ta samu Hajia Mama na cewa.
"Wannan kaya haka Khadijah kin kashe kuɗinki a banza ƙanwata wannan yarinyar ba matar auren Muhammad bane".
Cikin yin ƙasa da murya Umaymah tace.
"Karkice haka Hajia Mama".
Cikin ɓacin rai tace.
"Khadijah ai dole ince haka, ke har yanzu baki gane cewa wannan yarinyar ba matar ahlin masarautar Joɗa bace, a gabanki fa, taƙi shan madarar Barka da zuwa Masarautar Joɗa.
ta kuma kwaɓar dana hannun Jabeer wanda shine na Barka da zama magidanci.
Hakafa zatayi ta kwaɓar da duk wani abun ci gaba ko nasara a rayuwarsa."
Batool ce ta ɗan gyara zamanta cikin danne baƙin cikinta tace.
"Uhummm a tsallake ƴan uwa jinin sarauta aje a kwaso mishi bagidajiya ba fullatanar daji, ba dole tayi halin dabbobiba tunda cikinsu ta tashi. Tasan menene masarauta bare tasan ƙai dojinshi da kuma, nasabarsa."
Ta ƙarishe mgnar tana son maida hawayenta.
Allah ya sani tana son Sheykh Amman ta lura, Hajia Mama taƙi sa baki abin yayi gashi har an auro mishi wata.
Cikin murmushin Umaymah tace.
"Batool zaki auri mai matane?".
Cikin sauri tace.
"In wanine bazan auri mai mataba, amman in Hamma Jabeer ne, wlh ko mata uku gareshi da ƙwar-ƙwara biyar in zai aureni zan yarda in zama ta tara,
Kowa ya iya allonsa ya wonke".
Murmushi Hajia Kubra tayi tare da cewa.
"A lallai kam".
Ita dai Hajia Mama miƙewa tayi ta fice rai a ɓace.

Gimbiya Aminatu kuwa, murmushi tayi tare da cewa.
"Ji ƙarfin hali ita kafin uban Jabeer ya arota Allah ne kaɗai yasan adadin dukiyar da aka narka.
Sam iyayen mazan yanzu sai a hankali."
Cikin sauri Hajia Kubra tace.
"Matan ƴaƴan ma na yanzu ba irin na da bane.
Shiyasa aketa samun matsala tako ina kowa kansa ya sani".

Ita dai Umaymah murmushi tayi tare da cewa Juwairiyya.
"Juwai keda Hibba kuje ku kimtsa mata komai a ɗakinta ku shirya mata drower'nta.
Kana ku kimtsa mata kan dreesing mirror.
Kai kuma Jamil ɗauki bakon takalman nan ka juye takalman.
Juwairiyya kisa Shadda bakwai lace bakwai, atampa bakwai, kampala Bakwai, swiss voile bakwai.
A cikin atamfofin kisa
Super wax biyu English wax biyu, Holand biyu sai swiss atampa ɗaya.
Sai kusa a bakon.

Jamil sai ka kaisu wurin telan Juwairiyya.
Ayi ɗinkunan da wuri."

Haka kuwa akayi akani komai yadda tace.

Bayan sun gama kimtsa mata komai da jera komai a muhallin shi ne,

Suka fita, sannan Umaymah ta shigo, gefenta ta zauna cikin nitsuwa tace.
"Ɗiyata ga kayan sawarki naso ace sun iso tun kafin yau.
To sha'anin nesa, shiyasa kikaga bai iso da wuriba, duk kayan nakine kisa wanda kikeso a sanda kikeso.
Sabida ke akayi komai."
Cikin tarin jin daɗi da ganin darajar ta tace.
"Ngd Umaymah Ngd matuƙa, Allah ya saka da al'khairi".
Amin Amin tace kana ta miƙa tare da cewa.
"Naga kina son dogayen riguna ranar da zan aika kince su kikafi so, gasu an kawo miki su da yawa".
Murmushi tayi

Please Login or Register in order to submit comment