Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

wasu lokutan, saboda shi ne ƙaramin ɗan ta.


Mai sunan baba ya ɗan jima a gidan, sannan baba ya ce zai tafi, Ade ta din ga tambayarsa yaushe zai dawo, idan bai dawo ba, za ta ƙulle takalmanta a zaninta, ko ta katanga ta bi, ta gudu ta koma ƙauye.


Mai sunan baba ya ce "Ai ba za ayi haka ba"


"Ka rabu da ita, karen nan zan kawo ɗakinta na ɗaure, na ga ta wurin fita"


Ta galla masa harara ta ce "Tashi ke je ɗakina, ka samo masa ɗan biskit ɗin nan"


Alhaji Aminu ya ce "Biskit kuma? Ade kyautar nagge zaki bashi, me zai yi da wani biskit"


Mai sunan baba ya ga ƙoƙarin ta ma, rikicin taufan na ta ba na zage² bane ba.


Mai sunan baba har ya koma gidan da yake, yana al'ajabi, kuma ya yanke shawarar zai yi wa Mahmud zancen, koma ya zo lagos ɗin, ya je su ganewa idonsu, su san ta in da za a ɓullowa lamarin.


Dan baya son yayi gaggawa, a zo a gane cewar ba su da wata alaƙa.


***
Ammi ta kasa mantawa da matsananciyar cin amanar da babu uwani ta yi mata, har ta kai ba ta iya sakin jiki tayi magana a gaban kowa yanzu, saboda tsoro da tunanin kowa ma ba son ta yake yi tsakani da Allah ba.


Ranar da mai sunan baba zai koma, Iman gyara kala-kala, aka ƙalƙale ko ina, ta shirya girke² ta sha kwalliya.


Dama har kirari yake yi mata da ɗawisu sarkin ado, Iman akwai ado da kwalliya.


Sosai suka yi missing ɗin juna ita da shi, sai dai da ya kalleta, Alhaji Aminu yake tunawa da mahaifiyar sa.


Ya din ga jin tamkar yayi mata zancen, amma ya kasa.


Washegarin dawowarsa, da yamma ya shirya su ka yi wa mama siyayya, suka je gida gaisheta.


Mama tayi ta yi masa faɗa a kan yanzu yana da iyali, yakamata ya mayar da hankali a kan gidansa, ƴan samarinta sun ɗauke mata komai, kuma dubu ɗarin ma da ya turo tayi yawa, jiransa take yi ya dawo dama.


Ya ce "Ni fa ba ruwana, ƴar ki ce ta ce ayi haka"


Mama ta ce "Kuma sai ka biye mata?"


Iman ta ce "Mama idan bamu yi muku ba, wa muke da shi? Ayi ta saka mana albarka kawai".


Mama ta ce "Albarka da addu'a kullum cikin su muke, amma dan mun haifeku ba ya nufin, mu takura rayuwarku, ina fatan dai kun je wurin hajiyar?"


Iman ta ce "Gobe in Allah ya kaimu za mu je ammi, a can zan wuni, shekaranjiya na koma gida, idan na kuma zuwa faɗa za ta yi mini".


Mama ta ce "Ai faɗan na gyara ne, mun kai ku ɗaki amma kullum ku ba kwa gajiya da zuwa gida"


Iman ta yi dariya ta ce "Mama kenan".


Kasancewar umar akwai kyauta, haka ya din ga bayar da kuɗi, ga bikin Abubakar saura wata ɗaya kacal ya rage.


Mai sunan baba suka yi waya da Mahmud, ya tabbatar masa da shima zai shigo kano, dan haka umar ya ce idan ya shigo yana son su haɗu za su yi magana.


Nusaiba har ta shirya tafiya makaranta, sun yi sallama da ammi, ammi tana ta fama Sabir, ya isheta da fitina, tana ta mita ta ce makaranta za a kai mata shi, ta huta.


Barira tana mata dariya ta ce "Anya ranki ya daɗe, kin hana mamansa shi ma balle kai shi makaranta, idan aka kai shi, sai kin fi kowa damuwa"


"A'a ba wata damuwa gara a kai shi, tun da yayi baki"


"Ammi, ammi" Nusaiba ta shigo tana ƙwalawa ammi kira.


"Lafiya baki tafi makarantar ba?"


"Ammi wai yaya Mahmud ne ya dawo shekranjiya, wai ya je har gida ya yi wa Jabir dukan tsiya, ta ƙarfin tsiya ya saka shi a mota a fita da shi, ya kai shi ofishin ƴan sanda an rufe shi. Yau shi kuma ya wayi gari da ciwon ciki, a asibiti ma ya kwana bai san waye a kansa ba".






Ayshercool
08081012143
*MAMAN MEENAT COLLECTION, MAMAN MEENAT SUPPLEMENT/SKIN CARE*


*SHIN YAR UWA KINADA LABARIN* *SHAHARARRIYAR MAI SAYAR DA SUPPLEMENT DIN NAN KUWA?*
*TO IDAN BA KI SANI BA KIYI MAZA KI GARZAYA DOMIN KEMA KI SAMU RABONKI DOMIN ZATA GYARAKI TSAF KI FITO KAMAR SABUWAR AMARYA, KEMA KI SHAGA CIKIN MATAN DA SUKE HASKAKAWA KAMAR TAURARO. SHIN ƘURAJE NE SUKE DAMUNKI, KO KUMA MATSALOLIN JIKINE KAMARSU RAMA BUSHEWAR FATA KARANCIN NI'IMA NE KO BUDEWA NE, KO KUMA INFECTION? KO KUMA SO KI KEYI FATARKI TAYI LAUSHI KIDIN GA SHEƘI KINA HASKAWA? TO MAZA KI GARZAYO WURIN MAMAN MEENAT DOMIN KI SAMUN MAFITA CIKIN SAUKI, ACIKIN FARASHI ME SAUKI*
*SANNAN YAN UWA KUSANI DUK* *SUPPLEMENT DIN DAZAMU KAWO MUKU SAI MUNYI BUNCIKE AKANSHI DAN TABBATAR DA INGANCINSHI MUN TABBATAR DA CEWA BASHI DA WATA* *MATSALA GA LFY, AKWAI MASU CEWA SUNSHA SUPPLEMENT AMMA HAR YANZU SU BASUGA WANI CANJI BA, TO YAR UWA KODAI AN BAKI FAKE KO KUMA BA'A BAKI WANDA YA DACE DAKE BA, KO KUMA BAKISHA YADDA YA KAMATA BA, DOMIN KISANI YAR UWA KAFIN KI FARA SHAN* *SUPPLEMENT AKWAI WASU KA'IDOJI DAYA KAMATA ACE KIN KULA DASU KUMA KIN KIYAYE, MATUKAR KINASO SUYI MIKI AIKIN DA KIKESO CIKIN SAURI, WANNAN KA'IDODIN SAI KIN NEMENI ZAN SANAR MIKI, DOMIN BAZAN IYA KAWOSU ANAN BA SBD SUNA DA YAWA*


*Yar uwa muna da duk wani supplement da kuke bukata masu kyau da inganci tested and trusted, sayen na gari mai da kudi gida, gaskiya da Amana shine takenmu 08039437158.*


👉 *Supplements suna da yawa amma ga kadan daga cikin su.*


*1. Supplements na gyaran jiki ciki da waje*


*2. Supplements na gyaran gashi da farce, dasa haske mekyau ba irin na bleaching ba*


*3. Supplements mai da tsohuwa yarinya anti aging wanda zaisa ki kullum ki koma kamar yarinya matashiya*


*4. Supplements na karawa fata kyau da sheki glowing skin*


*5. Supplements na masu fama da ciwon jiki da stress da rashin samun isashshen bacci*


*6. Supplements na masu ciki, da masu shayarwa wanda zai kara miki lfy keda babynki*


*7. Supplements na gyaran jiki da gashi, kara hasken ido da sauransu*


*8. Supplements me kara lfy da karawa garkuwar jiki karfi.*


*9. Supplements na karin ni'ima da dandano da tightening ciki da waje*


*10. Supplements na magance cututtuka, kamar matsalar ido ulcer, infection, karawa garkuwar jiki karfi, etc*


*11. Supplements na gyaran nono da mazaunai breast/hips Enlargement*


*12. Supplements na gyaran HQ ciki da waje*


*13. Supplements na rage tumbi slimming capsule/flat tummy Lipton*
*14. Supplement na whitening/glowing skin*


*15. Supplement for Acne, dark spots remover*


*Sannan ga wadanda sokeso jikinsu yayi kyau sosai amma basa son susha supplement to albishirinku muna da kowanne irin mai na gyaran jiki da kuke bukata irinsu lotion, cream, soap, scrubs, face Cream,sun screen, serums concentrate, hair oil, hair cream face mask etc, sannan ga masu fama da matsalar ciwon jiki wadanda kullum sai sunsha magani suke jin dadi ko iyaye ko kakanni, to albishirinku kuma mun kawo muku cream, soap na ciwon jiki masu kyau da inganci wadanda indai kana amfani dasu ka huta shan maganin ciwon jiki da yardar Allah*


*Muna saida duk wasu nau'in supplement Lotion da kuke bukata, sannan Maman Meenat collection ba anan kadai ta tsaya ba muna saida turaruka kowanne irin na wuta dana jiki, da Airfreshners, sayen daya ko sari ke dai kawai neme ni a wannan number call or chat 08039437158*


Paid book ne, ₦500 via 0009450228, aisha adam jaiz bank, sai shaidar biya ta 08081012143, ga masu buƙatar vip post, suna iya garzayawa arewabooks su yi searching sunan book ɗin. Kar ku manta da subscribing YouTube channel ɗinmu na Cool hausa novels, domin samun daɗaɗan litattafan hausa na sauraro, ciki har da ƙanwar maza da yake daf da fara zuwar muku a kan channel ɗin*


https://www.youtube.com/@CoolhausaNovels


Susbcribe my YouTube channel please 🙏


*TALLA! TALLA!! TALLA!!!
*ƊANƊANO DAGA LITTAFIN NAZEEFA SABO NASHE, MAI SUNA ƘUDURAR ALLAH*


Ta Yaya zai zama jinina alhali ni na san bayan matana ban tab’a kusantar wata mace ba?” Ya furta kai tsaye yana kallon likitan da sakamakon gwajin yake hannunsa. Likitan yana jinjina kai ya sake furta “Tabbas Jaheed jininka don gwajin k’wayar halittarku da komai ya tabbatar kai ne mahaifinsa kafin a kai ga haka ma ko Kamanninku da suka zamo kwabo da kwabo sun tabbatar da Hakan koda Ba’a yi gwajin ba.”


Shiru na tsawon lokaci d’akin ya d’auka kowa da irin tunanin da yake a ransa ya kasa yarjewa zuciyarsa shine Mahaifin Jaheed duk da k’wararan shaidu. Abinda ya sani ko da wasa bayan matansa na aure na Sunna bai tab’a rik’ewa wata mace hannu ba, idan kuwa ya tabbata Jaheed d’ansa ne ta yaya ya samar da cikin nasa a jikin wacce aka kira mahaifiyarsa da ko a mafarki bai tab’a ganin mai kama da ita ba TABBAS AKWAI LAUJE CIKIN NAD’i. Mahaifiyar Jaheed ma Zata iya zama abar tuhuma da zargi. Kai tsaye zai iya cewa hakan zai iya zama K’UDIRAR ALLAH….


(*Ina ma'abota karance-karancen litatafan hausa, na san kun santa, Nazeefa sabo nashe, tsohuwar marubuciya, da ta saba nishaɗantar da ku, da ɗaɗan litatafan hausa masu ma'ana da ilimantarwa, ya kuke tunanin wannan turka-turka, DNA ɗin sa ya kasance daidai da na yaron da bai taɓa ganin mahaifiyarsa ba, haka zalika a iya saninsa tun daga ƙuruciya har girmansa, bai taɓa aikata zina ba? Ku kasance da Nazeefa sabo nashe, dan jin yadda zata warware wannan turka-turka a cikin littafin ƙudurar Allah. Masu buƙata kai tsaye za su iya tuntuɓar ta a kan lambar wayarta 08033748387*)


*Littafin kuɗi ne, ₦500 via 0009450228, aisha adam jaiz bank, sai shaidar biya ta 08081012143*






Miƙewa Ammi ta yi cikin sauri ta ce "A ina ki ka ji?"


Nusaiba ta ce "Yanzu su musa suke faɗa, wai a asibiti ya kwana ma, tun cikin dare aka kai shi"


Rikicewa ammi tayi, ta nufi ɗakinta, Nusaiba ta bita ta na cewa "Ammi me zaki yi?"


"Nusaiba asibitin zan tafi, ni babu wanda ya gaya mini ai"


Nusaiba ta ce "A'a Ammi, kar ki je su yi miki wani rashin mutuncin, ki fara kiran takawa ki gaya masa"


"Yaron ya kwana a asibiti, ki ce sai na kira takawa na gaya masa?"


"Dan Allah ammi ki bari ya zo tukuna, sai ku tafi tare ma, kar su cutar da ke" da ƙyar Nusaiba ta shawo kanta, ta amince a kira takawan tukuna".


Juma'a ce, dan haka rumaisa ta ce ba zata makaranta ba, dan jikinta babu daɗi ko ina ciwo yake yi mata.


Takawa sai lallaɓata yake yi, yana son ya fita aiki, sai sangarta take yi masa, da shagwaɓa kala-kala.


Wayar Ammi ya gani, dan haka ya ɗaga tare da yin sallama.


Cikin ruɗewa ba tare da ta iya amsa sallamar ba ta ce "Takawa, kana ina ne? Mahmud aka kwantar a asibiti, wai ya kwana yana ciwon ciki jiya, so nake na je"


Takawa ya ce "Dan Allah ammi ki kwantar da hankalinki, ki bari na je wurin aiki, idan aka saukko daga masallacin juma'a zan zo na kai ki ki duba shi".


"Baka da hankali ne? Ka san ciwon ciki kuwa? Yaron ya kwana a asibiti amma ka ce sai an idar sa sallar juma'a awa nawa? Idan zaka kaini ka zo yanzu, idan ba zaka zo ba zan yi tafiyata ko me za su yi zan jure tun da ni na kai kaina"


"Kiyi haƙuri gani nan" rumaisa ta zuba masa ido, bayan ya kashe wayar ya ce "Duk ta rikice a kan ɗan da bai san darajarta ba, nan zai yi ciwo ta je duba shi, ta hanata ganinsa ta ce bacci yake, ko baya son hayaniya amma za taje duba shi, ammi ba ta gudun abun da zai ɓata mata rai sam"


Ruma ta ce "Dan Allah zuciyar mutum ce a jikinka? Ka san me ake nufi da uwa da ɗa kuwa? Kai banda dalilin sihiri da nake da tabbacin shi ya raba ammi da daddy, kai kana zaton akwai dalilin da zai sanya ta zuba ido ta barwa wata mata ɗan ta.
To ai ko ni da abun da ke cikina bai zo duniya ba, da shi da Sabir, ban ga wanda ya isa rabani da su ba, kai idan aka ce za ayi asirin ma, sai na haɗa asirin da bokan na ci ubansu wallahi.
Dan Allah papa kaima ka sassauta wannan ƙiyayyar, yanzu bari in saka kaya in bika".


Ya ce "No, ki zauna a gida, zan je kawai"


Ruma ta ce "Hankalina ba zai kwanta ba, ka tafi da ni dan Allah, idan ba haka ba zan biyoka idan ka fita".


"Mimi kina da matsala, cikin nan ne bana son a gani".


Ta kalleshi ta ce "Saboda me?"


"Kin fi kowa sani ai, ba na son wani abu ya samu cikin nan naki, kullum cikin Addu'a nake yi Allah ya sa ki haihu lafiya, kin san komai ai"


"Babu abun da zai faru sai ikon Allah, ka tafi da ni saboda zatin Allah, hijjabi zan saka, ba wanda zai gan shi ai" kasancewar rumaisa ta ƙware a iya magiya, tamkar ƴar maroƙa, haka ya sanyata a gaba suka tafi.


Da shi da Nusaiba, da Ammi, haka suka rankaya asibitin da aka ce Mahmud yana can.


Gaba ɗaya Ammi ba ta cikin nutsuwarta, takawa ya ce "Ammi dan Allah ki kwantar da hankalinki, kin San ki na da high bp".


A rikicen dai Ammi ta ce "Kai ka san sani high bp, ka tambayar mini ɗakin da yake dan Allah "


Ruma ta din ga kallon ammi cikin tausayawa, haka ta shafe shekaru da soyayyar nan da tausayi suna nuƙurƙusa zuciyarta, ruma ta jinjinawa mugunta irin ta mummy.


Ba ƙaramin razana ammi tayi ba, ganin Mahmud a kwance ba ya motsi, ga ruwa an saka masa, ga kuma oxygen da take taimaka masa yana numfashi, gefensa kuma mummy ce a zaune.


"Innalillahi wa Innalillahi raji'un, Mahmud meya sameka haka?" Ammi ta yi maganar cikin rawar baki.


Jin muryarta ya sanya shi ya motsa, ya fara yi wa ammi nuni da hannunsa ta zo.


Cikin hanzari ammi ta ƙarasa, idonta na ta zubar da hawaye.


Ya miƙa hannunsa ya riƙe nata, sai dai ba baki, sai hawaye da yake zuba ta gefen idonsa.


Ammi ta riƙe hannunsa tana jejjera masa sannu.


Ya ɗora hannun a kan cikinsa.


Ruma ma ta ƙarasa gaban sa cikin kuka ta ce "Daddy meyafaru? Meya sameka?"


Wata irin miƙa yayi bakin sa yana zubar da kumfa, cikin sarƙewar numfashi ya ce "Daughter mutuwa zan yi. Ammi. Amm....Ammi na faɗa yau rumaisa, Ammi ki yi mini Addu'a cikina" yayi maganar tamkar numfashin sa zai bar gangar jikinsa.


Daga rumaisa har Ammi kuka kawai suke, Nusaiba ma kuka take.


Cikin kiɗimewa Mummy ta tashi cikin azama, ta ce "Mahmud ciwo ba mutuwa bane ba, kar ka sake cewa zaka mutu, haba Mahmud kar ka yi mini haka dan Allah " tayi maganar tana fashewa da kuka.


Ya buɗe ido a galabaice ya kalli Mummy, ya zare hannunsa daga na ammi, ya riƙo nata "Mummy na gode, na gode Mummy"


Ya sake zare hannunsa daga na Mummy, ya miƙawa adam, sannan ya cewa ruma "Ki ce masa ko sau ɗaya ya riƙe hannuna Daughter" ya yi maganar yana sake mimmiƙe wa.


Cikin matsanancin kuka da tashin hankali rumaisa ta kalli Adam ta ce "Papa dan Allah"


Adam da tuni ya karaya, kuma ya tsorata da lamarin, A hankali ya tako, ya zauna a kusa da rumaisa, ya saka hannunsa a na Mahmud ya rungume shi.


"Ina son ka ɗan uwana, Ƙaddara ce"


Mummy ta rasa in da zata sanya kanta, dan lafiya ƙalau Mahmud ya kwanta, idan har ta ce ba ta ƙaunar Mahmud ƙarya take yi. Saboda yayi mata biyayya fiye da yaran da ta haifa, kuma ta saka an ƙwace shi an bata shi, dan mugunta, amma kuma sai ta fara son sa daga baya.


Likita ne ya shigo, ya din ga yi wa Mahmud wasu allurai.


Bayan fitar likita, duk sun yi shiru sun zuba masa ido, Adam yana rungume da shi, rumaisa ta miƙe zumbur, dan tamkar ana mata raɗa ta ji komai.


"Me ya haɗa shi da jabir ne?"


Takawa ya ce "A ina?" Duk suka tsaya suna kallonta.


"Meyasa ya daki Jabir ya kulle shi?"


Duk suka zubo mata ido.


ganin da Mahmud yayi Mummy, tana cikin damuwa, ya sanya ya sakata a gaba, a kan ta gaya masa meke damunta, ta kasa ɓoye masa ta gaya masa komai. Ba ƙaramin girgiza yayi ba da jin abun da Jabir ɗin ya yi ba shi da ruƙayya, tun da ya fita a fusace, sai wayar Hajiya Lubabatu ta gani, ta tabattar mata da zata ga abun da za ta yi wa Mahmud muddin bai saka an sakar mata ɗa ba domin kuwa ta san muddin asirin jabir ya tonu ba zai yi sarauta ba, kuma ta fuskanci kamar yanzu Mummy ƙoƙari take taga Mahmud ne ya samu sarauta.


Sai a yanzu Mummy ta tuna da furucin hajiya Lubabatu.


Tashi rumaisa ta yi ta fara tashin Mahmud.


Takawa ya ce "Ya samu bacci fa"


"Tashe shi kawai, daddy"


Ya buɗe ido a matuƙar wahale ya kalleta.


"Meya haɗaka da jabir?"


"Bakomai" ya furta yana numfarfashi.


Ta ce "To koma me ka yi masa, babarsa ta ce zaka gani"


Takawa ya ce "Mimi bana son rigima fa, ke a ina ki ka ganta?"


Ruma ta ce "Ɗazu da asuba ina bacci, na gansu su na faɗa, ban san a kan menene ba, amma ita ta ce zai gani, jabir yana police station ko?"


Ammi ta tashi ta kamo ruma ta zaunar da ita, ta ce "yi shiru da bakinki" shi dai takawa a iya sanin sa, suna tare da ruma, kuma ba wani wurin suka je ba, balle ace ta ji.


Mummy ta hau bala'in cewar mahmud sun yi faɗa da Jabir, amma ba wani abu da Hajiya Lubabatu ta yi masa.
Tayi maganar tana karewa saboda kar a gane sun samu saɓani da Hajiya Lubabatu, kuma muddin asirin lubabatu ya tonu, na ta ne ya tonu.


Takawa ya ce "Mimi ba ta ƙarya a cases irin wannan, zan yi bincike a kai, duk wanda na gano da saka hannunsa wani abu ya same shi, wallahi sai ya fuskanci hukunci ko waye shi".


"Matarka ba ta ƙarya ni nake yi kenan?"


Ammi da sauri ta ce "Dan Allah ki yi haƙuri, ku yi haƙuri Takawa kar in sake jin bakin ka, rumaisa ku yi shiru mu yi masa addu'a".


Ruma ta ce "To ammi, amma wallahi ba ƙarya nake yi ba"


Mai sunan baba ne yayi sallama ya shigo, hankalinsa a tashe, "Subhanallah" yake ta maimaitawa saboda halin da ya ga Mahmud a ciki, dan kuwa sun yi waya jiya da safe, yake ce masa zasu haɗu yau.


Bai iya yi wa kowa magana ba, ya ƙarasa gaban gadon yana ambaton sunansa.


Gashi da an kira sunansa yake amsawa, ya buɗe idonsa ya kalli mai sunan baba.


"Mahmud, meyafaru haka ne? Wayarka na kira wata yarinya ta ɗauka ta ce mini wai kana Asibiti" ya cewa mai sunan baba "Ɗago ni"


Mai sunan baba ya sanya hannu biyu, ya ɗago shi, ya jingina da jikinsa.


Ammi ta din ga ajiyar zuciya ganin Mahmud a zaune.


"Ku yi haƙuri duk na tayar muku da hankali"


Mai sunan baba ya ce "Kar ka damu sannu ya jikin naka?"


"Da sauƙi, zan sha ruwa"


Mai sunan baba ya kalli Adam, Adam ya ɗaukko roba ya tsiyaya ruwa ya bawa umar, ya karɓa ya bawa Mahmud, ya karɓa ya sha sosai.


Ya ce "Alhamdilillah, ina ƙanwata tana lafiya?"


"Lafiya ƙalau, bata san me ke faruwa ba, na riga na fito sannan na kira wayarka, sannu Mahmud"


"Yauwwa yaya" kasancewar haka yake kiran umar.


Ammi ce ta ce "Mai sunan baba ya gida?"


Ya ce "Afuwan ammi, hankalina ne a tashe wallahi, ya gida ya mai jiki kuma?"


Ammi ta ce "Jiki da sauƙi Alhamdilillah"


Mummy kuwa sai cika take tana batsewa, Fauziyya ba ta taɓa ƙarewa mai sunan baba kallo ba sai yau, lallai Iman ta auri mai kyau, da cikar zati.


"Me zaka gaya mini ne ka ke nema na?"


Mai sunan baba ya ce "Ka ji da jikinka ka samu lafiya, kana tambayata me zan gaya maka" yayi maganar yana murmushi.


"Am curious about it" yayi maganar yana lumshe idanunsa, saboda allurar baccin ba ta sake shi ba.


"Zan gaya wa yayanka ya gaya maka"


"Wai Takawa? Ba zai gaya mini ba"


Mai sunan baba ya ce "Zai gaya maka mana, zaka ci abinci ne?"


Ya girgiza kai ya ce "Bari sai na gama farfaɗowa, idan kuma na mutu....


"Shhhh, zaka farfaɗo in sha Allah, har aurar da kai sai na yi"


Ammi bakinta ya ƙi rufuwa dan murna, ita ba ta san ya aka yi ma ta sa ta zo ɗaya da Mahmud ba, saboda Mahmud akwai taurin kai da rashin mutunci, mai sunan baba kuma akwai izza da son girma, amma yadda yake yi masa zaka gane akwai mutuntawa da girmama juna a tsakaninsu.


Ya kwantar da Mahmud, ya ce "Ka yi bacci, zan je gida ƙanwarka ta yi maka girki, mu zo ta duba ka"


"Kar ka wahalar da ita, ga Mummy ga Ammi ga daughter duk na wanda na samu zan ci".


"Ba wata Mummy, na ammi zai ci" Rumaisa ta faɗa tana harare-harare.


Fauziyya ta buɗe baki za ta yi magana, amma kwarjinin mai sunan baba ya cika mata ido, dan ta san ƙarya take, ta zagi rumaisa a gabansa ya ƙyale ta.


Ya kalli Adam ya ce "Ina son yin magana da kai"


Mamaki ne ya kama Adam, amma ya tashi ya bi bayan mai sunan baba suka fita.


Fauziyya ce ta ɗora da rashin mutunci.


"An yi magana wani ammi ce za ta bashi abinci, sai ka ce ammin wahalar sa ta sani, uwarmu ce dai ta yi masa duk wata wahala ta rayuwa".


"Da tayi mata fashin ɗan? Kallon biri ku ke masa yake yi muku na ayaba fa. Uwar me ta tsinana wa rayuwar ta sa ban da masifa, uwar riƙon arziki ce za ta raba uwa da ɗan ta, ta raba jini da jininsa, ta raba shi da ɗan uwan sa, yanzu dai shi ma ya san gaskiya, gurbin ido ba ido ba ne, kuma wallahi ko bayan shekara dubu, tuwo sunan sa tuwo"


Ammi sai ƙoƙarin hana magana take yi, amma rumaisa tayi mursisi ta din ga gasawa Mummy da Fauziyya magana, ita kaɗai su biyu ba tare da kunya ko tsoro ba.


Duk abun nan da ake yi Mahmud yana jin su, amma yayi shiru kamsr mai bacci.


Mai sunan baba ya kwashe komai ya gaya wa takawa, game da Alhaji Aminu, jikin takawa har tsuma yake yi ya ce "To yanzu Lagos ɗin zamu je, ko yaya za a yi? Mu ga shi Alhaji Aminun, idan ta kama tambayarsa zamu yi, ko ma a tafi da ammi sai ayi "


Mai sunan baba ya ce "A'a ina ga gara mu mu je mu tabbatar, tun da yanzu tana cikin damuwar rashin lafiyar Mahmud, dama da shi na so mu je, to gashi ba shi da lafiya"


"Bakomai, bari mu ga zuwa gobe in Allah ya kaimu, in dai ya ƙara warwarewa, sai mu je kawai, ina fatan Allah ya tabbatar ya sanya ƴan uwan iman ne "


Mai sunan baba ya amsa da Amin, har takawa ya juya zai tafi mai sunan baba ya ce "Na ce ba" ya juyo ya tsaya yana sauraren sa.


"Akwai buƙatar duk abun da ya faru a baya ya wuce, a fuskanci gaba.


A zamana da Mahmud babu abun da yake marari da so da ya wuce ka, you have to play your role as his senior brother, babu abun da yafi ɗan uwa daɗi. Ba zaka gane hakan ba sai ranar da babu shi a duniya"


Adam ya yi ajiyar zuciya ya ce "Haka ne, na gode sosai" mai sunan baba ya jinjina masa kai ya tafi.


Samha sun je duba Mahmud a asibiti, dan tuni labari ya zaga masarautar, Mahmud ba shi da lafiya, ƴan dubiya sun fara kaiwa suna komowa.


Sai dai fa cacar baki taƙi tsayawa a tsakanin Fauziyya Mummy da rumaisa.


Muraran yau ruma take nuna musu asalin tantirancinta.


Samha za ta saka baki ruma ta ce "Yi mini shiru, ba dake nake ja gayyar mushirikai maƙiya Allah, ai wallahi a doron duniya ban ga bokan da zai yi asirin da zai kamani ba, sai dai ku yi wa wasu".


"Su waye mushirikan?"


"Gaku nan gaba ɗayanku, ban da yawon asiri da ƙoƙarin rusa rayuwar mutane me ku ka saka a gaba, azzalumai maƙiya Allah"


A rikice ammi ta fita neman Adam, suka yi kiciɓis a hanya, ta ce masa maza ya je ya ɗau rumaisa ya mayar da ita gida.


Sai dai suna shiga ɗakin,

Please Login or Register in order to submit comment