Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ki ke soyayya da yaya Aliyu ba labari, kuma ko gaisheni ba kya zuwa yi"


Habiba ta ce "Sannu mama" suka tuntsire da dariya.


Habiba ta ce "Kamar in janyo lokacin candy rumaisa, ina ƙaunar Yaya Aliyu kamar me, Ruma aure da daɗi dan Allah?"


Hauwwaliya ta ce "Eh ɗan gaya mana"


Ruma ta ce "Eh to, ba nace babu ba, bana ce akwai ba, idan kun je kwa gani, idan ku ka yi sa'a ku ka auri irin mijina, to kun dace, ni da mijina bani da matsala, sai danginsa 'yan bala'i. Ku san kowa da kalar jarrabwarsa a gidan aure".


Hauwwaliya ta ce "To, Allah ya sassauta mana"


Suka amsa da Amin.


Da Adam ya koma gida, aka ce masa ruma ta tafi gidansu, dan haka ya tafi yana fatan Allah ya sa ba ta faɗi wani abun ba.


Wayar mama ya kira, suka gaisa ya ce mata rumaisa ta zo, zasu tafi.


Ba ta son tayi musu ko wani abu da zai sanya, a gane saɓani suka samu, dan laila ta gargaɗeta sosai a kan haka, ta ce mata duk wata matsala, in dai za su iya warwarewa a tsakanin su, kar ta bari wani ya ji, balle ya shiga. Galibin aure yana samun matsa a dalilin sako mutum na uku a cikin matsalolin auren.


Bayan motar ta buɗe ta shiga, ko kallonsa ba ta yi ba.


Har suka je gida ba ta kula shi ba, shi ma kuma bai iya ce mata komai ba, duk da ƙasan zuciyarta har ta fara jin tausayinsa, dan a kiɗime yake sosai da sosai.


Da suka je gida ma, a buɗe ta bar masa motarsa ta yi shigewarta cikin gida.


Ko tayi niyyar daina fushin, da ta tuna yadda ta ga Samha a tsaye a gaban sa, ta turo ƙirji sai wani irin baƙin ciki ya turnuƙeta.


Wanka tayi, ta je kitchen ta damo kununta, ta koma ɗaki tana sha. Ita kanta missing ɗin sa take yi sosai da sosai, saboda sun yi wani irin sabo sosai da sosai.


Kamar mara gaskiya haka yayi sallama a ɗakin, ta amsa masa ƙasa-ƙasa.


Ya ƙarasa ya zauna a kusa da ita ya ce "Rumaisa".


"Na'am" ta amsa a daƙile.


"Yanzu kina tunanin zan iya aikata abun da bai kamata ba kenan? Yakamata ki fahimce ni, ya ci ace kin san halina, wallahi rumaisa babu wani abu da ya faru, abun da ki ka gani ma is not intentionally ban san me ma zan ce miki ki yarda da ni ba. Amma dan Allah kar ki kawo komai a ranki".


"Amma fa tsayawa ka yi kana kallonta, fisabilillahi".


"Rumaisa a rayuwata bana tunanin akwai wanda na taɓa bi ina bawa haƙuri, kamar yadda nake binki a yanzu, dan Allah ki yi haƙuri, ko sai na durƙusa ɗin a kan gwiwoyina?"


Ta girgiza masa kai alamar a'a.


"To ki dube ni mana, kiyi haƙuri Please" yayi maganar yana riƙe hannunta cikin nasa.


"Na haƙura amma dan Allah kar ka sake kulata, wallahi ji na yi kamar na je kitchen na samo taɓarya na zo na rotse mata kai. Kawai ta wani tsaya ta gantsare a gabanka, wallahi na ji haushi"


Ya ce "Subhanallah, duk ba ta kai ga haka ba, nima ban ji daɗi ba amma ki yadda da ni, ai ni namu sun isheni, me zan kalla a na wata"


"Abun da bai fi murfin jarkar faron ba?"


Yayi murmushi ya ce "Har laifukana na baya za'a tayar kenan?".


"Eh ɗin, ka je ka kalli naka ko na Samha"


Yayi murmushi ya ce "Allah dai ya bada haƙuri"


Ta amsa da "Amin"


Ya rungumeta ya ce "I so much miss you, smile please"


Ta lashe cokalin hannunta ta ce "ba zan iya ba yanzu, idan na ce zan yi murmushi yanzu, yaƙe kawai zan yi. Ka ci abinci kuwa?"


"A ina zan ci, tun da baki bani ba?"


Ta ce "To mu je na sama maka abun da zaka ci"


"Yauwwa my dear, ana so na ana kaiwa kasuwa, an damu da ni amma ana ta wahalar da ni"


Ta kalleshi ta ce "Ka ke dai so na"


Ya ce "Na yadda".


Ta ce "To amma sai dai ka goya ni, ka kai ni kitchen ɗin"


Ya durƙusa ya ce "Zo ki hau"


Aikuwa ta miƙe ta hau bayansa tana dariya, ya goyata a bayansa, har kitchen.


A ranar dai suka shirya, rumaisa tayi iyakar ƙoƙarin ta wurin bin shawarar da anty laila ta bata, na cewa idan har namji zai iya yi miki laifi ya baki haƙuri, to ba ƙaramin kimarki yake gani ba, ba kowann namiji ne zai yi ba dai-dai ba ya nemi afuwarki, sai ma yayi ƙoƙarin nemo wani laifin ya jingina miki, duk dan kar ya nemi afuwarki.


Sosai aka shiga hidimar biki, ka'in da na'in, mai sunan baba kai ya ɗau caji sosai da sosai, abunka da wanda bai saba da hayaniya ba, nan da nan sai ciwon kai.


Gidan marigayi galadima Sharif ma, ya cika ya tumbatsa, mutane sai kaiwa suke suna komowa.


Mummy kuwa ba gaira ba dalili take tsinewa auren, tare da mummunan baki a kan haka.


Rumaisa kuwa ba ta a nan bata a can, takawa sai mita yake a kan ta nemi wuri ta din ga hutawa, kar sai an kammala biki, ta zo tana ciwon jiki.


Ranar da aka yi dinner rumaisa tayi kyau, haka amarya Iman da mai sunan baba, shi gaba ɗaya ma kunya yake ji, ko ɗaga kai baya son yi ya kalli taron jama'ar nan.
Yazo wurin nan ne kawai saboda iman ta matsa. Kamar da bikin rumaisa a wannan karon ma, kaiwa da komowa zaratan samarin gidan maman suka din ga yi, sanye da kaya iri ɗaya a jikinsu gwanin sha'awa ango ba shi da wasu abokai, sai classmates sai ƙannensa.


Ƙawayen ammi sun yi mata kara sosai da sosai, suka din ga liƙi suna kaiwa da komowa, duk wanda ya ga couples ɗin sai ya ce masha Allah, saboda kyau ne ya haɗu da kyau, duk da bai kai iman haske ba, amma kallo ɗaya zaka yi masa ka ce kyakkyawa ne.


Bayan an kammala dinner suka taso, Mahmud ne ya ɗaukko su a motarsa, Iman sai hamma take yi, saboda ta gaji.


"Kin gaji ne?" Ya tambaye ta lokacin da ta kashingiɗa da seat ɗin motar.


"Eh yaya umar, ko ina ciwo yake mini"


Yayi murmushi ya ce "To sannu, idan kin je gida ki kwanta ki huta sosai"


Ta ce "To ango"


Yayi murmushi, suka fara kaita gida, sannan suka wuce Mahmud ya kai mai sunan baba gida.


Washegari aka ɗaura aure, turaki ne yayi wa Iman waliycci. Aka ɗaura auren Umar Mahmud da Khadija Muhammad Galadima.


Ayshercool
08081012143
*MAMAN MEENAT COLLECTION, MAMAN MEENAT SUPPLEMENT/SKIN CARE*


*SHIN YAR UWA KINADA LABARIN* *SHAHARARRIYAR MAI SAYAR DA SUPPLEMENT DIN NAN KUWA?*
*TO IDAN BA KI SANI BA KIYI MAZA KI GARZAYA DOMIN KEMA KI SAMU RABONKI DOMIN ZATA GYARAKI TSAF KI FITO KAMAR SABUWAR AMARYA, KEMA KI SHAGA CIKIN MATAN DA SUKE HASKAKAWA KAMAR TAURARO. SHIN ƘURAJE NE SUKE DAMUNKI, KO KUMA MATSALOLIN JIKINE KAMARSU RAMA BUSHEWAR FATA KARANCIN NI'IMA NE KO BUDEWA NE, KO KUMA INFECTION? KO KUMA SO KI KEYI FATARKI TAYI LAUSHI KIDIN GA SHEƘI KINA HASKAWA? TO MAZA KI GARZAYO WURIN MAMAN MEENAT DOMIN KI SAMUN MAFITA CIKIN SAUKI, ACIKIN FARASHI ME SAUKI*
*SANNAN YAN UWA KUSANI DUK* *SUPPLEMENT DIN DAZAMU KAWO MUKU SAI MUNYI BUNCIKE AKANSHI DAN TABBATAR DA INGANCINSHI MUN TABBATAR DA CEWA BASHI DA WATA* *MATSALA GA LFY, AKWAI MASU CEWA SUNSHA SUPPLEMENT AMMA HAR YANZU SU BASUGA WANI CANJI BA, TO YAR UWA KODAI AN BAKI FAKE KO KUMA BA'A BAKI WANDA YA DACE DAKE BA, KO KUMA BAKISHA YADDA YA KAMATA BA, DOMIN KISANI YAR UWA KAFIN KI FARA SHAN* *SUPPLEMENT AKWAI WASU KA'IDOJI DAYA KAMATA ACE KIN KULA DASU KUMA KIN KIYAYE, MATUKAR KINASO SUYI MIKI AIKIN DA KIKESO CIKIN SAURI, WANNAN KA'IDODIN SAI KIN NEMENI ZAN SANAR MIKI, DOMIN BAZAN IYA KAWOSU ANAN BA SBD SUNA DA YAWA*


*Yar uwa muna da duk wani supplement da kuke bukata masu kyau da inganci tested and trusted, sayen na gari mai da kudi gida, gaskiya da Amana shine takenmu 08039437158.*


👉 *Supplements suna da yawa amma ga kadan daga cikin su.*


*1. Supplements na gyaran jiki ciki da waje*


*2. Supplements na gyaran gashi da farce, dasa haske mekyau ba irin na bleaching ba*


*3. Supplements mai da tsohuwa yarinya anti aging wanda zaisa ki kullum ki koma kamar yarinya matashiya*


*4. Supplements na karawa fata kyau da sheki glowing skin*


*5. Supplements na masu fama da ciwon jiki da stress da rashin samun isashshen bacci*


*6. Supplements na masu ciki, da masu shayarwa wanda zai kara miki lfy keda babynki*


*7. Supplements na gyaran jiki da gashi, kara hasken ido da sauransu*


*8. Supplements me kara lfy da karawa garkuwar jiki karfi.*


*9. Supplements na karin ni'ima da dandano da tightening ciki da waje*


*10. Supplements na magance cututtuka, kamar matsalar ido ulcer, infection, karawa garkuwar jiki karfi, etc*


*11. Supplements na gyaran nono da mazaunai breast/hips Enlargement*


*12. Supplements na gyaran HQ ciki da waje*


*13. Supplements na rage tumbi slimming capsule/flat tummy Lipton*
*14. Supplement na whitening/glowing skin*


*15. Supplement for Acne, dark spots remover*


*Sannan ga wadanda sokeso jikinsu yayi kyau sosai amma basa son susha supplement to albishirinku muna da kowanne irin mai na gyaran jiki da kuke bukata irinsu lotion, cream, soap, scrubs, face Cream,sun screen, serums concentrate, hair oil, hair cream face mask etc, sannan ga masu fama da matsalar ciwon jiki wadanda kullum sai sunsha magani suke jin dadi ko iyaye ko kakanni, to albishirinku kuma mun kawo muku cream, soap na ciwon jiki masu kyau da inganci wadanda indai kana amfani dasu ka huta shan maganin ciwon jiki da yardar Allah*


*Muna saida duk wasu nau'in supplement Lotion da kuke bukata, sannan Maman Meenat collection ba anan kadai ta tsaya ba muna saida turaruka kowanne irin na wuta dana jiki, da Airfreshners, sayen daya ko sari ke dai kawai neme ni a wannan number call or chat 08039437158*


Paid book ne, ₦500 via 0009450228, aisha adam jaiz bank, sai shaidar biya ta 08081012143, ga masu buƙatar vip post, suna iya garzayawa arewabooks su yi searching sunan book ɗin. Kar ku manta da subscribing YouTube channel ɗinmu na Cool hausa novels, domin samun daɗaɗan litattafan hausa na sauraro, ciki har da ƙanwar maza da yake daf da fara zuwar muku a kan channel ɗin*


https://www.youtube.com/@CoolhausaNovels


Susbcribe my YouTube channel please 🙏


*TALLA! TALLA!! TALLA!!!
*ƊANƊANO DAGA LITTAFIN NAZEEFA SABO NASHE, MAI SUNA ƘUDURAR ALLAH*


Ta Yaya zai zama jinina alhali ni na san bayan matana ban tab’a kusantar wata mace ba?” Ya furta kai tsaye yana kallon likitan da sakamakon gwajin yake hannunsa. Likitan yana jinjina kai ya sake furta “Tabbas Jaheed jininka don gwajin k’wayar halittarku da komai ya tabbatar kai ne mahaifinsa kafin a kai ga haka ma ko Kamanninku da suka zamo kwabo da kwabo sun tabbatar da Hakan koda Ba’a yi gwajin ba.”


Shiru na tsawon lokaci d’akin ya d’auka kowa da irin tunanin da yake a ransa ya kasa yarjewa zuciyarsa shine Mahaifin Jaheed duk da k’wararan shaidu. Abinda ya sani ko da wasa bayan matansa na aure na Sunna bai tab’a rik’ewa wata mace hannu ba, idan kuwa ya tabbata Jaheed d’ansa ne ta yaya ya samar da cikin nasa a jikin wacce aka kira mahaifiyarsa da ko a mafarki bai tab’a ganin mai kama da ita ba TABBAS AKWAI LAUJE CIKIN NAD’i. Mahaifiyar Jaheed ma Zata iya zama abar tuhuma da zargi. Kai tsaye zai iya cewa hakan zai iya zama K’UDIRAR ALLAH….


(*Ina ma'abota karance-karancen litatafan hausa, na san kun santa, Nazeefa sabo nashe, tsohuwar marubuciya, da ta saba nishaɗantar da ku, da ɗaɗan litatafan hausa masu ma'ana da ilimantarwa, ya kuke tunanin wannan turka-turka, DNA ɗin sa ya kasance daidai da na yaron da bai taɓa ganin mahaifiyarsa ba, haka zalika a iya saninsa tun daga ƙuruciya har girmansa, bai taɓa aikata zina ba? Ku kasance da Nazeefa sabo nashe, dan jin yadda zata warware wannan turka-turka a cikin littafin ƙudurar Allah. Masu buƙata kai tsaye za su iya tuntuɓar ta a kan lambar wayarta 08033748387*)


*Littafin kuɗi ne, ₦500 via 0009450228, aisha adam jaiz bank, sai shaidar biya ta 08081012143*








Mai sunan baba jin sa yake yi tamkar ba shi ba, wai yau shi ne yayi aure, abun da bai taɓa kawowa nan kusa cikin lissafin rayuwarsa ba.
Ya san iya karamci, an yi masa wurin bashi iman, sai addu'a yake yi, da fatan Allah ya bashi ikon riƙe amana.


Ƴan unguwarsu suka din ga gulma, daga rumaisa ta auri basarake, sun liƙe sun nace musu, saboda tsabar kwaɗayi da son abun duniya. sun ga bushashar da aka yi, da irin manyan mutane da suka halarci taron ɗaurin auren Umar.


Yayin da ƴan uwa da abokan arziki, ke ta yi wa mama barka, da cewar gidan sarauta sun ji daɗin auren ruma, shiyasa suka bawa mai sunan baba ƴa.


Iman ta rasa wanne za ta yi tsakanin farinciki da akasin sa, bayan duk turka-turakar, faɗi tashi da ƙalubalen, yau Allah ya yanke mata, sai dai akwai tsananin soyayya da shaƙuwa tsakaninta a amminta da su nusaiba da rabuwa da su take jin wani babban giɓi ne a tare da ita.


Manyan mutane ne suka hallaci bikin shaida auren, har da sarakunan maƙwabta, da manyan mutane masu faɗa aji.


Gaba ɗaya jikin Iman yayi sanyi, tana tunanin sabuwar rayuwar da za ta shiga, ko da wane kalar ƙalubale za ta zo mata sanin gaibu sai Allah.


Jin an ɗaura wa Iman aure kuwa, Jabir kamar ya haukace, saboda ya tabattar da ya riga ya gama rasata.


Ƙarfe takwas na dare, anty laila ta shirya Iman cikin lafaya, aka ɗora mata alkyabba, maroƙa sun cika sashin ammi, suna ta faman koɗa ammi.


Iman ta riƙe ammi tana ta uban kuka.


Duk yadda ammi taso ta daure ta kasa, ta din ga kukan ita ma.


Mai sunan baba kuwa shi ma kamar mace, Abubakar sai masifa yake masa ya shirya, azo a raka shi mutane su huta.


Bayan yayi wanka ya shirya, jiki a sanyaye ya shiga wurin mama, ya durƙusa a gabanta, ji yake kamar ya ce ya fasa, har ga Allah bayan Allah da ma'aikinsa yana ƙaunar mahaifiyarsa matuƙa.


Mama tayi murmushin ta cire hular kansa, ta shafa sumar kansa ta ce "Allah ya yi maka albarka, Allah ya albarkaci rayuwar aurenka, ya sanya ta zame maka sanyin idaniya. Na sanka babana amma zan sake jaddadawa a kula da amana, a kula da marainiya, ba a yi wa mace muzurai, mace uwa ce, abokiyar shawara ce. A kula mini da ita. Yadda ka tallafi rayuwar ƴan uwanka ka kula da su, Allah ya baka masu yi maka, mun gode mun gode Allah ya saka maka da alkhairi babana, Allah ya kula mana da ku Allah ya yi maka albarka"


Ya sanya hannu ya kama hannun mama a cikin nasa, amma ya kasa magana, zuciyarsa ta kai matuƙa wurin yin rauni, yayi shiru ya sunkuyar da kai.


Su hajiya Iya kuwa sai rafka guɗa suke yi, Gwaggo sai masifa take tana neman rumaisa, aka ce mata ai direbanta ya zo ya ɗauketa ya mayar da ita can gidansu mijinta.


Gwaggo ta cigaba da masifa "Rumaisa ba zata nemi wuri ta nutsu ta zauna ba, wannan kyan da take yi da sheƙi, da ƙyar idan ba ciki ne da ita ba, a garin wannan rawar kan sai ta zubar da shi tukuna, nayi magana ta ce ita ba ta da ciki, manya ne suke haihuwa, wai ita kunun gaya take sha ko na sabulu? Ita dai ta sani"


Hauwwaliya ta ce "Gwaggo kunun sabaya ta ce miki bana sabulu ba, ta ce ni ma zata bani na din ga sha. Ni yanzu jira nake ta ce za ta saka azo a ɗauke mu a tafi da mu gidan amarya".
"Oho muku dai, daga ke har ita".


Abubakar ne ya zo ya janye mai sunan baba suka fito, a mota ya kalli yadda umar ɗin yayi jugumm ya ce "Wai kuka zaka yi ne?" Yayi maganar yana dariya.


Mai sunan baba yayi masa shiru.


"Ango mai kuka, duk na gulma ne, da an ga Khadija za a ware, inyeee ango na mama". Ya din ga tsokanarsa, yayi shiru ya ƙi kula shi.


Takawa da kansa ya saka Iman a mota laila da ƙawayen ammi a motar suka je suka kai iman.


Hatta su Fauziyya sai da suka je gidan iman, domin ganin ƙwal uwar daka, sun kukkushe abubuwan da dama, sai dai duk yadda suka so gano makusa a jikin angon basu gano ba.


Gidan Iman ɗan madaidaici, dai-dai zaman amarya, sai dai an zuba mata dakakkun kaya, na gani na faɗa.


Zuwansu babu daɗewa, su mai sunan baba suka ƙaraso, har da Mahmud a tawagar angwaye.


Aka yi adduoi, ƙawayen ammi suka yi musu nasiha sosai da sosai suka tafi.


Takawa ya kalli mai sunan baba ya ce "Kamar yadda ka kawo mini taka ƙanwar ka ce amana, nima ga tawa nan, amanar marainiya ce a hannunka"


Ya kalli in da ruma take zaune kusa da iman, suke ta kuka, ya kalleta ya ce "Mimi tashi mu tafi" yayi maganar yana jan hannunta, da ƙyar ta tashi, iman sai kuka take suka tafi.


Takawa sai da ya zazzarewa Nusaiba ido, sannan ta tashi, saboda tare suke faɗuwa suke tashi da Iman a gida.


Kowa ya watse, daga shi sai iman, sai dai sun shafe lokaci, ba tare da wani ya ce uffan ba, mai sunan baba ya tashi, ya je ya rufe gidan.


Ya dawo falon, ya tarar da ita a in da ya bar ta a zaune, ya ƙarasa gabanta ya miƙa mata hannu ya ce "Ranki ya daɗe bisimillah"


A hankali ta kalli hannun nasa, amma ta kasa motsi, ya ƙara miƙa mata hannu.


A hankali ta miƙa masa nata hannun, ya riƙe ta, ta tashi tsaye ya ja ta zuwa ɗaya daga cikin bedroom ukun da yake falon.


Ya taimaka mata ta cire Alkyabbar jikinta, ya saka hannu ya ɗago fuskarta, fuskar tayi pink saboda kuka, sai jan mayafin take, tana rufe baƙin gashinta wuluk, da ya sha gyara.


Kallonta yake yi, wai wannan zuƙeƙiyar yarinyar ta sa ce, Alhamdilillah ala kulli halin.


Ya ɗan lumshe idonsa sannan ya buɗe su ya ce "Kukan me ki ke yi ne?".


Tayi shiru ba ta ce komai ba.


"Mu je mu yi alwala" ta jinjina masa kai, toilet ɗin cikin ɗakin suka shiga, ya kunna mata famfo ya ce "Bismillah" tare suke alwalar, sai dai da ya kai hannu idan hannunsu zai haɗu, sai ta janye nata.


Ya shammaceta ya ɗan watsa mata ruwan hannunsa, ta sunkuyar da kai tana murmushi.


Salla suka yi raka'a biyu, yadda mai sunan baba ya din ga kwararo addu'a ba ƙaramin burge Iman yayi ba, dan a rayuwarta tana ƙaunar namiji mai addini.


Bayan sun idar sun shafa, ya koma falo, ya shiga kitchen in da Mahmud ya ajiye kaji, da lemuka ya ɗaukko ya dawo ɗakin.


Gaba ɗaya a takure take, sai sunkuyar da kai take kamar mara gaskiya.


"Yaluwa, me zaki iya ci a nan?"


Murmushi ta yi ta ce "Yaya umar yaluwa kuma?".


Shima Murmushin yayi mata ya ce "Yeluwa mana, balarabiya a Nigeria".


"Idan Larabawa sauka ji ka babu ruwana".


Yayi murmushi ya tura plate ɗin gabanta ya ce "Bismillah"


"Na ƙoshi" ta faɗa a hankali.


Wata hamma ta kamata, tayi a hankali tana lumshe ido.


Ya ɗan ƙare mata kallo ya ce "Bacci ki ke ji zaki kwanta ne?" Da sauri ta ce"A'a".


Ya sake cewa "Bacci ko yunwa, wanne ne dalilin hammar?"


"Yunwa"


"Oya ci abinci" tamkar za ta nutse, haka take ɗan mintsunar naman tana kaiwa bakinta tana sunkuyar da kai.


Tashi yayi ya bata wuri, ya tafi gaban wardrobe ya buɗe, an shirya mata kayan sawarta, kuma duk ciki ba wanda aka ɗauka na lefenta aka ɗin ka.


Ya sauya kaya zuwa wata jallabiya, ya cire agogon hannunsa ya ajiye.


Ta nannaɗe sauran da ba ta ci ba, ta ajiye, ta tashi zata fita, ya ce "Ina zaki?"


"Can ɗakin zan je na kwanta"


"Mhmm, Ashe da bayan ɗaurin aure, sai ki yi zamanki a wurin ammi, nima na zauna a wurin mama. Dan na kusa yin kuka nima ɗazu kamar ke, bana son yaran nan su raina ni ne" tayi gajeriyar dariya.


Ya ce "wanko hannun ki zo"


Ta ce "To" ta shiga ta wanko hannunta, ta fito.


"Ki kwantar da hankalinki, ba abun da zan yi miki nima tsoro nake ji kamar ke, a gajiye ma nake kaina ciwo yake, i know what you are scared of, am scared too, ki shirya ki kwanta" wata irin Muguwar kunya ce ta kamata.


Har ƙoƙarin tuntuɓe take yi, ta nufi gadon ta kwanta.


"In baki bargo ne?"


"A'a yaya umar ai zafi ake yi "


"Shi hijjabin da kayan jikinki iska suke baki?"


"A'a"


"Trust me, ba abun da zan yi miki yanzu, nima tsoronki nake ji, ki sassauta kayan mana"


Da ƙyar ta canza kaya, zuwa wata doguwar rigar bacci, mai balance, ta raɓa da ƙyar da kwanta a bayansa.


Ba tare da ya waiwaiya ba ya ce "Kiyi Addu'a"


Ta amsa da "To"


Sai da ta tabbatar da gaske ba abun da zai yi mata, sannan ta yi bacci.


***
Rumaisa a gidan ammi ta so kwana, amma takawa ya ce bai yadda ba, tun da suka koma gida tayi wanka, take mitar ta gaji sosai.


"Papa ka yi mini sannu na gaji fa"


"Lokacin da nake cewa ki nemi wuri ɗaya ki zauna, ai baki ji ba"


"Mhmm, dan Allah kayi mini tausa to, ƙafata ciwo bayana duka jikina ma"


Takawa ya ce "Maganinki kenan"


"Wayyo mama na gaji, ka ce mini sannu"


"Ke ni tausayin ƙanwata ne ya dameni yanzu, ta shiga sabuwar Rayuwa Allah ya bata ikon jure ibada"


"Wai Iman, ai mai sunan baba ba irinka bane, na san ba zai mata abun da ka ke yi mini ba"


"Allah ko, saboda ga shugaban waliyyan ƙarshen zamani ko?"


Ruma har cikin zuciyarta ta ce "Allah da gaske nake, shi fa mai sunan baba babu ruwansa".


Ba ƙaramar dariya ta bawa Adam ba, kuma ita har ga Allah take gaya masa iya gaskiyarta.


"To ai shi idan ba ruwansa ke da ruwanki" da sauri ta ɓata fuska ta ce "Dan Allah wallahi bani da lafiya, gashi kuma na gaji".


"Lokacin da nake hanaki ai ba kya ji, maganin mara ji kenan" ba yadda ta iya da papa, haka ta ƙyale shi.


Bayan komawa bacci bayan sallar asuba, ringing ɗin wayarta ya sanya ta farka, murya ƙasa-ƙasa tayi sallama.


Nusaiba ta ce "Amarsu ta ango, baccin gajiyar ne haryanzu baki tashi ba?"


Iman ta ce "Bari Anty Nusaiba, gajiya fa akwaita"


"Ko a taho da ruwan zafi"


Kallon in da mai sunan baba yake kwance tayi, sai dai ya juya baya ta ce "Anty Nusaiba sai ka ce wata mai jego".


"To idan ba mai jego ba ce yanzu, nan da 9months dai an zama"


"Ina ammi?"


"Tana can tare da sauran baƙi, ita ta ce na kira ki ma, zaki yi baƙi wanda ba su samu zuwa jiya ba, za a taho miki da abinci"


Iman ta ce "To, Allah ya kawo su lafiya, ke ba zaki zo ba?"


Nusaiba ta yi dariya ta ce "Ai ruwan zafi na ce zan kawo miki, tun da kuma ba kya so shikenan"


Tayi dariya ta katse wayar ta ce "Allah ya shiryeki Anty Nusy"


"Ai da kin gaya mata ba ayi komai ba, tun da shi take son ji"


Gabanta ne ya faɗi, ba ta san idonsa biyu ba, ya juyo gaba ɗaya ya zuba mata ido, ta saka hannu ta rufe fuskarta.


Yayi murmushi ya janye hannun ya ce "Da kin gaya mata, duk a tsaroce ki ke, nima haka, duk tsoron juna muke ji, amma zamu iya nemanta da ruwan zafinta nan kusa ko nesa kaɗan".


Wato ba ƙaramin mamaki abun da mai sunan baban yake faɗa yake bata ba, bata taɓa zaton Wannan maganganun daga bakinsa ba.


Hular kanta da ta zame, ta bawa gashinta damar bayyana, ya shafa gashin ya ce "My pretty yellow. Tashi mu kintsa kan baƙin naki su ƙaraso".


Ta tashi zaune ta ce "In haɗa maka ruwan wanka ne?"


"Kar ki damu da ni, yi wankan ki"


Kafin Iman ta fito, cif ya ɗame gadon, gidan babu wani datti dama.


Kasancewar baya ɗakin, ya sanya ta saki jikinta, ta shirya ta fito ta same shi a falo, yana ta ƴan dube-dube.


"Yauwwa ƙaraso ki ga gidan naki, ɗan abun da talakan mijin naki yayi miki"


Ta ƙarasa ta ce "Ni wannan gidan ya fi mini kowanne kyau da tsari".


"Really?"


"Yeah"


"Jazakillah khair for appreciating it, Allah ya yassare mini in yi miki wanda ya fi wannan"


"Amin ya Allah" tare suka zazzagaya, ta din ga yabon gidan, da

Please Login or Register in order to submit comment