Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ga yaɓawa"


Usman ya ce "Dolenta ma kuwaa"


Aka ɗauko turare aka fesa mata, Usman ya ce "Ranar kamu ni zan kamaki, an ce da turare ake yi ko? Idan na din ga fesa miki, sai kin fara hayaƙi"


"Sai ka ce wata ita ce"


"Koma dai menene, ina sake jaddada miki, ki ka yi mini kwaɓa, da takalmi zan ladabtar da ke".


Ta kalli kanta a mudubi, ta ce "Kalli yadda ku ka mayar mini da ido, kamar wata sheɗaniya"


Yasir da yake zaune yana kallonsu yayi dariya ya ce "Koma dai wacece, idan ya zo, baby ka zo, you are welcome ya aiki? Ya family, kamar dai yadda ki ke gani a film, mussaman bollywood".


Ta buɗe baki ta ce "Taɓ, Allah ya tsareni, Bollywood ba taɓa mata suke yi da maza ba, wallahi ya taɓa ni, sai na gantsara masa cizo, babu namijin da zai taɓa jikina in tsaya ina kallonsa, ko a wurin ƴan bindiga, bana yadda, wallahi faɗa ake da ni" ga mamakinta sai ta ga gaba ɗaya sun tuntsure da dariya, Usman ya ce "Wannan bawan Allah yana ruwa, mama akwai buƙatar ilimantar da yarinyar nan kan aure"


Mama ta yi masa shiru, kamar ba ta ji ba, wanda a ranta tunani take yi, ta yaya za ta yi wa rumaisa bayanin wannan al'amari mai girma, yarinyar da ta tashi a kan iya abun da aka nuna mata shine dai-dai a gida, kome za ayi ba zata yadda ta canza ba, yanzu da an ce mata wani abu, tsaf za ta ce kenan da ƙarya ake yi mata.


Wata zuciyar ta ce "Ko da yake, ai ina ga zai ɗan ƙyaleta ta ƙara wayo, tun da saboda karatunta ma mamansa ta ce ayi auren'


'Namiji ne fa' wata zuciyar ta tunatar da ita.


Ta ɗan dafe kai ta ce "Yarinya ce, lokacin da aka yi mini aure, shekara sha biyar, na fi rumaisa girma sosai da sosai, amma lamarin aure abu ne mai faɗi"


Yasir ya ce "Mama magana ki ke yi ne?"


Ta ce "A'a kallonku nake yi dai".


Mai sunan baba ya shigo, hakan ya sanya duk suka yi shiru suka nutsu.


"Ke ki zo, ga mutumin can yazo, ki ɗau abun zama ki saka muku a soro, kar ki sake ki tsaya a waje, balle wannan iyayen saka idon su ganki".


Cikin rawar murya ta ce "Mama ni fa tsoro nake ji, gabana faɗuwa yake yi"


Mama ta buɗe baki tana kallonta, har idonta ya ciko da hawaye.


"To cinyeki zai yi?" Mai sunan baba yayi maganar yana tsareta da ido. Ta girgiza kai alamar a'a.


"To kukan uban me zaki yi? Wuce dalla, sai kin tayar mata da hankali haka kurum".


Huzaifa ya ɗau turare da darduma, ya ce "Bari na yi maza, na je shimfiɗa dardumar na fesa turare a soron, sai taho kina taku kamar gimbiya, dan gidan sarauta ba sa son hauma-hauma" ya ruga yayi soron da gudu.


Ya shimfiɗa, ya feffesa turare, ya dawo da sauri ya ce "To fito, ki ce masa ya shigo".


Ta fito tsakar gida zari silifas, za ta yi waje, Usman ya riƙeta "Wai ke rumaisa wace irin ƴar baƙin ciki ce? Yasin gidan sarautar nan sai kin je shi, ba zaki mana buƙulun zuwa gida mai kyau ba, canza wannan ɗan iskan takalmin, ko na cire shi, na tsinke ki da mari da shi, kuma idan ya shigo mintuna biyar, ki zo ki ɗauki kayan abincin nan ki kai masa, dole mu koya miki soyayya, dan ba zaki yi aure ayi miki kishiya ba"


Tana cusa baki, ta sauya wani ta fita, bagazan-bagazan ta leƙa wajen, ta ganshi a tsaye a jikin motarsa yana amsa waya.


"In ka gama wayar, ka shigo" ta faɗa tana riƙe ƙugu. Kamar bai san ta yi maganar ba, ya cigaba da wayar, ita kuwa ta koma soron, ta zauna ta mimmiƙe ƙafafuwanta.


Ya kai mintuna goma, kan ƙamshin turaren sa ya mamaye ilahirin soron, brown ɗin yadi ne a jikinsa, kansa babu hula, sai zuba ƙamshi yake, ta ɗaga kai ta kalleshi, kamarsa da Sabir ta sake fitowa sosai da sosai.


Ya nemi wuri ya zauna a kusa da ita, ta matsa can ƙarshen sallayar, tana kaɗa ƙafa.


Jin shirun yayi yawa, ba shi da niyyar magana, ya sanya ta ce "Ina wuni?" Ya kalleta ya yi shiru bai amsa ba.


"Ai dama na san ba amsawa zaka yi ba, dan a gida an ce in gaisheka ne, amma idan na gaishe ka, ba amsawa kake yi ba, ai ni na riga na gama sanin halinka kaf, daga A har Z"


Nan ma shiru bai amsa mata ba.


"Taɓ kana da aiki wallahi" ta juya masa baya, ta kalli wani wurin. Ya kalli bayanta, yana jinjinawa tsiwa da rashin jin ta, wai ta san halin sa daga A har Z. Can aka kwashi wasu mintuna, sai ta tuna abun da Usman ya ce mata ta tashi da sauri ta ɗauko kayan abinci nan.


Gaba ɗaya suka taso suna tambayarta yaya aka yi?


Ta ce "ba komai"


Usman ya ce "To, wallahi ki ka dawo da kayan Abincin nan, bai ci komai ba, to tabbss rashin mutunci ki ka yi masa, kuma zaki daku" ta gyaɗa kai, ta tafi soron ta tarar da shi, ta ajiye masa kayan a gabansa ta zauna ta ce "Ga abinci nan" ya ɗago ya kalleta ya cigaba da taɓa wayarsa.


"To, ni dai zan juya maka baya, ka ci, dan ba zan yi wahalar banza ba, tun safe ake azabtar da ni a gidan nan saboda zaka zo, zan juya maka baya, ka ci idan ba zaka iya ci a gabana ba"


Ta juya masa baya, ta ɗauko goruba tana ci.


A ransa ya ce "Na ga ta kaina ni Adamu, wai wannan ce matar da zan aura?"


Ta waiwayo ta ce "Wai ba zaka ci ba? To wallahi ba zaka ja mini duka ba.


Ta ɗauki coca-cola, ta tsiyaya a kofi, ta shiga hijjabinta ta sha, ta buɗe meat pie, ta ɗauki ɗaya, ta shiga hijjabinta ta ci, ta gutsuri wani ta ajiye ta ce "Yauwwa, dan ba zaka ja mini duka ba, an ce idan har na koma da shi ba ka ci ba, yaya usy zane ni zai yi"


Adam ya zubawa sarautar Allah ido, ita a rayuwarta ba ta san kara ba, idan ana neman mutum kai tsaye da ba ya rufi, to kowa ya bi bayanta.


Kamar wadda ta ci wani abun maye, ta takure abun ta, ta haɗa kai da gwiwa ta hau bacci, shi dai ikon Allah kawai yake kallo, wannan zance ya zo, ko kallon drama.


Ya mayar da hankali kan wayarsa, yana dannawa.


Usman da yake kaiwa yana komowa ya ce "Kai shirun nan yayi yawa, bari na duba"


Wata irin razana rumaisa ta yi "Iman!" Ta faɗa da ƙarfi, tare da faɗawa jikin Adam gaba ɗaya jikinta yana rawa, hakan yayi dai-dai da shigowar su Usman cikin rige-rige, domin ganin abun da yake faruwa, saboda ihunta da suka ji.


Ayshercool.
08081012143hi
*MAMAN MEENAT COLLECTION, MAMAN MEENAT SUPPLEMENT/SKIN CARE*


*SHIN YAR UWA KINADA LABARIN* *SHAHARARRIYAR MAI SAYAR DA SUPPLEMENT DIN NAN KUWA?*
*TO IDAN BA KI SANI BA KIYI MAZA KI GARZAYA DOMIN KEMA KI SAMU RABONKI DOMIN ZATA GYARAKI TSAF KI FITO KAMAR SABUWAR AMARYA, KEMA KI SHAGA CIKIN MATAN DA SUKE HASKAKAWA KAMAR TAURARO. SHIN ƘURAJE NE SUKE DAMUNKI, KO KUMA MATSALOLIN JIKINE KAMARSU RAMA BUSHEWAR FATA KARANCIN NI'IMA NE KO BUDEWA NE, KO KUMA INFECTION? KO KUMA SO KI KEYI FATARKI TAYI LAUSHI KIDIN GA SHEƘI KINA HASKAWA? TO MAZA KI GARZAYO WURIN MAMAN MEENAT DOMIN KI SAMUN MAFITA CIKIN SAUKI, ACIKIN FARASHI ME SAUKI*
*SANNAN YAN UWA KUSANI DUK* *SUPPLEMENT DIN DAZAMU KAWO MUKU SAI MUNYI BUNCIKE AKANSHI DAN TABBATAR DA INGANCINSHI MUN TABBATAR DA CEWA BASHI DA WATA* *MATSALA GA LFY, AKWAI MASU CEWA SUNSHA SUPPLEMENT AMMA HAR YANZU SU BASUGA WANI CANJI BA, TO YAR UWA KODAI AN BAKI FAKE KO KUMA BA'A BAKI WANDA YA DACE DAKE BA, KO KUMA BAKISHA YADDA YA KAMATA BA, DOMIN KISANI YAR UWA KAFIN KI FARA SHAN* *SUPPLEMENT AKWAI WASU KA'IDOJI DAYA KAMATA ACE KIN KULA DASU KUMA KIN KIYAYE, MATUKAR KINASO SUYI MIKI AIKIN DA KIKESO CIKIN SAURI, WANNAN KA'IDODIN SAI KIN NEMENI ZAN SANAR MIKI, DOMIN BAZAN IYA KAWOSU ANAN BA SBD SUNA DA YAWA*


*Yar uwa muna da duk wani supplement da kuke bukata masu kyau da inganci tested and trusted, sayen na gari mai da kudi gida, gaskiya da Amana shine takenmu 08039437158.*


👉 *Supplements suna da yawa amma ga kadan daga cikin su.*


*1. Supplements na gyaran jiki ciki da waje*


*2. Supplements na gyaran gashi da farce, dasa haske mekyau ba irin na bleaching ba*


*3. Supplements mai da tsohuwa yarinya anti aging wanda zaisa ki kullum ki koma kamar yarinya matashiya*


*4. Supplements na karawa fata kyau da sheki glowing skin*


*5. Supplements na masu fama da ciwon jiki da stress da rashin samun isashshen bacci*

*6. Supplements na masu ciki, da masu shayarwa wanda zai kara miki lfy keda babynki*


*7. Supplements na gyaran jiki da gashi, kara hasken ido da sauransu*


*8. Supplements me kara lfy da karawa garkuwar jiki karfi.*


*9. Supplements na karin ni'ima da dandano da tightening ciki da waje*


*10. Supplements na magance cututtuka, kamar matsalar ido ulcer, infection, karawa garkuwar jiki karfi, etc*


*11. Supplements na gyaran nono da mazaunai breast/hips Enlargement*


*12. Supplements na gyaran HQ ciki da waje*


*13. Supplements na rage tumbi slimming capsule/flat tummy Lipton*
*14. Supplement na whitening/glowing skin*


*15. Supplement for Acne, dark spots remover*


*Sannan ga wadanda sokeso jikinsu yayi kyau sosai amma basa son susha supplement to albishirinku muna da kowanne irin mai na gyaran jiki da kuke bukata irinsu lotion, cream, soap, scrubs, face Cream,sun screen, serums concentrate, hair oil, hair cream face mask etc, sannan ga masu fama da matsalar ciwon jiki wadanda kullum sai sunsha magani suke jin dadi ko iyaye ko kakanni, to albishirinku kuma mun kawo muku cream, soap na ciwon jiki masu kyau da inganci wadanda indai kana amfani dasu ka huta shan maganin ciwon jiki da yardar Allah*


*Muna saida duk wasu nau'in supplement Lotion da kuke bukata, sannan Maman Meenat collection ba anan kadai ta tsaya ba muna saida turaruka kowanne irin na wuta dana jiki, da Airfreshners, sayen daya ko sari ke dai kawai neme ni a wannan number call or chat 08039437158*.










Adam bai taɓa ta ba, sai bin ta da ya yi da kallo, idanuwanta na neman su kakkafe, sai daddagewa take yi, jikinta yana cigaba da tsuma.


Usman ya ce "Lafiya kuwa?"


Mai sunan baba kuwa wani irin takaici ne ya mamaye shi, ganin rumaisa a jikin Adam gaba ɗaya.


Takawa ya ce "Ban san meya sameta ba, gani na yi ta haɗa kai da gwiwa tana bacci, kawai ta zabura ta faɗo jikina".


"Iman! Iman ba ta da lafiya fa, Iman ba ta da lafiya" ta yi maganar cikin surutu da magagi.


"Wace kuma iman?" Mai sunan baba ya tambayeta a ƙule.


Haushi ne ya kama Adam, saboda yadda mai sunan baba ya raina wa kansa hankali, wai wace kuma iman, ya lura da yadda yake a ƙule, dan haka ya ture rumaisa daga jikinsa, ya ja da baya.


Mama tuni ta fito tsakar gida, dan jin abun da ya faru, amma ta kasa ƙarasawa soron, saboda jin nauyin adam.


Sosai take kuka tana neman abun riƙewa, "Iman fa, na gaya muku ba ta da lafiya"


Mai sunan baba ya saka hannu ya ɗagata tsaye, amma jikinta ya riga ya saki, tana neman ta faɗi.
"Ki buɗe idonki menene?" Ta sake rintse idanunta, kamar mai tsoron ganin wani abu.


Cak ya ɗagata ya shiga da ita cikin gidan, ya kwantar da ita a tsakar gida, gaba ɗaya suka rufu a kanta.


Adam har yayi niyyar tafiya, sai ya ga idan yayi haka bai kyauta ba, mussaman da ya ji tana ta ambatar sunan Iman.


Sallama ya yi ya shiga, ya tarar da su a kanta, mama tana girgiza ta, tana tambayarta menene.


Idonta dai a rufe, tana ta zubar da hawaye, ta ce "Iman, ba ta da lafiya sosai da sosai"


Mama ta ce "A'a jikinta da sauƙi ai, har an sallameta daga asibiti, tana gida".


Ta ɗaga hannunta ba tare da ta buɗe idon ba, ta ɗora shi a saitin zuciyar mai sunan baba, idonta a rufe ta ɗaga kai in da yake ta ce "Mai sunan baba, ka ji bugun zuciyarka, ai kai ka yadda ba ta da lafiya ko? Ku yi mata Addu'a dan Allah kar ta mutu".


Ya ce "To, kema ki yi addu'a"


Takawa ya ɗan yi gyaran murya ya ce "Ni zan tafi, Allah ya bata lafiya"


Mama da sai a yanzu ta lura da shi, ta ce "Yi haƙuri mai babban suna, wallahi tun da aka yi garkuwa da ita na kasa gane kanta, ina ga wani abun ta kwaso a zaman dajin da ta yi".


Adam ya ce "Allah sarki, Allah ya bata lafiya, abun ya bani mamaki, lafiya take zaune, ta ce idan ban ci abincin da ta kawo ba, an ce za a zaneta, da ban ci ba sai ta ci, ta ce ba za a gane ba, sai ta haɗe kai da gwiwa tana bacci, shikenan kuma ta fara ihu" yayi maganar cikin ƙoƙarin wanke kansa, yadda gaba ɗaya ƙartan nan suka zubo masa ido,sun ga ƙanwarsu a jikinsa, ga mai sunan baba sai muzurai yake yi.


Mama ta ce "Bakomai wallahi".


Usman ya ce "Lallai yarinyar nan baki da mutunci, dama zuwa ki ka yi ki ka cinye abincin?"


"Ba cinyewa na yi ba, dama ba na gaya muku ba zai ci ba, na san halin sa fa hmmm" ta yi maganar kamar wadda ta sha ta bugu.
Duk suka tsira mata ido, ta miƙa hannu tana yi wa adam nuni da ya zo.


Ba musu ya taka ya ƙarasa, ya sunkuya, ta riƙo rigarsa a hankali ta ce "Iman babu lafiya, kar ku zata da wasa nake yi, kar wani abun ya sameta. Kuma, kuma daga yau ba zan sake baka ko ruwa ba, yau haka aka din ga azabtar da ni, wai sai an yi maka girki kuma ka ƙi ci, to daga yau babu ni babu kai, tun da duka zaka janyo mini, sarki mai koriyar alkyabba " ta ƙarasa maganar tana murmushi. Sai kuma ta cigaba da zabura.


Ya kalleta ya ce "To, na gode, ba za a dake ki ba, zan tafi da abincin"


Ta kuma cewa "Yauwwa, wannan matar, da ta bamu ruwa ni da Sabir, ka tuna ta?"


Adam ya ce "Eh, na tuna"


"To ka san ta ce wai akwai gwagwarmaya a gaba, hmmm ba ka san fa me nake gani ba ko? To in gaya maka, wani abu na gani rannan a gidanku, kuma ma, wani zai je ya ɗebi turarenka baka sani ba, yauwwa har da maganin ka ma da ake shafa maka, ana nema".


Gaba ɗaya surutan da take yi babu ma'ana a wurinsu.


Mai sunan baba ya ce "Ya isa haka ki yi mana shiru"


Takawa kuwa ya ce "To, kin gama na tafi?"


"Eh ka tafi, amma fa kana tafe wannan matar tana binka, saboda tsabar taurin kanta, amma da kaina zan mayar da ita gurguwa"


Adam ya ce "Eh yakamata, yanzu dai ki cigaba da baccin, dama ammi ce ta aikoni, zan kira Aliyu a waya mu yi magana"
Ta ce "To" ta gyara kwanciyarta ta cigaba da barci.


Gaba ɗaya abun ya ɗaure musu kai, Adam ya ce "To mama sai anjima, Allah ya ƙara afuwa"


Suka amsa da amin, ban da mai sunan baba.
Usman ya ce "Ka tafi da abincin nan, ka cika mata alƙawarin ta".


Adam yayi murmushi, Usman ya bi bayansa.


***
Ko da ya ƙarasa gida, sashin Ammi ya wuce, dan gaya mata abun da ya faru, amma ya tarar ba ta nan, ya fito ya tambayi baba uwani, ta ce "Ai suna tare da iman, tana can tana ta fizge-fizge kamar za ta haukace".


What! Ya faɗa cikin tashin hankali, da sauri ya nufi ɗakin iman, sai dai ya je ya tarar da ita, a kwance tana ta Addu'a, ammi na ta shafa mata ruwa a ka, tana yi mata Addu'a, Nusaiba kuma na riƙe da hannunta.


Da sauri ya ƙarasa yana faɗin "Iman, me yake faruwa?"


Ta miƙa hannu ta riƙe nasa ta ce "Yaya Adam mutuwa zan yi, dan Allah ku yafe mini, nikaɗai na san me nake ji a kaina, baku san me nake ji ba, kaina kamar ana kafa mini ƙusoshi.


"Innalillahi wa Innalillahi raji'un" ya din ga maimaitawa, ya saka hannu ya janye piliown da take kai, ya kwantar da ita a kan gadon, ya din ga karanta mata duk addu'a da ta zo bakinsa, cikin ƙudirar Allah sai barci ya ɗauke ta.


Adam ya ce "Ammi, wai takamaimai me yake damun iman ne?"


"Takawa ina zan sani? Na ga na asibiti sam baya yi mata ma, na rasa in da zan saka kaina ma. To ya aka yi, kun tattauna ɗin, ya ka baro rumaisa? Ina son a satin nan idan iman ta warware a fara haɗa lefe, dan na turawa laila kuɗi, ta yi wasu sayayyar a can ƙasar"


"Babu lafiya" ya faɗa a hankali.


Ammi ta ce "Kamar yaya?" Nan ya kwashe komai ya gaya mata, ammi ta yi shiru ta ce "Ikon Allah, Adam akwai aiki ja a gabanmu, babban fatana yanzu shine in ga an yi auren nan, kuma bana fatan a ɗaga ko da rana ɗaya".


Adam ya jinjina kai Sannan ya ce "Bari na je na ga sabir, daga nan na wuce masallaci".


Tun da ya fita yake ta jujju
***
Rumaisa sai magariba sannan suka samu kanta, ta tashi daga wannan baccin, ba ta iya tuna komai ba, ta cigaba da sabgoginta.
Mama hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba, saboda gani take rumaisa aljanu ne ke son su hanata aure. Babu wanda yayi yinƙurin gaya mata abun da ya faru, suka biye mata aka cigaba da harkokin gidan kamar yadda suka saba.


Washegari Ammi ce ta kira mama da kanta a waya, tana tambayarta jikin rumaisa.


Mama ta ce "Jiki da sauƙi hajiya, na ce ko ɗaga bikin nan za ayi, a nema mata magani, alamu sun nuna iskokai suna damunta, kar ayi aure da larura".


"A'a maman rumaisa, Allah zai bata lafiya, wataƙila da an yi auren ta samu lafiya, wallahi kin ganmu nima iman haryanzu jiki yaƙi daɗi, na rasa abun da yake yi mini daɗi, ciwon kai ko sauka ba ya yi".


Shiru mama ta ɗan yi, kenan maganar rumaisa gaskiya ce?.


Mama ta ce "Allah ya basu lafiya baki ɗaya, in anjima zamu zo mu sake duba jikin nata"


Ammi ta ce "Ba sai kun wahalar da kanku ba, ayi mata Addu'a kawai".


Mama ta ce "Haba, ai babu wannan a tsakanin mu, bari ayi sallar magariba, rumaisa ta dawo daga islamiyya sai mu zo"


Ammi ta ce "To shikenan, ta samu ta ga ɗanta ma".


Bayan sun gama wayar, mama tayi ta Addu'a Allah ya sa ba aljanu ne suka buɗewa rumaisa ido ba, take gane-gane.


Da magaribar, tare da mai sunan baba suka je gidan su takawa, rumaisa na ta murna za ta ga Sabir.


Har ɗakin iman, aka yi musu izinin shiga, suka tarar da ita kamar mai shirin zarewa saboda surutai, duk suna kanta ciki har da Jabir.


Rumaisa ta ƙarewa ɗakin kallo, ta ce "Mama, ɗakin nan na yi mafarki fa jiya, ku cirewa iman pillown nan, mafarki na yi wata ƴar tsana tana soka mata allurai a kanta, yauwwa ba na ce muku iman ba ta da lafiya ba jiya?" Ta yi maganar tana ƙoƙarin tuna abun da ya faru jiyan.


Ammi ta ce "Rumaisa a ina ki ka ga ƴar tsanar?"


"Mafarki fa na yi, ki dafa pillown, ki karanta mata bisimillah da fatiha, amma dai wata ƴar tsana na gani a mafarki"


Abun sai da ya ɗaurewa kowa kai, Mai sunan baba kuwa tuni ya bar ɗakin, saboda yadda iman take, zaka san tana jin jiki ba kaɗan ba.


Ammi ta dafa pillown, ta karanto adduoi, Rumaisa ta riƙe hannun iman tana yi mata sannu.


Jabir ya tashi ya ce "Ammi, bari na je gida, Allah ya bata lafiya"


Suka amsa da Amin ya tafi.


Tattaunawa ammi da mama suka cigaba da yi, ammi tayi ta bawa mama ƙwarin gwiwa, a kan kar a fasa wannan auren.


Bacci iman ta samu, mama ta kalli Adam ta ce "Takawa, kai rumaisa part ɗina, ta ga Sabir, sai ka tambayeta abun da take buƙata na bikin"


Adam bai fiye yin jayayya da ammi ba, balle kuma yanzu da yake a gaban mutane ne, bai ce uffan ba, ya tashi ya fita, rumaisa ta bi bayansa tana murna, jin an ce za ta ga Sabir.


A hanyar sashin ammai, suka haɗu da baba uwani, cikin girmamawa ta risuna ta ce "Takarwarka lafiya magajin galadima, baƙuwa muka yi ne?"


"Eh" ya amsa a taƙaice yana fatan kar rumaisa ta yi wani shirmen, amma ga mamakinsa, ko kallon baba uwani ba ta yi ba balle ta gaishe ta.


Sai da suka yi gaba sannan ya kalleta ya ce "Baki iya gaisuwa bane?"


"Wa zan gaisar?"


"Matar da muka wuce, meyasa baki gaisheta ba? Gidan sarauta ba wuri ne da zaki gwada rashin ɗa'a ba, akwai girmamawa da karamci, ko da kuwa kai ne kake gaba da mutum"


Ba kunya ba tsoro ta ce "A hakan? Sau nawa na gaisheka a rayuwar nan baka amsawa, gidan sarautar da watarn wanda kake gaisarwa daban masu amsawa daban, ana ce maka an gaisheka ɗan talakawa, wannan ba wulaƙanci bane ba, ban kula kowa ba balle ayi mini wulaƙanci na ji haushi, ammi da wanda suke amsawa kawai zan din ga gaisarwa"


Wato ya fuskanci ita dai wannan yarinyar, defeating ɗin ta, ba abu ne mai sauƙi ba.


Sai da suka shiga ɗakin ammi, in da babu idon mutane, sannan ya dubeta ya ce "Idan ki ka cigaba da wannan taurin kan, ina gaya miki abu kina mayar mini da martani, zaki yi dana sanin aure a gidan sarauta, dan zai zame miki tamkar kurkuku mafi azaba, kowa zai yi ƙoƙarin yin amfani da ke wurin cimma burinsa, dole ki kiyaye".


Rumaisa ta ce "Na sani, gidan sarauta ba irin normal gida bane, ina gani a film, na indiya da sauransu, daga tsafi sai munafunci, abun ban tsoro, kowa ba abun yadda bane ba, da an ga baka da wayo, sai a cuceka, da ka yadda da wani, sai ya nemi ganin bayanka. Ai ni a duniyar nan kurku mafi azaba ita ce zamana a hannun 'yan bindiga, abu mafi razani kuma ganin mutuwar matar da ta bani kulawa kamar ƴar ta a lokacin da ake yi mini ƙamshin mutuwa. Abu mafi tsayawa a rai shi ne tunanin idan har gawarta tana da muhimmancin da za a kasheta a ɗau gawarta a mota a bar wurin da ita, saɓanin sauran mutanen da ake kashewa wurin, to waye ya saka ayi garkuwa da ita a kasheta, kuma ayi umarnin kashe ɗan ta? Abu mafi ban tausayi shi ne haihuwar jaririn da bai san komai ba, na din ga wahalar da shi da sunan kulawa, har koko na bashi, ya shafe kwanaki da ƙazantar haihuwa a jikinsa, bayan mun kuɓuta a ka yi yinƙunrin rabani da shi.
A tunaninka akwai wani abu mai wahalar mantawa kamar wannan? Ko wani irin ƙalubale ne, zan jure shi na rayu da sabir, kamar yadda na yi wa anty aisha alƙawari, amma ka ƙyaleni a yadda nake, ni ba ƴar sarauta bace ba, lokaci ɗaya ba zan iya zama irin ku ba". Tuni hawaye ya wanke mata fuska, ta taka a hankali ta ƙarasa gaban gadon Sabir, ya ƙara zama ƙato sosai, sai bacci yake yi.


Takawa kuwa kamar an gina shi, wasu gaɓoɓi ta taɓo masu muhimmanci, amma ya san yanzu da yayi yinƙurin ya cigaba da yi mata maganar, zata koma masa ainihin rumaisanta, ta fara rashin kunya.


Ta riƙe ƙafar sabir, tana kallonsa tana murmushi.


Adam yayi gyaran murya ya ce "Ammi ta ce, na tambayeki idan da abun da ki ke buƙata na shirin biki"


Maimakon ta amsa kawai sai ta hau dariya ta ce "Ni fa mantawa nake yi aure za ayi mini, ni bana buƙatar komai, su yaya Aliyu suna saya mini kaya, su mama kowa sai mini kaya yake yi".


Ya jinjina kai ya ce "Good, that's their part, a ɓangarena nake nufi, wanda ni yakamata na yi"


Ta girgiza kai ta ce "Za a saya mini komai, ni fa bana son ayi mini abu

Please Login or Register in order to submit comment