Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

yabawa ƙoƙarin sa.


Aka ƙwanƙwasa gate ɗin gidan, Umar ya je ya buɗe, ya ga Usman da Abdallah, da ledar viva a hannunsu.


"Mai sunan baba ko mu koma ne na ga kana kallonmu, mama ce ta bayar da abinci mu kawo" buɗe musu yayi, ya juya ya koma falon.


A kujerar da iman take ya je ya zauna, cikin murna Iman ta ce "Yaya usy sannunku da zuwa"


Usman ya ce "A'a ai mu yakamata mu gaishe ki, ina kwana antynmu"


Iman ta ce "Kai dan Allah har ka bani kunya"


Ya ce "Ai girmanki ne, dole a baki"


Ta shiga yi musu bangajiya, tare da tambayarsu ya mama.


Abdallah yayi ƙasa da murya ya cewa Usman "Ka tashi mu tafi, gulma ce a bakina, kar na yi misbehaving a samu akasi"


Usman ya ce "To mu tafi, nima ita nake son yi"


Suka tashi Abdallah ya ce "Bari mu tafi".


"Haba yaya Usman, daga zuwanku, ko ruwa ban baku ba"


"Bakomai ma sha a waje, tun da mai gida ya haɗe rai, baya buƙatar mu ne sai anjima"


Bayan sun fita ta ce "Yaya umar ka din ga dariya mana, ko smiling ne"


"Ban iya ba, tun da ke kina yi ai shikenan deejangala, bari mu karya ko, dan ni na fara jin yunwa".


Tare suka karya, duk ita duk a ɗarare take, tun da suka fara baƙi ya fice ya bar gidan.


Usman kuwa gulmar mai sunan baba suke yi, wai yadda ya wani zauna a kusa da Iman, wai shi mai gida.


Suna tafe rumaisa ta kira Usman, ya ɗaga ya ce "Ke kuma meye zaki dame ni?".


Ta ce "Daga kira me nayi maka to?"


"Ke rabu da ni, nima aure nake so rumaisa, ke kin yi aure, mai sunan baba yayi, Aliyu da yaya Habu suna hanya, jiya dan abun takaici, rige-rigen katifar mai sunan baba muka din ga yi, da tsofaffin kayansa. Kin ga yadda yake wani basarwa yau da muka je, wai shi maigida. Ke ma kina ta ƙarshe a gidanmu, amma ƙiri-ƙiri daga sunanki rumaisa an mayar da ke mimi, saboda aure, kallemu ni da Abdallah aka bawa kwanukan abinci muka kai musu. Allah ka aurar da ni, ko babyn nan a din ga ce mini"


Rumaisa dariya har da tuntsurawa, "Zaki yi dariya ne, wato ke kin tsallake, mijinki na ta lallaɓa ki, zuwa zan yi mu dai-daita da Hauwwaliya, daga baya mu yi kuɗi a tare, dama mutuniya ta ce, tun da yanzu mata sun fi son mai kuɗi muyi tuwona maina, kar na je na lalace"


Shi har ga Allah yake maganar, takawa da yake jin su ya ce "Usman idan ka lalace ina muka kama? ka samo mata, in dai aure ne zan yi maka na baka jari"


Usman ya ce "Subhanallah, Allah ya taimake ka dan Allah ka ce ba ka ji abun da na ke cewa ba, har kunya ta kama ni".


Suka yi tayi masa dariya.


***
Baƙi suka fara watsewa, saboda an kammala biki.


Gidan Iman ma mutane suka yi ta sintirin zuwa gidan ta, mai sunan baba yayi burus da ita, har ta ɗan sake daga tsoronsa da take ji.


Yau kiran sallar farko na asuba, ya tashi yayi nafilfilinsa da karatun Alkur'ani, ana daf da fara kiran sallar asuba, ya tashi da niyyar tashin Iman ta yi alwala.


Sai dai zancen ya canza, maimakon first night shi first asuba yayi, ƙarshe sai da hasken rana ya hudo, sannan sallar asubar nan ta yiwu.


Mai sunan baba kenan, komai nasa daban ne, sai dai kamar wanda ya yi laifi, duk ya diririce, mussaman ganin tana kuka.


Bayan ta idar da sallar asuba, ta kifa kanta a kan sallaya, a hankali ya kira sunanta "Khadija"


"Na'am"


"Ki tashi ki kwanta mana".


"A'a bakomai, ai gari ya waye ma"


"A'a ki kwanta dai ki huta, kina buƙatar wani abun ne?".


Ta ce "A'a"


"To tashi ki kwanta"


Ya ɗagata ya rakata kan gadon ta kwanta.


Har zai tafi ya ce "A cewa Nusaiba ta zo tayi aikin nata, ta kawo ruwan zafin duk da ma dai na yi da kaina".


Rufe fuska kawai ta yi ta, lumshe idonta tana murmushi.


Ƙiri-ƙiri mama ta kira mai sunan baba, ta ce masa maƙwabta za su zo, amma ya ce kar su zo, ba ta jin daɗi.


Abun da Iman tayi tsammanni, da kuma wanda mutane suke jiye mata, ba shi ta tarar a gidan mai sunan baba ba, mutum ne matuƙar kulawa.


Aikace-aikacen gidan kuwa ba ruwansa, tashi yake yayi abun sa, da ta motsa sai ya ce ta zauna ta huta, shi tausayin ta yake ji.


Ranar da zai koma kasuwa kuwa, shagwaɓa iri-iri a wurin Iman, kamar kar su rabu.


***


Ihun da rumaisa take yi ne tana salati, ya sanya takawa fitowa daga toilet a hargitse, ya nufota.


"Menene lafiya?"


Ya tarar da ita bacci take yi, tana ta fizge-fizge tana son ta tashi, ta ɗaga murya tana "La'ila ha illa anta subhanaka inni kuntu mina zalimin".


Da sauri ya ɗagata ya din ga karanta mata adduoi, yana tofa mata, ko da ta buɗe ido ta ganshi, ta saka ihu ta ƙwace tana haki.


"Mimi lafiya kuwa? Menene?"


"Ba kaine ka zo idonka na hayaƙi ba, zaka huda mini cikina da faratanka ba".


Gabansa ne ya faɗi ya ce "Ni kuma mimi?".


Eh mana tayi maganar hawaye sharkaf fuskarta.


Jiki a sanyaye ya ce "Mafarki fa ki ka yi, ni ina banɗaki".


"Da gaske mafarki ne, ba ka fasa mink cikin ba?"


"Duba ki gani".


Ta shafa cikin ta ta ce "Ni fa tun ina gida nake mafarkin idonka na ci da wuta, zaka soka mini farce a wuy, har a gaske fa watarn idonka yana yin hayaƙi"


Ya ɗan yi jimm sannan ya ce "Ki yi addu'a ki cigaba da baccinki mafarki ne"


Ta ce "Ba zan iya ba tsoro nake ji"


Ya rungumeta ya ce "Ki yi ta Addu'a"


Yayi shiru yana tunanin kenan rumaisa ciki ne da ita? In dai Aisha tayi irin wannan mafarkin, to ɓari take yi, amma rumaisa ta ce masa tun a gida take irin mafarkin.


Wata guda da auren su Iman.
Mai sunan baba bai taɓa zaton zai iya zagewa ya yi soyayya haka ba, babban abun da yake ƙara masa son Iman bai wuce matuƙar biyayyarta ba, da soyayyar da take yi wa mama, da ƴan uwansa ba, dan haka yake ƙara iya ƙoƙarin sa wurin ganin ya kyautata mata.
Tuni ta cigaba da zuwa makarantar ta, wasu lokutan kan ta dawo ya zo gida ya rage mata aiki, ranar kuwa da zata kai shida a makaranta, har makarantar yake zuwa kai mata abinci babu ruwansa.


Ƙawayenta suna yawan faɗa mata, tayi dacen miji mai son ta. Idan za ta tafi makaranta idan ba zai samu kai ta ba, shi ne yake bata kuɗin mota.


Tana zaune a falo da daddare tana shige -shigenta a system ɗin sa, tana typing ɗin wani assignment, ya fito daga bedroom ya kwanta a kan kujerar da yake, ya ɗora ƙafafuwansa a kan cinyarta ya ce "Me ki ke nema a computer ta?"


Ta shagwaɓe ta ce "Dubawa nake ko zan ga hoton ƴan mata"


Dariya yayi ya ce "Ni ina ruwana da wasu ƴan mata, ke ma dan kin liƙe ne ki ka same ni"


"Ko kuma mun liƙe ba" tayi maganar tana tura baki.


Tashi yayi zaune ya rungumota jikinsa ya ce "Na yadda ni na liƙe, tun a kallon farko da na ganki, na zata ma da aljana ce za ta aure ni, ashe ƴar autar ammi ce"


Tayi dariya ta ce "Ni fa da tsoro ka ke bani my, i just felt for you, ashe duk fasa aurena da ake a baya rabonka ce ni, Alhamdilillah for having a good husband like you my faruk" tayi maganar tana shafa sajensa


Murmushi yayi yana jin wata annashuwa, da soyayyarta na ratsa shi, ya sake rungumeta ya ce "Deejana, my pretty yellow girl, gaskiya kina so na da yawa".


"To ka ce kana so na nima"


Wata ƴar dariya ta bashi, ya ce "Ɗaukko carbi, ina faɗa kina lissafawa, har sai kin ji kin gamsu da ina son ki"


Iman ta sake narke masa ta ce "Ni waƙar soyayya ma zaka yi mini"


"Taɓɗijan, ai muryata ba ta waƙa ba ce, ban ma iya ba deeja"


"Muryar ka ta tsorata mutane ce" tayi maganar tana yi masa dariya.


"Eh ai an fi son haka, monster haka ba raini, tashi mu je mu kwanta, zaki school gobe in Allah ya kaimu"


Ta ce "To, bari na kashe system ɗin"


"Ahh, Baby an yi maka Gmail"


Mai sunan baba ya ce "Ba zaki daina babyn nan ba ko? Baby kamar ɗan daudu, gara ki ce mini faruk ɗin ai".


"Ai a waje ne ake maka kallon monster, ni a wurina babyna ne"


"Daɗinta ke ma a da monster ki ke gani ai".


"Eh yanzu kuma baby ba" tayi maganar tana duba Gmail ɗin.


Message ne a kan ana nemansa a Lagos zai je interview.


Ya ce "Anya wannan message ɗin nawa ne? Bana tunanin nawa ne"


"To na waye, naka ne mana"


Zai yi magana sai ga message ɗin Mahmud.


"An kiramu interview lagos, ban sani ba ko ka ga message ɗin, ranar Sunday zamu tafi, za ayi interview Monday, mun samu aikin nan"


Nunawa Iman yayi yana cigaba da mamakin abun, tamkar dai mafarki.


Iman ta din ga murna, tana addu'a, tamkar tun farko ba ta san zancen ba.


***
Duk da haryanzu bai gama komawa cikin nutsuwarsa gaba ɗaya ba, amma yayi ƙiba sosai abun sa, da gani ya samu nutsuwa sosai yanzu.


Sallama da aka yi a office ɗin ce ta sanya ya ɗago, ya amsa sallamar.


Jamil ne ya shigo fuskar nan babu annuri, shi ma Adam ya haɗe fuska yana jiran ya ƙaraso.


"Wurinka na zo"


"Ina saurarenka"


"Zuwa na yi na ji ina ka tsaya"


"Ina tsaye a in da ka sanni"


Jamil ya ce "Magana nake so mu yi ta fahimta, zuwa yanzu yakamata ace ka kammala binciken da zaka yi, ka wanke ni daga zargi da kuma zullumin da ka jefa ni a ciki kai da matarka".


"Jamil a kan me zaka yi zullumi, idan har ka na da gaskiya? Ka cigaba da harkokin ka kawai"


"Ba zai yiwu ba Adam, ya zama dole ku wanke ni, kuma ku tabattarwa duniya, bani da laifi".


"Jamil kana bani mamaki fa, ni da na dawo ban tayar maka da hankali na cigaab da bibiyar matata a kan lallai ka samu wasu bayanai ba, sai yanzu zaka zo ka cigaba da titsiyeni?"


"Dole in titsiyeka Adam, tun kan ayi mini wani sharrin, ka je ka ce mata akwai filin mai girma turaki, da ya sanya sunan aisha a matsayin magajiyarsa, ta na nema ta fara yi mini barazana da haka, ta sake ƙulla mini sharri"


"Duk da ba ka cigaba da bibiyarta ba, she won't go this far, amma duk abun da rumaia ta sanya a gaba, akwai ƙamshin gaskiya a cikin sa, dan haka ka fitar mini daga office"


"Adam ni ka ke kora daga office ɗin ka?"


"Na kore ka ɗin, a duniya ban taɓa tsammanin kai da Jabir zaku yi mini abun da ku ka yi mini ba, dan haka ka fitar mini daga office ".


Ringing ɗin wayarsa ya dakatar da shi da cigaba da magana, ganin kira daga makarantar su rumaisa, ya ɗaga kiran yayi sallama.


Shugabar makarantar su ta ce masa sun kai rumaisa asibiti tana ciwon ciki.


Bai sake bi ta kan Jamil ba, ya fice daga office ɗin.


Mai sunan baba kuwa har gari ya waye, yana doubting idan maganar nan gaskiya ce, sai da ya je gida ya samu Mahmud, Mahmud ya tabattar masa da hakan.


Ya tafi gida ya je ya sanar da mama halin da ake ciki, suka din ga murna suna yi masa Allah ya sanya alkhairi, shi dai ganin abun yake yi kamar wasa.


Laila kuwa sun fara shiri ita da yaranta da maigidanta, na komawa canada, maigindata sai nanata mata yake yi, ta je gidansu rumaisa yana nan yana jiran Yasir, zai fara laluba masa gurbin karatu a canada, da result ɗin sa ya zama ready a sanar da shi.
Mama ta rasa wane ɓangaren ma yakamata ta yi wa godiya ne, duk dai a sanadin rumaisa alkhairi sai samun ƴan uwanta yake yi.


Ruma kuasan tafi kowa shiga damuwa da komawar anty laila, saboda ko ba komai su yi faɗa su yi daɗi sun shaƙu ba kaɗan ba, tallafi rayuwar aurenta, ta wayar mata da sosai da sosai, ta fitar da ita daga cikin duhun da tsananin kunya da yi mata kallon yarinta, ya sanya mama kasa yi mata bayanin menene shi kansa auren.


Takawa ya je har asibitin da aka ce masa an kai ruma, ya tarar da ruma an saka mata ruwa tana bacci, likitan ya ce masa yana kyautata zaton food poison ne, dan bai san matar aure ba ce ba.
Ruwan yana ƙarewa, ya biya duk abun da aka kashe, ya ɗauke ta suka tafi gida.


Ya din ga yi mata mita a hanya, ko ciye-ciyen ta ne ya sanya ta haɗu da ciwon ciki, dan kwanan nan ciye-ciyen ya fi na kullum.


Sai dai da suka koma gida zuwa magariba, ta din ga amai ba ƙaƙƙautawa, dole ya ɗaketa ya mayar da ita asibiti.
Asibitin da suke da ganin likita ne, aka basu scaning suka yi suka kai wa likita, a nan ya tabbatar da rumaisa ciki ne da ita, har wata uku.


Ta rufe fuska ta ce "Na shiga uku"


Farincikin Adam ya kasa ɓuya, yayi ta yi wa likitan godiya, sannan ya ɗaukkota zuwa gida.


"Yanzu fisabilillahi da cikin ki ka din ga wannan hidimar da bikin nan, Allah ne ya rufa mini asiri baki watsar mini da shi ba".


"Ni fa ba wannan ne ya dameni ba, kawai kuma sai a ganni da ciki? Kuma sai in din ga zuwa makaranta da ciki, Ammi da mama ma su ganni".


Ya ce "Ammin da ki ka cewa na ce zan ƙara aure dan baki da nono"


Ruma ta ce "To duk ba kai ka janyo na faɗa ba, lokacin ban san abubuwa ba, kai kuma ka yi ta yi mini gori, ai maman Khadija da maman ilham sun kankaro ni".


"Suwaye hakan?"


Nan ta kwashe komai ta gaya masa, duk yadda aka kai ga sirri da ruma, idan hira tayi daɗi ita da takawa, sai ta kwashe komai ta gaya masa.


"Wannan kunun da ka ga ina sha na garin kunun sabayar maman Khadija ce, ƴar zariya ce, har kwatancen gidanta na sani bayan Federal Palladan 08033411249.
Maman Khadija kuma a no. Ai kawo road Kaduna 0813 561 3021. Tun daga zariya da Kaduna anty laila take sayo mana kayansu, a kawo mana har kano, ta haɗani da su ma in gaya maka, kai zaka cigaba sa saya mini"


Ya ce "Haba nifa in ce, dare ɗaya in ga abubuwa sun sauya haka, lallai madalla da wannan bayin Allah, dan ni suka kankaro ba ke ba, dole a cigba da sayabai".


"Yauwwa papan, ai na san ba zaka bani kunya ba"


Ya yi dariya, sannan ya din ga yi mata nasiha a kan kula da addu'a da zama da alwala, saboda irin akasin da aka din ga samu lokacin Aisha tana ɗauke da juna biyu. Ya kuma din ga lallaɓata tare da magiya a kan dan Allah kar ta bari kowa ya san da cikin nan, su yi shiru da bakin su, ta ce masa in sha Allah ba zata faɗa ba.


Abu kamar wasa mai sunan baba suka je interview shi da Mahmud, suna zuwa yadda yanayin abubuwan suka kasance, kai ka san akwai sanya hannun wani babban, dan babu wata shan wahala, dan shi bai ɗauki abun serious ba, dan cike link ɗin ma kawai dai dan Mahmud ya dame shi ne.


Offer sa ta fara aiki aka buga aka bashi, aka yi posting ɗin sa Lagos, with salary of 740k per month, kasancewar da phd in accounting aka ɗauke shi, Mahmud kuma aka yi posting ɗin sa port hacourt.


Sai jikin mai sunan baba yayi sanyi sosai, ya shiga lissafin yadda zai baro kano, ya bar matarsa da mahaifiyarsa, auren da ko watanni biyu ba su cika ba, ga ta ba cikakkiyar lafiya ba, ya baro ta, dama ta gama makaranta ne, sai kawai su tafi shi ban da katsina ma sai service da ya yi a Naija state, ban da haka ba wani dalili da ya taɓa raba shi da kano.


Rumaisa ba ta son tana cikin kallonta, takawa ya canza mata tasha, ya ce labarai zai kalla ko kuma ball. Sai dai yau ɗin ma haka ne, ya ƙwace mata remote ya canza tasha, kuma ya kwanta mata a kan cinya, ta haɗe rai tana tura baki.


Hira ake yi da senator Usman wakili a tashar, a kan ayyukan da zasu yi wa al'umma, muddin aka ba su dama aka zaɓe su, da kuma tabattar wa da mutane idan aka zaɓi ɗan sa ma, akwai tarin alkhairi da kyawawan ayyuka.


Tsaki yayi ya canza tashar, rumaisa ta ce "Meyasa ka canza tashar?"


Nan ya shiga bata labarin, tsamar da ke tsakaninsa da wakili, da yadda yana tsaka da bincike a kan sa, incident ɗin Aisha ya faru, hakan ya ɗauke masa hankali daga cigaba da bikcikarsa, duk da shugaban ƙasa ya kafa kwamitin bincikarsa amma babu wani kyakykyawan result, ƙarshe ma aka din ga cewa siyasa ce kawai, dan an ga za su tsaya takara hukumar DSS ke ƙoƙarin tozarta shi.


"Papa wakilin nan, sunan gari ne ko sunan mutum?"


"Oho musu, ina ga sunan family ne, da zarar na gane suwaye SMOKE, ko ban gano ba, zan cigaba da aiki a kan sa, bai dace da jagorancin al'umma ba"


A hankali ta furta "Tsakar dare, bayan anty Aisha ta fara rashin lafiya. Sha tara ya ce; wakili ko wakilin tsiya. Yakamata su yi magana a san yadda za ayi da matar nan, ban taɓa jin tausayin wani abu kamarta ba, ko dan cikin nan, ga waccan ƴar bala'in ta hana mu sukuni".


Still a bayanin da mutumin nan da yayi mata, wanda ya saya mata kaza da za su katsina, lokacin da ta tambaye shi ya aka yi suke da bindigogi da yawa, bayan jami'an tsaro ne kawai suke da ikon mallakar su? ya ce 'Yadda ake ware kason kula da harkar tsaro a ƙasar nan, haka ake ware mana namu kason makaman da ake sayowa na yaƙi daga waje wanda za a bawa sojoji, mu ma a bamu namu.
Ko da ta tambayeshi ya ce mata ita yarinya ce ba zata gane ba.


Bayanan nasa yayi dai-dai da bayanan da dattijon bafulatanin da aka ƙona rigar su, wanda ta tarar da shi shikaɗai, ta tsitsiye shi da tambayoyi yake gaya mata wasu rikice-rikicen da ake yi a wasu yankunan, yana da alaƙa da gano ma'adanai a yankunan, domin kawar da hankalin mutane, sai a ƙirƙiri tashin hankali a yankin, wasu tsirarin mutane su din ga kwashe ma'adanan, suna azurta kansu, wanda hakan ba zai yiwu ga karabutin mutum wanda bai san kan yadda za ayi amfani da ma'adanan ba. Wanda still wannan dattijon, shi ma a kan idonta, ya kai wa su sha tara makamai. Babban abun da ya bata mamaki bai wuce yadda mutumin yake ɗibar yanayi da iman ba.


'Anya ban makara wurin sanar da takawa wasu abubuwan da na sani ba?'


'Baki makara ba, alƙawarin da ki ka yi wa aisha ki ke ƙoƙarin saukewa, wanda ko a yanzu cikin kashi ɗari, kin cika tamanin da biyar!!!








*MASU BUƘATAR DOCUMENT, YOU CAN START MAKING YOUR PAYMENT, CIKIN SATIN NAN ZAI ZAMA READY IN SHA ALLAH 1K VIA 0009450228, AISHA ADAM JAIZ BANK BOOK2&3 KO KU TUNTUƁE NI A KAN LAMBAR WAYATA 08081012143 NA GODE*


Ayshercool.
O8081012143
WHAT'S APP ONLY PLEASE 🙏🥺
*MAMAN MEENAT COLLECTION, MAMAN MEENAT SUPPLEMENT/SKIN CARE*


*SHIN YAR UWA KINADA LABARIN* *SHAHARARRIYAR MAI SAYAR DA SUPPLEMENT DIN NAN KUWA?*
*TO IDAN BA KI SANI BA KIYI MAZA KI GARZAYA DOMIN KEMA KI SAMU RABONKI DOMIN ZATA GYARAKI TSAF KI FITO KAMAR SABUWAR AMARYA, KEMA KI SHAGA CIKIN MATAN DA SUKE HASKAKAWA KAMAR TAURARO. SHIN ƘURAJE NE SUKE DAMUNKI, KO KUMA MATSALOLIN JIKINE KAMARSU RAMA BUSHEWAR FATA KARANCIN NI'IMA NE KO BUDEWA NE, KO KUMA INFECTION? KO KUMA SO KI KEYI FATARKI TAYI LAUSHI KIDIN GA SHEƘI KINA HASKAWA? TO MAZA KI GARZAYO WURIN MAMAN MEENAT DOMIN KI SAMUN MAFITA CIKIN SAUKI, ACIKIN FARASHI ME SAUKI*
*SANNAN YAN UWA KUSANI DUK* *SUPPLEMENT DIN DAZAMU KAWO MUKU SAI MUNYI BUNCIKE AKANSHI DAN TABBATAR DA INGANCINSHI MUN TABBATAR DA CEWA BASHI DA WATA* *MATSALA GA LFY, AKWAI MASU CEWA SUNSHA SUPPLEMENT AMMA HAR YANZU SU BASUGA WANI CANJI BA, TO YAR UWA KODAI AN BAKI FAKE KO KUMA BA'A BAKI WANDA YA DACE DAKE BA, KO KUMA BAKISHA YADDA YA KAMATA BA, DOMIN KISANI YAR UWA KAFIN KI FARA SHAN* *SUPPLEMENT AKWAI WASU KA'IDOJI DAYA KAMATA ACE KIN KULA DASU KUMA KIN KIYAYE, MATUKAR KINASO SUYI MIKI AIKIN DA KIKESO CIKIN SAURI, WANNAN KA'IDODIN SAI KIN NEMENI ZAN SANAR MIKI, DOMIN BAZAN IYA KAWOSU ANAN BA SBD SUNA DA YAWA*


*Yar uwa muna da duk wani supplement da kuke bukata masu kyau da inganci tested and trusted, sayen na gari mai da kudi gida, gaskiya da Amana shine takenmu 08039437158.*


👉 *Supplements suna da yawa amma ga kadan daga cikin su.*


*1. Supplements na gyaran jiki ciki da waje*


*2. Supplements na gyaran gashi da farce, dasa haske mekyau ba irin na bleaching ba*


*3. Supplements mai da tsohuwa yarinya anti aging wanda zaisa ki kullum ki koma kamar yarinya matashiya*


*4. Supplements na karawa fata kyau da sheki glowing skin*


*5. Supplements na masu fama da ciwon jiki da stress da rashin samun isashshen bacci*


*6. Supplements na masu ciki, da masu shayarwa wanda zai kara miki lfy keda babynki*


*7. Supplements na gyaran jiki da gashi, kara hasken ido da sauransu*


*8. Supplements me kara lfy da karawa garkuwar jiki karfi.*


*9. Supplements na karin ni'ima da dandano da tightening ciki da waje*


*10. Supplements na magance cututtuka, kamar matsalar ido ulcer, infection, karawa garkuwar jiki karfi, etc*


*11. Supplements na gyaran nono da mazaunai breast/hips Enlargement*


*12. Supplements na gyaran HQ ciki da waje*


*13. Supplements na rage tumbi slimming capsule/flat tummy Lipton*
*14. Supplement na whitening/glowing skin*


*15. Supplement for Acne, dark spots remover*


*Sannan ga wadanda sokeso jikinsu yayi kyau sosai amma basa son susha supplement to albishirinku muna da kowanne irin mai na gyaran jiki da kuke bukata irinsu lotion, cream, soap, scrubs, face Cream,sun screen, serums concentrate, hair oil, hair cream face mask etc, sannan ga masu fama da matsalar ciwon jiki wadanda kullum sai sunsha magani suke jin dadi ko iyaye ko kakanni, to albishirinku kuma mun kawo muku cream, soap na ciwon jiki masu kyau da inganci wadanda indai kana amfani dasu ka huta shan maganin ciwon jiki da yardar Allah*


*Muna saida duk wasu nau'in supplement Lotion da kuke bukata, sannan Maman Meenat collection ba anan kadai ta tsaya ba muna saida turaruka kowanne irin na wuta dana jiki, da Airfreshners, sayen daya ko sari ke dai kawai neme ni a wannan number call or chat 08039437158*


Paid book ne, ₦500 via 0009450228, aisha adam jaiz bank, sai shaidar biya ta 08081012143, ga masu buƙatar vip post, suna iya garzayawa arewabooks su yi searching sunan book ɗin. Kar ku manta da subscribing YouTube channel ɗinmu na Cool hausa novels, domin samun daɗaɗan litattafan hausa na sauraro, ciki har da ƙanwar maza da yake daf da fara zuwar muku a kan channel ɗin*


https://www.youtube.com/@CoolhausaNovels


Susbcribe my YouTube channel please 🙏


*TALLA! TALLA!! TALLA!!!
*ƊANƊANO DAGA LITTAFIN NAZEEFA SABO NASHE, MAI SUNA ƘUDURAR ALLAH*


Ta Yaya zai zama jinina alhali ni na san bayan matana ban tab’a kusantar wata mace ba?” Ya furta kai tsaye yana kallon likitan da sakamakon gwajin yake hannunsa. Likitan yana jinjina kai ya sake furta “Tabbas Jaheed jininka don gwajin k’wayar halittarku da komai ya tabbatar kai ne mahaifinsa kafin a kai ga haka ma ko Kamanninku da suka zamo kwabo da kwabo sun tabbatar da Hakan koda Ba’a yi gwajin ba.”


Shiru na tsawon lokaci d’akin ya d’auka kowa da irin tunanin da yake a ransa ya kasa yarjewa zuciyarsa shine Mahaifin Jaheed duk da k’wararan shaidu. Abinda ya sani ko da wasa bayan matansa na aure na Sunna bai tab’a rik’ewa wata mace hannu ba, idan kuwa ya tabbata Jaheed d’ansa ne ta yaya ya samar da cikin nasa a jikin wacce aka kira mahaifiyarsa da ko a mafarki bai tab’a ganin mai kama da ita ba TABBAS AKWAI LAUJE CIKIN NAD’i. Mahaifiyar Jaheed ma Zata iya zama abar tuhuma da zargi. Kai tsaye zai iya cewa hakan zai iya zama K’UDIRAR ALLAH….


(*Ina

Please Login or Register in order to submit comment