Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

n'a tsaya ina kallon bakin kofar dakin ta, ina kallon gurinne sabi da tsananin tausayin ta danake Yi Sabi da masifar da ta tunkaro ratuwarta ganga Ganga.





Bayan shiga dakina, kwanciya ya nayi zanyi bacci Ashe ita ba bacci takeba takasa baccin, Wai kunsan maiyasa ta kasa baccin? Allah sarki baiwar Allah ,kawai Sabi da nace Mata I kiss you Kuma bansamu tayi min ba wannan dalilin ne ya hanata bacci, Ina kwance Ina nishadina sai jin bugun kofar ta nayi a hankula , da farko na tsora ta Amma Kuma sai na Dake nace "waye da cikin darennan za a damu mutane" siririyar muryar ta naji ta ce "yaya nice? Tana fadar Haka na gane wacece jikina a sanyaye nace "zarah lafiya bakiyi bacci ba?" "Yaya nakasa bacci burina kawai namaka abin da kake so bana jin dadi ace ka nemi Abu kuma nakasa yi maka" "uhm Zara,u kenan Babu komai kije ki kwanta" "a,a wallahi Yaya Ni sai na Yi maka" Babu yadda na iya Haka n'a taso jikina a sukwane n'a bude kofar ,matsa mata hanya nayi ta shigo sannan n'a Tura kofar, . Babban abin da nake tsoro shine yafaru a lokacin abin da zarah Bata sani ba shine inhar na soma kulafuci a kan Abu to Dole ne sai na sameshi domin Sha,awata halittace kamar yadda aka dasa a jikin kowane Dan Adam Nima Haka tawa take Amma tawa daban take da ta wasu, hannuna guda daya na daga na Dora a kan kafadar ta data kuma n'a saka shi a saitin mazaunen ta, na matseta a jikina na wajen "yan dak'iku, kafin daga bisani na Dora bakina a kan nasa ,cikin nutsuwa da solo irin n'a 'yan duniya bake kissing din bakinta kamar nasamu sweet.....


"Uncle! Uncle Fu ad!! Wallahi abbanmu yace idan bazaka zoba kayi ta zama ,Sabi da karainashi yakiraka ka zauna ,Haka Abba yace n'a fada maka"

Kamar saukar aradu yajiyo muryar Adeena tana kwalamasa Kira ,tsaki Fu ad ya daka ya ajiye littafin ya danyi shiru can Kuma ya lumshe Ido ya bude yace "Kai Amma Allah ya Isa wallahi sai da nazo daidai gurinnan za a katseni haba abbanmu yazakanin Haka ,Ni wallahi abin cinma har naji na koshi", Fu ad ya daka tsaki ya Mike tare da saka farar jallabiya ya bude kofa ya fito,yayi sama fuuuuuuu.

Tashin hankali wan da ba a samasa Rana abin da Fu ad ya manta shine Abba yace kada ya Bari Abeed ya ga wannan littafin gashi yabar kofar dakinsa a bude,



Abeed ne ta sakko daga dakinsa dan yadda yajiyo Adeena na kwala Masa Kira har sau uku tana zuwa tana cewa Abba Yana Kira Amma yaki fitowa, hakan yasa Abeed ya sakko domin yaga abin da Fu ad yake a d'akin har yaki zuwa Kiran da Abban Basu yake Masa,

Kai tsaye Yana zuwa d'akin ya shiga yayi sa a yasamu dakin a bude, bedroom ya huce ya Shiga dube dube , baiga komai ba kawai sai ya juyo zai fita, Nan take idanunsa suka hango Masa wannan littafin Dake bude a kan bed din fu ad, "innalillahi wa'inna ilaihirraju un! Abeed ya furta Hadi da cewa nashiga uku, take yaji jiri na Shirin kwasar sa , yayi saurin zama a kan bed din sharaf Yana kallon littafin idanunsa dauke da hawaye, hannunsa yakai kan littafin ya dakko yashiga shafawa Yana zub da hawaye masu zafi da dumi, "why Fu ad sirrina, Wai Mai yasa a gidan Nan akeson ayimin tonon siririne nashiga uku" Abeed ya fad'a tare da kifa kansa a tsakanin cinyoyinsa ,Nan take jikinsa ya dauki rawa yakaa ko motsawa daga gurin.



Shikuwa Fu ad bayan yaje Kiran da Abba yamasa tsabar zumudin ya cigaba da karanta littafin ,abin cinma karba yayi ya sakko da shi kasa ,Wai shi a nufinsa Yana cin abin cin Yana ci gaba da karanta littafin sa.


" Innalillahi wa'inna ilaihirraju un ! Ya furta lokacin da ya shigo dakinsa Bai San lokacin da yasaki a bincin ya kife a kasa ba, ganin yadda Dan uwana nasa ke kuka kamar ransa zai Fita, ga idanunsa dayayi jajur duk yazama abin tsoro, bakin fu ad har rawa yake wajen cewa "narantse da Allah Yaya Babu abin da nasani akai , yanzunan na Soma karantawa Dan girman Allah kayi hakuri Yaya" jikin Abeed a sanyaye ya Mike batare da yace Masa komai ba ya Soma takawa har sai da ya karaso gaban sa yace "so kake kaga komai ko, ko sokake kaji abin da yasa abbanmu ya tsaneni? Mezakayi da tarihin da ya shude , ko sokake kaji abin da Bai kamata kajiba, ban taba tunanin zaka iya daukar wannan littafin daga inda na ajiyeshi har ka ta ho dashi faransa, nayi tunanin daga inda labarin ya faru a inayan muka taso muka barshi, Ashe Kai so kake ka dawomin da ciwon da nakeso n'a manta a matsayin sabo" Abeed ya karasa maganar tare da goge hawayen sa ya dauki littafin ya fice dashi a hannunsa.


Shi kuwa Fu ad har lokacin jikinsa Bai daina rawa ba ,Sabi da tashin hankalin da yaga Ni a cikin idon yayan nasu, jiki a sukwane Babu kwari ya ja kafarsa zuwa bakin gadon ya zauna shaff ,tare da dafa Kai yace "innalillahi wa'inna ilaihirraju un! Innalillahi wa'inna ilaihirraju un !! Wallahi tsab zuciyata zata iya bugawa muddum ban karasa karanta littafinnan ba, domin ni yanzune nakarasaka Book d'in a zuciyata ban jin yadda na Soma karantawa Zan hakura da shi ba".


πŸ’”_____*DEPRESSION*_____πŸ’”
(DAMUWA)

*#CIN AMANA*πŸ’”
*#JURIYA*πŸ’”
*#SOYAYYA*πŸ’”
*#DAMUWA*πŸ’”
*#HAKURI*πŸ’”
*#YAFIYA*πŸ’”
*#KYRA*πŸ’”


*Chapter 13*

TO😌 TO😌 TO😌πŸ’ͺπŸ’ƒπŸ’ƒπŸ’ƒπŸ’ƒπŸ’ƒ DA KARFIN SA YAKE TAFE SHIN KIN SAN YADDA AKE TSANTSAR CIN AMANA KUNSAN YADDA AKE NUNA TSANTSAR SOYAYYA KARYA? KO KUNSAN YADDA ZUMA DA MA'DACI YAKE ,TO ALBISHIRIN KU MASU SAURARO MUTANEN ALKAIRI ,INA SON KU GYRA ZAMA DOMIN RAKASHE NI SHADIN GWANGWAGE KARATUN WANNAN LITTAFIN MAI TAKEN DEPRESSION (DAMUWA) 'YAR UWA KADA KIBARI ABAKI LABARI WANNAN SALON NA DABANNE DOMIN 'YAR'UWAπŸ’ƒπŸ’ƒπŸ’ƒπŸ’ƒπŸ’ƒπŸ’ƒ



🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼
_*DEPRESSION*_
*damuwa*
_*BY*_
_*HAFSAT UMAR ƊAN GORO*_
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼

_*JARUMAIπŸ’ͺ🏻WRITER'S ASSOCIATIONπŸ“š*_

_*Marubuciyar*_
1- Burina Mu'azzam
2- Ba Mahaifiyata bace
3- Babana ne sila
4- Ummu Amani
5- Amatullah
6- Zuciyarta
7- Mace Rayuwa
8- Rayuwar ƘasΖ™anci
9- Mar'atussaliha
10-Babbar sakayya
11-AFNAN
_And now_
πŸ’”_*DEPRESSION*_πŸ’”
*damuwa*
*BOOK one*

*Chapter 13*





***********




Abeed kuwa Kai tsaye sama yayi hannunsa dauke da littafin, abbanmu da sauran yan gidan suna zaune suna cin abinci suka ga hucewar sa da littafin a hannunsa ga hawaye a kwance fal a cikin idanuwansa, hankalinsune ta tashi ,da sauri Ammi ta Mike zata bi bayansa, abba ya dakatar da ita, kallonsu Adeena tayi Tace "Kai mai yasamu Uncle Dina?" "To Adeena Mai kika gani?" "Abbanmu kuka Naga yanayi ,Ni wallahi nagaji ku kullum bakwasan shi duk na fahimceku kullum kuntsaneshi sai kuyi tasashu kuka bansan Mai yayi muku ba" "to Adeena mudinne muka tsaneshi yanzu Kuma wakika ga yayi Masa wani abu Naga daga kasa ya hawo" "uhm uhm Allah ban Yar da ba Ni barima na tashi bazanci abincin ba ,dazufa da ker na rarrasheshi ya daina kukan yanzuma kun Kara sakashi kuka ko?"



"Kiyi hakuri my mommy anan gurin Babu wan da ya saka danki kuka ki daure kici abin cin kinji "



"A,a wallahi bazan ci ba" Adeena ta Mike zata bi bayan Abeed Abjeed ya ruko ta tare da daka Mata tsawa yace " ke ana Miki magana kina ke sai kin je to jeki din, kiga yadda zanyi kasa kasa Dake anan gurin".

Abjeed yayi maganar Rai a bace.


Gigicewa Adeena tayi ta fada kan abba tare da fashewa da kuka, cikin masifa abba yace "lafiyarka kuwa Abjeed ? Menene Haka dafa magana saΓ― kafara daka mata tsawa kabarta tatafi mana" "uhm abbana Kana fifita yarinyar nan bansan maiyasa ba , an hanata Abu ita ala Dole Tace sai tayi ,tabarshi yaji da abin da yake damunsa Mana ,haba dame zaiji da damuwar ka daina masa magana ko Kuma da takaicin nunawa Fu,ad inda litttafin sirrinsa yake,haba Abba nasan wallahi Babu Wanda zai fadawa Fu ad inda littafin Nan yake saikai,na rokeka Dan Allah ka barshi Haka, sokake ka dawo nasa da ciwon da ya Dade da warkewa, nayi imani Fu ad ya gana karanta littafin Nan ba Yaya Abeed ba hatta Kai da ammi kunshiga uku, to maiyayi zafi Dan Allah abin Nan ya isheni, Sabi da hakafa na tattara kayana na tafi Dubai sai gashi Kuna son dawo da sabuwar matsala" Abba dai shiru yayi ya kasa cewa komai, domin jikinsa ya karayin sanyi da wannan lamarin, tabbas Bai kamata ya sanarwa da Fu ad inda littafin Nan take ba ,shima ba Dan ra ayin kansa bane ya fada masane kawai dan ya daina ta kura Masa.


Abba Bai Gama tunanin da yake ba ya tsinkayo muryar fu,ad Yana cewa "akan Mai yasa ba ason nasani ,ko dai wani abun kuke boyemin ban sani ba? Abbanmu tun ba yanzu ba nake tambayarka asalin labarin abin da ya faru kaki ka saurareni balle ka fadamin ,ni maye lefina dannasan wannan labarin, shin ni ban cancanci nasani bane ake boyemin , da farko yaya Abeed n'a sameshi a daki na Yana kuka har da cemin so nake natona Masa asiri ,narasa gane Gaba daya inda kuka dosa ya kamata kuyi min bayani dalla dalla yadda zan gane" Fu ad Yana yimusu maganar idanunsa cike fal da hawaye, sannan ya ciga ba da cewa "da farko na fara karanta littafin , nagama saka Rai a ciki Yaya ya dauke book din to yanzu wa kukeso ya karasa karanta min?" "Nine " Abeed ya fad'a lokacin da ya fito daga d'aki idonsa na zub da hawaye "ba dai so kake kaji ba nine wan da Zan karasa maka, indai asirina kukeso ya tonu a shirye nake domin a yanzu duniyar batamin dadi sai zafi da kunci, yanzu nafi bukatar mutuwa fiye da rayuwa, bana son komai natsani duk wani Jin dadi na duniya, Fu ad! Badai labarina kakeson sani ba uhm karka damu zaka sani, kuma kaima ina mai tabbatar maka saikayi dana sanin karanta littafin sabi da....... " Bai karasa maganar ba yaji hannun Abjeed a bakinsa Yana hawaye shima Yana girgiza masa Kai alamar ya Yi hakuri kada ya fad'a , "Yaya Dan girman Allah kayi hakuri kada ka fada masa kabari kawai Tun da ka karbi littafin, "uhm Abjeed kenan ka sakeni nayi masa bayani Koda ace Ni ban fada masa ba watarana Dole ya sani, Kuma duk ranar da yasani zai kasance Yana Mai fishi da Ni da min Alla ya Isa duk lokacin da ya tuna Dani ko yaganni Koda ace bana Raye nasan sai tsinuwarsa da Allah ya Isa ta bini har kabarina ,Dan Haka ka barni n'a fadamasa komai Tun kan n'a mutu" "a,a dan Allah yaya ka daina fad'ar Haka ,idan Har ka Bari wannan mummunan labarin ta fito wallahi abbama bazai yafe maka ba" cikin tsawa Abeed yace "saΓ― mai shekara nawa tsawan shekaru da dama da suka shude abbanmu ya tsaneni Maine lefina ,ya manta duk wani bawa Bata tsallake kaddarar sa ,yamanta allane yake komai ,Ni kaina da ace Nina halicci kaina wallahi saina canza kaddarata Sabi da nafahimci banzo duniya a sa a ba, da ace Abba Yana sona kamar ku bazai so ace su Fu ad su karanta littafin Nan ba , shikkenan tun da Haka yakeso shima wani tarwatsewar family dinsa be"


Allah sarki Abba kwallar Dake kwance a idonsa ne ya karasa sakkowa ,lokaci guda yaji jijiyoyin kansa sun bayyana , Gaba ki daya tsoro da furgici ya Kama zuciyar Abba ,Sabi da tsabar tsananin zafin da kalaman Abeed sukayi Masa ,tabbas ya Fadi daidai Akan Fu ad sai dai dolene komai Daren dadewa komai ya bayyana.

Shikuwa Abeed Bai Gama karasa maganar Saba ya ga Fu ad ya yenke jiki ya Fadi, hannunsa ruke a daidai saitun ziciyarsa,


πŸ’”_____*DEPRESSION*_____πŸ’”
(DAMUWA)

*#CIN AMANA*πŸ’”
*#JURIYA*πŸ’”
*#SOYAYYA*πŸ’”
*#DAMUWA*πŸ’”
*#HAKURI*πŸ’”
*#YAFIYA*πŸ’”
*#KYRA*πŸ’”


*Chapter 14*

TO😌 TO😌 TO😌πŸ’ͺπŸ’ƒπŸ’ƒπŸ’ƒπŸ’ƒπŸ’ƒ DA KARFIN SA YAKE TAFE SHIN KIN SAN YADDA AKE TSANTSAR CIN AMANA KUNSAN YADDA AKE NUNA TSANTSAR SOYAYYA KARYA? KO KUNSAN YADDA ZUMA DA MA'DACI YAKE ,TO ALBISHIRIN KU MASU SAURARO MUTANEN ALKAIRI ,INA SON KU GYRA ZAMA DOMIN RAKASHE NI SHADIN GWANGWAGE KARATUN WANNAN LITTAFIN MAI TAKEN DEPRESSION (DAMUWA) 'YAR UWA KADA KIBARI ABAKI LABARI WANNAN SALON NA DABANNE DOMIN 'YAR'UWAπŸ’ƒπŸ’ƒπŸ’ƒπŸ’ƒπŸ’ƒπŸ’ƒ



🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼
_*DEPRESSION*_
*damuwa*
_*BY*_
_*HAFSAT UMAR ƊAN GORO*_
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼

_*JARUMAIπŸ’ͺ🏻WRITER'S ASSOCIATIONπŸ“š*_

_*Marubuciyar*_
1- Burina Mu'azzam
2- Ba Mahaifiyata bace
3- Babana ne sila
4- Ummu Amani
5- Amatullah
6- Zuciyarta
7- Mace Rayuwa
8- Rayuwar ƘasΖ™anci
9- Mar'atussaliha
10-Babbar sakayya
11-AFNAN
_And now_
πŸ’”_*DEPRESSION*_πŸ’”
*damuwa*
*BOOK one*

*Chapter 14*




Kuzo kuga tashin hankali wan da ba a samashi Rana , Gaba ki daya ilahirin mutanen dake gidan hankalin su yayi masifar tashi, abbane ya furta "innalillahi wa'inna ilaihirraju un! Innalillahi wa'inna ilaihirraju un !! Innalillahi wa'inna ilaihirraju un !! Fu ad" shikuwa Abeed zubewa yayi a kasa wanwar idanunsa, suba a lumshe ba su ba a bude ba yashiga zubar da hawaye Yana cewa "shikkenan abbanmu ,hankalin ka ya kwanta ,kagani ko Suma yayi yanzu ,to ka lissafa lokacin da yasan wannan labarin ya zaiji ,mutuwa zai ko uhm hankalinku ya kwanta, " itama Adeena tana gefe sai faman kuka take ganin yadda duk 'yan gidan suna kuka, jikinta a sabule ta Mike zuwa inda Abeed yake ta Kamo hannunsa ,saΓ― ta sakΓ© fashewa da kuka Tace "uncle maiya sameka, waye wan da ya saka ka kuka?" Dan Allah Uncle ka fadamin waye ya saka ka kuka ,nasan ba zai huce abbanmu ba ,kayi hakuri kaji " shidai Abeed kallonta kawai yake cike da tausaya wa yake kallon ta bakinsa yayi Masa nauyi yakasa cewa uffan sai dai kawai kallon ta da yake, sauran karfinsa Gaba daya ya tattaro ya Mike tsaye tare da karasawa idan fu,ad yake , d'ago kansa yayi still har lokacin baya motsi ,ganin Haka yasa Abeed ya sa hannu ya d'aukeshi daga kasan kamar wani karamin yaro, ya Soma tafiya Yana Dan tangadi, har ya fara sauka daga kan step d'in ,Adeena ce still ta sake binsa a baya tana kuka tana cewa "uncle meyasami uncle Fu ad ,ko dai ya mutu ne?" Batare da ya Bata amsar abin da ta tambaye Saba ya ce "ko ma ciki" ta bare Baki zata cigaba da kukan Abjeed ya daka Mata tsawa, take Tasha jinin jikinta ta koma , Abjeed ya bisu abaya har zuwa parking space na gidan, motar ya bude ya saka shi aciki ya rufe sannan ya dawo zai shiga cikin motar, shima jikinsa ya Soma rawa, a take jiri ya dauke shi ya zube a gurin, "innalillahi wa'inna ilaihirraju un! Innalillahi wa'inna ilaihirraju un !! Ammi ta furta lokacin da take Kara sowa gurin, take ta zube a gaban Abeed tana kuka kamar ranta zai fita tana cewa "shikkenan komai ya kare ,Daman abin da nake gudu kenan gashinan ai, ka kashemin su hankali ya kwanta" ta cigaba da kuka, Abba da ya biyo bayan ammi yaga abin da ya faru, take kafafuwan sa suka kasa daukar jikinsa ,lokaci guda yayi zaman dabaro Yana bon su da kallo" Abjeed kuwa yama rasa mai zaice domin idan gani yake kamar idan ya zauna zuciyarsa zata iya bugawa, share kwallar idonsa yayi Wanda ya kada yayi jajur, ya ce "shikkenan abbanmu ,hankalin ka ya kwanta, gasunan Zan tafi na barmaka su ,domin bazan iya jure irin wannan abin da akewa Yaya ba, zuciyata bazata iya dauka ba, idanuwa na sunyi nauyi da kallon irin wannan tozarcin, badai ya Abeed bane gashinan abbana kaci Gaba da nuna masa tsana, wallahi n'a tabbata idan hakan taci gaba da faruwa wataran zuciyar yaya zata buga ,kuma ni yanzu Zan tafi na bar gidannan kada Wanda ya nemeni Dan bazan iya zama inaji Ina gani a tona wannan mummunan abun a Gaba n'a ba" Yana Gama fadar Haka ya kalli hanyar fita ya Soma tafiya, abbane ya taso dashi da Adeena dagudu Adeena ta fad'a jikinsa tana kuka tana cewa "uncle Ina zaka Dan Allah kada katafi ,idan katafi wane zai nunawa uncle Dina soyayya , na fahimci kaikadai kake damuwa da damuwarsa Dan Allah karka tafi ka dakata" hannunsa ya duzge daga nasa ya cigaba da tafiya, Dan ko kallon inda Abba yake Bai Yi ba ,shima Abban rukosa yake Yana lallabasa Yana cewa "don Allah kada kace zaka tafi ,idan ka tafi waye wan da zai kula da Yan uwanka, Kai kadaine zaka iya taimakon mu a halin yanzu dan Allah ka tsaya" "abba bazan tsaya ba , lokacin da yaya yake rokanka ka saurare shi ,baka saurareshi ba nunawa Kai kamar ba ayin afuwa a duniya ,shi kamar ba danka ba alallai Dole Dan Allah ya jarafce shi saika tozar tashi, ita zaran wacece ,da shi da ita wane yafi kamata ka so ,kada ka manta shifa dankane na jini wan da ka Haifa da kanka , ba dakko shi kayiba ba sa daka Aka baka ba, ita Kuma zarah fa, wallahi Abba koka gaggauta canza halinka ko ka hadu da fishin Allah ,Kuma duk da Haka Allah bazai kyale kaba dolene sai an maka hisa bi da Yaya Abeed ,Dan ya aikata wani abun Bai kamata a ce ka hanzartar da rayuwar sa ba, dan Haka ni Baby ruwa na kaje indai sune ,gasunan kamar yadda ka hada abin da kanka saΓ― ka warware Kai kadai idan Fu ad ya farka, Nina tafi bazan sake waiwayar kuba harsai ka koma yiwa yaya magana kamar yadda kake min, sannan ka nuna masa kauna kamar yadda ka nuna min" daga Haka Abjeed ya fita daga cikin gidan Baki daya Yana goge hawayen Dake Shirin gangaro Masa.




"Adeena maza ki..."karka cemin komai abbanmu " Adeena ta dakatar da shi da sauri "abbanmu meyasa zakayi Mana haha, duk da Ni yarinyace karama ,za a iyacewa bansan menene so ba Amma nasan komai, nasan da cewa baka son uncle sannan Kuma baka kulashi, to meyasa ,abbanmu banason jin komai amsa kawai nake son ji, abbanmu bakasan zafin da zuciyata take min ba ko, to ciwo nakeji a duk lokacin da naji ka batawa uncle Rai ,inajin zafi da daci acikin zuciyata , yau nima naji sha,akwai son sanin asalin labarin A.K FADAMA ?"



"Nikam nashiga uku dan Allah abar wannan zancen daga baya ayi ,abba kazo mukamashi musa a mota muje asbiti kada su mutu" Ammi ta fada tana share hawayen.




"Mu kadai baza mu iya daukan Abeed Musa shi a mota ba, Adeena Maza jeki kirawo malan mai gadi ya taimaka Mana " batare da Adeena Tace komai ba ta karasa inda Mai gadi yake, ta kirawo shi, a tare suka taho zuwa inda Abba yake, durkusa wa Mai gadi yayi yace "subahanallahi alhaji Mai yake faruwa Haka , Naga alhaji karami a kasa ,lafiay?" "Lafiya ba lafiya ba yanzu dai ka taimaka mana musa shi a mota" ah Tom shikkenan " mai gadi ya fad'a tare da mikewa ya daga Abeed Abba ma ya Kama kafarsa ita ma momy ta tallafo shi ,Adeena ta bude kofar motar, suka sakashi a mota, yau dai abin da abba Bai taba yiba shi yayi ,wato tuki da kansa, batare da Bata lokaci ba Abba ya Soma Jan motar Mai gadi ya bude gate suka fita,










Gudu Abba yake sharara wa akan titin Yana tuki gumi Yana faman karyo Masa, idanun Nan nasa kuwa, sun kada sunyi jajur, Haka ya daure ya cigaba da tukin har ya karasa wani babban asbiti dake garin faransa , hon yayi wa Mai gadin ya bude, sanan ya danna hancin motar ciki, Yana shiga yayi parking a parking space din asbitin ,Ammi ce ta fito da gudu ta shiga cikin asbitin, tun daga bakin kofa take kwalla musu Kira, doctor's din fitowa sukai da sauri hankali q tashe suke kallonta, "lafiya ?,lafiya kuwa Baiwar Allah" "inafa lafiya Dan Allah ku tai maka Mana kada su mutu " " hajiya Ina yaran suke?" "Suna mota" Ammi ta fita suka bita a baya Har harabar asbitin, ba bu wani Bata lokaci Aka fito da bed aka dorasu a Kai sanan aka turasu zuwa ciki, ammi da Abba kuwa sun kasa zaune sun kasa tsaye sukai su dawo sukai sukoma Haka suka dinga Yi ,kowa yakasa zaune ya kasa tsaye.








Shi kuwa Abjeed tun da ya fita daga cikin gidan su Babu inda ya nufa sai , adama wa, ma,ana A.K FADAMA EXCITED , Yana karasawa ya bude kofar d'akin da ya shiga, Nan take abubuwa da dama' suka Shiga dawo Masa a wanan lokacin, take ya Soma tuna abubuwan da suka faru lokacin da suna zaune a cikin gidan, anan ne rayuwar da sukayi da abin da ya faru ya Soma dawo Masa sabo fill, bakin gadonsa ya samu ya zauna tare da dafa Kai , ya lumshe Ido ya furzar da iska daga bakinsa yace "innalillahi wa'inna ilaihirraju un! Innalillahi wa'inna ilaihirraju un !!wanan masifar da mai tayi kama, yaya Abeed Kana cikin jarabawar rayuwa" Yana tsaka da surutai shi kadai ya ga wayarsa tana ruri bugu biyu ya daga, abbane ,"hello Abjeed kana Ina Dan Allah ka dawo" "a,a abbana wallahi bazan dawo ba indai har gidan kane bazan sake dawowa ba," "haba Abjeed maiyasa zakace Haka indai Akan abin da nakewa Abeed ne na daina Ni dai BURINA kawai ka dawo" "allah abba bazan dawo ba shikuma yaya Abeed ka cigaba da masa abin da kakeso indai nine na hakura da gidan ka ,kaje Kai da allah abba ko Mai kakeyi Allah Yana ganinka indai abin da kayi dai dai ne Tun aduniya zaka ganu, kafin na kashe wayar Nan Ina son Abba na Dada tunatar maka da wata magana da ka manta, ba Kana cewa Yaya Abeed shine Mai kefi ba ,to kaima kana da laifi idan ka manta Ni Zan tuna maka, duk abin da Yaya Abeed yayi Kaine musabbabin komai Kar ka manta da wannan ,mommy azeema itace wadda zata baka wannan amsar , Ina fata yanzu ka gane inda na dosa" "na sani Abjeed ban manta ba wannan dalilin ne yasa nake son ganin zarah a rayΓ© bana son ta mutu dan Allah ka dawo karka ta fi ka barni kamar yadda Dan uwanka yazeed ya tafi ya barni abaya" "wallahi abba komai zakai bazan dawo ba ni danasan inda yaya yazeed yake a yanzu ma binsa zanyi" Yana Gama fadar Haka ya katse wΓ yar batare da ya sake cewa komai ba .

Abba kuwa zaman durshen ya sakeyi a gurin tare da kallon ammi yace "shikkenan shima yatafi" "nashiga uku Wai shima Abjeed din ya tafi ya barmu kenan?" Innalillahi wa'inna ilaihirraju un! " Ta sulake a gurin a sume.


πŸ’”_____*DEPRESSION*_____πŸ’”
(DAMUWA)

*#CIN AMANA*πŸ’”
*#JURIYA*πŸ’”
*#SOYAYYA*πŸ’”
*#DAMUWA*πŸ’”
*#HAKURI*πŸ’”
*#YAFIYA*πŸ’”
*#KYRA*πŸ’”


*Chapter 15*

TO😌 TO😌 TO😌πŸ’ͺπŸ’ƒπŸ’ƒπŸ’ƒπŸ’ƒπŸ’ƒ DA KARFIN SA YAKE TAFE SHIN KIN SAN YADDA AKE TSANTSAR CIN AMANA KUNSAN YADDA AKE NUNA TSANTSAR SOYAYYA KARYA? KO KUNSAN YADDA ZUMA DA MA'DACI YAKE ,TO ALBISHIRIN KU MASU SAURARO MUTANEN ALKAIRI ,INA SON KU

Please Login or Register in order to submit comment