Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

tace"objection ya mai shari'a ya kamata barrister IKLAS ta daina karyata Abida tun ba a tarbata ba"


Alkali yace"barrister ki kiyaye"


Gaban RAYHAN taje tace"zaka iya tuna abinda ya faru ran 3/3/2019


Yace"a Lagos misalin karge 9:pm nafito shakatawa na bige mutum da mota ta ina fitowa naga Abida ne nan na kaita asibiti bayan Dr ya duba ta yace tana bukatar hutu nan na sallame mu


Muna fitowa Abida ta roke ni akancewa in taimaketa ta kwana a gidana saboda duk ya cika da jama'a kasancewar anyi conference ranan nikuma na amince ma akan da gari ya waye zata taxi


Bayan kwana biyu naji bata da tafiya nan na tambayeta tace mun zuwa anjima zata tafi"


tace"ran 7/3/2019 fa mega faru?"


Yace"bayan nayi mata magana na koma d'aki na kwanta kawai sai naji ana shafa ni da sauri na bude ido ganin Abida nayi kwance cikin shigar karuwai ta fara roko na wai sai nayi lalata da ita ni kuma naki out of anger nayi mata dukan siya na fitar da ita gaban jama'a anan tayi barazanar kunyarta dani a idon duniya"


Barrister Aisha ne tace"objection ya mai shari'a karya akewa Abida dan ta tabtar mun tana minna ran 3/3/2019 wanan shari ake mata"


Barrister IKLAS tace"ya mai shari'a ina son kotu tabani damar kiran Dr shegun"


Alkali yace"kotu ta baki dama"


Tace"Dr shegun ko kasan wanan Matan da mutumin"


Yace"eh na san su"


Tace"ai na kenan?"


Yace"a lagos dan ran 3-3-2019 wanan mutumin ya kawo ta asibiti akan ya bugeta da mota"


Tace"nagode"


Wajen Abida taje wanda zuwa yanzu ta gama sadakarwa zatayi loosing case itako barrister Aisha haushin Abida take ji zata breaking record


Tace"me ya kaiki office d'in RAYHAN ranan 8/5/2019?"


Tace"kasuwanci "


Barrister IKLAS tace"wani irin kasuwanci?"


Tace"naje ne akan ina son yayi ta kera mun takalma ina sari"


IKLAS tace"amma ba company kera takalma kika je ba na motorci ne kuma in as far as I can remember ke Dr ce ba kasuwanci kike yi ba"


Tace"eh naje can ne baya nan shine na zo na kera motorci"


Barrister"IKLAS tace"ya mai shari'a wanan yana tabbatar mana cewa Abida ba kasuwanci ya kaita ba taje dan yiwa RAYHAN sharri"


Barrister Aisha tace"objection ya mai shari'a barrister bata da shaida da zata Nina cewa RAYHAN bashi ya aikata laifin da ake zargin shi ba"


Barrister IKLAS tace"Niko nike da shaida,ya mai shari'a ina son malam bashir ya zo gaban kotu"


Alkali yace"malam bashir ka zo gaba"


Yana fitowa IKLAS tace"kotu yasan miye sunan ka da sana'ar ka ko aikin da kake yi"


Yace"sunana bashir ina cikin ne a company RAYHAN nine mai kula da duk wani abu da ya shafi wuta lantarki har da cctv camera wato in charge of maintainance"


Ai Abida na ganin bashir sanda hanjin cikinta ya kad'a


Barrister IKLAS tace"ran 7-5-2019 na samu labarin Abida ta zo niman alfarma wurin da kud'in masu yawa"


Yace"eh haka ne"


Ko zaka iya gaya mana wani irin alfarma ne?"


Yace"tazo akan cewa tana so inyi tempering da CCTV camera oga yana daina aiki na kwana d'aya dana ki amincewa sai tayi mun barazana sai kawai na nuna mata na amince amma a gaskiya banyi mata aiki ba"


Tace"ko zan iya ganin casset d'in wanan rana?"


Yace"eh"cassete d'in ya ciro a aljihu ya mika mata


Alkali ta bama nan aka samu abin kallo akayi playing


Duo abinda ya faru wanan rana kowa ya gani


Barrister IKLAS tace"da wanan hujjojin da shaidu nike son wanan kotu mai adalci ta wanke RAYHAN daga zargi because I have been able to prove beyond reasonable doubt RAYHAN is innocent and free from all charges"


Alkale yace"barrister Aisha ko kina da tambaya?"


Tace"no ya mai shari'a


Alkali yayi gyran murya yace...






Maman
Noorul
Hudah✍✍
Luv u my fans
Pls share
[3/18, 00:42] Hubeey Kn 2: πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„
IKLAS
πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹
By maman noorul
Hudah


🌟GORGEOUS WRITERS FORUM🌟


🌟G.W.F.🌟


Home of gorgeous,interllingent,and expert writers,we are the best among the rest.




Dedicated to my family


πŸ…Ώ3⃣5⃣&3⃣6⃣


Bismillahi Rahmanir Rahim


Abida tace"wai ke me kika dauki kanki ne? Kina gani ke zaki iya kare shine a kotu?wanda ya fiki ma ya kasa balle ke"


Ba tare da IKLAS tayi magana ba ta wankawa Abida mari Abida na son tayi magana ta kara wanka mata mari


Kafin Abida tayi kwakwara motsi ta kara wanka mata mari


Abin na kokari ramawa ta rike hanun ta ta murd'a shi tace"the first slap is for defaming my husband & the second is for making my husband talk of the town,and third is to remind you that iam a barrister who is capable of saving my husband from your clutches"


Cikin azaba Abida tace"live me alone"turata IKLAS tayi ta fad'i kasa da k'yar ta mike tace"wallahi baki isa ki kubautar da RAYHAN data sharri naba wallahi sai tayi 7 years in prison "


IKLAS tace"ni IKLAS nayi miki alkawari jibi ina shiga kotu bazan fito ba sai tare da miji na sanan zan kunyata da ke a idon duniya inda ko anyi gwanjo ki naira biyar babu wanda zai siya ki,infanct i will deal with you to extend that you beg for mercy,I will unvail the mask behind that your ugly and faded face,then you will learn never ever to underestimate a woman in love"


Abida tace"wallahi RAY...."bata karasa ba IKLAS tace"dont you dare call my husband name with that your filthy and smelling mouth of yours,because if you do that i will not hesitate to cutoff your tongue"tura ta tayi gefe sanan ta ja motar ta ta bar ta tsaye baku bude


IKLAS ne tayi parking mortar ta a parking lot na station tana fitowa minal ta kira ta tace"minal ina station ne kisa me ni a station"


Shiga tayi ta zauna sai ga wani police ya fito da RAYHAN yana tureshi"


Kallon police d'in tayi tace"how dare you treat him like a criminal"


Shiru police d'in yayi tace"if you ever do that again i will sew you to court"


Yace"sorry ma tashi tsaye tayi ta leka window station d'in dan taji hayaniya tace"this press will never live us alone"


Juyowa ta kalli police din tace"you can go I want to have a word with my client"


Yana fita RAYHAN dake tsaye cikin 3qurtr da vest ya karaso da gudu ya rungumeta tightly yana kuka yace"please my wife take me away from here I don't like it here please help me ba don halina ba dan soyyaya li da ma'aiki"


Nan da nan zuciyar ta ya sinks amma sai tayi controlling ta fara tureshi amma ina yayi mata mugun runguma tace"please let me breath"


Sai a sanna ya sake ta zama tayi ta kalleshi tace"you can seat"


Shima zaman yayi ya kalleta itama kalloshi tayi sai ta basar tace" yaya sunan ka?"


Kallonta yayi a ran shi yace" bata ma san sunana ba lallai ina cikin matsala"murya ta ne ya dawo dashi daga duniya tunani


Race"please don't waite my time I said what is your name?"


A sanyaye yace"RAYHAN Mohammed d'ahiru"


Tace"zaka iya gaya mun tsakanin ka da Abida I mean every detail"


Yace"eh"


Nan ya kwashe komai ya fad'a mata sai dai ya boye mata kwana biyu da Abida tayi a gidanshi na lagos haka kawai yaji yana jin kunya sanar da ita


Kallonshi tayi ta kuma cewa"make sure you tell me every detail"nan RAYHAN ya fara kame kame da k'yar dai yayi ya samu courage ya fad'a mata gaskiya abinda ya faru


Wani kishi ne ya taso mata ta kalleshi a ranta tace" you will pay for sleeping with another woman under in the same roof bari a gama wanan shari'a"


Amma a fili tace"is that all"yace" yes"nan dai ta cigaba da tambayan shi yana bata ansa


Tana gamawa ta fito yan jarida suka rufe ta suna yi mata tambayoyi


Wata tace"how do you fell fighting for a rapist?"


Ai fusace ta kalleta tace"how dare you call my husband a rapist?if you do that again I will have your television station shutdown and I will make sure you route in jail"


Minal ne ta karaso suka shuge mota sai alheri FM wajen Abdul


Tun daga rana IKLAS tayi ta bincike dan bata barci sai dai bata kara komawa station wajen RAYHAN ba amma kullum sai tayi kuka akanshi inta tuna Inda ya rungume ta yana kuka sai taji ta tsani Abida tace wallahi tun da kika sa RMD kuka sai wulakanta ki


In dare yayi bata barci haka zatayi ta nafilfili tana kaiwa Allah kukan ta


'Bangaren RAYHAN ma haka ne kullum cikin tunani IKLAS yake yi ji yake da bai yi wasa da damar da Allah ya bashi a baya ba a fili yace"illar rashin biyyaya kenan ga iyaye ga shi yau na shiga saka mai wuya


Yau ya kama 14/5/2019 yau za a zauna a kotu da sassafe IKLAS ta tashi ta shirya nawal ta kai ta wajen mamy daddy yai ta yi mata addu'a mamy tayi mata addua sosai fita tayi ta je bakin masalacin jumma'a wajen da almajirai ke zama sadaqa tayi ta rabawa




Misallin karfe 9:pm ta isa kotu karfe goma dai-dai aka fara shari'a








Maman
Noorul
Hudah✍✍
Luv u my fan
Pls share
[3/18, 00:42] Hubeey Kn 2: πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„
IKLAS
πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹
By maman noorul
Hudah


🌟GORGEOUS WRITERS FORUM🌟


🌟G.W.F.🌟


Home of gorgeous,interllingent,and expert writers we are the best among the rest.


πŸ…Ώ3⃣9⃣&4⃣0⃣


Bismillahir Rahmanir Rahim


Alkali yace"base on the evidence presented before me wanan kotu mai Adalci ta wanke RAYHAN daga zargi dan bai aikata laifin da ake zargin shi dashi ba asalima sharri akayi me,


Wanan kotu zata ci tara Abida nasir na million uku sanan kuma RAYHAN zai iya shigar da kara in yaso akan sharri da tayi me wanan shine hukunci wanan kotu"buga guduma shi yayi mutane suka ce kotu"


Bayan alkali ya fita minal tayi saurin fita ita da islam ummi ko da wuri taje ta rungume IKLAS sai godeya take mata Abba da daddy ko murna Abba yace"nagode da Allah ya bani suruka irin IKLAS Allah ya albarkaci rayuwanta"


Cikin murna daddy yace"amin"fita sukayi suka bar kotu cike da farin ciki


Ummi tace"IKLAS ina waje ina jiran Ku"


Tace"toh"


RAYHAN dake tsaye yana ganin ummi ta bar cikin kotu da gudu ya karaso ya runguma IKLAS yana kuka itama sanda tayi hawaye amma bata bari ya gani ba


Tace"dun Allah ka tsake ni mutane na kallon my"


Girgiza kai yayi yace"matata na tuba dun Allah ki yafe mun"


Karasowa barrister Aisha ne yasa ya tsake ta


Barrister Aisha ta mika mata hanun alamun handshake tace"na dade ban gwabza da barrister da ya caza mun kai ba irinki"


Murmushi IKLAS tayi tace"i have to because my client integrity is at stake"


RAYHAN a ranshi yace"client that mean bazata iya cewa ni mijin ta bane gaskiya na cuci kai na"


Barrister Aisha tace"amma akwai personal relationship tsakanin ku ko?because the way inda kikayi fighting case d'in with passion is as if you want bring the whole roof down"


Kafin IKLAS tayi magana yace"ai matata CE"


Tace"no wonder gaskiya kayi sa'ar mata"


IKLAS ne ta kalli witness stand ta gan Abida tsaye ko motsi batayi ba murshi tayi mata ta kashe mata ido d'aya


Fita tayi ta a cikin kotu RAYHAN ko sai binta take kamar jela


Tana fitowa ko sai yan jarida suka rufe ta da tambaya wasu taba su ansa wasu kuma tayi shiru


RAYHAN ko da an tambaye shi sai ya washe baki yace"she is my wife"


Abida na fitowa yan jarida suka rufe ta ana cewa dama ashe ke lesbian ne karuwa"


Mai yaja hankalin ki kika yiwa RAYHAN sharrin zina?yanzu dai musan ki yi hankalin dan matan shi ta Nuna miki nobody meses with her husband and go free"


Wata tace"ta kika ji datayi humiliating d'inki a kotu?"


Shuru tayi tana hawayen bakin ciki,tana tsaye sai ga minal da Islam tare da wasu mata sun karaso wajen ta nikkeken gawayi minal ta shafa mata a fuska sauran kuwa suka fara halbin ta da dutse gashi jama'a sai tsine mata akeyi


Abun dai sai wanda ya gani dan hayaniya suka tada


IKLAS ko ta jingina da mota tayi folding hanuwanta tana kallon Abida,


Abdul ko yace"wanan yariyan akwai masifaffiya yanzu ko ina ta samo mutan nan oho"


Da k'yar police suka kwace Abida ta hanyar sawa wajen tear gas


Da k'yar Abida tayi iya tafiya taje wajen tap dan wanke fuskar ta


IKLAS tace"ummi ina zuwa"


Ummi tace"toh"


Nan ummi ta kalli RAYHAN tace"RAYHAN ka ga yariyar nan na da hankali ko da abin nan ya faru bata bar nawal ba dan tare ta tafi da ita gidansu wanan yana nuna mana tsakani da Allah take son jinin ka dan da wata ce ma ko kallonta bazatayi ba tunda tana fushi da ubanta dun Allah ka rike ta da amana,amma abin da ke d'aure mun kai ina IKLAS taje ne har Abida ta kwana gidan Ku"


Gaban shine ya fad'i amna ya dake yace"ai a lokacin ta tafi hostel ne"


Ummi tace"OK toh Ku kiyyaye gaba"


Abida na juyowa bayan ta gama wanke fuska kawai sai tagan IKLAS a gaban ta IKLAS tasa mata kafa ta fad'i kasa


Tace" that is where you belong to,iam here to warn you to stay away from my husband"


Abida tayi dariya wanda da k'yar tayi shi tace"you humiliatad me and you have to pay for a price for that,wallahi sai na kwa da ke a doron kasa kamar inda na kawar da ta farko "


IKLAS tace"ni kuma sai nayi sanadiyar ajalin ki inshaallahu" nan ta juya ta bar ta zaune


IKLAS tunanin maganar Abida takeyi tace"me take nufi da ta farko kodai ita ta kashe maman nawal?no ai ance wajen haihu ta mutu"


Dawowa tayi tace"ummi bari in tafi gidan mamy in d'auko nawal"


Ummi tace"toh RAYHAN shigo mu tafi tare"




Ai da sauri yace"ummi ni matata zan bi"


Ummi tayi murmushi ta shige mota da Islam


Minal ko na gefe tana ta zazzagawa Abdul rashin mutunci wai ai dashi aka had'a baki aka yiwa aminiyanta wulakanci


Shiko Abdu l said kallon ta yake IKLAS ne ta karaso race"minal ni zan tafi gidan mamy ko zaki zo in rage miki hanya?tunda baki zo da mota ba"


Minal tace"je ki wanan munafikin zai kai ni"


Murmushi IKLAS tayi ta ja mota dan already RAYHAN ya baje a gaban mota


Basu yi tafiya mai nisa ba IKLAS tayi parking a gefen titi tace......






Pls kuyi hakuri da spellings error ko mistake bana samu lokaci editing ne








Maman
Noorul
Hudah✍✍
Luv u my fans
Pls share
[3/18, 00:42] Hubeey Kn 2: πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„
IKLAS
πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹
By maman noorul
Hudah


🌟GORGEOUS WRITERS FORUM🌟


🌟G.W.F.🌟


Home of gorgeous,interllingent,and expert writers,we are the best among the rest.


πŸ…Ώ4⃣1⃣&4⃣2⃣


Bismillahir Rahmanir Rahim


Tace"fitar min daga mota"


Kallinta yayi yace"meyasa?"


Tace"saboda bana son ganin ka"


Yace"ni mijin kike gayawa haka?look my IKRAY please let baygone be baygone let forget about the past and start a new new life"


A fusace tace"ai said get the hell out of my car"


Yana so yayi magana ta katseshi dacewa"now"


Ya bude kofa zai fita tace"kana ji?"


Ya juyo ya kallaeta tace"ina son kafin in dawo ka rubuta mun takarda saki na dan tunda bama son juna gomma mu rabu"


Yace"inji wa yace ni bana sonki?"


Tace"kai da bakin ka ko ka manta ne a mota ranar kamun bikin mu kace ni da kai na zan nimi ka sake ni toh lokaci yayi"


Zaiyi magana tace"pls banison tsurutu kafin indawo ka rubuta mun takarda na please in ba haka ba zan kai ka kara kotu"


Fita yayi jiki a sanyaye itako taja mota ta bar wurin


Hanun yasa a kai yace"na Shiga uku yau na ga illar rashin biyyaya meyasa tun farko na wulakanta ta?hmmm wallahi ko za a kashe ni ba zan sake ta ba"


'Bangaren minal ko Abdul ya kaita gida har zai ganin taki fita a mota yasa yace"mu kawo gidan"


Tace"eh na sani ban dai gan daman fita bane ko kana da abin yi?"


Yace"no na isa?ai ban isa ba"


Kallonshi tayi tace budurwan ka nawa"


Cikin jin haushi da mamakin tambayar a ran shi yace"niko Allah ya had'a ni da masifaffiya kome zatayi da yan matana oho"


Tace"da kai fa nike fa"


Yace"su uku ne"


Ai ihu tayi tace"what?"


Yace"menene?


Tace"ba komai shawara zan baka,ka daina kula mata dan baka isa yin budurwa ba kaga mu mata bamu da alkawari kar su zo suyi betraying d'in ka"


Kallonta yayi daga sama yace"toh umma"


Tace"in banda abinka,kai guda nawane da zaka fara budurwa"


Dariya ma taso ta bashi ga takaicin maganan ta na cewa shi guda nawane


Har zata fita ta dawo ta kalleshi tace"karka bari na kama ka da budurwa"


Yace"toh umma"


Tace"Allah ya maka albarka a je gida a huta"


Tana fita a motar yace"lallai ma yariyar nan ta rainani wato ma yaro ta d'auke ni amma me take nufi da kar in kula mata?"




IKLAS na Shiga gida mamy tace"kai IKLAS kinyi kokari a kotu ai mun gani a tv amma wanan abida anyi sinnaniya yariya amma naji dadi da Allah tons asirinta"


Murmushi IKLAS tayi tace"mamy ina nawal?"


Tace"tana ciki ai tun d'azu take kuka wai sai an kaita wajen mummy da daddy ta"


Shiga d'aki ta tayi tace"nawal ina kike ne?"


Nawal dake b'oye bayan labule ta fara dariya IKLAS tace"oh baby ni ake boyewa"


Nawal tafito ta rungumeta


Nawal tace"mummy ina daddy na ba kince yau zai dawo ba?"


Tace"eh daddy ki ya dawo yana gida yanzu haka"


Nawal ta kwaso takalmin ta tace"mummy mu tafi gida"


Tace"toh"


RAYHAN ne gaban Abba sai faman fad'a yake yi yace"ashe dama ban isa da kai ba?ince karkayi abu amma San da kayi"fad'a yayi me sosai tare da nuna b'acin ran shi ya kuma yi me kashedi yace"wallahi in ka kara janyowa kanka masifa toh ba ruwana da kai,in ba dan an gode yariyar nan ta tsaya maka ba da yanzu kana gidan yari dan sauran lauyoyin kin tsayama suka yi sha-shasha kawai"


Hakuri RAYHAN ya bashi da nuna me yayi nadama


Daga karshe Abba ya hakura


Abba yace"jeki gida ka same iyalin ka kwana biyu basu gan ka ba




D'akin ummi ya je ya zauna nasiha tayi me sanan ya ci abinci


'Bangaren Abida kuwa bayan ta bar kotu gidan Mahmud ta je


Mahmud yace"ashe ke wawiya ne?meya na tare ta a titi kiyi mata magana baki san by doing dat kin yi challenging d'in ta bane gashi yanzu instead of ki raba su kin had'a su"




Tace "ai ban tab'a experting zata yi winning barrister Aisha ba"


Mahmud yace"ki bar mun gida yanzu dan baki da amfani a wajena yanzu"


Kallonshi tayi tace"haba Mahmud dan na fad'i so d'aya zaka Kore ni yanzu fa bani da wajen zuwa dan an Kore ni a wajen aiki kuma sanin Lanka ne babu Wanda zai taimake ni balle a bani aiki"




Yace"wanan damuwar ki ne banawa ba"korar kare mahmud yayiwa Abida


Tana barin gidan mugu ya taimake ta zuwa gidan shi




IKLAS na barin gidan mamy gidan anty EESHA taje kiran minal tayi tace sameta a gidan nan ta kira Islam ma




Islam na zuwa ba da dadewa ba minal tazo ba tare da b'ata lokaci ba suka fara ba shawarwari EESHA tace"dole ne ma a gasa RAYHAN"Islam tace"ai ya zama dole tunda bai da muntunci"




Harararta Minal tayi tace"kamar da gaske"


Islam tayi murmushi dan yanzu ta fara gane halin minal tace"hmmm ke dai ki fita fad'a wallahi"




Anty EESHA ta kalli IKLAS tace"karki bari yasan weakness d'in ki meaning karki bari yasan kina son sh"


Nan dai suka ci gaba da hira kafin suka bar gidan




IKLAS na kaiwa gida ta sami RAYHAN a palour dagudu nawal taje ta rungumeshi




Kallon IKLAS yayi yace......




















Maman
Noorul
Hudah✍✍
Luv u my fans
Pls share
[3/18, 00:42] Hubeey Kn 2: πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„
IKLAS
πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹
By maman noorul
Hudah


🌟GORGEOUS WRITERS FORUM🌟


🌟G.W.F.🌟


Home of gorgeuos,interllingent,and expert writers,we are the best among the rest.


Dedicated to Hassana Mohammed Bana aka hassy looks


Naga korafin ku akan ina sa turanci diyawa a novel dina please kuyi hakuri zan gyra ko da dai bana jin hausa sosai amma zan yi kokari in rage


πŸ…Ώ4⃣3⃣&4⃣4⃣


Bismillahir Ramanir Rahim


Yace"IKRAY sannu da dawowa"


Nawal ne ta rungume shi tace"daddy oyoyo,ina kaje baka dawo ba mummy kullum sai tayi ta kuka"


IKLAS a ranta tace"ka ji yariya da tunan asiri"amma a fili tace"nawal muje kiyi wanka"


Nawal tace"toh mummy"


Haurawa suka yi suka barshi tsaye


Yace"kodai tana sona ne?kila saboda ta tausaya min ne"


Shigar su IKLAS bada dadewa ba sai gata ta dawo


Tace"ina sako na?"


Yace"dun Allah IKRAY zauna muyi magana mu fahimci juna"


Tace"babu wani fahimtar ka da zanyi ka dai bani takarda na"


Yace"na roke ki dan soyyayar ki da ma'aiki ki taimaka min"


Zama tayi tace"ina jin ka"


Yace"IKRAY ki taimaka min ki yafe min abubuwa dana yi miki a baya wallah......"


Katse shi tayi da cewa"wanne daga cikin laifin ka zan yafe ma?ruwan daka wasa mun a titi makarantar mu?koko kulle ni da kayi a police station? dan na taimaki yarka koko jamun gashi da kayi a mota ranan kamu mun kodai wulakanci da kayi mun a lagos?wanda sanadiyar sharin da tsohuwar budurwa ka tayi mun kayi mun duka da sanda nayi jinya a asibiti,kuka ta fashe dashi"


Ya rike mata hanun yace"dun Allah ki yafe mun wallahi nayi nadama kuma na yafe kuskurena kiyi hakuri yanzu ina son ki har cikin zuciyata"


Dariya tayi tace"kana sona?karya kake yi dan kai da bakin ka kace mun bazaka tab'a sona"


Yace"dun Allah ki manta baya mu gina sabon rayuwa"


Tace"ni dama ba sonka nikeyi ba ina da Wanda nike so biyyaya ce tasa nike ta bin ka sau da kafa,kuma karka d'auka na taimake ka ne dan inason ka ne,na taimaka ma ne dan na tsani zalunci kuma ko waye ke cikin wanan halin zan taimaka me"


Shiru yayi idanun shi sunyi jawur yace"yanzu IKRAY a gabana kike gaya mun kina da wanda kike so ki tuna fa akwai aurena akanki"


Tace"miye wani IKRA? Sunana ba IKRAY bane kuma ai shiyasa nace ka sauwake mun inje in same shi"


Yace"gaskiya bazan iya sauwake miki ba kuma ni ba wai dan kin taimakeni nike sonki ba na dade ina sonki tun a lagos na fara sonki amma a lokacin bagane so bane na d'au sha'awa ce kawai a ranan da nike shirin fad'a miki ranan wanan abin ya faru"


Tashi tayi tace"toh tunda kace bazaka sake ni ba ka zauna cikin shiri dan ni bazan tab'a sonka ba"


Kicin tashiga tayi girgi ta jera a dining,haurawa tayi sama tayi wanka ta shirya cikin riga jeans da top tayi bala'i yin kyau ko d'ankwali bata d'aura ba tayi parking dogon gashinta


D'akin nawal taje zaune ta hango ta saman gado tana wasa da teddy tace"baby zo muje muyi dinner"


Saukowa sukayi suka zauna a dinning suka fara cin abinci


Suna zaune sai gashi ya sauko karasowa yayi
Ya ja kujera ya zauna


Nawal tace"daddy muci abinci mana"


Ai da sauri IKLAS tace"daddy baya jin yunwa ya koshi"


Kallonta yayi ta harrare shi bayan nawal ta koshi tace"mummy barci nike ji"


Tace"toh je d'aki ki kwanta"


Bayan nawal ta tafi yace"IKRAY ina abinci na?"


Tace"ban dafa da kai ba"


Yace"yanzu harda abinci ma baza ki tausaya ki bani ba kwanana nawa banci abinci kirki ba"


Ko kallonshi batayi ba ta tashi ta dawo palour ta zauna tana kallo


Zama yayi a ranshi yace"nasan zansha fama amma inshaallahu zan jure dan ni na jawowa kai na"


'Bangaren minal ko tana kwance a d'akin ta agogo ta duba taga 8:pm tace ko ina yake yanzu?ko me ta tuna naga ta tashi da sauri wayar ta ta d'auka tayi dialling number Abdul


Tace"ina kake?




Bata jira mai zai ce, ba tace"kazo ina niman ka yanzu"


Yace"to umma"


Abdul dake zaune yana kallo ta kira shi tsaki yayi bayan sun gama waya,da kamar baza shiba sai kawai ya mike ya d'auki makulli mota




Yana zuwa ya......












Maman
Noorul
Hudah✍✍
Luv u my fans
Pls share
[3/18, 00:42] Hubeey Kn 2: πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„
IKLAS
πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹
By maman noorul
Hudah


🌟GORGEOUS WRITERS FORUM🌟


🌟G.W.F.🌟


Home of gorgeous,interllingent,and expert writers,we are the best among the rest.


Dedicated to RUKKAYA admin GORGEOUS WRITERS FORUM ina yin ki irin sosai d'in nan


πŸ…Ώ4⃣5⃣&4⃣6⃣


Bismillahir Rahmanir Rahim


Abdul na kaiwa kofar gidansu minal ya kirata

Please Login or Register in order to submit comment