Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ƙaddaro sai dai ta san muddin auren Safiyya ya mutu to wani sabon tashin hankalin ne domin kuwa abokiyar zamanta da kuma sauran mutane ba za su bar ta ta rayu cikin farinciki ba sun ringa jifanta da maganganu da kuma kiranta da MAI FARAR ƘAFA.




Ganin Safiyyar ta tsaya riƙe da akwatin ta kasa gaba ta kasa baya sai Mamar ta sunkuya ta ajiye kofin hannunta cikih sauri ta nufi wajen ƴartata zuciyarta na mata wani irin rauni da bashi da misali ko kwatankwaci tana zuwa suka rungume juna domin Mama ba sai an mata bayani ba yanayin da ta ga Safiyya a ciki yanayi ne da take ganinta a ciki a koyaushe idan rabuwar aure ta gifta mata, bare kuma akwatin fa ta gani shi zai ƙara tabbatar mata da hakan. Tun da suka rumgumi juna Mamar ke ta faman bubbuga mata bayanta alamar lallashi sabo da Mamar ta kasa furta komai harshe da laɓɓanta sun mata nauyi.


"To fa! Na dawo in ji ɗan yawon duniya, baƙon jiya ne ya ƙara dawowa? Allah suturu buƙwi in ji kishiyar mai doro, taɓɗi! Ai dama banza ba ta kai zomo kasuwa tun da abin kirki bai gaji kare ba in ya yi ma dukansa ake. Ai sai ko dangana dan babu mai iya zama da ƴarki MAI FARAR ƘAFA! Haka kawai talauci ya baibaiye shi bai ji ba bai gani ba wannan shi ne aure na uku da ƙananan shekarunta kowane gidan biyu ta haihu wannan na ukun kuma an ƙoro miki ita da tsohon ciki haihuwa ko yau ko gobe kai a yanzu ma naƙuda za ta iya tashi mata, ai abin da ya dace kawai ku samu dajin Allah ta'ala ku kafa bukka ku zauna ku rungumi ƙaddararku, kun ga kun keɓe kan ku daga jama'a babu wanda wata masifa za ta samu tun da kun nisanta da mutane dan kin san dai ko gidan nan ta zauna samun Malam raguwa yake a toh gwara ta fidda rai daga zaman aure dan ko aure ɗari Safiyya za ta yi sai an sako ta!" Muryar Umma Asiya ta karaɗe kunnuwan Mama da Safiya da ke rungume da juna sun yi mutuwar tsaye duk da sun saba jin maganganu sama da haka ma amma na yau sai suka fi na kullum zafi wai su koma daji su gina bukka su zauna su kaɗai wato ma sun zama annoba, har da faɗar ko aure ɗari ta yi sai an sake ta.
MAI FARAR ƘAFA
(JAHILCI NE )


NA


MAMAN AFRAH


FCW

GAJERAN
LABARI


FREE BOOK🥳


Page 5️⃣➡️6️⃣


Cikin rashin kuzari Mama ta saki Safiyya daga rungumar da ta mata ta juyo tana kallon Umma Asiya da ke tsaye ƙofar ɗakinta tana wani hura hanci da ɗaga kai.


"Wai hayaniyar mai nake ji ne? " Cewar Malam da ya fito daga ɗakinsa yana wani baza babbar riga.

"A'a Malam gani ai ya kori ji, gata nan dai wannan mai ƙashin tsiyar ce wacce bata da ƙashin arziƙi mijin nata ya ga ba haza ya mata abin da ta saba ji da gani wato ya warware igiyar aurensa daga kanta, domin ya ga ba zai iya fuskantar raɗaɗin babun talauci ba shi ne nake cewa tun da ta ƙara kaso auren nata ta taho gida bayan ƙannenta duk suna gidan aurensu amma ita ta gwammace ta zo take haɗa kafaɗa da mu duk da dama kuma auren nata ma kasada ce yo kasada mana auren da baka da tabbas ɗin zamansa kullum kana jiran tsammani" Ta faɗa tana wani taɓa hannuwa tare da maida ɗaya hannun haɓarta. Mama kuwa kawai kallonta take idanunta cike da ƙwalla dan ta san makirci irin na sobar zaman nata shi kuwa Malam Sadiq dama duk abin da ta faɗa masa tamkar ta yi zane ne a kan dutse dan ba ya ji ba kuma ya gani.


"Ke! Safiyya wato dai auren naki ne kika ƙara kashewa a karo na uku? To tun da ke bakya son zaman aure sai dai zawarci to ki san da saninki cewar na gama ɗaukan ɗawainiyarki dan yanzu kin kai munzalin da za a ce mijinki ne zai ɗauki ɗawainiyarki to tun da bakya son zaman aure ni babu akuyar da zan siyar ta dawo tana ci mini danga, dan haka ki kwana da sanin ke ce ci da shanki da kuma suturarki a cikin gidan nan. Tun da babu Allah a ranku daga ke har uwarki kullum aikin ku biye-biyen Malamai kuna tsotsewa mazan da suka aure ki samun su da kuma arziƙin da suka mallaka" Cewar Malam yana aikawa Mama da Safiyya wata uwar harara mai tattare sa tsabagen jin haushinsu.




"Malam ko da bin Malamai sauran abin fa a jikinta yake baka ga ƴaƴana da suke da ƙashin arziƙi ba su suna can lafiya limi a ɗakin mazansu ba kullum arziƙin mazansu yana haɓɓaka ba, ai kawai in ka ga ba za ka iya ba ka hankaɗa keyarta daga gidanka ta nemi ko gidan haya ne ta tare dan ba zai iyu ake zaginka a gari ana cewa ka hana ƴarka zaman AURE ba basu san FARAR ƘAFARTA bace silar komai tun da dai ka san mu ma idan ta zauna a gidan nan ba tundun tsira muka hau ba samunka raguwa yake abinci ma yana neman gagararka samu" Umma ta faɗa cikin wat murya mai ɗauke da amon kissa da kisisina, har da wani karkata kai gefe dan maganganunta su ratsa majiyar sautin Malam ɗin da kyau kar fa a samu tangarɗa duk da ta san hakan mai wahala ne a samu.




"Safiyya ki je ki kama hayar gidan da za ki zauna dan ni ba zan cigaba da zama da ke ba tun da kin ƙi zama a ɗakin miji, tun da ƙaddararki ce zama ba aure sai ki ware daga mutane dan kar FARAR ƘAFAR da kike da ita yake shafar jama'a" Sautin muryar Malam ya karaɗe majiyar sautin Safiyya wacce dama ta kwana da sanin faruwar haka sai dai bata yu zaton abun har zai yi tsamari haka ba. Wani duhu ta fara gani yana mamaye ma'adanar ganinta domin maganganun Malam da na Umma har wani amsa kuwwa suke mata musamman wurin da Malam ya ce wai ta nemi gidan haya ta zauna kenan abin har ya kai mahaifin da ya haifeta ya koreta daga gidansa, shin idan har wani ya mata abu za ta ji haushi ko ciwon hakan bayan wanda shi ne silar wanzuwarta a duniya ya ƙyamaci ta raɓe shi.




"Gaskiya ka faɗa ai gwara ka faɗi gaskiya kar ka ƙwari kan ka, tun da ka dai gani duk auren da ta yi sai ta yi kashi kamar fara" Cewar Umma tana kallon Malam.


"Bangane sai ta yi kashi ba?" Ya tambaya da alamar tambaya a fuskarsa.


"Yo duk auren da ta yi sai ta haihu mana haihuwa kamar kaza shikenan ita haka za ta yi ta barbaɗen ƴaƴa ta haihu a can ta tafi can ta haihu"


"To ai yanzu komai ya zo ƙarshe tun da ni dai na faɗa mata ta kama haya kin ga ko nan gaba ta samu mai kwasarta (Mai aurenta) Ta san idan ta ƙunso cikinta ma ta fito daga gidan mijin ita za ta ɗau ɗawainiyar yaron to za ta hankalta ta zauna a gidan aurenta" Cewar Malam yana gyara zaman hularsa a kansa.


"Haba Malam Safiyya fa ƴarka ce ko wani ya faɗi magana a kanta ko ya gujeta bai kamata a ce kai ka kasance cikin masu aibatata da kuma gudun taɓarta ba ko kuma ƙin ɗaukan ɗawainiyarta ai ita macece da idan aka koreta daga gida aka ce ta ɗauki ɗawainiyar kanta tamkar an bata lasisin shiga gurɓatacciyar rayuwa ce ta karuwanci ko wani abu makamancin haka bai...


"Majida ya isheki wato har rainin ya kai ban isa in yanke hukunci ba sai kin tsaya gatse-gatse a gabana kina min bita da ƙulli dukan kabarin kishiya, wato ni ban san abin da ya dace da wanda ya kamata ba sai ke, to ki sani ni dai na ce ta je ta nemi wajen zama in ta ga za ta kyautata rayuwarta wannan ruwanta, in kuma za ta munana ta shiga wata bauɗaɗɗiyar hanya shi ma duk ɗaya wai an ce da karuwa hayo gado, idan kuma kin ga za ki bita to hanya a buɗe take amma ki sani zan daddatse igiyar aurena daga kanki"


Wannan furucib na Malam shi ne ya sanya Safiyya jin wani irin hautsinawa mararta ta yi tare da wani murɗawa
mata a take ta fara jin gabaɗaya duniyar na juya mata, hannu ta sanya ta dafe mararta.Mama da ta lura da halin da ɗiƴar tata take ciki a hanzarce ta yi saurin riƙo ta tana cewa


"Safiyya mene ne?"


Safiyya kuwa ta kasa furta wa mahaifiyarta komai, ganin da Mama ta yi naƙuda ce ta taho gadan-gadan sai kawai ta fara tunanin abin yi dan bata son ƴarta ta haihu a gida sabo da gudun matsala.


Safiyya kuwa duk da babu wani sauran kuzari a tattare da ita haka ta yi dibarar janye jikinta daga jikin mahaifiyarta ta juya riƙe da pos ɗinta ɗaya hannun kuma ta saki marar tata ta dafe bango, juya wa ta yi ta ɗaga ƙafarta da niyyar barin gidan nasu dan ta ji dai mahaifinta ya ce ba za ta zauna masa a gida ba sannan kuma ya ce matsawar Mama ta bi ta to zai yanke igiyar aurensu wannan dalilin ne ya sanya ta janye jikinta daga mahaifiyarta domin ta tafi ita kaɗai ta gwammace komai ma ya same ta idan ta tafi ko da kuwa a ce mota ce za ta yi ɗiban karan mahaukaciya da ita a hanyar to tana ganin za ta fi samun sauƙin idan ta koma ga ubangijinta domin tana ɗauke da tsohon ciki a kuma halin naƙuda dan haka zai kasance ta yi mutuwar shahada a kan abubuwan da take fuskanta na daga ƙaddarorin da suke afka mata wanda mutane suka yi wa hakan babbbar fassara ta jahilci suka danganta komai a gareta.


Tafiya ta fara yi tana ɗaga ƙafafunta da take jin tamkar wani gagarumin dutse aka ɗora wa ƙafafun nata a haka ta tunkari ƙofar gidan gadan-gadan. Mama kuwa yadda take jin zuciyarta ta gwammace auren nata ya mutu auren da bashi da wani alfanu a tare da ita bayan cizgunawa da bautar da ita sa ake yi a gidan Malam ba ya jin maganar kowa sai ta Umma ko ƙarya ko gaskiya shi dai duk wani abu da xa ta faɗa ko ta aikata shi ne dai dai duk da cewar ana zargin kamar akwai sammu a al'amarin amma abin ya yi yawa tamkar ba Mama ce uwar gidansa ba.


"Majida tun da kin zaɓi bin ɗiyarki ki j na sawwaqe miki na yanke igiyar aurena guda ɗaya a kan ki" Mama ta jiyo maganar Malam a kunnuwanta, maganar da ta ƙara tsanantawa Safiyya ciwon naƙudar da take ji, domin har lokacin jan ƙafa take bata fita daga gidan ba kuma tana iya jiyo duk maganganun da suke wanzuwa suna wakana a cikin gidan.


"A hayye ayyiriri yiriiiiiiii" Umma ta rangaɗa wata uwar guɗa da sautin ta ya zama tamkar ana bugawa Safiyya guduma a kunne.


"Allah sa haka ahi ne mafi alkairi" Shi ne kaɗai abin da Mama ta iya faɗa ta juya.


"Hehehehe ba haka aka so ba dai ƙanin miji ya fi miji kyau, to Umma ta gaishe da Aisha, Malam dai ya jefar da ƙwallon mangwaro ya huta da ƙuda" Cewar Umma wani farinciki yana mamaye zuciyarta.

Mama dai bata ƙara ko da waiwayensu ba ta bi bayan ƴarta. A dai dai bakin ƙofar fita ta cim mata, tana dafa bango tana tafiya dan lokacin ma kamar haihuwar ta zo dab.






*ANNUR*


Tun da ya baro ƙofar gidan su Safiyya ya kama hanya amma jinsa yake tamkar ba shi ba gani yake kamar idan ya tafi ba zai sake ganinta ba saƙe-saƙen da yake ta faman yi wanda ya sanya kwanyarsa ke barazanar tashowa jin ya rasa makamar lamarin sai kawai zuciyarsa ta yanke masa cewar ya dawo ya samu inuwa ya faka motar daga nan zuwa dare ba zai fidda ran ganinta ba dan haka a take ya juyo da kan motar ya dawo dan yana ganin wannan ce kaɗai hanya mafi sauƙin da zai sake ganinta a yau dan idan ya tafi ba ya fidda tsammanin wataƙila ya ɗauki dogon zango kafin idanunsa su sake yin tozali da ita. Yana shawo kwanar idanunsa suka sauka a kan wacce ya dawo domin ya ganta sai dai duk da cewa daga ɗan nesa ya hango ta hakan bai hana shi ganin wata riƙe da ita ba.


"Ikon Allah mai kuma ya same ta, ko dama bata da lafiya? To ko dai kukan da nake ganin tana yi dama bata da lafiya, ko dai tana da matsala a ƙwaƙwalwarta? Shin ina za a kaita? Mene ne dalilin da ya sa ba za ta yi tafiya ita kaɗai ba sai an riƙe ta?" Zuciyarsa da ke ta faman bugawa da ƙarfi take masa saƙe-saƙen tambayoyin da shi a karan kansa bashi da amsar su. A sukwane ya ƙaraso ƙofar gidan sai da ya ɗan gota ƙofar sannan ya tsaya, a ɗan tsorace ya kafe su da ido yana son gano ainihin amsar tambayarsa. Aikuwa ya samu amsar domin idanunsa ne suka sauka a kan tirtsetsen cikinta wanda ɗazu so ya masa shamaki da ganinsa. Gabansa ne ya bada wani saurin duuuuum har wani zaro idanu ya yi sai kace wanda aka ce idan ya ƙifta idanun zai ga abin da bai yi zato ba.


"Innalillahi wa inna ilaihir raji'un, kenan dama matar aure ce?" Wani sashin na zuciyarsa ya jefa masa tambayar.


"Ko dai cikin shege ne ta yi shi ya sa kullum take kuka?" Wani sashen zuciyarsa ya wurga masa tambayar da ta kusa barazanar tarwatsa masa tunninsa a lokaci guda kansa ya ɗauki wani ciwo.


"Ƙarya neeeeee ba cikin shege bane" Ya faɗa a fili yana dafe kansa da hannu biyu yana jin wani tashin hankali marar misaltuwa yana mamaye dukkan ilahirin zuciyarsa.
MAI FARAR ƘAFA
(JAHILCI NE)


NA

MAMAN AFRAH

FCW
GAJERAN LABARI


FREE BOOK🥳

Page 7️⃣➡️8️⃣

Wani sarawa kan nasa ke masa wanda yake jin tamkar ana soka masa kibiya a tsakiyar kan, har lokacin yana dafe da kan nasa sai ambaton Allah da yake jerowa a cikin zuciyarsa yana son ya samu sassauci game da sabon yanayin da ya far masa lokaci guda. Mama kuwa riƙe da Safiyya suka zo suka gota motar da yake ciki suna takawa a hankali dan dakyar Safiyyar ke iya tafiya Mama kuwa ganin halin da ƴarta ke ciki ya mantar da ita wanzuwar kowace damuwa da ke cikin zuciyarta yanzu burinta bai wuce a ce Safiyya ta haihu lafiya ba domin ta san duk wata mace da take cikin halin naƙuda to kuwa ba a ƙaramin siraɗi take ba siraɗi ne da yake kan rayuwa ko mutuwa.


"Sannu Safiyya Allah ya raba ku lafiya kin ji bari mu damu abin hawa mu je asibitin" Cewar Mama tana jin tausayin halin da ƴar tata ke ciki.






Safiyya babu abin da ta iya furtawa mahaifiyarta, dan yanzu haƙoranta na sama ta saka ta danne leɓenta na ƙasa sabo da tsananin azaba da take ji na ciwon naƙudar tana raya wa a ranta cewa ita dai haihuwa har kullum sabuwa take dal a leda ba a sabo da ita bare mutum ya ce ya yi ya sake.


"Ba dan babu kyau mutum ya toƙarwa kansa mutuwa ba da na roƙi na ar duniya a cikin wannan yanayin sai dai sabo da jarabawar ƙaddarorin da Allah ke jarabta ta da su ba zan biye wa faɗar mutane ba zan yi a addu'ar Allah ya kawo mini mafita domin yana ji yana kuma gani" Cewar Safiyya a zuciyarta.


"Ya Allah ka bamu ikon cin jarabawar da kake mana ni da mahaifiyata, ka fitar da ni daga cikin ƙangin jifan da mutane suke mini a kan cewa ni MAI FARAR ƘAFA ce ni nake talautar da mutane daga arziƙin da ka musu bayan babu mai talautarwa sai kai babu mai bayarwa sai kai tabbas suna magana da JAHILCI amma ni bani da yadda zan yi na fahimtar da su ya rabbi kana amsar addu'ar mai naƙuda a lokacin da take naƙuda, Allah ka amshi addu'ata ka kawo mini ƙarshen ƙunci da nake ciki ka bani miji wanda zai zauna da ni ba tare da zargin duk abin da ya rasa ni ce sila ba"




"Wayyo kin ga wannan ɗan sahun ma mutane ne a ciki Allah ka kawo mana ɗauki kar yarinyar nan ta haihu a titi" Ta jiyo muryar Mama na katse mata zancen zucin da take.


*Annur*


Idanunsa da suka masa nauyi wanda har yake wani ƙaƙance su sabo da yadda ya ji suna neman gagararsa ya yi kallon da su, a hankali ya juya ƙofar gidan da ya gan su a tsaye sai dai wayam ya hangi wurin, aikuwa da sauri ya saka hannu ya mari gefen fuskarsa dan duk tunaninsa mafarki ne ko kuma kawai ganinsu ya yi a idon zuciyarsa ba a zahiri bane ya yi hakan yana fatan Allah sa dai mafarkin yake dan ba ya son ko kaɗan yarinyar sa yake kwana da ita yake tashi da ita a cikin zuciyarsa yake tsara komai na rayuwarsa tare da ita ba ya taɓa yin mintina ba tare da ya tuna da ita ba ta zama wani ɓangare a zuciyarsa amma a wayi gari cewar ita ɗin mallakin wani ce tabbas ya san ba ƙaramin ƙunci da tashin hankali zai shiga ba. Sai dai yana maida kallonsa gaban inda hancin motarsa yake kallon tarrr ma'adanar ganinsa suka sauka a kan su, kamar yadda ya gansu ɗazu a ƙofar gidan ana riƙe da ita yanzun ma hakan ne sai dai wacce ke riƙe da ita yanzu ta shiga tsakanin kafaɗarsa saɓanin ɗazu da take riƙe da ƙugu da hannunta.


"A gaske ne Annur ba mafarki kake ba ita ce dai ɗauke da cikin haihuwa" Ya ji wani sashe na zuciyarsa ya kai masa amsar tambayarsa ta ɗazu. Idanunsa ya kafe a kansu yana jin bugun zuciyarsa na tsananta a yadda yake ji yanzu ya kasa gane haushinta yake ji ko tausayin halin da take ciki. Laimar da ya ji ta sauka a kan fuskarsa ita ya tilasta shi ɗakko hannayensa da ke dafe da kansa ya shafa fuskar da su aikuwa ya tabbatar da danshin hawayen da ke waricinsu a kan kumatunsa. Da sauri ya sanya hannayen ya share hawayen yana saka haƙoransa ya danne laɓɓansa da su idanun ya runtse da ƙarfi domin yana so ya aro jarumta domin ya samu ƙarfin gwiwar tunkararsu domin ya taimaka musu dan ya ga suna da buƙatar taimakon.




"Hasbunallahu wa ni'imal wakil, ni'imal maula wa ni'imal nasir, ya hayyu ya qayyum bi rahmatika astagis, aslihli sha'ani kullahu wala takilni ila nafsi ɗarfata ayn" Ya faɗa a fili yana buɗe idanunsa da ya runtse a hankali ya ji nutsuwa na ziyarta ruhi da gaɓoɓin jikinsa wata nannauyar ajiyar zuciya ya sauke key ya yi wa motar ya fara tuƙa wa cikin nutsuwa da ƙwarewa ya nufi wurinsu a lokacin da yake hango wacce ke riƙe da ita ɗin tana ta ɗaga wa wani ɗan sahu hannu wanda ya wuce bai tsaya ba. Sai da ya ɗan gota su kaɗan ya tsaya sannan ya iyo baya kaɗan har sai da ya zo saitinsu, cikin sauri ya fito ya gewaya sashen da suke tsaye da yake ba daga ɓangaren ƙofar da ya fito suke ba, a kan kyakkyawar fuskarta ya sauke idanunsa wanda ganin fuskar a saka shi jin wani maganaɗisu ya masa dirar mikiya dan bai taɓa yin kusanci da fuskarta haka ba yana hangota ne a kullun daga nesa, kafin ya sauke idanun nasa kan haƙoranta da ta danne laɓɓanta da su wanda ke jere rerasa tamkar masara a jikin sosuwarta. Da sauri ya ɗauke idanunsa daga kanta wanda duka wannan kallon ya yi sa ne a tsakanin sakanni, ya mayar da kallons kan matar da take riƙe da ita da yake yanzu a tsaye suke ba tafiya suke ba ya lura kamar dai ta kasa cigaba da tafiya ne shi ne suka ɗan dakata ta huta. Yana sauke idanunsa a kan matar ya mayar da su kan ƴar mamaki yake kamanninsu ɗaya sak banbanci kawai ita wacce ta riƙe ta, ta manyanta saɓanin wacce aka riƙe da yarintarta, a take ƙwaƙwalwarsa ta shaida masa cewa mahaifiyarta ce.


"Dan Allah idan ba damuwa ku shiga na kai ku inda za ku je" Ya faɗa da ɗan sauri tamkar wanda yake da in'inna. Mama da dama take neman abin hawa kamar ruwa a jallo jin zai taimaka musu babu wani tunanin komai ta ce


"To babu damuwa mun gode" Ta faɗa duk da muryarta akwai ɓurɓushin damuwa amma kallo ɗaya za ka mata ka san ta ji daɗin furucinsa, dan dama ta matsu ta gansu a asibiti ko dan ƴarta ta haihu a hannun likitoci ba a wannan tangararan titin ba dan bata san iya lokacin da za su ɗauka suna neman abin hawa ba da yake unguwar tasu tana a can cikin lungu ne. Kuma yau ko dan tana cikin halin son samun abin hawan ne duk sai ta ga babu abin hawan.




Ita kam Safiyya ko a bata ce ba sabo da ita yadda take ji yanzu za ta iya hawa ko da amalanken shanu ne dan ya rage mata wannan tafiyar da take yi tana jin tamkar ciwon ake ƙara mata. Annur kuwa da sauri ya buɗe ƙofar bayan yana riƙe da murfin har mahaifiyarta ta saka ta ciki da sauri ta koma ɗaya ɓangaren ta shiga domin ita ƴar da ta zauna ta kasa matsawa sabo da tsananin ciwo, Annur ɗin ne ya rufe ƙofar ɓangaren Safiyyar yana jin wani tausayinta na mamaye masa zuciya ganin ta kifa kanta a jikin kujera tana ta faman ambaton "Wash Allah na, Alhumma ajirni fi musibati waklifni kairan minha"


Duk da yana hana zuciyarsa ganin ita ɗin mallakin wani ce amma sai da ya ji tamkar ya je yake lallashinta. Cikin hanzari ya buɗe mazaunin direba ya shiga ya tada motar ya haura titi. Yana tuƙi yana ta saƙar jaki.


"Ashe fa bata sanni ba, yadda nake jin ta a zuciyata duk zatona ita ma hakan ne, duk a tunanina ita ma zuciyarta ta san da zaman tawa zuciyar, mafarkinta da nake a kowane bacci da zai ziyarci maganaina ashe ita abin ba haka bane" Har ya karya kwanar da za ta sada shi da wata unguwa mai suna GUSAU.


"Bawan Allah General hospital fa za ka kai mu"Muryar Mama ta katse masa tunaninsa.


"Gwara dai a je privet hospital" Ya ba wa Mama amsa hankalinsa na kan tuƙin da yake.


"Ka dai kai mu na gwabnati ba asibitin kuɗi ba wannan asibitin ba ƙaramin kuɗi za a kashe ba idan za a haihu a cikinsa"


"Babu damuwa zan biya mata komai" Ya faɗa cikin sanyin murya yana jin ko wani ne zai iya kashe ko nawa ne a kansa indai a kan lafiya ne ko taimako bare wacce yake ji dalilint ma zai iya bada abin da ya mallaka bare kuma ita da kanta.


"Matar aure ce" Wani sashen na zuciyarsa ya katse shi.


"Allah da iko yake, kai amma mun gode Allah saka da alkairi" Cewar Mama tana jinjina abin alkairin a ranta ɗazun nan

Please Login or Register in order to submit comment