Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

hadari Yakan zazzagaye gidansa, Dan dudduba abubuwa abinda ke bukatar gyara ya gyara na killacewa a killace.


Yana cikin zagayen ne kuma wayarsa dake cikin aljihunsa ta soma kara.


Koda ya duba, ganin sunan sunan Dr. Sulaiman ne ya sashi d’agawa.


Bayan sun gaisane kuma Dr. Sulaiman din yace.


“Dr batun tafiya Mascow fa, komai ya riga daya Kankama, Insha Allah nanda 2 to 3 weeks masu tafiya zasu tafi.”


“Okay.”
Kawai Rayyern din yace atakaice tare kuma da katse kiran.
Sabida iskar ta fara saukowa,
Ci gaba yayi da zagaye wajen, harta side din su Baba Maud’o kuwa saida yaje ya duba, Ganin komai normal ne yasashi dawowa cikin gida.


Wanda zuwa lokacin kuwa iskan ya taso gadan gadan.


Lokacinne kuma Abban shima ya shigo, tare da neman waje ya zauna.


Baba Mauɗo Kuma ya shiga side ɗinsu


Rayyern din kuwa windows din dake abude ya rurrufe.


Yayinda Abba kuwa ya zuba masa ido, adai-dai lokacin kuwa shi kadai yasan me yake rayawa acikin zuciyarsa da kuma abinda yake tinawa


Rayyern kuwa Bayan ya gama rurrufe ko inane, idanunsa suka sauk’a akan k’ofar falon Jannart, da iska ke bud’eshi yana rufewa shi gib da karfi.


Juyawa yayi kamar zai haura sama kuma sai ya fasa ganin Abba nata kallon shi sai kuma ya kalli wannan kofar.
Anutse ya nufi kofar tata, Koda ya isa hannunsa yasa ya tura k’ofar, tare kuma dasa kansa acikin falon, yayi hakanne kuma saboda nan ne kadai falon daya rage da bai duba ba.


Ahankali ya sauk’e idanunsa akan Jannart Wacce ke zaune akan kujera.


Sanye take cikin wata riga Marar nauyi, wanda tayi mata kyau sosai, ga kuma gashin kanta dake watse dan ko d’ankwali bata dashi.


Idanunta da hankalinta kuwa, duk yana ga tv inda take Kallon wani cartoon mai abin dariya.


Idanunsa ya d’an janye daga kallonta, had’e dajan d’an guntun tsaki, kaitsaye kuma ya wuce dan rurrufe windunan falon.


Sautin tsakin nasa ne kuma yasa Hankalin Jannart dawowa kansa, da sauri ta juyo, ganinsa da tayi ne kuma yasa ta, saurin tashi ta gyara zamanta.


Saidai kuma gaba daya babu mayafi akusa da ita, hakan yasa ta d’an takure jikinta waje daya.


Shikuwa Rayyern ci gaba da rufe windows din yayi har ya juya ya fuskanci tsakiyar falon.
Sai kuma ya ɗan juyo kansa ya kalli bayanshi ganin yadda labuyen suka a harde alamun iskane ya hardesu, ba tare daya juya ba.
Ahankali kuma ya dan Mika tsawonsa, dan son gyara labulen daya hard’e asama sabida iskar sosai ya daga hannunsa sabida windows din sunada tsawo sosai.


Hakan kuwa shi yasa rigarsa ta d’age ta ɗanyi sama.
Daga cibiyarsa zuwa kasa suka bayyana,
Dai-dai lokacin kuwa Jannart ta sauk’e Idanunta akan shatin, saman mararsa kasan cibiyarsa da kuma black boxer din dake jikinsa.


Wanda ya kara haska farar fatarsa.


Idanunta ta zubawa wajen, bata ko k’yaftawa, saboda yanda shatin marar tasa ya bayyana sosai, ga kuma hasken da wajen ke dashi kana ga wani tattausan gargasa dake kwance daga ƙasan cibiyar tasa har zuwa ƙasa sosai inda robar boxes dinsa ke manne da jikinsa har ana iya ɗan hango saman mararsa kana asalin dogon wondon kuma yayi ƙasa sosai kan mazauna sa wanda haka yasa shatin surar jikinsa bayyana.


Wani irin rawa takejin jikinta da idanunta sunayi.
Yayinda gaba ɗaya tsikar jikinta ke mimmiƙewa tsaye.
Wani irin harbawa zuciyarta keyi mai tafe da tsoron abinda idonta bai taɓa katari dashiba.


Rayyern kuwa kanshi na sama, baima san tana kallonshi ba.
Saida ya gama warware labulen.
ahankali ya d’an sauk’e hannunsa sama, tare da juyowa ya sauk’e idanunsa akanta da sauri ya sunkuyo ya kalli setin inda take kallo a jikinsa.


Fuskarsa ya tsuke tare da tab’ewa kana ya watsa mata wata Zazzafar hararanta cikin takaici yace.


“Meye? Mayya kawai cinyeni zakiyi ne?”


Da sauri ta kauda idanunta tayi daga garesa, tare da mikewa tsaye ta d’auki wayarta yayinda wata azabebbiyar kunya ta rufeta.


Ahankali ta dan Raba zata wuce zuwa daki.


Shikuwa Rayyern cikin tsautsayi, labulen da yake gyarawan ya ture wani goran ruwa dake gefe, hakan kuwa shi yasa ruwan ya malale awajen.


Juyawa shidinma yayi da niyar fita, dai-dai lokacin kuma Jannart ta iso sukayi gab da gab, batare da sun Ankara ba kuwa, saiji yayi gaba daya tsantsi ya debe sa Suuuuuu haka ya tafi idanunsa ya zaro, tare kuma da fad’awa kan Jannart, wani irin masifeffen tsorone da fargaba ya rufeta wanda yasata rumtse idanunta jin sun tafi suuuu sun f...!!!






*GARKUWAR taku ce dai MA'AURATA, da masu shirin aure, da masu jego, da yan gayu masu son k’amshi kece raini, da gyaran da zaike maimaita muku dararen forkon kuruciya*


Ko kunsan Jikinmu na da sinadaran hormones da suke taimakawa dan’adam akan komai musamman lokacin da mace take mu’amalar aure da mijinta. Mafi akasari wannan hormones din ne ke samun matsala ko su yi sanyi koma su daina aiki kwata-kwata shi ne dalilin da zai sa mace tace bata jin sha’awa ko bata san dadin aure ba. Albishirinku ina da kayan da ke taimakawa wannan sinadaran du dawo aiki tukuru don karkato miki da kimarki wajan mai gida sannan su taimakawa wannan sinadaran hormones dinki su dinka secreting din ni’ima wadatacciya da zata taimaka miki ki gamsu mijinki ya gamsu fiye da tunaninki. Note: Kayana ba sa tsinka ruwan ni’ima suna dai taimakawa hormones dinki ne su tsattsafo da ni’imar musamman wacca cutar sanyi ko dattin mahaifa ya dankarar da su ya hana su yin aikinsu yanda ya kamata. Haka zalika idan kina da kyau ki kara da wanka. Zaki iya amfani da magani na na gargajiya wanda zai gyara miki sex hormones din kullum ki kasance cikin humidify wato cikin damshi mai albarka kamar yanda ake son mace. Yana gyara miki mara.


Sai kamshi. Hajiyata daure ki fara amfani da turarena ki ji irin salon kamshin sa salo ne da zai daidaita ki da mijinki ya kankaro miki da kimarki a wajansa. Siyan na gari mayar da kudi gida.


Ga masu buƙata ga number' wayata wanda nake whatsApp dashi 09097853276 kimin mgn ta whatsApp in har kin tabbatar kin shirya saya mu dai-dai ta, kayana ba ƙanana bane, shiyasa bana harkan karanta, muddin kinsan baki shirya sayaba Please kada kiyi min mgn ki bari sai kin shirya kuɗinki a hannu, ba ina nufin kayana bana talaka bane, no akwai ƙananan set na masu karamin karfi, banson aimin mgn a ɓatamin lokacin aiyukana a shirme baki shiryaba. Shine karantan da bana so.
0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU. In kin shirya ga number ta ga kuma account number ta wanda in mun gama mgn zaki turo kudin ki, kana insa miki kaya a mota, duk ƙasar da kike kayana zaije gareki, amman fa in kinada dalilin zuwan nasune🤝🏻sayan na gari meda kudi gida.


Dan Allah masu son kaya in dai kin san baki shiryaba baki da kudi a ƙasa ki huyar dani da kanki kasa kimin mgn.


GARKUWAR MA'AURATA


By
*GARKUWAR FULANI.*
22/12/2021, 19:45 - 🥰🥰: Matar da hoton fuskarta ya cika fuskar wayar.


Wani irin harbawa yaji zuciyarsa tayi da karfi, wanda har saida hakan yasa shi zaro idanunsa waje.


Da matukar mamaki yake Kallon fuskar matar, Wacce bata da wata maraba da fuskar Ramadan, domin kuwa tsananin kaman Ramadan daya hango akan fuskarta ne ma, ya sanyashi jin wani irin bugun zuciya.


Lokaci daya kuma yaji wani irin nauyi, da kuma dattakun matar ya cika idanunsa, Yayinda daga cikin zuciyarsa kuwa, wani irin girma, kima, karamci, martaba da kuma haibar matar ne ke hauhawa cikin duk harbawar da zuciyarsa keyi.


Ganin fuskar matar ne kuma yasa, kowanne kofar gashi dake jikinsa budewa, take yaji wani irin sanyi na ratsa shi tako Ina, Yayinda kuma nutsuwa ke kara saukar masa.


“Mammy Ina kwana!!”
Ya fad’a cikin tausasa murya daga can cikin maƙoshinsa har zuwa kan labbansa.


Daga b’angaren Mammy kuwa da ta tsura masa ido bata ko k’yaftawa, wani irin abu itama takeji acikin zuciya da gangar jikinta, lokaci daya kuma taji zuciyarta tayi rauni sosai, tabbas Kallon fuskar Rayyern din da tayi ayanzu, yana tattare da wasu abubuwa da dama, ciki kuwa harda abunda ke kwance acikin zuciyarta, a mafi rinjayen tsawon shekarun rayuwarta.


“Lafiya Maud’ona ya jikin ka?”


Mammyn ta tambaya cikin boye rauni, da kuma damuwar dake kwance akan fuskarta yace.


“Alhamdulillah jiki na yayi sauki Mammy.”


Rayyern din ya bata amsa, cikin sanyi da kuma sigar tausasawa.


Riyyam-nsra kuwa dake zaune agefe idanu ya zubawa, Hamma Rayyern din nasa.


Mammy kuwa Daga can b’angaren ta, murmushi ne ya dan bayyana akan fuskarta, cikin tsananin kulawa da kuma muryar tausayawa tace.


“Allah Ubangiji ya karamaka lafiya, ya kareka aduk inda kake, ya tsare gabanka da bayanka, ya kuma nisanta ku da duk wani sharrin mutum da aljan, Allah ya baku zaman lafiya kaida iyalinka, ya albarkaci rayuwarku ya cika haske a rayuwarku Allah yayi maka al'barka!!!.”


“Ameen thumma Ameen Mammy nagode sosai.”


Rayyern din ya fada cikin nuna tsananin jin da d’insa, domin kowacce kalma da Mammyn zata fad’a, jinsa yake yana tasiri acikin zuciyarsa, Yayinda kuma yakejin wani irin farinciki na musamman yana lullub’eshi.


Mammyn ma Ganin farinciki kwance akan fuskarsa ne yasa ta jin dadi aranta, cikin kuma sakin fuska tace.


“Ya Ramadan da Mamyn ku?”


“Lafiyansu kalau Mammy, saidai Ramadan ya tafi wajen aiki, Mamy kuma tana k’asa.”


Ya bawa Mammyn amsa asake, yana mejin Karin nutsuwa na saukar masa sabida mgnar da yakeyi da itan.


“Masha Allah Allah ya taimaka, Ina Surukata Jannart, fatan itama tana lafiya.”


Mammyn ta tambaya da kulawa.


Idanunsa ya d’an lumshe tare kuma da bud’e su alokaci guda, cikin kwarin jikin daya samu yace.


“Lafiya yanzu ta sauk’a k’asa.”


Murmushi Mammy tayi, tare da jinjina kai, cikin farincikin dake da d’a mamaye zuciyarta duk bayan minti guda tace.


“To bari na bawa Zaytoon ku gaisa, gatanan duk ta tsareni da ido.”


Murmushi Rayyern din yayi dai-dai lokacin kuma, Mammyn ta mikawa Zaytoon dake gefen ta wayar.


Karb’an wayar Zayton tayi, tare da fadada fari’ar dake kan fuskarta, cikin muryarta mai dan sanyi tace.


“Hamma Rayyern.”


Saurin d’ago idanunsa yayi, ya kalli kyakkyawar yarinyar da ke magana acikin wayar, wanda muryarta tayi masa sak da wata muryar da yaji kwanannan , idanunsa ya Dan bud’e da kyau, tare kuma da zaro su waje, badon komai ba kuwa saidan Ganin still kamanin yarinyar sak na Ramadan ga kuma kamannin muryarta da waccar tsohuwar kamar dai yadda kamannin Muryar Ramadan Riyyam-nsra da ita Zayton ɗin a can wani sashin na zuciyarshi kuwa kamarsa da Riyyam-nsra ne ya fado masa “Yah salam”.
Yace a ransa a zahiri kuwa,
Idanu ya dan zubawa yarinyar, har na tsawon minti daya, kafun daga bisani ya fadada fara’ar dake kan fuskarsa, cikin sakewa yace.


“Na’am Zayton.”


Murmushi Zayton din tayi, kana cikin jin dadi tace.


“Sannu Hamma Rayyern ya jikinka, Ina fatan dai kayi sauki sosai, kuma kana cin abinci sosai ko?.”


Wani irin Murmushi Rayyern din yayi, wanda har saida kyawawan hakoransa suka bayyana, tashin farko yaji matashiyar budurwar tashiga ransa sosai.


“Jikina da sauki sosai Zaytoon, amma banason Ina yawan cin abinci saboda kada na zama ɗan lukuti kamarki.”


Dariya sosai Zaytoon ta kwashe dashi, saboda daga jin yanda yayi maganar ma kasan akwai tsokana aciki.


“Haba Hamma Rayyern ni har wani jiki ne dani, kanaga saboda banida jiki ne ma ai, Riyyam ya rainani, Hamma Rayyern Ina Auntyna Jannart take?”


Zaytoon din ta tambaya, cike da kulawa.


Murmushi yayi tare da d’an shafa lallausan sumar kansa, cikin muryar tausasawa yace.


“Tana k’asa.”


Kai Zaytoon din ta jinjina, tare kuma da dan rausayar dakai, cikin nuna kulawarta agaresa tace.


“To ka gaishemin da ita kaji, sannan please Hamma Rayyern kana kulawa da kanka kaji, Allah Ya baka lafiya mai amfani.”


Idanunsa ya d’an lumshe tare kuma da sauke Ajiyar zuciya, saboda sosai yaji dadin addu’ar da yarinyar ta masa kana har cikin ransa yake jin sonta a ransa.


Wanda har hakan yasa shi cewa.


“Ameen nagode Zaytoon.”


Kai Zaytoon din ta jinjina, Yayinda shikuwa Rayyern ya mikawa Riyyam nsra dake zaune agefe wayan.


Da sauri Riyyam da zuciyarsa ke cike da farinciki ya karb’i wayan tare da fuskantar screen din wayar, cikin kula dajin dadi yace.


“Mammyna yau kam kinga Hamma Rayyern dinmu ko.”


Kai Mammyn ta jinjina, cike da jin dadi tace.


“Kwarai kuwa Riyyam yau kam naga Rayyern.”


Tayi maganan cikin kasa da murya, ta yanda Riyyam dinne kadai zai iya Jiyota.


Jin abunda ta fada dinne kuma yasa Riyyam nsra tashi, rike da wayan a hannunsa kaitsaye ya nufi dakin Ramadan.


Shikuwa Rayyern maida kansa jikin kujera yayi, tare da lumshe idanunsa, ahankali yake lumshe idanunsa, yana mejin wani irin nutsuwa na saukar masa.


Mammy da Riyyam kuwa basu wani jima suna magana ba, Mammy ta katse kiran.


Acan Ethiopia kuwa bayan Mammy ta ajiye wayanne, Ta zame daga zaunen da take tare da durk’usawa k’asa tayi sujjada.
Na nunawa Allah tsananin jin dadinta, da kuma godiya agaresa, domin komai da yake faruwa shine ya tsarashi, shine kuma yake bawa ahalinta dama ita kanta kariya akoda yaushe.


Acan b’angaren Jannart kuwa Anutse ta kammala gasa masa roasted fish, tare da matsa masa ruwan lemon tsami aciki, kamar yanda ya gaya mata yana buk’atar abu mai d’an tsami tsami, bayan ta kammala had’a masa roasted fish dinne kuma, ta soma kokarin yi masa miyan kase kamar yanda ya buk’ata, saidai kuma kasancewar miyar tana daukan lokaci sosai, shiyasa gama ta ba yanzu yanzu ba.




Rayyern dake zaune afalo kuwa, Ganin almost 1hour ya kare ba akowa masa abincin nasa bane, yasa shi haurawa saman sofa ya kwanta.


Ahankali yake lullumshe idanuwansa, wanda da’alama kuma bacci yakeji, duk da cewar kuma yana jin yunwa, amma hakan baisa baccin yaki daukarsa ba.


Domin yana nan akwance cikin abunda bai wuce 20mn ba, bacci ya d’aukesa, kasancewar acikin magungunan da yake sha akwai mai dan saka yawan bacci.




2hours later.


Ahankali yake bude idanunsa, wanda suka shafe sama da awa biyu a kulle.


Mik’a ya d’anyi ahankali tare da ambaton sunan Allah acikin zuciyarsa.


Ahankali ya dan tashi zaune, tare dasa hannu ya shafa kan lafaffen cikinsa, da keyi masa kukan yunwa.


Numfashi ya d’an fesar akasalance kuma, yakai dubansa izuwa babban agogon dake cikin falon.


1:25 pm dai-dai agogon ya nuna masa, wanda hakan ya sashi d’an yunk’urawa ya mike.
Musamman saboda ganin da yayi lokacin sallah yayi.


Hannayensa ya zura acikin aljihun wandon dake jikinsa, kaitsaye kuma cikin tafiyar, dake nuna ya Dan samu karfin jikinsa ya nufi bedroom d’insa.


Koda ya shiga cikin bedroom din Anutse, ya soma kokarin rage kayan dake jikinsa.


Bayan ya cire trouser’n dake jikinsa ne kuma, ya d’auko wani towel ya d’aura akan waist d’insa.


Direct toilet ya wuce, inda ya had’ewa kansa ruwan wanka mai d’an d’umi.


Anutse yayi wankan nasa tare da d’auro alwala ya fito.


Koda ya fito daga toilet din kuwa wani irin kamshin shower jel ne ke tashi ajikinsa, Yayinda kuma tausassun gashin jikinsa suka kwanta lub.


K’awataccen sajen dake kwance akan fuskarsa kuwa, shek’i take tayi saboda danshin ruwa dake jikinta.


K’arasawa gaban mirror yayi, tare da d’aukan mini towel ya shiga goge ruwan dake jikinsa.
Komai nasa da nutsuwa yakeyinsa.
Hakan yasa duk wanda zai kallesa sai yaji ya burgesa.


Had’add’en body lotion d’insa ya shafa, sai kuma turaren companyn Gucci daya shafa ajikinsa.


K’arasawa gaban drawern d’insa yayi, inda ya ciro wani riga da wandon companyn Ouchpan masu kyau da taushi.


Rigar irin long sleeve d’innan ne, sai kuma wandon daya kasance tight, Wato mai dan kama jiki, amma kuma irin jeans dinnan ne, masu yanayi da crazy.


Anutse ya zura kayan ajikinsa, tare da d’aukan wasu simple shoe ya zura akafafunsa.


Masha Allah! Ba k’aramin kyau kayan sukayi masa ba, kasancewar su black colour kuma shiyasa suka k’ara bayyana, hasken da fatarsa ta k’ara.


Ahankali ya d’an ciji jajayen labb’ansa, tare kuma dasa hannunsa ya shafa cikinsa dake kukan yunwa.


Fuskarsa ya d’an kwab’e tare da karyar da wuyansa gefe, Allah ya sani yunwa yakeji sosai.
Domin har wani jiri jiri yakeji.


Wayarsa dake kan gado ya d’auka, tare kuma da nufan falon nashi kaitsaye.


Koda ya fito idanunsa ya sauk’e akan dining table din dake cikin falon, saidai kuma rashin ganin an ajiye masa abunda zaici ne yasa shi b’ata fuska, tare da d’an rausayar da idanunsa, cike da kasala da kuma yunwa ya nufo main falon nasu kaitsaye.


Acan b’angaren Jannart kuwa bata jima da kammala had’a abincin ba, kasancewar kuma garin ana d’an yanayin zafi shiyasa, Koda ta kammala had’a abincin a tray, kaitsaye part dinta ta koma.


Wanka tayi da sabulun beauty touch, wanda yasa gaba daya jikinta ya d’au sassanyan k’amshin sabulun.


Bayan ta fito daga wankanne kuma ta shirya kanta, cikin wani had’add’en English wear gown, wanda kwata kwata bashi da nauyi, kasancewar kuma rigar tight gown ne shiyasa ya bayyana duk wani shape din jikinta.
Harta kan nipples dinta kuwa saida ya bayyana, sosai rigar tayi mata kyau, tare da k’ara bayyana tsararren surar jikinta.


Turaren oud mai kamshin gaske ta shafa ajikinta, bayan ta tubke dogon gashin kanta, wanda yasha kitson da Mamy tayi mata ne kuma, ta yafa wani mayafi mai kauri ajikinta, daya rufe duk wani shape dinta, tayi hakanne kuma saboda sanin da tayi cewa, akwai maza agidan.


Juyawa tayi Ahankali kuma Cikin nutsuwa ta fice daga cikin dakin.
Kaitsaye kitchine ta nufa, dan daukan abincin da ta dafa din.


Rayyern kuwa Ahankali yake saukowa daga matattakalan steps din.


Cikin nutsuwa da kuma d’aukar hankali yakeyin kowanne takunsa.


Ahaka yake saukowa daga kan steps din.
Hannunsa daure akan cikinsa, yana shafawa tare da d’an lumshe idanunsa.




“Mamy Mamy!!”
Sunan Mamy yake kira ahankali, cikin kuma muryarsa da tayi sanyi sosai, saboda rashin k’arfi da kuma yunwan da yake fama dashi.


Adai-dai lokacin kuwa Jannart ta k’araso tsakiyan falon, Jin kamar muryar mutum ne kuma yasa ta d’aga kanta, karab kuwa Idanunta suka sauk’a akansa.


Kyawawan Idanunta ta d’an zuba masa, tare da soma Kallon shigar dake jikinsa, Wacce tayi masa kyau sosai.


Dai-dai lokacin kuma shima ya sauk’e idanunsa akanta.


Ahankali ya zame tare da zama akan steps din karshe dake kan matattakalan, idanunsa ya d’an lumshe tare dasa hannu ya dafe cikinsa, wani irin numfashi yake sauk’ewa mai d’auke da gajiya, cikin sanyin muryar dake nuna gajiyawarsa ya k’wala kiran sunan Mamy.


“Mamy tana d’akinta.”
Jannart din ta bashi amsa, tare kuma da d’auke Idanunta daga kallonsa.


Idanunsa dake alumshe ya d’an bud’e, tare da k’ara d’aura hannunsa akan cikinsa.
Wanda yayi Dan ƙugin yunwa, har saida Jannart din ta jiyo sautin.


D’an kallonsa tayi, gaba daya duk ya marairaice, ya wani zama abun tausayi, da dukkan alama Yunwa ce ke wahalar dashi.


“Meye kike wani kallona haka kamar zaki cinyeni, ni yunwa nakeji.”
Rayyern din ya fad’a yana me sauke mayun idanunsa akanta.


Wanda kuma hakanne yasa tayi saurin dauke Idanunta daga kallonsa.


Batare kuma da tace masa komai ba ta juya, Cikin nutsuwa ta wuce kitchine.


Da idanu yabi bayanta, har saida yaga wucewarta cikin kitchine din kafun ya tashi ya dawo cikin falon.


Jannart kuwa tray da plates ta d’auko, tare da dawowa falon.


Ahankali ta sunkuya dai-dai zata ajiye tray din agabansa ne kuma, mayafin dake jikinta ya zame ya fad’i.


Saurin ajiye tray din tayi tare da juyawa da sauri dan daukar gyalen nata.


Juyawan da zatayi dinne kuma yasa, Rayyern din sauke Idanunsa akanta.


Ganin inda idanun nasa suka sauk’ane kuma, ya sashi saurin rumtse su, tare kuma da kawar da kansa gefe sabida gani yayi tamkar nimples ɗin ta zasu tsole mishi ido, kasan cewar batasa bra ba yasa breast ɗinta ke tsaye kam nimples ɗin sunyi tsaye cur motsin da take yasa duk ƙirjinta rausayawa kara rumtse idanunshi yayi sabida ganin abin da yakeyi duk da ya rufe idon.


Itakuwa Jannart cikin sauri ta d’auki mayafin nata ta yafa.
Saboda kunyan da taji ya lullub’eta ne kuma yasa ta kasa d’ago kanta ta kalleshi.


Ahankali ta bud’e food flasks din, roasted fish din ta zuba masa, sai kuma miyar kasen shima da ta zuba masa shi, awani plate na daban dasa mishi tuwo kwaya ɗaya.


“Gashi.”
Ta fad’a cikin wata irin sassanyar murya, still batare kuma da ta d’ago ta kalleshi ba.


Akasalance ya d’ago kansa, tare da mik’a hannayensa alaman ta basa plate din.


Sai Alokacinne kuma ta d’ago Kai ta kalleshi, kasancewar kuma tana d’an nesa dashi ne, yasa dole saida ta matsa gab dashi.


Ahankali ta d’an ajiye guiwowinta akan tattausan carpet din dake malale atsakiyar falon.


Hannayenta duka biyu ta sanya wajen Ganin ta mik’a masa plate din.


Ak’ok’arinta nayin hakanne kuma, batare da duk sun Ankara ba, Rayyern din yasanya hannunsa ta k’asa zai karb’i plate din, hakanne kuwa yasa shi sauk’e tafukan hannayensa, akan lallausan fatar hannayenta, masu tsananin taushi tamkar auduga.


Wani irin abu Jannart taji acikin jikinta, wanda har hakan yasa tsikar jikinta mimmik’ewa, lokaci daya kuma gyalen ta ya zame zuwa kan kafad’unta, hakan yasa lallausar sumar kanta ya bayyana.


Idanunsa ya d’an zubawa gashin kan nata, Yayinda ita kuwa ahankali ta zame hannunta daga cikin nasa tare da sanya hannu ta jawo gyalen zuwa kanta.


Dai-dai lokacin ne kuma Mamy ta fito daga d’akinta.


Ganin Rayyern da Jannart din atare ne kuma, ya sakata sakin murmushi Cikin kulawa tace.




“Babana lafiya kuwa Ina sallah naji kana ta rabka min kira.”


D’agowa yayi ya d’an kalli Mamyn, cikin yanayin sigar shagwab’a yace.


“Mamy To ba yunwa nakeji ba.”


Murmushi Mamyn tayi, tare kuma da neman waje ta zauna.
Cikin sakin fuska tace.


“To Rayyern Idan kanajin yunwa, baga matarka ba, komai ita zaka tambaya ba niba, kuma ga abincin ma, Ina naga ankawo ma, Jannart sannu da aiki.”


Mamyn ta fad’a tana Kallon Jannart, da ta janye jikinta daga kusa da Rayyern din.


D’an murmushi tayi, batare kuma da tace komai ba, ta dawo kusa da Mamyn nan k’asan sofa ta zauna.


Shikuwa Rayyern d’an k’aramin bakinsa ya taɓe, kana ashagwab’e cikin kuma yanayinsa na marar lafiya, ya soma cin abincin da Jannart din ta kawo masa.


Tun aloman farko da yayi kuwa, ya lumshe idanunsa, saboda dadi da kuma gardin kifin daya ratsa shi, bugu da kari ga kuma ruwan lemon tsamin da taste d’insa, ya hadu dana kifin sai ya bada wani dandano na daban.


Ci gaba dacin abincin nasa yayi, duk da cewar bata wani sa masa da yawa ba, saboda sanin halinsa da tayi na rashin son cin abinci.


Mamy da Jannart kuwa hira suke d’an tab’awa kad’an kad’an.


Wanda hakan yasa sam basu ma lura da cewar Rayyern din ya cinye abincin ba.




“Bank’oshi ba fa.”


Maganar Rayyern din ya katse su daga hirar da sukeyi.


D’agowa Jannart tayi, karab kuwa idanunsu suka sark’e acikin na juna.


Saurin janye Idanunta daga kallonsa tayi, tare kuma da mikewa ahankali, ta k’arasa inda yake zaune.


Mamy kuwa Murmushin jin dadi tayi, tare kuma dajin wani sanyi aranta, saboda dama burinsu ne Ganin Rayyern din yaci abinci ya kuma fara sakewa da matarsa.


Jannart kuwa durk’usawa tayi agabansa, tare da daukan plate din, ta soma kokarin kara masa gasashshen kifin.


“Idan ba rowa bama tayaya za’a bawa mutum abunda ansan bazai ishesa ba.”


Rayyern din ya fad’a k’asa k’asa ta yanda, yasan Jannart dince kawai zata iya jiyosa.


Aikuwa karab maganganun nasa, suka sauk’a acikin kunnuwanta kasan cewar tana kusa dashi ainun kuma hankalinta na kanshi.


Hakan yasa Ahankali ta d’ago Idanunta ta kalleshi.


“Malama meye?”


Ya tambaya yana me tsareta da idanu da tsuke fuska.


Fararen hakwaranta ta sanya, Ahankali ta ciji labb’anta, Cikin yanayin sanyi da kuma, yanayinta mai kama da shagwab’a, ta d’an maida bakinta gefe, alaman murgud’a baki.


Idanunsa ya d’an zaro, saboda ganin abunda tayi masa din, duk da cewar kuwa hakan da tayi din, ba k’aramin k’ara mata kyau yayi ba, musamman saboda yanda lips dinnata suka sha, oil lipgloss.


“Me bakin rashin kunya.”


Yayi maganan k’asa k’asa, tare da motsa k’afarsa Ahankali, wanda kuma niyarsa shine ya take mata yan yatsun k’afarta.


Dai-dai nan kuma Abba da Baba Maud’o suka shigo cikin falon.


Hakanne kuwa yasa shi maida k’afartasa.


Jannart kuwa plate din ta tura masa gabansa, tare da komawa baya ta zauna.


“Sannu da shigowa Abba, Baba Maud’o sannu.”


Jannart din ta fad’a cikin girmamawa.


Murmushi dukansu sukayi, kana cikin jin dadin girmamasu da Jannart din keyi, Baba Maud’o yace.


“Yauwa Jannart sannu, ya gidan?”


“Alhamdulillah.”
Ta amsa tana me dukar da kanta k’asa.


Abba ma fuska asake, yana me zama akusa da Rayyern din kuma yace.


“Yauwa Jannart, sannunki .”


Baba Maud’o ne ya kalli Rayyern din cikin kulawa yace.


“Maud’ona ya jikin naka.”


Murmushi Rayyern din ya d’anyi, kana cikin sakin fuska da nuna Jin dadin kulawar Baba Maud’on yace.


“Alhamdulillah Baba Maud’o yanzu kam jikin da sauki.”


“Masha Allah Allah ya kara sauki, dama

Please Login or Register in order to submit comment