Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

gama sake shiba yace.


“Baba Maud’o an bani Rayhanna, d’azun Abba yake fadamin.”


Murmushi Baba Maud’o yayi tare kuma da Kallon Rayyern din, jikin taya shi murna yace.


“K’warai kuwa Ramadan nasani, Abbanku ya fad’amin na tayaka murna sosai.”


Murmushi mai kama da Dariya Ramadan din yayi, tare da juyowa ya fuskanci Baba Maud’o, kana ransa asake yace.


“Baba Maud’o na kasa b’oye farinciki na, hankalina ya kwanta, yanzu bani da wani sauran fargaba, kana min addu’a please Baba Maud’o, Allah yasa albarka acikin had’innan.”


Murmushi Baba Maud’o yayi wanda har saida sautin ta, ya fito fili cikin sakin fuska yace.


“Insha Allah Ramadan, addu’a kuma kullum inayinta, Allah yasa matarka ce ya kuma kawar da duk wani fitina.”


“Ameen Ameen.”


Ramadan din ya amsa, tare da mikewa kaitsaye ya nufi cikin gidan nasu, kasancewar dare yayi kuma bacci yakeji.


Washegari.


*Mascow*


Ahankali yake driving motar da yanayinsa, dake bayyana tsananin gajiyar da yake d’auke da ita da yunwa.


Kaitsaye gida ya nufa, dai-dai ya hau wani titi ne kuma, wayarsa dake gefe ta soma kara alamun shigowar kira, share wayar yayi, kamar bazai d’aga ba kuma sai ya d’auki wayar, Ganin sunan Abbansa ne kuma ya sashi d’aga wayar da sauri.


Tare dayin Sallama.


Daga can b’angaren Abba ya amsa.


Shikuwa Rayyern din cikin sanyi yace.


“Abba yasu Mamy da Baba Maud’o.”


Abba dake zaune afalo gyara zama yayi, tare da cewa.


“Duk Suna lafiya, Mamynka tace agaisheka, ya Jannart take?”


sake gyara zaman wayar akan kunnensa yayi, kana cikin nutsuwa yace.


“Lafiyanta Qalau.”


Kai Abban ya jinjina tare da cewa.


“Masha Allah To bata wayan mugaisa.”


Jin abunda Abban ya fad’ane kuma yasa shi, danna Horn din motarsa, cikin dan ladabtar da murya yace.


“Abba bana gida, amma yanzu nake kokarin komawa.”


Daga can b’angaren kuwa jin Karan Horn din mota ne, yasa Abban yarda da abunda Rayyern din yace, cikin jaddadawa yace.


“Shikenan babu damuwa, Idan ka koma saika had’ani da ita.”


“To Abba Allah Yasa kada na manta.”


Jin abunda Rayyern din ya fad’ane kuma, yasa Abban yin shiru, Cikin d’an yanayin bacin rai yace.


“Rayyern!”


Da sauri ya amsa da
“Na’am Abba.” domin jin yadda Abban ya kirashi ba wasa


“Rayyyern!!”
Abban ya kuma kiranshi a dake.
“Na’am Abba.”
Still Rayyern din ya sake amsawa cikin fargaban umarnin da za'a bashi ko fada


Abban kuwa ransa ab’ace yace.


“Rayyern ni kake cewa, Allah yasa kada ka manta hadani da matarka?”.
Da sauri ya jujjuya kansa tamkar yana gaban Abban.
Shi kuwa Abba cikin dakile murya yaci gaba da cewa.
“Bansan Wacce irin rayuwa kakeso kayi da yarinyar nan ba, Wacce irin rayuwace haka Rayyern, Jannart matarka ce fa, wallahi wallahi Allah saiya tambayeka, akan hakkinta, baka kyautawa Rayuwarta Rayyern, akan ka afarayin aiki da kasuwanci da karatune? ko kaine kawai ma’aikaci a duka duniyar nan? Meye ka d’auki kanka da bazaka kula da matarka ba? kasani ko yau ka mutu Allah zai kama ka, da rashin sauke nauyinta dake kanka, kuma kasani ban baka ita ka tafi da ita don kayi ta wofantar da ita ba, tayaya zakana irin wannan sakacin, kullum Kai baka gida, baka da lokacinta kenan?”.


Lips d’insa ya d’an taune, cikin sanyin murya yace.


“Abba kayi hakuri...”


“Nayi hakuri dame Rayyern?”.
Cikin girmamawa yace.
“Abba kayi haƙuri akan komai ma na tuba”.
Cikin fada Abban yace. “Bani zaka bawa hakuri ba kasan Wacce zaka bawa hakuri, yarinya tana zaune ak’ark’ashinka amma baka San abunda ya dace ba, tunda ta tafi batayi waya da kowa ba, ka kulleta awaje daya, sannan yanzu Ina maka magana, kana cewa wai Allah yasa kada ka manta, shikenan yayi maka kyau Allah yasa ka manta ɗin!!!”.


Abban ya fadi maganan atsawace, kuma cikin fushi lokaci daya kuma ya katse kiran.


Da sauri Rayyern yabi wayar da kallo, lokaci daya kuma yaji duk zuciyarsa babu dadi, ajiye wayar agefensa yayi, domin dai-dai lokacin ya iso gida.


Yana gama dai-dai-ta parking, ya bud’e murfin motar ya fito.


Hannunsa rik’e da waya da kuma, ledodin takeaway din da yayi musu ya nufi cikin falon gidan.


Yana shiga kuwa ya zauna akan daya daga cikin kujerun falon.


Wayarsa ya dauka ya sake dialing numbern Abban.


Har saida wayan ta kusa katsewa kuwa, kafun Abban ya d’auka.


Jin Abban ya d’auki wayarne kuma yasashi, kwantar da murya cikin sanyi yace.


“Dan Allah Abba kayi hakuri, zanyi yanda kake buk’ata.”


Daga can b’angaren Abba azafafe yace.


“Hakurin me kake bani ne Rayyern?.”


Rayyern din kuwa sanin halin Abban nasu, Idan har yayi fushi ne yasa shi, sake yin k’asa da murya cikin tausasa harshe yace.


“Naji Abba kayi hakuri Dan Allah! In sha Allah zan kiyaye zanyi yadda kukeso”.


Idanunta ta bud’e da sauri, saboda jin muryarsa da tayi, da dukkan alama kuma tasan waya yakeyi.


Saurin tashi daga kwancen da take tayi, tare da Kai dubanta ga kofar dakin nata.


Duk yau zaman gidan bayayi mata dadi, saboda kadaici, ga kuma wani irin masifaffen kewa daya cika zuciyarta, tana matuk’ar son tayi magana da Abba Kabir dinta, wannan dalilin yasa ta yanke cewar, Idan ya shigo yau din zata rok’esa aron waya.


Da sauri ta zuro da k’afafunta k’asa, batare kuma da ta damu da shigar riga da wandon dake jikinta ba, kaitsaye ta nufi falon, kanta sanye da hulan sanyi, sai kuma wani bedroom shoe mai kyau.
Riga da wandon dake jikin nata kuwa, bak’aramin bayyana shape dinta sukayi ba, duk da cewar Suna da kauri, amma sunyi mata kyau sosai, Dan saita fito kamar irin y’an matan turawa dinnan, domin saboda tsabar zaman waje d’aya, har wani yellow da ja skin dinta yayi tsabar fari.


Ahankali ta bud’e kofar dakin ta fito.


Tana fitowa kuwa yana sauke idanunsa akanta.


Saurin yin kasa da kanta tayi, tare da karasowa cikin falon.


Shikuwa tun fitowarta ya kasa d’auke idanunsa, daga kallonta saidai fuskarnan tasa babu alaman Murmushi.


Ahankali ta zauna akan carpet, tare da nannad’e k’afafunta.


Rayyern din kuwa Ganin ta zauna ak’asan san ne, yasa shi gyara zamansa, tare da kwantar da murya cikin ladabi yace.


“Abba gatanan na shigo cikin gidan.”


Yana gama fadin hakan ya mik’a mata wayan.

Ai kuwa kaman jira take har hannayenta, na rawa wajen amsar wayar.


Tana karawa akan kunnenta, tayi Sallama.


Abban ne ya amsa mata, cikin kulawa da kuma sakin rai yace.


“Jannart ya kike ya gida, fatan komai da komai lafiya.”


Ajiyar zuciya ta sauke cikin tsananin jin dadi, tace.


“Lafiya k’alau Abba yasu Mamy, Ramadan da Baba Maud’o.”


“Duk Suna lafiya, gama Mamyn naku anan kusa bari na bata.”


Cikin jin dadi Jannart din ta jinjina kai, Jin Mamy ta karb’i wayanne kuma yasa ta karyar da wuya, cikin muryar shagwab’a tace.


“Ina wuni Mamy.”


“Lafiya kalau Jannart dinmu, wallahi munyi kewarki sosai, fatan dai kina nan lafiya.”


Mamyn ta tambayeta cike da kulawa, hadi kuma dajin dadin samun Jannart din.


“Nima nayi kewarku sosai Mamy, nayi kewarku sosai da sosai garin ba dadi sam Mamy, Ina Ramadan?”


“Ramadan yana can wajen aiki, kullum saiya tambayeki.”


Mamyn ta fad’a tana nazartar kalmar Garin ba dadi sam da Jannart ɗin ta fadi, shadar zaman doya da manja sukeyi kenan.


Jannart kuwa Kai ta kwantar kana cikin sanyi, tace.


“Ayya Mamy kice ina gaishe sa, Idan kunyi waya da Riyyam nsra ma kice ina gaishesa.”


“To Jannart Insha Allah zasuji, amma Ina dai babu wata matsala kam?”


Kai Jannart din ta d’an sunkuyar, cikin tausasa murya tace.


“Eh Mamy babu komai.”


“Masha Allah haka akeso ai, amma dai kina kulawa da sanyi, Dan naji ance sanyin garin daban yake dana kowacce k’asa.”


“To Mamy.”
Jannart din ta amsa, daga hakane kuma sukayi sallama da Mamyn, sosai Jannart taji dadin wayar da sukeyin, musamman taji zuciyarta tayi sanyi.


Acikin kaso 50 na damuwarta duka sun kau, dama matsalarta kewa ne kawai.


Ahankali ta zare wayar akan kunnenta, tare da mik’o masa.


Idanunsa dake alumshe ya bud’e tare kuma dasa hannu ya karb’i wayar.


Itakuwa Jannart maida kanta k’asa tayi, tare da sauke idanunta akan yatsun k’afarsa, wanda taga yana d’an motsa su Ahankali.


Idanu tad’an zubawa yatsun nasa, bakinta kuwa Ahankali yake motsi da alama, wani abu take son fad’a.


Rayyern dake zaune asamanta kuwa, Akasalance ya Kai dubansa gareta, karab kuwa idanunsa suka sauk’a akan saman kirjinta, kasancewar rigar da ta saka din mai d’an fad’in wuya ne, shi yasa saman kyawawan breast dinta suka bayyana.


Janye idanunsa gefe yayi, tare da maida kansa ya kwantar ajikin kujera.


Itakuwa Jannart d’agowa tayi ta kalleshi, Ahankali ta d’an had’e hannayenta waje d’aya.


Cikin daddad’an murya da kuma sanyin yanayi, mai kama da rok’o tace.


“Ummmm... Dan Allah kakiramin Abbana!!!”


Ta k’are maganan cikin seizing voice, lokaci daya kuma Idanunta suka kawo ruwa.


Yanayin yanda yaji sauti da Amon muryar nata ne, kuma ya saka shi bud’e idanunsa, tare da Kallon cute face dinta.


Ahankali ya mik’o mata wayar, ba tare kuma daya ce komai ba, ya maida kansa.


Itakuwa Jannart cikin jin dadi ta mik’e tsaye, da wayartasa ahannunta kaitsaye ta nufi dakinta.


Tana shiga kuwa tayi dialing numbern Abba Kabir.
Cikin sa’a kuwa bugu biyu wayar ta shiga.


Rayyern kuwa Ganin ta shiga daki ne, ya sashi tashi shima ya wuce nasa d’akin, bayan yayi al'wala ne kuma ya wuce masallaci.


Jannart Kuwa tanajin Abba Kabir ya d’aga kiran, ta kara wayar akan kunnenta, lokaci daya taji tamkar zatayi kuka, cike da matsanancin kewa, batare da ta iya amsa sallaman da yayi mata ba tace.


“Nayi kewarka sosai Abbana.”


Daga can b’angaren Abba Kabir kuwa, Jin muryar Jannart d’insa ya sashi lumshe ido, shima cike da tsananin kewa hadi da jin dadin, kiransa da tayi yace.


“Muma haka Jannart dina, munyi kewarki sosai, ya Mascow din, fatan duk kuma nan lafiya.”


“Lafiya K’alau Abbana, yasu Aunty Dijat dasu Hafeez, Allah nayi kewarsu sosai, har ma da Daddy na.”


Ta kare maganan cikin shagwab’a.


“Duk suna nan lafiya Jannart, suma kuma sunyi kewarki, Ina Rayyern din?”


Abba Kabir din ya tambaya, Dan waigawa bayanta tayi, kamar Wacce takesa ran ganinsa sai kuma tace.


“Yana lafiya Abba.”


Kai Abba Kabir din ya jinjina, cike da jin dadin jin muryoyin juna, haka suka sha hirarsu, bayan sun kammala wayar ne kuma ta tashi tayi Sallah.




Shikuwa Rayyern bashi ya dawo gidan ba, saida yayi sallan Isha, Koda ya shigo cikin falon, zama yayi akan sofa tare da d’aukan, abincin daya shigo dashi ya danci kad’an.


Bayan ya kammala cin abincinne kuma ya mik’e tsaye, direct dakinsa ya wuce, yana shiga ya soma rage kayan dake jikinsa.


Wani fari kal din towel ya d’aura akan waist d’insa, tare da nufar toilet kaitsaye.


Duk da cewar yana jin gajiya sosai ajikinsa, amma hakan bai hanashi yin wanka anutse ba, yana fitowa daga wankan direct gaban dressing mirror d’insa ya nufa.


Wani d’an k’aramin towel ya d’auka, tare da soma goge jikinsa dake jik’e da ruwa, sosai gargasan jikin nasa suka kwanta lub, ga wani hasken fatarsa daya sake bayyana.


Body lotion kawai ya shafa ajikin nasa, sai kuma turarensa mai dadin kamshi, bayan ya gama shafa mai dinne kuma, ya saka wani wandon boxer ajikinsa.


Duk da sanyin da ake yi kuwa, haka ya nufi kan gadonsa ya kwanta, batare da ya saka riga ko rufe kyakkyawar surar jikinsa ba.


Kwanciyar rub da ciki yayi tare da jawo laptop dinsa, ya soma dannawa.


Acan b’angaren Jannart kuwa, Koda ta idar da sallan nata, kwanciya tayi akan gado, zuciyarta cike da nishadi, saboda duk wani damuwan dake zuciyarta ya kau, yau tayi waya da Abbanta da kuma su Mamy, taji komai yayi mata wasai.


Gyara kwanciyarta tayi, juyawan da zatayi ne kuma Idanunta suka sauk’a, akan wayar Rayyern da ta ajiye akan bedside drawer dinta wayar na kawo haske alamun kira.


Da sauri ta d’an dafe goshinta, saboda ita gaba daya ma ta manta da batun wayar.
Sanin da tayi cewar zai buk’aci wayarne, kuma yasa ta tashi daga kwancen, wasu takalman ta saka tare da miƙa hannu zata jawo wayar.
Garin hakane ta amsa kiran.
Juyo fuskar wayar tayi da niyar taga wake kira sai taga ashema ta amsa kiran.
Sabon number ne, da sauri ta kalli rubutun dake ƙasan number Ethiopia ta faɗa cikin nazari, alamun daga can kiran yake.
Kiran na gab da sinkewa ta amsa da addu'ar ko Riyyam-nsra ne,
Da sauri ta kara wayar a kunne jin muryar Riyyam-nsra yana cewa.
“Asssalamu alaikum, Hamma Rayyern”.
Cikin sakin fuska da jin daɗin tace.
“Wa alaikassalam Riyyim”.


“Lahh My Aunty”.
Riyyam-nsra ya faɗi cikin jin daɗi da so da mutuntaka.
“Na'am Riyyam-nsra yasu Mammy da Zaytoon.”


“Duk suna lfy, mu Aunty nayi kewarku, kullum ina son in kiraku bani da number ku Hamma Radaman ɗan wulaƙanci sai yau ya turo min”.
Hanyar fita ta nufa tare da cewa.
“Allah sarki autan Mammy i miss u so much wlh”.
Cikin jin daɗi yace.
“wlh na fiku kewa gaba ɗaya yanzu Ethiopia ta daina min daɗi ma yaseen”.
Ya ƙare mgnar yana shiga falon Mammynsa.
Ita kuwa Jannart
murd’a handle din kofar tayi ta buɗe kana ta fito kaitsaye ta nufi dakinsa.
Suna masu ci gaba da mgn da Riyyam-nsra.


Ahankali ta murd’a handle din k’ofar d’akin nasa, tare dasa K’afarta ciki.
Cikin wani irin yanayi t...!












By
*GARKUWAR FULANI*
22/12/2021, 19:59 - 🥰🥰: Akan Barrister Kabir, Wanda shigowansa kenan cikin falon, duk da kuwa yaji abunda suke fadad’in amma saiya yi kamar bai ji komai ba.


Ganinsa da sukeyi dinne kuma yasa Dr Lukman da kuma Alhaji Abdu Tababa yin shiru, tare da soma kallon kallo atsakaninsu, Wanda kuma hakan alamace dake nuna zallan rashin gaskiyarsu.
Alhaji Bala tambari kuwa wani irin kallon ƙasa-ƙ’asa yakeyiwa Barrister Kabir ɗin mai kunshe da alamomi masu tarin yawa.


Alhaji Idi Sale daka ta kuwa wani kallo ya shiga yiwa k’anin nasa, irin kallonnan mai d’auke da ma’anoni daban daban.
Saidai kuma gudun kada Barrister Kabir din ya zargi wani abu, yasa Alhaji Idi Sale dakatan ya d’anyi gyaran murya yace.


“Barrister kazo adai-dai domin kuwa magana muke akan yanda zamu fad’ad’a kasuwancinmu, musamman company’s dinmu, way’anda ayanzu shareholders dinmu suka soma janyewa, badan komai ba kuma saidan sabon Companyn Mainasara wanda ayanzu mafi yawan y’an kasuwa dake cikin jihar Kano, dama na sauran garuruwa, harda mak’otanmu, suka zuba hannayen jarinsu acikin companyn, Wanda hakan kuma bak’aramin tawaya ya kawo ga namu companyn ba.”


Ya k’arasa maganan a dai-dai lokacin da Barrister Kabir ya gama, k’arasowa cikin falon tare da neman waje ya zauna, akan d’aya daga cikin kujerun falon.


Ajiyar zuciya Barrister Kabir ya sauke, kafun ahankali ya d’ago ya soma kallon kowannensu d’aya bayan d’aya.


“Hakan yana da kyau tabbas, domin ni kaina nafahimci cewar, shareholders din companies dinmu sun soma ja baya, musamman kamfanoninmu na kayan masarufi.”


Ya ida maganar yana me kallon Dr Lukman da yake sharce gumin daya kwanta agoshinsa, Wanda kuma Gumi ne na tsananin rashin gaskiya da tashin hankali domin haka nan yake jin fargaba in ya kalli ƙwayar idon Barrister Kabir ɗin.


Alhaji Idi Sale Dakata kuwa, hannunsa yasa ahankali ya dafe zuciyarsa, cikin wani yanayi mai wuyar nazarta yace.


“Shin ka samu wani labari adangane da b’atan Jannart kuwa?”


Yanayin yanda yayi tambayar ne, yasa Barrister Kabir d’ago Kansa ya kalli Yayan nasa.


Tsawon mintuna biyu kafun ya girgiza Kansa, kana cikin nazartar fuskar yayan nasa yace.


“Babu wani labari akan b’atan Jannart, amma dai nasan y’an sanda na bayyane da kuma ss suna nan suna aikinsu akan hakan.”


“Allah yasa aganta, domin kuwa mahaifinta yana cikin tashin hankali da alhinin rashinta, kuma ganinta ne kadai zaisa ya warke daga wannan ciwon daya kamashi.”


Engineer Alkali Baba ya fad’i hakan, yana me kallon Alhaji Idi Sale Dakata.


Barrister Kabir kuwa Kansa ya sunkuyar, tare da sakin wani b’oyayyen murmushi.


Acikin ransa kuwa cewa yayi.


“Lallai watarana Gaskiya za tayi halinta tabbas, watarana fuskokin da suke dauke da murmushi ayanzu, sune wanda zasu kasance cikin bakin ciki da danasani mara amfani da tarin kunya.”


Da alama kuma su Alhaji Idi Sale Dakata’n, sun manta cewar da Lawyer suke tare, Wanda ko yaya aka fadi maganar daba gaskiya ba zai iya gane ta hanyar nazartan ko wanne harafi da ƙididdigansa filla-filla.


Daga haka kuwa Shirune ya biyo baya atsakaninsu, inda kowannensu ya kasance da abunda yake sakawa acikin zuciyarsa.


Musamman Alhaji Idi Sale Dakata, Wanda zuciyarsa ke ci gaba da tsara plan din dake yawo acikin tunaninsa, shi kad’ai yasa tsarinsa haka kuma shi kad’ai yasan inda ya dosa.
Abubuwa uku dake cikin zuciyarsa lallai tabbas saiya cimmasu, koda kuwa hakan yana nufin rasa wasu rayukan.


Yayinda Dr Lukman kuwa babu wani abu dake sukar zuciyarsa akullum, face nasara da kuma d’aukaka had’i da cigaban da Dr Rayyern Bashir Muhammad Mainasara ke samu, musamman akan aikin likitancinsa.
Tabbas wuta ne keci a zuciyar Dr Lukman, Wanda ayanzu bashi da wani buri da ya wuce, kawar da Dr Rayyern a doron k’asa kamar yanda ya alk’awarta wa kansa, cewar watarana tabbas za’a wayi gari babu Dr. Rayyern Bashir Muhammad Mainasara.


Shi kuwa Barrister Kabir abunda ke cikin zuciyarsa, ingantaccene wanda ya tabbata watarana sai ya faru, matukar yana raye to Tabbas saiya Bayyana b’oyayyen sirrin da aka bunne tsawon shekaru.


*Ethopia*


Riyyam nsra.
Munafukan idanunsa da sukayi ja sosai ya lumshe, tare da sake gyara kwanciyarsa, kana ahkanli kuma ya sake tura hannunsa cikin mararsa.


Batare da an d’au koda minti daya ba kuma, ya sake bude idanun nasa inda ya sauke ganinsa, akan wata kyakkyawar yarinya wacce hoton videon ta ya cika gaban wayarsa.


Sosai yake kallon yanda yarinyar ke motsa duk wata gab’a najikinta da sunan wai rawa.


“Shonah!”
Ya karanta sunan da yarinyar ke amfani dashi, wacce kuma da dukkan alama musulmace, saidai wayewa da kuma rudin shaidan hadi da sharri da illan dake cikin TIKTOK yasa ta koma tamkar y’ar arna marassa tarbiya da al'k’ibballah.


Sake gyara kwanciyarsa yayi, tare da kurawa breast dinta idanu, kasancewar shatinsu ya fito ta cikin t-shirt din dake jikinta.
Duk da cewar yau yafara ganinta a TIKTOK din, amma tayi masa sosai, domin all videos dinta duk na banza ne, Dan ko sau d’aya babu inda ta saka kayan kirki wanda duk tawagar ibilasan TIKTOK d’in kanyi haka wai dan a samu Follower dan yin tutiya da al'ummar da zasuyi ta ingiza su ga hanyar halaka mai fad’i musu gsky suyi mishi taken Allah ka aika munafukinmu can nesa... Sun mance daga bakin magautanka ko mahasadanka kake saurin gane kurenka har ka gyarashi in kana da shi ɗin in kuwa hasadace kawai tasa a sukeka ko a ɓatanci gareka to ai su mahasada gishirine na ci gaban rayuwan ɗan Adam, domin idan Ubangiji yayi nufin ɗaukaka wani bawa nasa to a harsunan magautanka mahasadansa zai ɗaukaka shi!


Bio dinta daya karanta ne kuma yasa shi, following dinta saboda yaga tasa tutar Nigeria, Wanda kuma hakan alamace dake nuna cewar y’ar Nigeria ce.


Take kuwa yaga tayi following dinsa back, before 10 second kuma saiga DM dinta ya shigo wayarsa sabida ganin sunanshi yayi following nata kawai ya isheta abin al'fahari domin sanuwarsa da shuhurarsa ya wuce zaton mai zato.


Idanunsa yad’an zazzaro take kuma yasaki wani irin shu’umin murmushi, ko kusa baikawo aransa cewar zatayi accepting nasa haka ba dan shi kansa yaga kanta yana hayak’i shaidan na kad’a mata tana juyawa da bin linzaminsa.


Shiga cikin DM din nata yayi, inda ta rubuta masa sak’o kamar haka.


“Hey handsome how are you?”.
Inda akarshen rubutun tasa masa wani d’an banzan Emoji dake nuna kwarewarta a iskanci.


Ganin emojin ne kuma yasa Riyyam sake sakin murmushi, cike da shauki ya rubuta. “Sexy.” tare da tura mata, Dan yasan zata fahimci abunda yake nufi dan yasan mafi akasari duk kanwar jace, tabbas akwai na gari a TIKTOK amman basu da yawan watsastsun more especially in akayi duba da shigar mutun da kalamansa sabida mafi aksarinsu tawagar TIKTOK sun zama tamkar rainon karnuka.


Aikuwa take tafahimta.


“You want?”


Ya karanta sakon da ta turo masa, inda jikinsa na b’ari yayi mata reply da.


“Yeah I want.”


Emojin murmushi ta turo masa, take kuma saiga wasu bad videos dinta sun shigo wayar tasa, tare da message na “Where are you living?”


“Oh My God she’s hot”


Riyyam din ya fada da d’an karfi, tare da zaro harshensa ya lashi labb’ansa, tare da kurawa videon da yake kallo din idanu.


Yanda yaga yarinyar naked ya masifar tayar masa da hankali, take yaji yanason yin video call da ita.


Hakan yasa cikin gaggawa ya tura mata number dinsa, tare da sawa ta turo masa nata.


Da hanzari yayi dialing numbern nata to face time.


Dai-dai lokacin kuwa Zaitoon ta turo kofar dakin nasa, bakinta dauke da sallama.


Amatukar zabure ya kifa wayartasa, tare da juyowa yana kallon Zaitoon din, da munafukan idanunsa na rashin gaskia.


Itama Zaitoon din kallonsa tayi, ganin da tayi duk yana zabure ne kuma yasa ta, watsa masa harara tare da cewa.


“Are you okay?”


“Yea I’m okay, mekika shigoyi dakina?”


Riyyam din ya tambayeta yana me hade fuska, tare dayin rau rau da idanunsa.
Alamun dai rashin gaskiya.


“Oho mezanzo nayi ad’akin dan rawan TIKTOK? Mammy ne tace nazo nakiraka.”


Zaitoon din ta fada tana me hararansa, batare kuma da tajira maizaice ba, ta juya tayi tafiyarta.


Tana fita kuwa Riyyam din ya zaro wayarsa, tare da ci gaba da watching videon yarinyar.


Sam kwata-kwata ajikinsa baya majin cewa, hakan da yakeyi badai dai bane, bayan kuma ada ba haka yake ba, fitowar TIKTOK ne duk ya sauya masa rayuwa, kuma ayanzu yanajin cewa yakai Namiji, yaje stage din da yakejin Mace ne cikon rayuwa.
Subahanallah saboda waya kawai arana, baisan irin yawan zunuban da yake dibarwa kansa ba, nau’in Zina babu Wanda bayayi kamar dai yadda matan TIKTOK ke bada dama ta wurin bayyana surar jikinsu, yayi zina da ido sannan yayi na baki, still kuma yazo yayi na gaskiya.
Wanda a zahirin gsky taɓararsa ma da d’an sauk’i akan wasu da suka meda man hajar dandalin yad’a fasadin luwad’i da maɗigo ya subahanallah.


Haka dai ya b’ata lokaci yana kallon videos din yarinyar, batare daya tuna cewar Mammy nakiransa ba.


Wannan itace banzar d’abi’ar Riyyam nsra wanda, Mammy dama y’an uwansa basu san yanayi ba.


Wanda kuma hakan k’addarace kana kuma rubutaccen Al’amari wanda Allah Ya rubuta, dole kuma saiya faru.
Ta k’ark’ashin sakacin iyaye da sakarwa yaransu wayoyi kara zub’e suyi tsiyar da suke so.


Kano Nigeria


Murmushin Mamy tayi tare da kallon Ramadan da yake gyara zaman hulan kanshi sai k’amshi yakeyi.
“Toh naga dai alamun sauri kakeyi, kaje kawai sai ka dawo muyi mgnar!”.
Cikin jin dad’in hakan ya saki murmushin da fuska tare da cewa.
“Dad’ina da ke Mamy na saurin ganuwa, sai na dawo”.
Ya ida mgnar yana mai fita.
“Allah ya kikaye hanya, ka gaida min surkar tawa”.


“Amin zataji”.
Ya faɗi yana fita.


Yana fita kai tsaye side d’in Baba Maud’o ya nufa,
Kai tsaye cikin d’akinsa ya nufa, yana mai sallama a saman lips ɗinshi.
Wani irin masifeffen bugun zuciya Baba maud’o yaji, lokacin ɗaya cikinsa ya fara ɓari miƙewa yayi cikin zafin nama, ya juyawa ƙofar shigowa baya,
da sauri Ramadan ya tsaya ganin alamun yanzu Baba Maud’on ya fito wonka don dashi sai gajeren wando,
shiru yayi baiyi mgna ba haka shima Ramadan sai dai idanunshi da ya zubawa k’eyan Baba Maud’on cikin wani irin yanayi,
Shi kuwa Baba Maud’o hannunshi yake miƙa wa gefen gadon inda rawanin buzayensa yake, yana mai son jawowa,
Da sauri ya kuma kauda kanshi jin muryar Ramadan na cewa.
“Afwan Baba Maud’o dama zan sallamekane zan tafi gun Rainaha”.
Cikin daburtacciyar murya ba tare da ya juyoba yace.
“Masha Allah Ramadan sai ka dawo”.
Kasake Ramadan ɗin yayi ganin sam Baba maud’on yaƙi juyowane yasa ya juya ya fita.
Mota ya shiga kai tsaye ya nufi gidansu Raihanan.


*RUSSIA*


Mascow.


5:30 pm.


Dai-dai daya bayan daya suke fitowa, daga cikin babban theatre room din, da suka kwashe sama da awanni 4 acikinsa, suna gudanar da Kidney surgery.


Ahankali yake tafiya yana me kokarin Zare, hand gloves din dake hannayensa.


Wassai yakejin zuciyarsa, babu wani damuwa domin yayi archiving duk wani abunda yakeso, domin kamar koda yaushe yauma yayi nasara akan surgery din da sukayi, kuma shi yayi winning.


Wanda hakan yasa matsayinsa ya zama na musamman akan sauran Doctors, din da sukeyin aikin tare.


Dr Pola Denemith wanda shine babban shugaba awajen. ne ya karaso inda Rayyern din yake, tare da mika masa hannu, cikin jinjinawa yace.


“Congratulations succeeder”.


Murmushi Rayyern din yayi, Wanda ya bayyana tsananin kyawunsa, hadi da zallan kwarjini da kuma haiban da yake dashi.


Cikin muryarsa ta nutsuwa akoda yaushe yace.


“Thank

Please Login or Register in order to submit comment