Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

nace bari nazo na duba ka.”


Baba Maud’on ya fad’a yana me mik’ewa tsaye.


“Ameen Nagode Baba Maud’o.”
Rayyern din ya amsa.


Shikuwa Baba Maud’o juyawa yayi ya fice daga cikin falon.


Hakanne kuma yasa Abba ma tashi yabi bayan Baba Maud’on.


Dai-dai lokacin kuma Riyyam nsra ya fito falon, hannunsa rike da wayarsa.


Anan kusa da Rayyern ya zauna, Ganin kuma irin delicious din da Rayyern din keci ne, yasa shi dan tand’e baki.


Cikin dan yanayin zak’uwa yace.


“Gaskiya Hamma Rayyern kana cin dadi, tun Ina sama nake jiyo kamshin abincin kan nan gsky My Aunty kina mana ƴan ubanci.”


Hararan wasa Rayyern din ya d’an watsa masa, shikuwa Riyyam din wayarsa ya ciro, tare da dannawa numbern Ramadan kira.


Mamy da Jannart kuwa murmushi sukayi.


Bugu biyu kuwa Ramadan din ya dauka.


Cikin zak’uwa Riyyam din yace.


“Albishirinka Hamma Ramadan, yau kada Kaci komai awaje, ka dawo gida Aunty Jannart irin miyar ranan tayi.”


Daga can b’angaren Ramadan yace.


“Ai ganinan ma Ina dawowa, kace Aunty Jannart ta ajiyemin nawa.”


“To.”
Riyyam nsra din yace, daga haka ya katse kiran.


Rayyern kuwa d’ago kansa yayi ahankali, tare da Kallon Mamynsa cikin sanyi yace.


“Mamy d’azu munyi waya da Mammyn Riyyam tace tana gaidaki.”


Murmushi ne ya bayyana akan fuskar Mamy, cikin jin dadi tace.


“Masha Allah Ina amsawa.”


Juyo da kallonta ta kumayi inda ta sauke idanunta akan Riyyam nsra.
Cikin nuna kulawa tace.


“Ni kam Riyyam baka tab’a had’ani da Mammynka ba ko awaya, bani hotonta na gani mana Idan kana dashi.”


Murmushi Riyyam nsra din yayi, cikin tausasawa da jin daɗin satan amsar da Mamy ta bashi mgnar ta yace.

“Ayyah Mamy yi hakuri, amma babu hoton Mammy awayana sabida randa zanzo na sai sabuwar waya kuma na bar waccar a gida.”


Ya kare maganar yana dan karyar da wuyansa gefe.


“To had’ani da ita mana muyi video call.”


Mamyn ta fad’a tana me kallonsa.


Wani irin bugawa yaji kirjinsa nayi, wanda hakan yasa shi sadda kansa k’asa.


“Tayaya zai had’a Mamy da Mammynsa video call?”


Yayiwa kansa tambayar.


Mamy kuwa Ganin yayi shiru ne yasa ta cewa.


“Lafiya kuwa Riyyam inayi maka magana kayi shiru, had’ani da ita muyi magana.”


Kansa ya d’an langwab’ar gefe, cikin kuma yarda da k’aryar da zuciyarsa ta tsara masa yace.


“Ayya Mamy d’azu muna waya dasu, naga kiran ya katse, ashe wai Zaytoon ce ta raɗa mata wayar a ƙasa, dana sake kira kuma baya shiga, saida ga baya Mammy kecemin wai, cameran wayan nasu ya samu matsala, saidai ko voice call.”


D’an Jim Mamyn tayi, kamar me nazartar wani abu kuma saitace.


“To Wayar Zaytoon fa?”


“Ai Zaytoon bata da waya, Mamy ta hana ta rik’e waya, tace wai bayanzu ba.”


Ya k’are maganan yana me waskewa, gudun kada kowannensu ya fahimci cewar bashi da gaskiya.


Kai Mamyn ta jinjina, kana cikin gamsuwa da bayanan nasa tace.


“Ai hakan da Mammyn naka tayi shine daidai, barin waya ahannun y’a Mace budurwa adai-dai wannan lokacin hatsari ne, kodan wannan babbar masifa ta Tiktok dinma, saidai Wacce Allah Ya kare kawai.”


Murmushi Riyyam din yayi, cike dajin dadin yanda karyar tasa ta samu karb’uwa kuma ya samu sun kauda mgnar ma.


Rayyern kuwa mik’ewa yayi, saboda dama ya kammala cin Abincin.
Anutse ya nufi sama, saboda surutun nasu na damunsa.
Har ya fara haurawa yace.
“Uhum Mamy ai su kansu yara masa basu waya da barinsu yin shuhura a social media babbar masiface, yanzu kigafa yadda Riyyam-nsra yake kamar mazari, wanda a baɗini kuma Allah ne kaɗai yasan me yake shukawa”.
Ya ida mgnar ya juyowa ya tsurawa Riyyam-nsra ido.
Wanda shi kuwa yayi wani irin firgita dan sai yake ga Hmma nasu ya gane komai da yakeyi ne.


Mamy kuwa cikin yarda da yaron tace.
“A babu ma abinda yakeyi”.
Uhum kawai yace yaci gaba da tafiyarsa.


Tashinsa awajenne kuma yasa ita kuwa Jannart sakewa, bayan ta gyara wajen da yaci abincin ne kuma ta dawo, suka zauna ita da Riyyam hira suka sha sosai, suna nan zaune dai har Ramadan ya dawo.


Bayan sunyi sallan magriba ne kuma, Jannar din ta zuba musu sauran ragowar abincin Rayyern din sukaci.


After 3day.


Alhamdulillah acikin kwanaki ukun nan, jikin Rayyern ya k’ara sauki sosai, domin babu laifi yanzu ya samu karfin jikinsa.
Domin yana iya fitowa har can compound din gidan, wajensu Baba Maud’o, sannan har motsa jikinsa yana iyayi yanzun.

Ab’angaren Jannart kuwa tun ranan bata sake sakashi a Idanunta ba.
Sosai kuma takejin dadin zaman gidan, musamman ayanzu da duk sanda Ramadan ya dawo, sukan zauna suyi hira sosai, harma game sukeyi.


Ga kuma wayarta dake d’ebe mata kewa, kasancewar ta bud’e Twitter, Instagram, da kuma Tiktok, da wani suna na daban, bawai original account dinta da kowa ya sani ba, sunan da ta bud’e dashi kuwa, ba wai normal sunane da kowa zai gane ba.
Akomai nata da Unique kawai take using.




Acan b’angaren gidan su kuwa.


Har dai zuwa yanzu babu wani mai gamsashshiyar nutsuwa acikinsu, more especially Alhaji Idi Sale dakata.
Momy da kuma Abdull, wanda abun ya had’e musu biyu, rashin lafiyar Dadyn da kuma b’acewar Jannart.




Yanzu ma zaune su Alhaji Idi Sale Dakata, Alhaji Abdu Tababa, Dr. Lukaman, da kuma Barrister Kabir, Alhaji Bala Tamnari suke acikin katafaren dakin ganawa'n Alhaji Idi Saleh Dakata.


D’ago da kansa yayi ya kalli Alhaji Bala Tambarin, cikin dan yanayin damuwa yace.


“Wato Alhaji Bala, har yau ina mamaki kan al’amarin daya shafi yaron nan Rayyern, musamman akan company’s d’insa, akullum hab’aka abubuwan nasa sukeyi, na kuma rasa gano tushe da madafan arzikinsa, saboda ayanzu haka nasa ayimin bincike akan sabon companynsa, ankuma tabbatarmin da cewa, zuwa yanzu ankawo komai da komai na amfani acikin companyn, kama daga kan engines dama dai sauran abubuwa, saboda har anfara sarrafa kayayyakin abinci, amma naji ance bazasu fara fitar da kayayyakin nasu ba, sai farkon shekara mai kamawa ina mamakin dukiyar yaron dan a iya wannan Company nasa zaikai biliyoyin kuɗi da sunfi shekarunsa yaushe aka haifesa har ya yarasu.”


Kai Alhaji Bala Tambari’n ya jinjina, cikin gamsuwa kuma yace.


“K’warai kuwa nima nasan da haka Alhaji Idi Saleh Dakata.”


Gyara zama Alhaji Abdu Tababa yayi, kana cikin takaici yace.


“Wannan abu ni Ina mamakinsa, amma Meyasa ba zaka dakatar dasu ba Alhaji Bala? Naga Kaike kula da duk wasu harkan filayen da ake gine gine masana'antu, ni har yauma ina mamakin tun farko ma meyasa ka basu takardar izinin fara ginin companyn?”


Murmushi Alhaji Bala Tambarin yayi, saboda shi yasan meya sani, kamar yanda suka kasa gane waye, Dr. Rayyern Bashir Muhammad Mai-nasara din, to shima hakane.


Dr. Lukman ne ya cab’i zancen da cewa.


“Gaskiya dai kam, amma ni yanzu sauki na daya, abubuwanshi na harkar asibiti gaba daya sun dakata, yafi maida hankalinsa, akan abubuwan da suka shafi companyn.”


Barrister Kabir dake zaune agefe ne ya saki wani murmushin jin daɗi.


Tare da gyara zamansa, Cikin nutsuwa yace.


“Anaka tunanin kenan Dr. Lukman, domin da alama baka da labarin cewa, acikin kwanan nan akwai likitotinsa da ya ware kusan guda biyar dashi na shida, way’anda zasu tafi Russia Mascow yin wani course, baya ga haka kuma Idan sunyi wannan course din sun dawo, akwai ci gaba na musamman wanda za’a samu, a hospital din nasa, domin zasuje suyi course dinne, akan abunda ya shafi dashan k’oda, dana zuciya aikin ƙwaƙwalwa da juyen jini ga masu cutar sikila uwa uba da safarar tunanin kwakwalwar ɗan Adam, dama dai sauransu, kuma Insha Allah zasu kawowa K’asa cigaba.”


Idanu Dr. Lukman ya d’an zazzaro, cikin bakinciki takaici da kuma kunci yace.


“Wallahi kwata-kwata Barrister bani da wannan labarin, kuma ai wannan plant din nima, najima da tsarashi azuciyata, wanda kuma nakeso na aiwatar acikin hospital dina, amma kuma sai next year nakeson haka, why? Why? Wannan yaron ya shigemin hanci, komai zanyi saiya rigani kafin ma in tuna abu shi yayi, na shiga uku Anya zai barni na ci gaba arayuwata kuwa?”


Dr. Lukman din ya fad’i haka cikin tashin hankali, saboda ya fahimci cewa, duk saurinsa Dr. Rayyern din yana gaba dashi akan komai.


Boyayyen Murmushi Barrister Kabir yayi, tare da maida kansa ya ajiye ajikin kujera, yayi hakanne kuma saboda yanda yaga, hankalin Dr. Lukman din ya tashi sosai.


Alhaji Bala Tambari kuwa, gyara zamansa yayi...!






*Albishirinku! Ma'aurata, GA GARKUWAR KU nan tafe muku da tsarabobi na musamman gareku ma'aurata daga cibiyar mgnin mata mai taken GARKUWAR MA'AURATA*


NI DAI AYSHA ALIYU GARKUWA.
Ina matukar mamakin wani irin lokaci da ya riske mu mai wahalallan fassara. Kullum dai magana daya ce, akan ma’aurata, fada, rashin jituwa, mutuwar aure, akan kuskure kalilan, rashin kula, rashin yi wa juna uziri. Toh wai duk me ya janyo hakan? Na zurfafa a tsananin tunani hakan ya tilasta min bincike mai tarin yawa wanda ya kai ni ga gano inda matsalar take? Shin yar’uwa ke macece amma kin san wacece mace ku? Kin san me ake kira mace kuwa? Mace ita ce matar da take zama iyali a wajan namiji ta zame masa bango, sanyin idaniyarsa, ta zame masa gata da farin cikin rayuwarsa ta zame masa ruwa abar kore ƙishinsa ta zame masa mayafi mai karesa daga gigitar kadaice, ta kuma dorar da mijinta kan turbar gaskiya, ta kashe masa jiki da salonta ta rikita shi da baiwa da ni’imar da Allah ya bata idan har ta san hanyar mayar da kanta sabuwa dal awajanta, wato kullun takasance masa tamkar amarya har ya kasa tantance daren amarcinsu da sauran dararen rakun rayuwar su.


Wannan ita ce mace. Ina da wata saukakkar hanyar da zaki zama abar so da kulawa da soyayya a wajan mijinki ta hanya mafi sauki, 09097853276 hanyar ita ce ki gwada amfani da kayana na gyara ki gani, ina mai tabbatar miki da in sha Allahu sai kin dara da murna sai kuma kin gode min. Kayana kaya ne da aka yi shi da zallan itacanmu na gado marasa illa a cikin jikin dan adam musamman mace, kaya ne da suke taimakawa (sex hormones 😍) dinki.
Misali kina kallon India😘, hollywood, Asian film🥰 kina ganin yanda mazansu ke nunawa matansu tsananin soyayya kamar su ba su kyautar ransu!?
Saboda me hakan? Saboda suna sadaukar da lokacinsu wajan gyara jikinsu da kayan da ke tsattsafo da ni’ima cike da tsukewa, kayan nan kuma ana yinsu ne zallar magungunan gargajiya wanda ba su da illa domin haɗine na ingantattun itatuwa da yayansu.
Ina baiwar Allahn da miji ke daure mata fuska babu hirar arziki?
Zo ki ji yar’uwa zan baki gumbata da zallar gari wanda aka yi su da nagartattun itacen da ke da matukar amfani a jikin mace. Gubar ciko, gumbar tsalle dole, gubar da ba'a baiwa mai kishiya, garin maɗi, garin mallaka, tsumin goron tula, tsumin tsartai, tsumin maratsi, pala-pala butar sirri, kwanon k’asaitacciyar mace, furar mata madararta gareki Hajia takenta sha yanzu mgni yanzu,
Ina mata masu fama da sanyi? Sanyin mara ki zo na hadaki da magani na na sanyi wanda yake wanke mara ya fitar da duk wata cuta da ke samun mazauni a wajan.
Ina da ciccibi mai kyau. Ina da hadin amare mai kyau wanda zai gyara yarinya ya kankaro mata kimarta akwai hadin mai jego wanda muke yinsa na asali inada kekkyawan Hadi maida tsohuwa yarinya.




Akwai daya bangaren wato *KAMSHI*
Kimarki gyaranki da kamshinki. Matan da suka gane suka san yanda za su kankaro da mutunci su ne masu amfani da kayan gyara da kuma sanyaya jikinsu da kamshi, ina da turaren wanka da na bandaki na daki na jiki da na kaya dana tsuguno kamshin turarena na dabam ne mai sanyaya zuciyar wanda ya shaka ina da kayan kamshi na amarya da na maijego da na uwargida da dukkan macen da take kokarin mayar da kanta mai daraja a idon kowa ta zamo sarauni a idon mijinta, akwai shu'umar humra, sayan na gari maida kuɗi gida, banda karanta yayin gyara Hajia.


Zaku iya samun kayyakina a duk garin da kike, zakiyi min mgn ta whatsApp number na 09097853276 domin yin zaɓinki, ko karin bayani, zaki tura kuɗin ta account na 0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU in mun gama mgna zan sa miki kaya a mota yazo duk garin da kike, in baki shirya saya yanzuba Please kada mu wahal da juna ki bari sai kin shirya kafin kiyi min mgn.


🤝🏻🥰😘 Daga taku AYSHA ALIYU GARKUWA
*(GARKUWAR MA'AURATA)*




By
*GARKUWAR FULANI*
22/12/2021, 19:45 - 🥰🥰: Jannart suuu suka tafi, cikin tsoron kaiwa k'asa Jannart ta sanya hannayenta akan damatsan sa, tare da rikesa k'am, kana ta rumtse Idanunta da masifan karfi.


Aikuwa duk da yin hakan da tayi bai hanasu kaiwa k'asa ba, cikin abunda bai wuce 1second ba gaba d'aya duk suka zube awajen saidai shi ya koma kasa ita a sama.


"Auchhhhh!!"
Rayyern ya fad'a da k'arfi tare da rumtse idanunsa.


Wanda ya fadi hakanne kuma saboda buguwan da yayi, ga kuma Jannart da ta fad'o saman k'irjinsa wacce tsoro yasa ta maƙalƙale masa.


Jannart din ma wani siririyar k'ara ta saka, musamman da kirjinta ya bugu ajikin nasa kirjin sosai taji tsayayyun breast ɗinta sun bugi kirjinsa.


Atare duk suka rumtse idanunsu, saboda zafin fad'uwar da sukayi ne kuma, yasa duk kowannensu ya kasa yin k'wakk'waran motsi.


Still Har yanzu kuwa hannayen Jannart nakan dantsen hannunsa, tayi masa wani irin rik'o dake bayyana tsoronta.


Yanayin yanda suka kasance ahaka dinne kuma yasa, d'an kunnen Jannart din mak'alewa da gaban rigarsa, Ahankali ta d'an d'aga kanta, saidai jin rigar tasa ya kama d'an kunnenta ne yasa ta kasa d'agowan, saboda wani zafi da taji.


Dai-dai lokacin kuwa gaba d'aya duk wani haske dake cikin d'akin ya d'auke, saboda d'auke wuta da akayi sabida iskar data turbude garin Kano baki ɗaya, ga kuma yanayin garin kwata kwata babu wadataccen haske yayi duhu.


Shi kuwa Rayyern al'amarin ya magaga ya zarta zatonsa ya kama hanyar wata fitinenneyar duniyar da bai san sa ita,
Sabida yadda yake jin wasu irin masifaffun abubuwa suna tsikarinsa sabida yadda yaji sauƙan Cabɓullenta bisa nasa ƙirjin.
Wani irin maraitaccen numfashin yaja can ƙasan maƙoshinsa tare cusa kanshi tsakanin wuyanta da kafaɗarta wani numfashin ya kuma sha sabida sassayan ƙamshinta da ya zuƙa.


Idanu Jannart ta d'an rumtse, cikin gajiya da kuma zafin da take d'anji ajikinta, ta d'an sake matsar da kanta saman kirjinsa, wanda kuma burinta shine ta samu ta zare d'an kunnenta daga jikin rigarsa.


Hakan da tayi d'inne kuma ya bata daman jiyo bugun zuciyarsa, wanda take tafiya da sauri sauri dib-dab-dib-dab.


Idanunta ta d'an lumshe tare da soma d'an jujjuya kannata, dake kwance saman kirjinsa, saboda ta kosa dan kunnen nata ya fita.


Shikuwa Rayyern dake kwance ak'asanta, hannunsa d'aya yasa ya kama gefen ba yansa, tare kuma da lumshe idanunsa, Ahankali k'amshin dake fita ajikinta, da kuma wanda ke fita acikin gashinta ke ratsa cikin hancinsa.


Sosai yake iya jiyo bugun zuciyarta daga cikin kirjinsa.


Idanunsa ya kuma rumtsewa adai-dai lokacin da yaji tana murza kanta akan chest d'insa.
Lokaci d'aya kuma yaji wani irin abu nabin kowani sashi na jikinsa.
Yaarrr yarrrrr haka tsikar jikinsa ke zubawa, Yayinda duk wani kofan gashi na jikinsa, ke bubbud'ewa.


Tun da yake aduniyarsa bai tab'ajin hakan ba, bai kuma san menene hakan ba, sai ayanzu da yaji yanda d'umin numfashin Jannart d'in, ke dukan wuyansa, ga kuma yanayin yanda yaji tana juya kanta akan kirjinsa, da wani irin salo.
Bugu da k'ari for the first time daya tab'a kasancewa da Mace haka, tunda yake aduniya hakan bai tab'a faruwa dashi ba sai yau, bai tab'ayin kusanci da Mace sosai haka ba bai tab’a sanin ya ake fuskanta ba in anyi kusanci da juna.


Idanunsa ya d'an sake rumtsewa, tare kuma dasa hakorinsa ya ciji jajayen labb'ansa.
Kwata kwata bazai iya jurewa kasantuwarsu ahaka ba, domin shi kam awajensa hakan bak'on lamari ne, da bayajin k'wak'walwarsa zata iya d'auka saboda abubuwan masu yawa ke ɗaurewa da kwancewa a sasan jikinsa.


D'an yun k'urawa yayi da niyar tashi, amma sai yaji ya kasa, saboda Jannart din dake kansa, da kuma bayansa wanda ya d'an rik'e.


"Wayyo Allah, ke ki tashi akaina mana, ko doki kika samu ne?"


Ya k'are maganan da wata irin fitinenniyar murya yana me taune lips d'insa.


Jannart dake kwance akansa kuwa, Jin abunda ya fad'a d'inne kuma yasa ta turo d'an k'aramin bakinta, gaba Cikin yanayin shagwab'a tace.


“Ni bazan iya tashi ba, d'an kunnena ya mak'ale ajikin shirt dinka, Idan na tashi da k'arfi kuma kunnena zai yage."


"To ya yage din mana sai meye, nidai da halla malama tashi akaina, da nauyinki zanji Koda zafin fad'uwan da nayi, Dan mugunta ma ai ke ya kamata ki fad'a k'asa ba niba."


Ya fad'a yana me yunk'urin tashi zaune.
Hakanne kuma yasa Jannart din sakin wani k'ara tare da manna kanta da ƙirjinsa da kyau kana ta kara rumtse damatsan hannunsa, saboda d'agowan da yaso yi ya sa tajin kunnenta zafi sosai.


"Auchhh kunnena."
Ta fad'a cikin wata irin shagwab'abbiya kuma kasalalliyar muryar, daya sashi komawa ya kwanta lib.


Hakan ko yasa ta ɗan ɗago, sai kuma tayi maza ta sake fad'awa jikinsa, saidai awannan karon atausashe kirjinta ya fad'a kan nasa.


Wani irin shocking yaji tun daga k'asan k'afarsa, har zuwa tsakiyar madigan kansa wanda hakan yasa Rayyarn nasa wani irin masifeffen harbawar daya sashi furta.
“Aushhhhhyyyyyohhhhh”.
Yaja sautin da karfi dan abin yazo masa a bazata.


Taushi da kuma tudun tagwayen abu biyu masu kamar audugan da yaji
Akan kirjinsa ne, yasa shi rumtse idanunsa da sauri, tare kuma da dunk'ule hannayensa.


Lokaci d'aya kuma numfashinsa ya soma wani irin fusga, Yayinda zuciyarsa kuwa ta shiga bugawa a millions.


"Yah Salam wayyoooooooo Allah na ni mema ya shigo dani wannan jarabebben d'akinne? Why Rayyern Why?"


Ya fad'i hakan azuciyarsa, yana mejin tamkar yasanya hannayensa ya tureta, ko hakan zai sa ya daina jin abubuwanda yakeji na game dukkan sasan jikinsa gaba ɗaya, wanda kwata kwata arayuwarsa baima sansa ba to amman kuma haka nan sai yaji ya kasa baya son tureta, sai yakeji tamkar su tabbata a haka.


Jin sautin bugun zuciyartasa ne kuma, yasa Jannart d'an d'agowa, saidai bata wani Kallon fuskarsa da kyau saboda duhu.


"Meyasa zuciyarsa ke bugawa fast fast haka?"


Tayiwa kanta tambayar, dai-dai lokacin kuma Cikin ikon Allah ta samu ta zare d'an kunnenta daga jikin rigar tasa.


Hakanne kuma ya bata daman d'ago Kanta, tare da mirginawa cikin sauri ta sauk'a ajikinsa.


Jin ta sauk'a daga jikinsa ne kuma, yasa shi sauk'e wani irin ajiyar zuciya tare da mikewa tsaye cikin sauri wani irin haushin sauƙan nata daga jikinsa ne ya rufesa har kamar ya saki kuka.


"Mcheeeww mutun sai nauyi kamar dutse."


Ya fad'a abayyane yana me shafa bayan rigarsa, dake Jik'e da ruwan.


Jannart kuwa duk da cewar baya ganinta, sosai baki ta murgud'a masa, tare da d'aukan wayarta tamik'e tsaye.


Kaitsaye d'akinta ta wuce, domin shima Rayyern din yana tashi, baijirayi komai ba ya nufi hanyar fita daga cikin dakin.


Ahankali yake tafiya yana d'an ciccije bakinsa, har ya gama fitowa daga part din Jannart din.


Dai-dai ya fito falonne kuma idanunsa, suka sauk'a akan Abba dake zaune bisa kujera.


Hakanan yaji kirjinsa ya buga, lokaci d'aya kuma yaji wani irin masifeffen kunya Abban nashi ya kamashi, akaro na farko kuma kenan yanzun, agaba d'aya rayuwarsa da yaji kunyan Abban nasa ta kamasa.


Tamkar wani marar gaskiya haka yayi k'asa da kansa, kana cikin sanyi ya taho sad'ab sad'ab ya haura sama sam ya kasa ya mishi mgn, sai yakeji tamkar Abba yaga abinda ya faru.


Da kallon mamaki Abba yabi bayan Rayyern din, musamman da yaga yanda bayan rigar Rayyern din, ke jik'e da ruwa, wanda kuma shi a iya saninsa, ko digon yayyafi ba'ayiba balle ko yace shiya jik'a Rayyern din.


Ajiyar zuciya kawai Abban ya sauk'e, tare da mik'ewa shima yayi b'angaren sa.


Rayyern kuwa yana haurawa sama, rigar dake jikin nasa ya cire.


Tare da sanjata izuwa wata, Ahankali ya d'an zauna abakin gadonsa tare da jawo Laptop d'insa ya soma hidimar tafiyarsu Mascow.


Saidai gaba daya ya kasa daina jin k'amshin Jannart din acikin hancinsa.


D'an rumtse idanunsa yayi, tare kuma da bud'esu alokaci guda, cikin d'an yanayin k'osawa yace.


"Fitinanniya."


Acan b'angaren Jannart kuwa Koda ta shiga d'akinta, kwanciya tayi lub akan gado, tare da d'aukan wayarta ta soma buga game.
Duk yanda taso maida hankalinta akan game din kuwa abun yaki, domin hakanan takejin k'amshin jikin Rayyern din, ya kasa barinta tayi sukuni, duk da cewar baya wajen amma mayen kamshinsa yana wajen.


Fuskarta ta d'an ya mutse, tare da shagwab'e murya, cikin kasa da murya tace.


"Ai duk shiya jawo muka fad'i, da wani k'amshinsa awajen."


Yanayin yanda tak'are maganan tana murgud'a baki, Idan ka gani zakayi tunanin agabansa take.


Almost 40minute kuwa ana tsula iska kana hadarin gaba d'aya ya washe, dai-dai lokacin kuma aka soma kiraye kirayen sallan magriba.


Atare duk mazan gidan suka wuce masallaci, Abba, Rayyern Ramadan da kuma Riyyam-nsra.


Acan suka iske Baba Maud'o ma, wanda shi yakan riga ma kowa dake gidan tafiya masallaci.


Koda sukayi sallan magriban kuwa, basu fito daga masallacin ba har saida suka sallame sallan Isha.


Koda suka dawo gida, anan kan dining table suka zauna, Yayinda Abba kuwa ya wuce sashinsa kaitsaye.


Mamy ne takai masa abincinsa, Ramadan da Riyyam-nsra kuwa Jannart ce tayi saving d'insu.


Ubangayyan kuwa bai hawo kan dining table d'in ba, anan cikin falon ya zauna, batare kuma daya ce akawo masa nasa abincin ba.


Itakuwa Jannart tana sane dashi, amma saita share batare da ta tambayesa ko yana buk'atar abinci ba, ta nemi waje ta zauna, tare da soma tsakalan abincin da ta zubawa kanta.


Rayyern dake zaune kuwa Ganin Mamy ta fito daga b'angaren Abba ne, yasa shi mik'ewa tsaye.


"Babana kai bazakaci abincin bane?"
Mamy ta tambaya da kulawa.


Fuskarsa ya d'an yamutsa, cikin kuma halinsa na rashin son yawan mgn daya tashi masa yau din yace.


“Ba'a bani ba”.
Yanayin yadda yayi mgnar yana kuma kallon Jannart ƙasa-ƙasa ne yasa, Mamy yin murmushi tare da cewa.
“To bari a kawo maka”.
Cikin kauda kai yace.
"No Mamy ni nakoshi."


"Amma Babana kafasan baka jima da tashi daga ciwo ba, Meyasa bazaka maida hankalinka wajen cin abinci akan lokaci ba?"


Mamyn ta fad'i haka cike da nuna masa, tsananin soyayyar da takeyi masa.


D'an marairaice fuskarsa yayi, hakan yasa yayi tamkar k'aramin yaro.


"Seriously Mamy nak'oshi ne, kuma anjima zansha tea, yanzu bari naje wajen Abba."


Ya k'are maganar yana me nufan sashin, Abban kaitsaye.


Mamy kuwa da Idanu ta bishi har saida ya shige part din Abban, kafun ta janye idanunta tare da dawowa kan dining table din ta zauna.


Ahankali Rayyern ya tura k'ofar d'akin Abban ya shiga bakinsa d'auke da sallama.


Abba dake zaune akan carpet, yana cin abinci ne ya d'ago kansa, tare da amsawa Rayyern din sallaman, fuska asake yace.


"Rayyern shigo mana."
Abban ya fad'a cikin kulawa.


K'arasowa cikin falon Rayyern din yayi, tare da matsowa ya rusuna agaban Abban nasa, cikin girmamawa had'i da ladabi yace.


"Abba barka da warhaka."


Kai Abban ya jinjina, tare da d'aukan d'aya daga cikin spoons d'in dake, kan tray din abincinsa ya mik'awa Rayyern din.


"Muci abinci."
Abban ya fad'a cike da kulawa.


Kansa ya d'an rausayar gefe, tare dasa hannu ya shafa cikinsa, cikin sanyi yace.


"Abba nak'oshi."


Kallonsa Abban yayi kamar zaice wani abu kuma saiya fasa, saboda dama yasan halin Rayyern cin abinci akai-akai bawai ya wani damesa bane sai daifa idan ya ritsa abinda yakeso ba sauki.


Rayyern kuwa d'an gyara zamansa yayi, tare da fuskantar Abban nasa, cikin muryar dake nuna girmamawa yace.


"Abba dama akan maganan tafiyarmu Mascow ne”.


D’an zuba mishi ido Abba yayi kana ya dauki cup ruwa ya dan sha kana ya aje tare da cewa.
“Uhum ina jinka".
Gyara zamansa ya danyi tare da ci gaba da cewa.
“Yanzu mun kammala komai ranar tafiyan nata matsowa, kuma Ina d'aya daga cikin way'anda zasu tafi, saboda ni nema zanyiwa sauran Doctor's din jagora, da nayi tunanin bazanje ba, amma kuma sai naga zuwan yana da muhimmanci, saboda akwai babban likita daya daga cikin malamaina nacan, daya nunamin dacewar zuwan nawa, tunda duk way'anda zasuje din ak'ark'ashin kulawana suke, To ya kamata na kasance tare dasu."


D'an dakatawa da cin abincin Abba yayi, tare kuma da d'ago kansa ya kalli Rayyern din, cikin gamsuwa yace.


"Masha Allah, ashe har tafiyar tayi kusa, zuwa nanda yaushe ne zaku tafi?"


"Nan da sati biyu Insha Allah."


Kai Abba ya jinjina tare da cewa.
"Allah ya kaimu, amma naji ku biyar zaku tafi, saidai ka

Please Login or Register in order to submit comment