Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

wannan katon a gabanta yana magana kamar ze kuka abinda bata taba ganiba shiyasa takasa cewa komae,
Murmushin jin dadi abbansu kawae yake yaname addu ah azuciyanshi allah yasa mimi tafarason bassam ne donshi yanason bassam sosae yana kaunar ganinsu cikin sahu namasoya kullum yana addu ar allah ya daedata tsakaninsu hakan kuma kullum ya gagara kusan shekara nawa ana abu daya zuwa yanzu takusa kare karatunta afara shirin aure abinda kullum yake dagawa mimi hankali kenan, kaf cikin family dinsu bawanda besan irin sonda bassam kewa mimiba ita kuma akasin haka har magana ake gaya masa akanta amma yana shanyewa,abban yace ayya mimi shalele aymasa afuwa bashida lpy murmushi meenal tasaki na mugunta sannan tace....


TAKU A KULLUM NANA BMB.


08147110349
[7/28, 8:20 AM] Nana BMB: 💝💖💝💖
RABONKWADO....
BOOK 2


NA NANA BMB




page 31-32
Ya bassam anjima indae kayimin abinda nakeso to shikenan mun shirya cikin zakuwa yace aikuwa komenene fadeshi zanyi mikishi insha allah takara sakin murmushi tace tom shikenan sezuwa anjima zan gaya maka yanzu kaga gurin baki zamu cikin jin dadi bassam ya amsa mata yanajin kamar yafi kowa sa ah aduniya hasana kuwa tunani take me yayarsu zatasa ya bassam yayi anjima allah yasa wahala zata bashi,suduka suka tafi masaukin bakin mutanen abbansu nata zuwa yimasa murnar dawowar mimi ko ince meenal koda meenal taga irin manyan mutanen dake halartarsu se abin yabata mamaki tasoma tunanin shin wani matsayine haka da abbansu mimi ne seda azhar abban nasu yasamu yafita da masu tsaronsa,
Hakanne yasa umminnsu cewa su tashi sushiga gurin hajiya suna tafe bassam da meenal cikin tsari abinnsu ummi tanata kallonnsu tanajin dadi har suka isa fadar hajiya matattarar jama ah bah tundaga kofa zakana jiyo maganar mutane itadae meenal nata ido se baza idanu take kamar me, koda shigarsu cikin parlour dinnan yadauki shewa suna cewa yayi mrs bassam dama sune agaba suka fara shiga tsayawa tayi kaf takarewa 'yan dakin kallo kama daga kan manyan har zuwa matasan 'yan mata da samarin cikin murmushinta tace yes kufada ku kara mrs bassam,se kowa kuma yay galala yana kallonta cikeda mamaki hasana take kallonta kodae yayarsu tasoma son ya bassam ne? bassam farin ciki yarasa inda zetsoma ranshi ma sewani isa yake yana basarwa yana kallon kowa dae dae irin yayi winning dinna,sabanin da dayake komawa abin tausayi, nandanan kuwa kowa yasoma tofa albarkacin bakinsa umminsuce tafara tsugunnawa tagaida hajiya cikin fulatanci sannan tazauna gefenta ita kuwa meenal tana zuwa tayi rashe rashe kan cinyarta tace kakus how are u? hajiya tarike baki tace mimi wato kakus nakoma kuma yanzu to nabi are u din dagudu,cikin dariya hasana tace ay hajiya da sabon salo yayar tamu tadawo,ummi tace salon iya shege uwattawa zata kira da kakus bama kaka bah,
Wata dattijiwar matace gefensu zaune wanda sam meenal bata kula da ita bama tadaega anata gaisawa da 'yan dakin seda tagama gyara kallabinta taharde kafa cikin rashin mutumci tace wato mimi yayi kyau hajiya kawae kika sani tunda itace tahaifi uwarki nida nahaifi ubanki ba ah bakin komae nakeba koh! jiyowa ummi tayi wanda tinda suma gaisawa hankalinta yakarkata gurin malama suna hira tace kiyi hakuri yaya babba ashe baku gaisaba bawae don wani abu bane,cikin kallon rainin hankali tace sumaya kema bansa dakeba meye naki aciki batada bakin magana ne seku tokarna kumajin bakinki da mimi nake magana yanzu, dakin yadauki shiru wannnan yatabe baki wannan yay tsaki haka suka dingayi cikin kasa da murya bassam yace to wannan bala e wannan tsohuwa zata fara jikin meenal asanyaye tamike tazauna agabanta tana kallonta tanata regewa ummi albarka,meenal kamar me shirin aikata abin azziki ta karkace tasoma fanyara uban kuka da ihu tamkar waddaa ake duka wayyo nashiga ukuna jama ah ashe yaya babba bata sona bata kaunata ansaceni nakusa mutuwa amma nadawo tana zagina ashe dama bata sona bataso nadawo gidannan bah abbanmu kadawo kaji abinda yaya babba ta aikata sotake dama taji ance namutu,duka 'yan dakin mamakine yadaskarar dasu suka kasa cewa uffan haka yaya babba tasau baki kamar sauna tana kallon ikon allah, meenal ganin babu wanda yatankata yasata mikewa takara azamarr kukantaa harda sheshsheka tana bubbuga kafafu, hakanne yajawo hankalin gwaggo dake daki akwance tatakarkaro tayo waje tana tafiya dakyar saboda tsufa jin kukan meenal datake karayine yasata magana kae kae meyake faruwane? wanene yake kuka ay meenal da gudu takarasa gunta tariketa tana cewa kitemakeni ashe yaya babba bata sona ansaceni nakusa mutuwa amma ina daga dawowata tana gani na tasoma zagina,jikin gwaggo har karkarwa yake tajata har zuwa gaban yaya babbar tana cewa kin kyauta halimatu allah yawadaran wannan hali naki shin kekuwa seyaushe zakisan kin girma? yanzu daga dawowar yarinya zaki fara zaginta saboda bakida mutumci duk hakuri irinna safiyya gashi yau seda kika kureta to wlh bari ubanta yadawo sena gaya masa kiyayyar dakikewa 'yar tasa inbanda hauka irin naki halimatu keda jikarki saboda banzan riko irinnaki kindau abu kinsawa zuciya haryanzu yaki wucewa agurinki sumaya da mahaifiyarta kullum cikin hakuri suke dake to ki kiyayeni kinji nagaya miki bari kuma mijin naki yadawo shima, kowa jikinshi yayi sanyi don abin yagirme kan kowa dake cikin dakin,
To itama yaya babba abin yasha kanta wae yau mimice da wannan makircin yarinyar da ko magana batasonyi yau itace harda ihu da kururuwa da hada makirci cikin jimami tace don allah gwaggo kiyi hakuri wlh banufina kenanba babu wani bakin nufi azuciyata ay abinda yawuce yariga yawuce gani nayi kawae tashigo ne tazauna amma bata kulaniba nayi mata maga na yaya babba tana magana tana matsar kwallah, caraf meenal tace gwaggo ay nadago zangaisheta naga tana hararata, salati gwaggon tafara tana sanar da ubangiji yaya babba kamar tayi kuka tace wlh karya take min gwaggo,zaki aikata wlh halimatu zaki aikata abinda yafi hakama bakin halinki kuma wannene bansaniba to wlh ki kiyayeni tunkan musa kafar wando daya dake itadae yaya babba juya kae kawae take tana bawa gwaggo hakuri har hajiya tasa baki amma abanza seda takarewa yaya babba cin mutumci takoma dakinta, yaya babba cikin zubar hawaye tariko hannun meenal tace don allah mimi kiyi hakuri wlh inasonki kije kibawa gwaggo hakuri kada tafadawa kakanki inya dawo kinsan fushinsa shiga uku zanyi wlh,
Wani murmushin mugunta meenal tasaki tashare hawayenta tace lah yaya babba bakomae sonake dama kawae aramawa ummi cin mutumcin dakikae mata ay nasan kina sona wace kakace zataki jikarta koba hakaba yaya babba, itadae majina tasharce tana jinjina kae tace ni haryanzu nagaza yaddarwa kaina wae jikatace kemin wannan ibar albarkar, daga gefe wani saurayi yamike yace kae impossible wannan ba mimi bace gaskiya, jin wannan furucinne yasa 'yan hanjin meenal juyawa kawae takuma saka kuka hajiya tace sadiq ka kiyayeni saboda yarinya tacanza zakace ba ita bace kan tarufe bakinta kuwa meenal tasoma kwarawa gwaggo kira jiki nabari kuwa yace allah yabaki hakuri wlh kingama nafita yay waje dasauri, ragowan 'yan dakin dariya suke amma banda bassam mamakin meenal ya dabae bayeshi kallonta kawae yake yana haka kanwarsa tashigo parlour din tazauna donjin abinda kefaruwa amma seta fara mika sakonta ga bassam tace ya bassam mama ce tace nakiraka takira wayanka akashe,saurin dafe goshi bassam yayi donshi wlh yamantama wayarshi ta tarwatse gidansu mimi, kawae yamike yafita kaf kowa ranshi kal abinda meenal tasa akawa yaya babba dama ta gallabi kowa,kowa cayake yaushe mimi takoma haka kuma daga dawowarta da abinda tadawo kenan itadae bin bakunan kowa take da ido bawanda tasani ma shiyasa bata tankasu sedae karantarsu datakeyi.
Misalin karfe biyar na yamma motar yousep ta tsaya a kofar gidansu nana nadiyace tafara fitowa tasha kwalliya tanata zuba kamshi tashiga gidan bayan tayi knocking anbude mata kujeran baya yousep yakoma yakwanta ya lumshe idanunsa yanajiran abar kaunarsa meenal ita kawae yakeda burin gani ayanzu....


TAKU A KULLUM NANA BMB.


08147110349
[7/28, 8:20 AM] Nana BMB: 💝💖💝💖
RABON KWADO....
BOOK 2


NA NANA BMB




page 35-36
Zuwa yanzu su meenal anzama 'yan gari a gidan fulani koya yanzu yasaba da surutun meenal kuma ana magana akan canzawarta lamarinta kamar asiri yanzu ta dawo saurarar bassam wanda hakan bakaramin farantawa abbansu rae yayba ummi kuwa yau lpy gobe babu kullum cikin ciwo take tunanin 'yar uwarta take akowani time makarantar da aka canzawa mimi yanzu babu wanda yasan inda takoma saboda tsaro daga ummi se abbansu kadae suka sani saura 'yan watanni tayi candy,
To su nana suma yau sukusa watanni uku danyin cabdyn su itada mardy damuwan nana takaro saboda rashin ganin yousep abin kaunarta wannan dalilinne yasa yanzu nana kullum setabi driver dauko mimi a school shikuwa yousep yana zuwane don babyn shi meenal sam auntie batasan cakwakiyar dake faruwaba mardy ma dae hakan take kullum cikin ddamuwa saboda mimi tacanza mara tanata zarya gidansu amma abanza dama nana bata shiga sabgarsu,
Yau friday takama yau daddy yadawo daga dubai se dare ya tattara iyalan nashi a parlour seda yayi gyaran murya tukunna yace shin nana kinada saurayi tsayayye ne wanda kikeso bata taba tsammanin tambayarba cikinta kuwa yabada wani kara mimi kuwa addu ah tafara azuci allah yasa kada nana tace tanason yousep suduka ita suka zubawa idanu seda daddy yakuma maimaita tambayar sannan tafara i nda inda takasa magana ma auntie tace wani irin shirmene wannan nana ana miki magana kina kame kame hannu yadaga mata daddy yace kyaleta ay abin bana fada bane idan batadashi ayba matsala bane karatu zatayi dama kada natauye mata hakkine ko aure takeso yanzu shiru takumayi auntien takuma cewa kinaji to kinyi shiru kanta a sunkuye tace zancigaba da karatun daddy inada wanda nakeso yatafi karatune shima bedawoba cikin gamsuwa daddy yace to allah yasa haka shiyafi alkhairi, sosae auntie takewa nana kallon mamaki shin wanene nana takeso batasaniba? kallon mimi yayi yace ke kuma meenal inaso kimaida hankalinki kan karatunki kawae banason shashanci kiyi iya abinda yake gabanki kawae kanta asunkuye tace insha allah daddy, idan mimi tana magana cikin sanyinta daddy seyay ta mamaki yadda meenal tasauya haka, sanya musu albarka yayi suka tashi suka nufi makwanci zuciyar nana cikeda fargaba tana tunanin yadda zata bullowa lamarin kota wani haline kuwa setasan yadda taraba meenal da yousep tunkan asan suna soyayya,
GIDAN FULANI
Zaune suke a parlour suduka hasana tana koyawa twins homework ita kuma meenal tana kishingide tana karatu a book dinta don saura 3 days takoma school ummi nadaga gefensu tayi zurfi cikin tunaninta meenal tana kulada yanayinta tanason tambayarta damuwarta amma bahali meenal yanzu angirma anzama cikakkun 'yan mata takara girma kamar ba itaba tazama 'yar gayu kullum kara kyau take makeri nakara kerowa fata natasheki tajee hutu,itama tunanin talula na yadda zata koma gida amma tarasa taya zata fara kullum intayi yunkurin yin maganar seta kasa saboda tsananin tausayin ummi datakeji kamar tayi kuka intana ganinta cikin damuwannan shiyasa takasa tabuka komae amma zuwa yanzu ruhinta yayi gida mussam dataji tanayin candy bajumawa za ah musu aure itada bassam iya yanzu kuma tasan ya muhammad dinta yakusa yadawo wa gida bawan allah kowani hali yake ciki tana cikin wannan tunaninne taji twins sunfado kanta suna kikkifta mata idanu alamun tabasu satar amsa sam batasan mesukeyi bama mikewa hasana tayi tana cewa wlh yaya tagaya muku kunfadi murmushi tasaki don ganin irin kallonda twins suke mata se suka bata dariyama kiri kiri kuma hasana tahanata magana suna cikin wannan drama din abbansu yadawo yauma fuskarsa dauke da tashin hankali yayi sama batareda bata lokaci ba kuwa ummi tabishi, sosae ta girgiza dajin kalamin bakinsa cewar jami ay sungano cewar harda sa hannun 'yan gidansu a sace mimi da akayi yanzu su ake lalube zaha gano kusuwaye sunjima suna tattaunawa kozasu san suwaye amma tunaninsu be basu kowaba har lokacin sallan ishah yayi yafito suka tafi masallaci shida twins itama umman tasu fitowa tayi sukayi sallah taredasu meenal koda suka idar sukayi addu ah suka shafa sannan ummi tariko hannunsu dukansu tajawota kusada ita sannan tace yaku diyae na yau zan sanar daku abinda kullum kuke burin kusani akan abinda yahaifarmin da ciwo mimi kullum kina tambayata damuwata amma ina miki shiru to yau zancireku aduhu baki dayanku,
TUSHEN LABARIN


TAKU A KULLUM NANA BMB.


08147110349
[7/28, 8:20 AM] Nana BMB: 💝💖💝💖
RABON KWADO....
BOOK 2


NA NANA BMB




page 33-34
Zamanta kenan a parlour takira mimi awaya tashaida mata sun iso gata a parlour mimi jitae kamar tasa kuka haka ta daura dankwalinta tafito tana rike da wayarta tana saukowa daga steps idanunta nakan nadiya haka itama da mamaki take kallon mimi zama tayi gefenta tana mata murmushi cikin sanyinta tace sannu dazuwa sam mamaki yahana nadiya magana kallon jikinta tayi taga me nadiya take kallone haka amma bataga komaeba zuciyanta ce tasoma shiga rudani daganin kallonda nadiya take mata,
Ahankali takae hannunta tarike nata cikin mamaki tace auntie wow haka kika koma masha allah mimi tayi murmushi tace keda ya yousep dinne kukazo nadiya tadaga mata kae tace kuma baki kirashiba auntie bayan gawayan ahannunki yana cikin wani hali sabodake ke naga babu abinda yadameki kodae kindena yinsa yanzu kinyi new catch ne wayar nadiya ta ansa tace bari naga abinda yasami wayan, ga mamakin mimi kawae segani tayi tacire pin din wayar nandanan dadi yakamata ganin numbers dinda tadanna,messeges dinda nadiya taganine bata budeba tace yanzu auntie meyahanaki bude sakon yayana haka nifa amma bari dae nabude sakon naga meya kunsa, saurin fisge wayar mimi tayi tana fara ah tace meyasa zaki ganemin sirri, nadiya tace sokike nagani dama tunda kika ki budewa nibasena bude mikiba, wai ina yayane? kanta rufe baki taga nana n nasaukowa daga steps tana mata fara ah har takaraso tazauna taname cewa nadiya kun iso kenan,eh yaya munsameku lpy? nana tace lpy kakau yajikin yayan naki, dasauki yaya kinga yanzuma ina mata maganarshi tana shareni nana takalli mimi wadda tayi zurfi cikin duba sakonnin wayar duka na yousep ne sena nana guda daya se sakon muhammad daya daga mata hankali se miss calls data gani ciki harda sunayen mutanen dabata saniba wato su mardiyya dube dubenta kawae take awayan tamantama da nadiya gurinta tazo koda tayi arba da hoton meenal zuciyanta bugawa kawae take tana matukar mamaki dole baza ah ganetaba kuwa,
Tuni ran nadiya yabaci ganin irin wulakancin da mimi ke mata abinda bata taba yimata bah da nana kawae suke hira harta gaji tace wae auntie wani irin wulakancine haka kikemin tunda kika zaune kike basar min kamar bakisa dani agunba meyake faruwane, mimi ta aje wayan tace sorry nadiya kinji bawulakanci nayi mikiba naga kuna magana da yayane, nadiya tana shan juice dinda aka kawo mata tace to ya yousep fah ke yake jira tunda nashigo bazaki gunnashiba harsena yi magana shirunda tajine yasata dagowa taga ashe mimi tacigaba da danne dannenta awaya bakin ciki ya isheta kawae tamike tadauki jakarta tace yayarmu bari natafi bazan iya jure wannan wulakancinba gaskiya allah yabamu alheri zuciyar nana kal da farin ciki tace tsaya nadiya nazo nawa yayan naki sannu nana tamike tabi bayanta,
Dole mimi batasoba ta aje wayan tabi bayansu har tashige gaban motanma yousep yana hango mimi yasauke ajiyan heart sedae fuskarsa babu fara ah ganin nana dayayi daga cikin zuciyanta mimi tace kaene ya yousep din kahadu babu karya dole meenal tasoka seda takarasa gaban motan tarusuna tace ya yousep ina wuni cikin sanyin muryanta shikuwa kasa magana mah yayi yazuba mata idanu nana kuwa jitake kamar ta galla mata mari don ganin irin kallonda yousep kemata jin baze amsataba yasata kallon nadiya tace sorry sis love banyi haka donna bata miki raeba, caraf yousep yace no nadiya tanada gaskiya baby dole tayi fushi yanzu kin watsar damu baruwanki damu, cikin marae raece fuska tace ya yousep bahaka bane kufahinceni kajee sauke ajiyan heart yayi yace baby indae kinason nafahimceki toki bari iyayenmu sushiga lamarinmu,
koda nana taji haka batasan sanda tafisgi hannun mimiba sukayi ciki tana cewa sorry kwayi waya ya mujaheed ne yake kiranmu idonta tafda kwalla tayi maganar yanzu da biyu dama yousep yay maganar seguwa gashi yaga abinda yake tunani kuna zuciyarshi tashigayi yana tunanin mezewa nana yahuce shikuwa haka yafigi motan yay gaba nadiya na mamaki,
Yinin ranar gidan fulani sunyishine cikeda mamakin sauyawar mimi surutu kamar aku kowa bashi labarin irin azabar datasha take ko ina agidan yadauka abinda meenal tayiwa yaya babba kowa yaji dadi sam meenal takasa tantance iya adadin al ummar dake wannan gida dataga wannan taji sunansu zata kuma ganin wasu har zuwa dare suka koma bangarensu shikuwa bassam mahaifinsa yay masa kiran gaggawa bedawoba har wanna lokaci ummi sama tahaura donyin wanka sukuwa su meenal suna parlour sunata hira dadi yacika su hasana yau yayarsu tabasu lokacinta,
Suna cikin hira se ganin abbansu sukae kamar daga sama dukansu kuwa suka tsorata da ganin fuskan abban nasu babu alamar annuri atare da ita ciki ciki ya amsa musu sannu dazuwan dasuke masa ko twins be kallaba ya haura sama, yana shiga bedroom din ummi tafito daga wanka tana daure da towel ganin yanayinshine yasata tsayawa tace lafiya kuwa, dogon tsaki yaja jikinshi har rawa yake yake saboda bacin rae yasoma cire rigan jikinshi yana cewa sumaya bansan mezanwa imam inhuceba arayuwar nan, cikin firgici ta dafe kirjinta tace wani imam kake nufi?cikin cije baki yace imam dae mijina safiyya, habawa tuni takaraso kamar zararra tarikeshi hannuwanta na kerma hawaye wani nabin wani tace ina 'yar uwata take ina yakaemin ita meyake faruwa da ita?
Iska yafitar dags bakinshi mezafi sannan yajawota jikinshi yarumgumeta yaname cewa am so sorry sumaya imam yaci amanar mu ya yaudaremu yasaki safiyya ahalin yanzuma besan inda takeba harma yaje yayi wani auren se ayau da dubunshi tacika allah ya hadani dashi yanacan nasa a kullemin shi sakin jikin dayaji tayi masane ajikinsa ya tabbatar da tariga tasume cikin kidima kuwa yadagota amma ina sam bata numfashi jijjigata yake yana kiran sunanta amma ina hankalinshi atashe yakwantar da ita kan bed yadauki wayanshi dakyar ya iya lalubo number din doctor yakirashi bugu daya yadaga wayan bejira komaeba yace jikin sumaya yatashi doctor nan da mintina biyar tayimaka a cikin gidannan ya yanke waya, yadebo ruwa a bowl yanata shafa mata ajiki kozataja numfashi amma abanza dole jiki asanyaye yadauko kaya yasaka mata, yasoma sintiri adakin, bajimawa doctor yakirasa yabasa umarnin shigowa ayyada su meenal suka ganshi sumasan ba lafiyaba yasharbe da gumi sosae dagani bakaramin azababben sauri yashaba yawucesu,
To numfashin ummi be daedaetaba harzuwa 11 sedae koda ta tashi kara daga musu hankali tayi kuka take tamkar ranta zefita tana kiran sunan safiyya seda doctor yamata alluran bacci tukunna aka sami salama,su hasana suna parlour hankalinsu yamatukar tashi tasan jikin umminsune yamotsa tunda sukaga shigan doctor, se bayan tafiyan sane abban yake shaidamusu suyi hakuri suje su kwanta jikin ummine ya motsa amma dasauki ranar dae suduka gurin meenal suka kwana suna cikin jimami,
Tome karatu haka rayuwa tacigaba da gudana tsakanin gidansu mimi da gidansu meenal wani irin kauna meenal takewa su ummi dakuma tausayinsu da kulawanda suke bata hakanne yasa takasa bayyana musu gaskiya tana jin tausayin ummi batasan halinda dazata shigaba kullum tana tunanin ina mimin take shin mafarkinta da takeyi tana ganin auntie nadukan mimi gaskiya tana gidansu a matsayinta, idan suna tare da bassam masoyinta take tunawa yousep haka zataci kukanta takoshi sam batada mafita ayanzu sosae meenal take mamakin rayuwarta itadae kullum cikin addu ah take allah yakawo mata mafita a rayuwarta tana tunanin 'yan uwanta wani hali suke ciki ayanzu tawani bangaren tana mamakin yadda ummi take kamata da wasu alamomi amma tayi kamar bata ganiba, tasha yimata fulatanci amma takasa maida mata martani haka idan da fulatanci suka hadu suna hira sedae tayi shiru tana saurarensu,
To mimi kuwa harkawo iyanzu sunkasa daedaeta kansu da nadiya kullum cikin mita take mata yanzu shareta takeyi batason yimata magana haka suke kullum a school zuwa yanzu ta diga ayar tambaya akan auntie tana tantama akan ba itace tahaifi meenal bah saboda irin muguntar da takeyi mata abu kadan tahau sharara mata mari kuma tashanye don acewarta allah ne yakawota wannan rayuwa shiyasa tayi tawakkali garesa take jure duk wata wahala tawani bangaren kuma soyayyar mujaheed tagama kasheta hartanajin bazata iya komawa gida batare data aureshiba don tasan mezataje ta tarar soyayya suke zubawa abinsu haka yousep ma don acewarta meenal take riritawa soyayyarta, NI NANA NINAGA ABINDA YAGIRMI KAENA WANNAN KWADON BAKA KENAN, mimi tanason sanin halinda mahaifiyarta take ciki amma bahali tasaba da kowa agidan haka suma sunsaba da shiru shurunta yanzu magana seta gadama tana waya dakowa harda mardy sedae ita sosae taga canji hakan kuma beyk mata dadiba ko maganar muhammad mimi batason tayi mata shiyasa abin yake damunta sosae bata iya kiran muhammad mugun jin tsoronshi take ko sunanshi suka ambata se heart dinta taharba bare yakira awaya abata jikinta har bari yake saboda kallon da yake mata me tarin ma a noni dayawa komae ya ajeshi agefe seya dawo tukunna don saura 5 mount yadawo kenan kullum mimi cikin addu ah take allah yabaiyyana meenal tabar gidannan kafin yadawo cikinsa....




TAKU A KULLUM NANA BMB.


KUYI HAKURI DA RASHIN TYPING DINA SOSAE AIKI NE YAKEMIN YAWA.


08147110349
[7/28, 8:20 AM] Nana BMB: 💝💖💝💖
RABON KWADO....
BOOK 2


NA NANA BMB


page 37-38
TUSHEN LABARIN
UMMI tace yaku 'ya 'yana kunsani kaf cikin yola babu wanda besan dazaman gidan fulaniba sedae bare gidane na family gaba daya dukanmu kanmu ahade yake gida me cikeda farin ciki dakuma tarin ni imomi gamida nishadi dukwanda yazo gidanmu seyayi marmarin dawowa sabida yadda muke gudanar da rayuwarmu,bangaren gidanmu kuwa mahaifina su ukune mahaifiyarsu tahaifa hashim shine nafarko se osman sae autanta abdullahi shine mahaifinmu nida 'yar uwata kishiyar mahaifiyar su babanmu wato gwaggo itama tanada danta kuda daya sulaiman shikadaene tahaifa, to kunsani dae 'ya'yan abbah hashim 6 ne matansa biyu inna hafsatu da inna maimuna,se abbah osman shikuma kunsan matarsa dayace dama halimatu wato yaya babba kenan isarta da ikontane yasa taci wannan suna yaya babba 'yan biyu tahaifa abdul halim shine hasan allah yajikanka da rahama marigayi se abdul hamid shine usain wato mahaifinku, yaya babba tana matukar kaunar hasan sosae marigayi ko ayanzu duk wanda yazauna da ita seta bada labarinshi, to sena ukunsu abdullahi kasancewar beyi aure da wuriba yagama karatunsa tukunna wannanne yasa duk 'yan uwanmu nawajan uba suka girmemu mahaifiyarmu amina wato hajiya duk cikinsu halimatu itace take haddasa bala i batason zaman lapiya sedae hajiya kullum cikin hakuri take da ita wannan dalilinne yada suke zama inuwa daya sabanin ragowan matan nasu lokacinda hajiya tahaifemu 'yan biyu annuna manaso kamar me mukadae allah yabata 'yar uwata itace babba safiyya wasu nakiranta da hasana haka nima wasu kan kirani da usaina duk da bakowane yake ganemubama mahaifinmu yanaji damu sosae gata ba irin wanda baya nuna mana, to se dan gwaggo sulaiman lokacinda yatashi aure anshiga matsala agidannan saboda ze auro kado ba ah cikin family dinmu takeba balaraba kanwar abokin mahaifinkuce ya aura seda akayi tashin tashina kafin abarshi ya aureta sedae ansami akasin abinda manya suke gudu sam balaraba batada kirki ga girman kae bawanda take gani da mutumci hatta mahaifinku dayake aminin yayanta da tasanadiyyarshi ma tashigo cikinmu bata ganin hakan 'yar ta daya itama tahaifa wato asiya duka halayyar babarta seda takwashe

Please Login or Register in order to submit comment