Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

nafahimci damuwan keda auntienki ne ko hakuri zakiyi meenal watarsna se labari kita mata addu ah itadae mimi amsawa take azuci kuma tana fargaban tome auntn takewa meenal?komawa parlour din sukayi aka cigaba da hira dob tayi tunanin kodae wata ayka aykar dannata yaywa 'yar mutane donba ah shedar dan yanzu,sedare suka tattara suka tafi koda suka isa dukda darene hakan behana mimi gane gidan part biyu bane ga tsaruwa iya tsaruwa gidan yatsaru kayanta da mujaheed yaketa kaewa daki yasata gane acan masaukinta yake bawanda yazauna hira sabida dare yayi kowa yanufi makwanci,ita kuwa seda takarewa dakin kallon tsaf sannan tadauko wayan meenal takunnata tazauna kan bed tazubawa wayan idanu....


TAKU A KULLUM NANA BMB.


08147110349
[7/28, 8:20 AM] Nana BMB: 💝💖💝💖
RABON KWADO....
BOOK 2


NA NANA BMB


page 19-20
Tana tafiya cikin sanda harta isa inda yake tasa hannu tarufe masa idanu tana bayanshi sedae mujaheed bakaramar tsorata yayiba addu ah yasomayi ba kakkautawa ita kuma jin yadda yake jero addu o ei yasata fashewa da dariya tajanye hannayenta dariya harda tafa hannu tana nunashi koda yabude idanunshi suman zaune yayi yana kare mata kallo ay yau ganiyay tamafi koyaushe kyau yadda take dariya kamar sakarae yake kallonta seda takare dariyar tata tace kae yayana haka kake da tsoro dama sam bemaji metake cewaba saeda takae hannu ta dungure masa kae sannan ya lumshe idanunsa tana murmushi tace kunya kakeji nabaka tsoroko,
Bude idanunsa yayi dasuka soma sauyawa wayarshi yadauka yaga time har kusan biyu saurama ya jinjina kae ya aje wayan bazato taji yajawo hannunta yana daga zaune tana tsaye harseda ta dsngane daga jikinshi kirjinta yasauka akan fuskarsa yasauke ajiyan zuciya dakyar ya iya furta my dear kinbani tsoro over mekikeyi anan bakiyi bacciba shirun datayi masane yasashi dagowa yana kallonta suka hada idanu yadda nashi yacanzane bazata iya jurewa kallonshiba ta sunkuyar dakanta kasa tace nayi bacci farkawa nayi,sukayi shiru nadan lokaci sannaa taji numfashinsa awuyanta yana cewa nimafa sena rama tsoron dakika bani kishirya jinsa yanzu ato,bata fahimci meyake nufiba sema rintse idanunta datayi tana murmushi hakanne yabashi damar karewa kirjinta kallo gaba daya rigan ta zanzare dan kadan tarufe mata kirji bakin cikine yakamashi ganin karcewar datayi haryanzu akwae shatinta,hannu yasa yadan shafi gurin,habawa aykuwa kamar an tsikareta tabude idanunta tana kokarin kawcewa seyanzun ta tuna ayadda tafitoma don manni irinna mimi takasa kwacewa don riko mekyau yamata kuma yaki dena abinda yakeyi mata haushi sosae yatiketa takae baki tacizar masa hannun dole yasaketa tajuya dasauri zatabar gun tabdi tana juyowa taga yama cimmata saboda tsoro takife agurin ido kawae take kwalowa tana bashi hakuri cikin shan kunu yace tonima wayace ki tsoratani,ganin abin nashi gabama yakeyine yasata sakin kuka tana ture hannunshi tana cewa nika kyaleni banaso kukan tane yasashi tattaro hankalinshi yacire hannunshi cikin rigarta tamike asukwane kuwa tanufi cikin gida tana hawaye masu zafi koda tashiga dakin nata tasake fashewa da kuka tafada kan bed tana jin zafin mujaheed sosae azuciyanta donme zetaba mata jiki ita ba matar saba kuma ba ita yakesoba meenal yakeso ziyi mata haka, shima mujaheed kayanshi yatattara yakoma daki yanajin haushin kansa abinda yayiwa mimi,seda taci kukanta takoshi sannan bacci yadauketa,
WASHE GARI
Da wuri mimi ta tashi tayi wanka tashirya ta tasa kayan meenal agaba tanata kallo natafiya tana tunowa da muryar auntie takejin zuciyanta na harbawa tanajin fargaba dukda batasan gidanba amma zuciyanta bata kaunar tafiya gidan,tare sukayi breakfast dasu auntie saratu banda mujaheed donbe shigoba kallo daya sukayi mata sukasan tayi kuka sekuma basarwa take don karsu gane wani abu, daddy yana shirin fita aikine nujaheed yashigo yana waya seda yakammala sanan yagaida iyayen nashi mimi nagefe tanata zumburar baki ita ala dole anmata badae dae bah beko kulataba dasu mummy kawae yake hira har suka fita zata raka daddy din bakin gate suna fits yatashi yaje yazauna a dining yasoma breakfast dinsa beko kalli inda mimi takeba,seda daddy yashiga motan yarufe kofan sannan mummy taruza kanta tana masa magana cewar kajawa danka kunne yafaja girmansa meenal yarinyace tsaf zata rainashi kana ganidae yau kogaisawa basuyiba zuba mata ido daddy yay yana murmushi harta kare maganarta,sannan yace niba abinda zancewa dana kema idan kika gaya masa ay yayi,mujaheed yasan abinda yakeyi saedae ita meenal daganin wannan yarinya zeyi fama da ita itazakiyiwa fada kada ta lalatamin yaro,hade rae tayi tace kaedama indae akan mujaheed ne kada sonkanka dayawa goyon bayanshima kake kamar batare dakae muganshiba jiya a garden yanama 'yar mutane ayka aika,kace zata lalata wancan katon yaron duka nawa take metasani mah katseta yayi dacewa aydama ku mata haka kuke kuyi tsokana kuma kuce anmuku ba dae daeba inbanda jiya kintaba ganinsa yamata wani abu nifa bazanga laefin danaba wani kinibibinne yafito da ita daga dakinta cikin wannan dare tasameshi har inda yake kuma babu shiga ta mutumci itacefa takae kanta don dana ba dutse nahaifa bani,so kigaya mata taringa suturta jikinta harsuyi aure kada kada ta lalatamin tarbiyarr yaro da ace dakinta yabita ne wannan to zega abinda zefaru kuwa to amma yanzu laifi na 'yarkine,duka meenal matasani arayuwarta dazata iya wannan aikin,dariya yayi sosae sannan yace ki kyale zanceb kankanta duk inda mace take to macen ce so kidena yimata kallon karama aynazu akama 'yar can aure seta zauna harda murnarta kike abinki keni koyanzu my son keson yin aure yimasa zanyi donnaga 'yar takima kila setafiki iya rike miji! dama yatada motansa kafin takuma magana yaja motansa yana dariya yana cewa sekun dawo matafiya agaidasu Dr maryam sun saba mummy da daddy irin wannan drama din soyake dama yakunnota kan yafita,
Seda yagama breakfast dinsa sannan yadawo kusads ita yazauna zumbur kuwa tamike cikin fushi yarike hannunta tajuyo cikin tsiwa suna hada ido tayi lakwas da ita rae abace yace baki iya gaisuwa ba koh cikin tura baki tace ina kwana yadda tayi masa maganar ne yasa ranshi yakuma baci kawae yasaki hannun nata yamike yafice daga parlour din tabishi da harara harda murguda masa baki,yana fita mummy tashigo tace meenal kingama hada kayankidae koh anjima zamu tafi kamar tayi kuma ta daga mata kae seda tazauna tace meyake damunkine kika shiga damuwa tundazu bakomae mummy, tomeya hadaki dayayanki nanma shiru batace komaeba, mummy tasauke ajiyan zuciya tace aduk sanda zakiji gurin yayanki kiringa suturta jikinki kafin kije kinga ba aure kukayiba saboda gujewa hudubar shedan, ay zuciyar mimi tsinkewa tayi tana kwalo idanu kardae mummy tagansu jiya dakyar ta iya daga mata kae alamun to don takasa dagowa, yawwa meenal allah yayi miki albarka kije kirasa kimtsa kayanki koh, tamike jiki asanyaye tanufi dakin abin duniya yaymata yawa tarasa abinda yake mata dadi tanajin wayar meenal tanata ringing amma taki kulata sotake taga mujaheed amma ko motsinshi batajiba har karfe biyu tayi narana sosae take kuka tunda tafito awanka tamakasa shirin daga ita towel tana haka taji ance kukan me kikeyi?tayi saurin dagowa suka hada ido kunyace takamata tasunkuyar dakanta kasa cikin tura baki tace to ay bakuka nakeyiba kaenane yake ciwo,betankataba yajuya zefita yace kitashi kishrya kifito mutafi kemuke jira zamu gidansu inna dagacan muwuce rintse idanunta tayi don sam tamace batasa kayaba ga towel din dukya tattare ganin zefice ne sayata saurin saukowa tazura hijab tace yayana cikin sanyinta, ay zuciyar mujaheed tawani harba jin muryar meenal dayayi tacanza wanda bakowane zefahimci hakanba takowa tayi har inda yake tazagayo tatsaya agabansa idonta tafda kwallah tace sokakeyi natafi nabarka nifa banason tafiyar nan kagayawa mummy tabarni banason tafiya nabarka nafison kasancewa dakae koda yaushe bazanyi farin cikiba indae kayarda aka maedani gida kuma sena dena yima magana, tana kuka tamatsa ta dora kanta kan kirjinshi tana kuka tana cewa pls yayana pls....


TAKU A KULLUM NANA BMB.


08147110349
[7/28, 8:20 AM] Nana BMB: 💝💖💝💖
RABON KWADO....
BOOK 2


NA NANA BMB


page 17-18
Yinin ranar tare suka kasance cikin nishadi sae bayan la asar suka tafi gidansu innah basu suka dawoba se bayan ishah suka sami auntie saratu tana zaune a parlour fuskanta daukeda damuwa suduka suka zauna gefenta kan carpet mujaheed yace menene yafaru mummy naganki cikin damuwa tayi murmushin karfin hali tasa hannu ta shafi kansa tace babu komae my son dubanta takae ga mimi wacca tazuba musu idanu tace meenal kishirya gobe insha allah nida mujaheed zamu rakaki gida
Damuwa karara tabayyana afuskan mujaheed kamar yay kuka yace haba mummy abari hutun natama yakarasa karewa mana kamar mungaji da ita nasan wlh auntie ce zata kiraki tabata maki rae, batabi takan zancen nashiba tace kamantane bayan boko tana zuwa islamiyya ne gobe insha allah zamu tafi takalli mimi wadda kirjinta ke dukan uku uku tace kije kishirya kayanki kinji meenal kada karatu yadinga wuceki,kamar zatayi kuka kuwa tace don allah mummy kubarni anan nibanason komawa gidan,girgiza mata kae tayi tace kiyi hakuri meenal mahaifiyarki kebidarki shin ina kika aje wayankine seyanzunma mimi ta tuna da wata waya tunda safe dasukayi waya da inty bata karabi takan wayanba,tana daki shine abinda tace to tashi kije ki kirata jikinta asanyaye tamike tashige dakin shima mujaheed yanufi nashi guri cike da bakin ciki,aunty saratu itama tahaye sama abinta ran kowa babu dadi,koda mimi tashiga ciki jitake kamar tasa kuka itafa wlh tagaji da anje wannan gida ace za ah tafi nan gashi wannan auntien dagani bakin hali gareta tanata masifarta ita kadae tajiyo karar wayan harseda takusa tsinkewa sannan taje tana gani tasan auntien ke kira yadda meenal tayi serving number din picking call din tayi sedae tunkan tafara magana tasoma jin ruwan bala ei wlh meenal kiji tsoron haduwata dake tunda kinzama mara mutumci yanzu 'yan uwanki basuda mahimmanci agareki da iyayenki kira nawa nayi miki seyanzu zakiga daman dagamin waya sabida kinsamu guriko! sati daya mukace kiyi kidawo gida shine kika zauna dake suma basusan darajar karatun da kikeyiba gajiya dasauraren ihun mimi takatseta dacewa pls auntie kiyi hakuri bagobe zandawoba,kadama kidawo kiyi zamanki kinji duktsiya dae ay sekin dawo garemu mimi bata iya jure fadan don haka tayanke kiran ta aje wayanma tashige toilet abinta,
Meenal ce akwance kotashi bata iyayi dakyar take bude idonta duk jikinta yay yaushi tawani kojale sae kace ba itaba azuci kawae take iya ambaton allah haka tayini ahaka sedare taji anshigo dakin ko daga kae takasa motsi kawae take iyaji nawanda yashigo daga bisani taji ankuma fita,sam yanzu tafidda rae da rayuwa addu ah take allah yasa intamutu anan to tamutu 'yar aljannah tadena tunanin kubuta mutuwa kawae take hange don ta sallama rayuwarta ayanzu,
Wani irin kara kara takeji akunnenta kasa kasa mamakinta bekareba seda aka kuma shigowa kara take kuma shiga kunnenta tsawa da hargagi kawae take jiyowa takasa mikeww zaune donhaka tarintse adanunta tasadakar yauce ranarta takarshe aduniya,
Bazato tajee an dan dora mata wani abu awuyan tsoro kuwa yakara rufar mata ta daskare akeance wata murya tajee ance yanaga kamar bata numfashi, daga kusada ita tajee ance bata mutuba numfashinnedae yake barazanar daukewa,se awannan karon tayi karfin halin bude idanunta tazubasu kan mutumin ga hasken fitilinsu duk da haka dishi dishi take gani ashe yatsunsane yasa awuyanta kuma kakin sojane ajikinshi,ba bata lokaci yadauketa cak yanufi waje da ita karar datake jine yake gigita mata kunne haryanzu batayi tunanin karar bindiga takejiba duk tafiyan dataji anayi da ita taki bude idonta sam seda taji wata san sanyan iska naratsata yasata saurin bude ido sedae duhu tagani ako ina hakan ya tabbatar mata anfito waje,seda ya isa bakin motansu sannan yashimfideta yadauko goran ruwa yabata tasoma kwankwala seda takoshi sannan tasoma maida numfashi bazato taji karar data firgitata tasaki dan guntun fitsarinta tasulale kasa saumamma!
Mimi cikin baccinta taketa mutsu mutsu da alamu mafarki take firgigit kuwa tafarka tana sauke numfashi siraran hawayene ke bimata fuska tana murmushi tadaga hannayenta tana mika godiya ga ubangiji ya allah kaene abin godiya allah kasa mafarkina yazamo gaskiya meenal dinsu takuta daga hannan azzaliman cen,kasancewar tana menstruation ne yasata batayi sallaba tamike tamaida hular kanta tafito palour domin shan ruwa rigar baccine ajikinta 'yar yaloluwa gata shara shara komae breast dina kana gani saboda batasa bra bah, fridge tabude tadauki ruwan tasha abinta tanemi guri tazauna se sauke ajiyan zuciya takeyi sosae takejinta wani wasae da ita gajiya tayi dazaman parlour din ita kadae yasata mikewa sam bacci yakauracewa idanunta takuwa bude kofa tafita abinta kofan daze sadaka da dayan part din nagidan tazubawa idanu" da alamu wanan mimi din batada tsoro kamar meenal" tafiya take harta dangane da garden sedae abinda yabata mamaki shine ganin mujaheed datayi zaune kan daya daga cikin kujerun garden din yanata danna laptop dinsa duka hankalinshi nakanta sam bejitaba dagashi se gajeran wando,wani irin farin cikine ya lullubeta ganin masoyin nata datayi itakanta tarasa dalilin farin cikin dakeji tunda tafarka abacci sanda tafara ahankali tana nufar inda yake," waeshin mimi tamanta suturar dake jikintane"?


TAKU A KULLUM NANA BMB.
08147110349
[7/28, 8:20 AM] Nana BMB: 💝💖💝💖
RABON KWADO....
BOOK 2


NA NANA BMB


page 21-22
Sam mujaheed besanda sanda yamata kyakkyawan rumguma yanadan yasunkuya saitin kunnenta yana cewa am sorry my dear zanyi kewanki matuka but iyayenki ne suke bukatanki kusadasu bamuda iko akanki nidake seyadda sukayi damu kwaedae meenal in dae kina sona kina kaunata dayawa kina gama secondary school kibari amana aure hakan shine ze bamu damar rayuwa atare harzuwa karshen rayuwarmu,bugun zuciyartane yakaru tana tunanin taya zatayi aure bada sanin iyayentaba?
Dan matsatan dayayine yadawo da ita tunanin data lula tayi saurin janye jikinta takoma bakin kofa tace to yayana nayarda kafita nashirya sedae gani tayi yakara matsota sosae harsunajin numfashin juna yace kinutsu meenal bawani abu zanyi mikiba bazan kara aikata abinda nayimiki a garden bah nasan ban kyautaba kiyi hakuri kawae yajanyeta gefe yabude kofan yafita suna paulour suduka suna jiranta sauri sauri tashirya takwaso kayanta tafito suka kaemata mota suka nufi gidansu su innan sukayi musu sallama sannan suka dauki hanya kuma mimi ansami abinyi abinda take so kallon duniya idanunta nakan hanya,
GOMBE
Meenal ce kwance kan gadon asibiti gefenta kuma wata matace azaune tazuba mata ido ba tsammani taga meenal din tasoma bude idanunta tanadan motsi harta bude idanunta tangaran matar kuwa tadurkusa ta rungume meenal tana kukan dadi tasoma magana sedae me? sam bahausa matar takeyiba fulatanci take yarawa tana mika godiyarta ga ubangiji daya tashi kafadun yarinyarta,tamkar zuciyar meenal zata fito waje haka takeji duk abinda yafarune yashiga dawo mata sedae tunaninta yatsayane atime din da mutuminnan yake bata ruwa sedae tafarka taganta anan yanzu matar tana dagata tajuya suka hada idanu komae na na tunaninta yatsaya saboda tsorata ita kanta matar seda tafuskanci hakan karkashin zuciyan meenal addu ah take sosae saboda wannan matar tarike fuskanta itace take yawon zuwa mata a mafarki tana kuka tana mika mata hannuwa rintse idanunta tayi tana cewa dama mutuwa nayi kenan gashi naga wannan matar shikenan nabar gidamu har abada tana wannan tunanin ne muryar wata yarinya tadoki kunnenta wadda tashigo yanzu bazata wuce shekara shadaya da rabiba sewasu twins yara maza dasuka biyota abaya kyawawa dasu masha allah sukuma bazasu wuce shekara 7 bah zuwa 8 yarinyar tana cewa UMMI! wae haryanzu yayarmu bata farkaba jin yarinyar tayi hausa yasa meenal saurin bude idanu tana kallonsu ganin hakanne yasa yarinyar farin ciki mara misaltuwa taje takwanta akanta tana murna kamar me yaryarmu munyi kewanki kullum cikin kuka muke munrasa inda zamu tsoma rayuwarmu ina fata babu abinda azzulam can sukayi miki koh, shiru meenal tayi musu taki tankawa kowa sedae ido kawae datake binsu dashi jikinta asabule tamike tsaye tana kallon yayar tasu kamar tayi kuka takalli matar tace UMMI meyasamu yayar mune bata magana hannunta tariko tace hasana kiyiwa yayarku uzuri bata gama dawowa dae daeba bata juma da farkawaba twins suna gefe sunzuba mata idanu suma, idonta tafda kwalla tace allah sarki yayarmu allah yasaka miki yabaki lpy kokarin mikewa zaune take ummin ta temaka mata ta tashi tasa mata pillow abayanta tazuba mata idanu ko kiftawa batayi hasana takalla tace kira abbanku kisanar masa yayarku ta tashi bamusu kuwa tadauko waya cikin jaka, ummin mamaki take yadda meenal take kallonta haka hannunta tariko sosae tana cewa kiyi hakuri MIMI kinji kinriga kindawo gida kiwantar da hankalinki babu abinda zesameki,wata faduwar gabace tasami meenal jin an ambaci mimi seyanzu komae yadawo mata tuni tafara ambaliyan hawaye tana girgizawa matan kae ita yanzu taya zata ganar dasu ba ita bace mimi seyanzu ta tuna itace matar datakejin kukanta awaya yanzunkam mamakinta yakare ta tabbatarda ba mutuwa tayiba to amma wacece wannan matar rarrashinta ummin tasu tashigayi dakalami da dada masu kwantar da hankali itama hassana gefenta tazo tazauna tace sorry kinjee yayarmu nakira abbanmu yanzu zezo kidena kuka kinji tasa hannu tana share mata hawaye haka twins kafafunta suka rike suna cewa pls yayarmu karkiyi kuka, tunda meenal take bata tabajin nutsuwar zuciya da farinciki irin wannan bah ganin ita kadae sukema wannan rarrashin ga nuna kauna da kalawa hakanne yasa hawayenta kin tyayawa duksetake ganin abin wani iri yau ana mata irin wannan rarrashin bandaki tace musu zata shiga don haka ummin tasu ta rakata bakin bayan tatsaya daga kofa tana jiranta,
Tana cikin bandakin abban nasu yashigo da sallamarsa kana ganinshi kasan yana cikin farin ciki suduka sukayi kanshi cikin fillacin yasoma magana shima cayake ina mimin take ummin tanadaga bakin bayin tayi masa nuni da hannu alamun tana ciki hasana tace abbanmu yayarmu ay bata magana,itama fulatancin tayi masa magana,meenal tana daga cikin bayin tana jiyo yadda suke magana sedae sam ko kalma daya bazatace ga abinda suke tattaunawaba don sun juye harshensu tuni idanunta yadinga tsiyayar hawaye tagama abinda takeyi amma takasa fitowa kamar tasa kuka catake ya allah wani irin mutanene wadan dan ka kawoni cikinsu bansan mesuke cewaba ganin batada mafitane yasata dole bude kofa tafito, ummin takamota har kan gadon tazaunar da ita, sannan tayi mata hausa tace mimi inane yakemiki ciwo yanzu,girgiza mata kae tayi alamun bakomae, abban nasu yace to alhmdlh 'yata tadawo gida lpy makiya kuma sedae suji kunya ankusa kama wadanda sukeda sa hannu a saceki mimi alkawari nayi bazan taba kyale kosuwa sukayi mana hakaba wlh, kuma tunda allah yanufa kin farka ayau zamu koma gida bazaki kara kwanan hospital dinnan bah duka gaba daya gari yadauka 'ya ta tadawo so nan babu wani tsaro gara mutafi gida acan hankalina zefi kwanciya sam umminsu batayi masa musuba yana maganar tana hadawa meenal tea mekauri a cup tabata tasha takoshi sosae taji kwarin jikinta dama ga drip ansa mata ba iyaka,
GARIN KANO
koda suka isa janbulo gidan alhj abubakar horn biyu gateman yabude musu gate suka shiga gidan bayan sungaisa da megadin, nana tana kwance tadora kanta akan cinyar auntien tasu ita kuma auntien tana karatun jarida,koda suka shiga parlour din nana tamike cike da mamaki tana kallonsu sunshigo bawani hayaniya, aduk sanda meenal tayi dawowa irin wannan tunkan motansu ta tsaya zata fita aguje tayi ciki tana kwala musu kira sallamar dasukayima kasa amsawa nana tayi saboda mamaki se auntie ce ta aje jaridar ta amsa musu,koda suka hada idanu da mimi zuciyar tace tawani irin jarbawa saboda yadda tayi mata kwarjini ga girman dataga takara dakuma cika ido babu fuskar data fado mata seta safiyya,hakadae ta daure aka gaggaisa mujaheed yana dariya yace nana yadae meenal din taki tacanza mikine kikayi poster haka kina kallonta da mamaki nana tace sosae makuwa tacanza ya mujaheed wannan ba halin meenal bane akwaedae wani abu ganima nake kamar ba itaba shida mummy sukasa dariya kana yace lallae nana abinnaki aziminne toke meenal kinji mimi nazaune tadanyi guntun murmushi don ita tunda suka shigo tajee mutanen basuyi mataba duk zuciyanta acunkushe yake mussam irin kallonda dataga auntien nayimata, nandanan aka cikasu dakayan ciye ciye mimi ruwa kawae ta iyasha saboda bata yanayi me dadi nana kuwa takasa dena kallon mimi saboda mamaki auntie duk wannan baragadar babu komae kasa jurewa nana tayi tace waike meenal lafiyanki kalau kuwa suduka kallo seya koma kanta murmushi tayi mata again tace lafiya kalau fah ba abunda kedamuna tafiyan nance tasa kaina yana ciwo ko magana banasonyi amma bawani abu mekika gani,wlh ban yardaba shine abinda nana tace kawae, sosae auntie take mamaki yadda mimi take magana da aji cikin yauki amma saboda abindake cimata zuciya ko kulata takiyi hirarsu suke da mummy ita kuma nana sunayi da mujaheed hakanne yasa mimi juyawa takwanta akan kujera ta lullube fuskanta da mayafinta,
Suna cikin fira munaheed yakira muhammad vidio call yana shaida masa aysun iso aje wayan yayi yadda zega kowa suna gaisawa mummy ce tafara tsokanarshi tana cewa kadae zama dan can can ho dae ko muhammad kememe kodan hotunma kaki zuwa kamana,mujaheed yana dariya yace lallae mummy ina zedawo bakisan yadda kasar nan take gara masabane kilama acan zesamo muku sirika yajuya ya kannewa muhammad ido yana dariya,mummy tace a ah wlh allah karya biye bakinka bakada kirki allah yatsaremu duka takae masa yagoce, auntie ma tayi dariya tace tomeye aciki kae muhammad kataho tasu inyaso shima mujaheed kataho masa datasa kuyi anko bashikenanba, yakuwa gimtse dariyarsa yace haba auntie wlh allah yakiyaye ni inada wadda zan aura,ay nana kamar an mintseleta tamike tazauna gefenshi tana cewa wow ya mujaheed wacece wannan fadeta naji don allah,hararnta yayi yace to uwar gulma bangayawa su mummy bah seke muhammad yace aikin banza to kada kafada mana,mummy tace shakuriminka muhammad aynama santa ko ince munma santa, dasauri mujaheed yace pls mummy kiyi shiru mana, muhammad yace aishikenan kuma munma dena damun kanmu tunda munsanta abinda zamu ganta meye nadamuwa kada kafada kila bata azziki bace kake hana musani mudae indae batayi manaba dole acanza, dariya sosae mujaheed yayi yace bakasan kowaceceba zaka fara yimata rashin ta ido inda kuma kanwar kacefa? nepar kan muhammad ne yadauke haka itama auntie dakyar yatattaro nutsuwarsa muhammad yace banganeba,
Zaka gane nan gaba kadan cewar mujaheed.
Tambayarsa yayi yace ina meenal ne nibanjita tunda muka fara waya, tana kwance mimi tana kunshe dariyarta don bakaramin dadi hirar tasu takeyimataba, kallonta mujaheed yay yana murmushi yace kaganta tana hutawa takwaso gajiya murmushi muhammad yay metarin ma ano ni dayawa yace to nunamin ita nagani waca irin gajiyace haka dazatasata shareni,
Wayan yadauka ya isa inda take kwance tanajinshi tarufe idanunta ya yaye mayafin fuskanta tabayyana kafansa yadora kan tata yada yatsansa babbashi yana mata susa a tafin kafan nata tanata mamar mamar da idanunta kana gani kasan ba bacci takeyiba dariya take shirinyi saboda abinda yakeyi mata tasaki murmushi har dan dimple dinta ya lotsa abinda muhammad yakeson tabbatarwa dama kenan wani irin gumine yake tsatstsafo mishi mikewa tayi tari kafan nashi tace kae yayana kaga katasheni ina bacci tayi maganar cikin shagwaba shikuma yarankwafo saetin kunnenta yace baki gaisheda yayankiba yay maganar harda dan cizar mata kunne muhammad ya lumshe idanunsa time din tadago tace yaya ina wuni, bekara bari yaji mezata ceba yakashe wayan....


TAKU A KULLUM NANA BMB.


08147110349
[7/28, 8:20 AM] Nana BMB: 💝💖💝💖
RABON KWADO....
BOOK 2


NA NANA BMB


page 23-24
Muhammad jiyayi karatun yafice mishi a rayuwa gida kawae yakeson komawa domin tabbatar da raenin hankalin da wannan mimi din keshirin yimasa shin ya akayi meenal zata koma haka tabbas ba ita bace to ina takaemin meenal dita ya akayi koea yakasa ganewane kodae nine bana gani dakyau kae ina baze yiwuba sam kasa nutsuwa yayi yanata zagaye a room dinsa zuciyarsa na azalzalarsa yakoma Nigeria,koda yakashe wayan mimi kallon mujaheed tayi da mamaki shikuma

Please Login or Register in order to submit comment