Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kanta don tarasa bakin magana,yana sauke idanunshi kan kirjinta yaga dan jini yabata mata saman rigarta kadan dake milk ce cikin damuwa yace hasbinallah meenal haryanzu baki warkeba agurinnan kallonshi tae taga meyake magana akae taga yana kallon kirjinta tayi ssurin maida kanta kasa kuwa, bazato ba tsammani taga yakae hannu kan kirjin nata gefen rigar yadan janye yana kallon karcewar da tayi yana yamutsa fuska kanar zeyi kuka yanzunma dayatsansa daya yadan shafi gurin yace ina maganin dakike shafawa agurin?lumsassun idanunta tabude tayi masa nuni da inda inda suke a ajiye yadauko yazauna kuwa dakanshi yasa tissue yagoge mata gurin yashafa mata maganin harya gama idanunta yana lumshe, gyara zamansa yayi sannan yakira muhammad koda yakara waya akunne yace sorry muhammad gata ay yanzu nashigo ne,mika mata wayan yayi ta ansa hannunta narawa tamkar anmata dole tace hello! cikin fada kuwa yace wae baza ah bawa meenal wayanba ne bae rufe bakiba yaji tace ina wuni,bae amsataba kawae yace bawa mujaheed wayan mika masa wayan tayi jikinta asanyaye,tsaki yay ya anshi wayan yace to meye kuma,mujaheed nizaka rainawa hankali ina meenal take,da mamaki mujaheed yace bangane ba ayni haka raenawa hankalin bagata tanama maganaba kace tabani gata ni cikin haushin yamika mata wayan,koda takara wayan akunne sunan daya kirata dashine yasa zuciyarta rudani sweety yakara kiran sunanta, cikin sanyin muryanta tace na am dan shiru yayi sannan yace meyake damunkine kifadamin gaskiya,babu komae babu abinda yake damuna dama yamata tambayarne donyakarajin muryanta,bashi wayan shine kawae abinda yafurta tabashi wayan kuwa ta lula duniyar tunani shin towaye wannan kwalla taf a idanunta,yankewa tunaninta yayi jin mujaheed yayi sama da ita abakin kofa yasauketa yasaurin zura mata hijab dinta na sallah yakama hannunta suka fita harcikin mota yasakata sannan yakuma kiran muhammad amma vidio call ya aje mata wayan kan cinyarta yazauna gefe shima yazuba mata ido, ya allah koda suka hada ido tacikin waya kasa kuma kallonsa tayi dagashi se gajeren wando iya gwiwa,dakyar ta iya kakalo murmushi tace sannu yaya kana lpy baima jitaba saboda irin kallonda yake mata,cikin tuhuma yace ina wayanki kika kaeta?tayi shiru cikin jin haushin hakan yace badake nake maganaba ne, yaya bansan inda takeba wlh,yayi kyau bakisan inda takeba sam babu abinda yadameki saboda kinsamu freedom na yawo ko bakidamu da halinda zamu shigaba kullum zuciyata cikin fargaba take da tunani marasa dadi akanki daddy yakikkira kinki daga wayan karshe wayannaki akashe su nana harsun gaji dakiranki ma, ko awayan mujaheed base ki kiramuba wani irin haline kikeson daukane yanzu?
Kayi hkr yaya bazan sakeba tayi maganar idonta tafda kwallah zatayi kuka har mujaheed seda yayi mamakin yadda takewa muhammad magana,MEENAL! yakira sunanta zuciyarshi tabda tambayoyi kala kala, meyake damunki?yanzunma bata dagoba tace bakomae,sosae tabashi haushi kawae yakashe wayanshi ma,
Da mamaki mujaheed yace meenal meyasa zakiyi masa magana ahaka ne sokike yagane bakida lpy,tagirgiza masa kanta,to kada kikuma amsashi awannan mood din pls kisaki jikinki,yanzunma kae kawae tadaga masa yakama hannunta suka koma cikin hospital din se kallon ko ina take harda wae waye saboda time dinda aka shigo da ita cikin asibitin bata hayyacinta sun shiga room din datake zara tana zaune tayi tagumi tana ganinsu kuwa tasaki murmushi tace ya mujaheed ina kukajene ina nan har tsoro yasoma kamani,murmushin yamata shima yace nakaeta motane tayi waya da yayanta kinsan basusan abinda yafaruba bawanj guri tajeba ay, wae zara kinsan inda wayan meenal takene,tagirgiza masa kae alamun a ah, bewani zaunaba yay musu sallama yatafi don jiranshi su sameer sukeyi,
Tana kwance duk ta rame tabushe dakyar take bude idonta haka zama ma gagararta yakeyi saboda yunwa ta dagazata ruwane kawae take iya samu tasha abayi,numfashintama dakyar yake fita bata kara ganin mutuminba tundaga ranar hawayene kawae yakebimata fuska data lumshe idanunta lapiyayyaen abinci take hangowa tana hadiyar yawo,cikin wahalalliyar muryarta take cewa ya allah kadauki raena kozan huta dawannan ukubar sun tafi sun barni da yunwa ko kukama kasawa tayi,baccin wahale yadauketa kamar amafarki kuwa taji shigowan mutumin tabude ido ahankali taba wanan gardin mutumin shine dae yadawo hannunsa daukeda bindiga dakuma cup tayi saurin tashi zaune cikin tashin hankali take kallonsa harya karaso ya tsugunna agabanta, batare dayayi maganaba yamika mata cup din hannunsa, bamusu kuwa ta ansa fresh milk ce aciki batajira meze ceba takafa baki tas tashanyeta dataga hakan bematabama tasa hannu tana lashe kofin, yadda takeyi nema tabashi dry yay murmushi,cup din ya anshe yamika mata waya takuwa ansa takara akunne dukda hankalinta yanakan bindigar dayake nunata da ita,hello! tacikin wayan kuwa taji kukan wata mata tana cewa mimi ina fata dae basuyi miki komaeba nakasa bacci diyata narasa inda zan tsoma rayuwa, shiru meenal tayi saboda yadda kukan matan yake taba mata zuciya basuyimin komaeba tacewa matan, to nagode allah mimi kiyi hkr kinji allah ze kubutar dake kullum cikin addu ah muke yimiki, kasancewa meenal ba itabace mimi yasa hawaye zubuwa daga idanunta masu zafi kafin tayi magana kuwa ya anshe wayan yakashe tasoma binsa da kallon tsana,da murmushi yamike yace madarar dakikashace tasaki jin kwarin gwiwar yimin rashin kunya kiyi kome kikeso duka kwana nawane yarage miki aduniya,ficewa yayi abinsa,tabishi da harara sam tadena tsoron mutuwar ma ko kadan muryan matarne kawae yake mata yawo ajiki, mikewa tayi tayo alwala tazo tasona sallah abinta don ayanzu itace mafita agareta, tana idarwa tasoma rero karatun Alkur ani,
washe gari
Su sadiyane sukazo yiwa meenal sallama zasu tafi gida domin biki yakare jiya anmika ango dakinsa,duka dasu mom akazo da inty, gashi harda zara za ah tafi hakanne yasata samusu kuka wlh ita se ansallameta, mujaheed azuciyansa yace daman nasan za ah rina haka, lallabata yasomayi cewan tabari tadan sami sauki,mom tace a ah mujaheed kira doctor dole amata abinda takeso aitamayi har aka gama biki tana asibiti,zara tayi dry tace kinji mom itama banata bikin takeyi anan bah suduka sukasa dry kuwa banda mujaheed dayayi murmushi kawae yana kallonta ta tura baki gaba tana hararan zara,sunsha hira sosae sanan doctor yasallamesu suka tafi gida da murnarta se kallon gari take abinta. ...


TAKU A KULLUM NANA BMB.


08147110349
[7/28, 8:20 AM] Nana BMB: 💝💖💝💖
RABON KWADO....
BOOK 2

NA NANA BMB


page 11 -12
Koda suka karasa gidan kowa yanata shirin tafiya gida abinsa ita kuwa mimi tayi lamo tanata kallon gidan don yau ta taba zuwansa seda su zara suka gama shirinsu sannan tazauna gefen meenal tace to meenal zamu tafi sae allah yakaemu naki bikin muzo musha shagali,murmushi mimi tay batareda tadagoba tace hmmm,inty ma murmushin tayi tana kallonta,sosae tafiyar su zara tasa sukaji babu dadi ga mimi bata wani magana sedae kallo kawae gidan yayi shiru bakaman jiyaba wayar meenal inty tadauko tace meenal gawayanki koda naga miss calls dayawa sena kashe miki wayan tunda ya mujaheed yace bayason asan bakida lpy,murmushin karfin hali tayi mata ta ansa tana godiya tasoma juya wayan ahannunta yinin ranar inty tafuskanci meenal tacanza sam batason magana ko ana hira sedae tai murmushi, kasa jurewa tayi tace pls meenal menene yake damunkine sam bakyason magana yanzu murmushi tamata tace wlh babu abinda yake damuna, to ko inkira miki ya mujaheed?setabawa mimi dry tagirgiza mata kae tace a ah, tom shikenan muje mukwanta kikara hutawa anjima gidan ya sameer zamuje ku gaisa da amarya don shima yace gobe zaku wuce gida,
tunda mimi ta anshi wayan meenal takeson ganin abinda yake cikin wayan amma da security awayan dole takashe wayan ta ajiyeta,bayan ishah su inty suka tafi gidan sameer mujaheed yana driving dinsu mimi nagefenshi se inty abaya suna ta fira har suka karasa bakarya kam gidan sameer yahadu haka auntie salma matarsa tanada kirki sosae se nan nan take dasu tanatama mimi sannu don sameer yabata labarin komae koda yatambayi salma ina sameer tashaida masa ay yana bedroom dinsa, kae tsaye yawuce dakin nasa sukuma ancikasu dakayan ciye ciye,
Akwance yasamu sameer yana danna laptop dagashi se boxer murmushi yayi kawae yazauna kusa dashi yakae masa duka abaya kamar yasani kuwa yazille, yajuyo yazuba masa uwar harara,dry mujaheed yay donya fahimci abinda sameer yake nufi,hannunshi yahade guri daya yarike baki yace oh ni mujaheed shin sameer duka yaushe kasan zakin amarcin nan ne dazaka dinga turomin baki harda hararata munzo mun katsema jin dadi koh inkayi hakuri dagayau bazaka sake ganinaba dakudi seka nemeni,
murmushi sameer yay mesauti yagyara kwanciyarsa yajuyo yana kallonsa yaharde hannayensa abayan kansa yace mujaheed bazaka ganeba ne yau nakeson fara cin amarcina amma don iskanci irinnaka karasa sanda zaka kawomin su inty seda daddare don mugunta irintaka duka sameer yakae masa saboda dariyar dayakeyi masa dan iska ainasan dama dabiyu kaimin haka,saeda nujaheed yay dariyarsa son ransa sanaan ya tsagaita yace kace amarya wanaka takeyi shiyasa naganka duk ba adaidaeba,kallon kafafun sameer yasomayi har zuwa sama,yakuwasa hannu yature masa fuka yace munafiki mekakeson kallone juyawa yay yakifa akwance abinsa yana dariya shima,
Jinjina kae mujaheed yayi yace tabdijan babbabar magana dole ka kasa fitowa kagaisa dasu inty wlh amarya tarufawa kanta asiri tabada kae bori yahau,mintsininshi sameer yafara yana cewa allah yashiryaka mujaheed bansan sanda ka kara zama hakaba duk jarabata ay ban kaekaba tundani bana rawar sanyi dashan magani ehe! kamakalewa 'yar yarinya ai meenal zatae fama da ..... Saurin toshe masa baki mujaheed yayi yace to mara mutumci naji bari nabarma dakin kasan yacca zakayi wlh kafito don bayanzu zamu tafiba, cije baki sameer yay yana girgiza kae yace habawa mujaheed zan ramane,
Mujaheed yana fitowa yasamu salma takunna musu TV sunata kallo abinsu inty tana ganinshi tace kae ya mujaheed harka fito badae tunyanzu zamu tafibah, girgiza mata kansa yayi alamun a ah yana murmushi haka salma itama murmushin jin dadi tayi jin bayanzu zasu tafiba mujaheed na ankare da ita azuciyansa yana cewa habawa yarinya zakiyi bayani ne,fitowansa da dan jumawa sameer yafito shima yazumbula babbar rigarsa ta daurin aure se muzurae yake yazauna kujeranda mujaheed kezaune wanda yaketa faman dry kasa kasa, gaisawa sukayi yanata ma mimi sannu da jiki yalura da dariyar da mujaheed kemasa matsawa yafarayi kusa dashi mujaheed namatsawa shima yana kara matsawa harya kureshi akarshen kujeran seya seya mike yay waje yana murmushi yasan yanzu ze iya kunyatashi gaban kannensa,
Duka hankalinsu nakan TV basusan mesukeyiba sameer yay dry yamike yabi bayanshi yana cewa karamin dan iska dakatsaya kaga meze faru,haka kawae kazomin gida kahanani sakewa,
Awaje suka cigaba dahirarsu gwanin burgewa har lokaci yajama basu saniba intyce tafito tanata kwala musu kira takuwa hangosu zaune saman mota kiran da take musune yasa dukansu suka zuba mata idanu tayi tace ya mujaheed mom ce tace mutaho gida dare yayi,
Cikin masifa sameer yace wani irin shashancine wannan zaki dinga yimana irin wanan kiran ni nazacima wani abune yafaru wlh sim sim itadae takoma ciki, murmushi mujaheed yay yazo dafda kunnensa yace kwantarda hankalinka aibacazatai dakae wani abu yasamu amaryaba daze hanaka cin amarcinka yau bare kasauke mata kwandon masifa yana gama fadin hakan yay saurin dirowa akan motan yay ciki tunkan sameer yay magana, kwafa yayi kuwa yabishi abaya kayan azziki salma tahadawa su inty suna shirin tafiya sameer yace wae meenal meke damunkine naga kinyi shiru kawae abinki, caraf inty tace ay tunda tadawo haka take bamagana gida takeso ay,kallon inty tayi tace allah sis bagida nakesoba kawae maganan ne baya kaena,sameer yay murmushi yacewa mujaheed to inkun koma yaushe zaka maidata gidannasu kenan,ay mimi tanajin haka taji cikinta yabada wani kara jin ashema ba agidansu ya mujaheed takeba, tabdijan babbar magana!
Maganar mujaheed dinne ya katse mata tunani yana cewa muna komawa bawani jumawa zamu tafi ay hutun nasu yakusa karewa sunkusa komawa school don muhammad ma yanata azalzalata,lebe sameer yarike a ah kaji masu kanwa fah jarababbe yanzu dae munji sit abinmu tunda yabar kasar saura shekara nawa yadawone,mujaheed yay dariya yace kaidae bari masifaffen bah saura shekara daya da rabi yadawo, time dinda yashekara biyu ba irin faman dabanyi dashiba yadawo gida yay hutu amma yaki yace wae inya dawo baze kuma komawa ba,sameer yace to kada yakoma mana shifa yayiwa kanshi ay muma hutunmune sosae magan ganunsu suke daurewa mimi kae, ahaka sukayi sallama suka tafi gida zuciyanta cikeda tunani kala kala....


TAKU AKULLUM NANA BMB.


08147110349
[7/28, 8:20 AM] Nana BMB: 💝💖💝💖
RABON KWADO....
BOOK 2


NA NANA BMB


page 15-16
Messeges dinda suke shigowa cikin wayanne yadawo da ita tunanin datakeyi tanason duba me ake turowa haka amma babu hali haka ta aje wayan ta tashi tayi alwala tazo tayi nafilfilinta da addu o ei tana nan zaune taji wayanta yasoma ruri tamike dahanzarinta ta dauki wayan sunan data ganine kan screen yasata kasa daga wayan anyi serving number din da"hearty" har wayan ya tsinke bata dagaba se akaro nabiyune tadaga wayan azuciyanta tana cewa ko muhammad dinne to, daga cikin wayan tajiyo muryar yousef kamar zeyi kuka muryanshi harrawa yake yace my baby sosae zuciyanta yatsananta bugawa jin muryan nashi dasunan daya kirata dashi,shirun da tayine yasashi cewa shin meyasa kekuwa kika azabtar dani haka why inaji ina gani bacci yagagareni ina cikin tashin hankali meenal menene yake faruwa haka kullum cikin mafarkinki nake marasa dadi meya samekine, pls talk to me mana kozan sami nutsuwa,cikin inda inda tace wayana ne yasami matsala shiyasa kajini shiru but am so sorry,sosae taji sauke ajiyan zuciyansa yace yaushe zaki dawone banyi tsammanin zaki iya tafiya wani guri ki dade baki nemeniba,mimi tace bahaka bane nakusa dawowa ay kada kadamu kajee yanzu bacci zanyi zamuyi waya gobe batareda tajee meze ceba takashe wayan tanata zaro idanu harda guminta kamar wadda tayiwa sarki karya,koda meenal tafado mata arae se hawaye shar allah sarki meenal masoyinki yana bidarki amma sedae kinyi masa nisa allah ya tseratar dake kidawo cikin 'yan uwanki namiki alkawari zan riritamiki soyayyarki harzuwa sanda zaki dawo,jikinta asanyaye tahau kan bed takwanta zuciyanta fal da tunani kala kala,
Washe gari
Tunda tayi sallan asuba takwanta bata kuma sanin inda kanta yakeba tayi nisa abaccinta aunty saratu harta gama shirya musu breakfast amma shiru bata fitoba tayi mamaki tunda kullum tare suke girkin tunda tazo amma yau ko motsinta hakanne yasata shiga dakin nata taganta akwance tanata sharar baccinta ganin haka yasata yin murmushi tajuya tace lallae meenal anshawo gajiyar biki,har mujaheed yafito bata tashiba don haka sukayi breakfast dinsu sukadae,
wajan karfe 12 rurin wayanta yatasheta takuwa lalubeta cikin bacci tadaga wayan batasan kowayeba jin muryan inty datayi yasata watstsakewa tamike zaune balaifi sundan taba hira sannan tashiga bathroom koda tafito seda tagama shirinta tsaf tafito parlour aunty saratu nazaune taganta tasoma murmushi tace meenal seyanzu allah yanufa kenan antashi gaisawa sukayi tanemi guri tazaun, a ah yazaki zauna kije kisamawa kanki abin kari koh,inda allah yatemaki mimi tayi mata nuni da dahannu inda kitchen din yake,
Indomie kawae tadora tahada tea tana tazauna a kitchen din tana dan kurban tea din,talula tunaninda tasaba taji anmata doss akumatu,tayi saurin juyowa kuwa suka hada idanu taga ashe mujaheed ne yamata kiss a kumatu lallausan murmushi yasakar mata itama tamayar masa tace yayana ina kajene zama yayi gefenta yace ayke zanwa tambayar ina kikaje haka ina baccinki yakaekine bata cemasa komaeba sema murmushi datayi masa,ruwan indomie dinda tadorane yatafasa kamshi kuwa yacika kitchen din harda hadiyan yawunsa yace my dear mekike girka mana haka me dadi dariya tadanyi tace indomie cefa bawani abu bane jinjina kae yayi yace masha allah matata ta iya girki kenan maganarshi seta bata kunya tasunkuyar dakae tana murmishi,koda yaga seya gyara zama yace meenal arayuwata inason matata ta iya girki inaso sosae kuwa,to yayana allah yabaka wadda tafini hadawa mah,saurin girgiza mata kanshi yayi yace no ina bazan taba samun wacca tafiki agurinaba babu ita bazan gantaba kaf 'yan matan duniyar nan kekadaece wadda nake kauna kike zaune azuciyata tsawon lokaci bazan iya jure tashinki bah ayanzu meenal ina matukan kaunarki kuma inason yin rayuwa dake tahar abada muzauna matsayin miji da mata,kawae dae fatana shine bazaki kiniba meenal inason sanarwa iyayena amma inajin fargaba bansan meye azuciyanki bah bakuma nason ayimiki dole arayuwa indae bakya sona kada kikee fadamin kada kiji nauyina asoyayya babujin nauyi meenal nibazanyi miki doleba zan hakura koda kuwa hakan zezama ajalina, burina dae kullum kikasance cikin farin ciki,
Sauke ajiyan heart yayi yace dukda kinada yarinta meenal amma hakan bashine zahanaki sanin so bah inason jin furicin ki abindake cikin zuciyanki kigayaminshi yanzu meenal,duk maganan dayake kan mimi yana kasa idanunta nata zuban hawaye tanaji wani irin zafi azuciyanta jitake kamar takwala ihu duk wanan kalaman nasa bada ita yakeba da meenal yake,ita kuma tun randa tafara ganinshi zuciyanta takamu dakaunarsa,sedae shikuma meenal yakeso, wata ziciyan tace mata kada kiga laefinsa tunda meenal yasani bakeba, hearty ne yafado mata arae wato yousep sosae kanta yadaure to ayga wanda meenal takeso ma bashiba, oh ya allah katemakeni wlh nakamu da kaunarsa matuka har inaji zafi idan yana furta kalaman kauna yana kiran sunan meenal yazanyine idan na amince mishi meenal tadawofa, kodae nafada mishi gaskiya ina baze yiwuba gaskiya bazan iya jure rashinkaba mujaheed koda meenal tadawo bazan iya rabuwa dakaeba, rintse idanunta tayi hawaye nafita, ya allah kaine kadai kasan nufinka na kawoni cikin wadan nan mutane allah kasa hakan shiyafi alkhairi agaremu,
Hannunda tarike cup din tea dinne taji yarike danashi hannun cikin yanayin tausayi yace pls say something meenal,hawayenta tashare datago suna kallon juna tace ina kaunarka yayana ina tabbatar maka sonda nake maka yafi wanda kake yimin ina hawayen farin cikine ayanzu dajin kalamanka,kayimin alkawari koda anan gaba bazaka taba juyamin bayaba komenene zefaru anan gaba kada ka kini bazan iya jure rashinkaba arayuwata tana magana tana masa kuka,hakan kuwa bakaramin tafiya da mujaheed yay wani irin sanyi yana ratsa masa zuciya jinshi yake kamar yafi kowa sa ah,yana zuba murmushi yasa hannu yana share mata hawaye yamatsa daf da kunnenta yana cewa i promise u my dear komin wahala bazan taba barinkiba meenal kece farin cikina zan zame miki bango jigo a rayuwarki so pls stop cry am always with u,sam mimi tarasa farin ciki take ciki ko bakin ciki batajin dadi idan yana ambaton meenal,tanajin yadda yake ambatun meenal yana mata kalami masu dadi,
Jiki babu kwari tamike tasoma juye indomie dinta a plate shikuma yafita zuciyanshi kal da farinciki tabare egg dinta guda uku tafito jiki babu kwari,suka zauna tare sukaci indomie din mommy di nakallonsu duk abinda suke tana ankare dasu farin ciki sosae ya lullubeta....


TAKU A KULLUM NANA BMB.
08147110349
[7/28, 8:20 AM] Nana BMB: 💝💖💝💖
RABON KWADO....
BOOK 2


NA NANA BMB


page 13-14
Mujaheed yana ankare da mimi gaba daya yanzu tasauya komae nata dasanyi takeyinshi bata wani surutu sedae murmushi inta kama to bewani damuba yana tunanin duk sabida abinda yasametane takoma haka,
Koda suka kwanta bacci inty tanata latsa wayanta abinta itakuwa mimi seta juya mata kada taga hawayenda takeyi abin duniya ya isheta kamar tasoma tsala ihu,cikin zuciyanta tana cewa mekikeyi ne haka mimi kinkuwa kyautawa diyar mutane, wato "meenal" allah ne kadae yasan halinda take ciki inma tana raye kekuma gashi kina amfani da farin cikinta,rintse idanunta tayi tana dafe zuciyanta,yanzu yazanyi da rayuwata ni mimi ina komawa gidanmu meenal zasu kwashe idan tana raye sanan sudawo kaena komawata gida sam ba alheri bane gashi inason ganin mahaifiyata,zuciyata takamu da kaunar mujaheed matuka bazan iya barinshi cikin tashin hankaliba da kowama na meenal ina tausaya musu sosae dole nahakura da rayuwata nazauna inda allah yakawoni kuma shikadae yasan nufinshi nayin hakan,ya ubangiji ka kubutar da ita domin tadawo garesu nima nakoma nawa family din,tanata magana azuciyanta bacci yasaceta batare da tasaniba,
WASHE GARI
Tunda suka tashi inty kamar zatayi kuka duka 'yan biki suntafi se sukadae itada mimi itama kuma gashi yanzu zata tafi dawuri sameer yazo donyi sallama da aminin nashi mom tanata rarrashin inty itama mimi na nata jimamin azuci batasan wani kalar gidaba kuma yanzu zasu jitake dama suyita zamansu anan kayan azziki suka hada mata su mom sosae sannan suka tafi,suna hanyane yake cewa meenal ina wayanki ne?hankalinta nakan hanya tace tana cikin jakana,to meyasa kika kasheta meyasa kikeson rufe wayankine yanzu kowa yayta kiran wayanki akashe laifina suke gani jiya auntie ba irin fadan dabatayi minba awaya akan kin rufe wayanki kindena nemansu why?har daddyn ku tace bakya kiransa cikin damuwa take kallonsa harya gama sannan tace am sorry yayana banasonne sufahimci wani abu yasamenine amma yanzu tunda naji sauki muna zuwa zan kunna wayannawa murmushi yayi dajinjina kansa jefi jefi suna hira harsuka karasa gidan sedae mamakine yacika mimi ganin tsoffi datayi tanata tunani tasandae wadannan sunyi tsufa bazeyiwu ace iyayensabane inna tana salla se baba agefe yana lazimi yana ganinsu kuwa yasoma tafa hannuwa yana cewa oyoyo oyoyo 'yan jikokina sundawo gida sannaunku dazuwa,sosae mujaheed yaji dadin ganin kakannin nasa dayayi,yazauna gefen baba yana cewa tsoho meran karfe kaci zamaninka kanacin nawasu yana dariya yay naganar shima baban hakan yace fadi ka kara yaro naci zamanina inacin naku cakwas dani yaranka kaga nafika tsadadden jiki koh dakaene kakae shekaruna ina zaka ganu,mujaheed yay murmushi yace haba baba jifa jikin naka ai ina tunanin munkusa fara dakan gumba agidan nan,baba yay murmushi yadamki damtsen mujaheed yace tokumu gwadane innuna maka tsohon kashi ba irinna yarintaba,zafinda yajine yasashi cewa wlh naji baba nayarda amin afuwa, yakuwa sakeshi yana fara ah yace ja irin yaro allah yashiryaka mujaheed,dubansa yakae kan mimi tana zaune tanata sake sakenta yace meenal meke damunki ne kikayi shiru haka kamar ruwa yacinyeki koduk gajiyan bikinne,murmushi tayi tace a ah baba,girgiza kae yayi yace a ah dakwae abinda kedamunki ayda kalau kike dayanzu gidan nan bama jishi shiruba, zuciyan mimi kuwa tawani harba dajin furucinshi ita mezatace musune sam batasan surutu ko kadan hawan mata kaema yake inyayi yawa,kallon mujaheed baba yayi yace meke damun jikalletane se kallonta yake yana mata alamu da ido amma kanta yana kasa,dan yake yayi yace gida takeson komawa ne,se ayanzun tadago takalleshi tana yana mata inkiyi da idonshi tagane nufinshi kada tabari agane tashiga matsala,baban yace to koyau zaka maidatane ya girgiza kae yace a ah haba bayauba dae hakuri zatayi,
koda inna ta idar da sallah mimi tahubawa idanu tana murmushi alamu taji ana kallonta koda tadago kuwa suka hada idanu tayi saurin sunkuyar dakanta tace ina wuni sororo da mamaki ta amsa mata wanda inda dane datuni taje ahaye mata cinya,inna tace sabon salo lallae meenal gida akeso kaga yadda tayi wani ladaf kamar wadda akayiwa mutuwa keda kikace bazaki komaba kinzo kenan sedae suyi hakuri ashe kinfasa zama gurin saratun kenan,to ay setazo takwashi kunyarta taji abinda kikeso yanzu,sosae suke hira avinsu cikin jin dadi wanda mimi nata murmushi ne kwae har tsokanarta inna takeyi sedae tayi murmushi sosae taji tsofaffin sunshiga ranta,sunkuwa yi mamakin yin shirunta kuwa haka su mummy suka karaso itama taga mimi cikin wannan yanayin nashiru mujaheed yanata zuba tabararsa yaga yadda mummy kezuba masa harara yarasa meye dalilin yin hakan, daga karshema hannun mimi takama shiga daki suka zauna tace meenal fadamun abinda yake damunki kada ki kuskura kiyimin karya meyasa kikeson komawa gida kada ki boyemin idan mujaheed yay miki wani abune just tell me duka gaba daya kincanza jikinki yayi sanyi haka zaki koma musu gidan,murmushi mimi tayi tace wlh mummy babu abinda yayimin kuma gida nakeson tafiyaba, banason maganane dayawa haka nakeyi dama indae ina menstruation gashi yace auntie ma takirashi,
Seyanzu tasauke ajiyan zuciyan da harseda mimi taji tace ok yanzu

Please Login or Register in order to submit comment