Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

manta da ita,kuma banyi zaton wannan mgnr zata saka ki dawo da mutuwar fatima sabuwa ba"






Ya ilahi!!πŸ€¦πŸ»β€β™€Fatima!Fatima!!Fatima!!komai fatima?Waya fada masa mutuwa ce yanxu tasa nake kuka?to idan ba mutuwar ba mezaisa nayi kuka?mutuwarce ma kawai ta sakani kukan.Na raya a raina.




Dukkansu suka shigo suka tsaya mufida na tmbyr me akayimin don ina tunanin sunga lkcn danayo daki da gudu.




Kuje kawai ba abinda ya sameta kawai rigima ce irinta nernah"ya fada yana janyoni jikinsa.




A hankali yake busa min iska cikin kunne na,hakan yasa nayi shiru ina sauke ajiyar zcy Har bansan lkcn da bacci ya daukeni ba.






Dana farka ni kadaice a bedroom din,don haka wanka nayi na shirya cikin wata doguwar rigar atamfa.


Mai kawai na murza dan har lkcn banajin dadin jikina kuma bazance taqamaimai ga abinda ke damuna ba.




Mubina ce da iman kawai wai sauran sun fita zasuyo shopping sbd gobe zasuyi resuming school.




Wayata na dauka nahau watsap inda na fara krtnta wani novel a wani grp,duk da ba wani fahimta nake ba amma novel din da alama zaiyi dadi da ma'ana.




Sai daf da magriba suka dawo,saida kowa ya gabatar da sallah sannan aka baje kayan da suka siyo suna duddubawa.


Nidai ina maqele da hannunshi tun lkcn da suka dawo a masallaci shi da shahid ya riqoni.




Yaya ya kamata pa a fara siyan kayan baby tun yanxu"mubina tace.


Nidai kishingida nayi a jikinsa inajin yadda yake murza hannuna a hankali.




Waya fada miki anan zamu sayi kayan baby?zuwa end of dis month nake saka ran tpy Dubai,acan zan fara hado kayan"




Inajinsu sunata hira akan tpyr tasa nidai bance komai ba hasalima idona a lumshe yake dan haka kawai sai naji banaso ya tafi.




Yaya gaskiya babyn nan yana wahalar da sister,ni gani nakema rama yake sakata"mufida tace.




Banji yayi mgn ba sai jin hannunsa nayi akan fuskata.




Karkiyi bacci mana bakici abinci ba"ya fada bayan na bude ido.




Yaya ko Lunch din da mukayi ma bata ci ba wlh"inji mubina.




Aa banason rashin cin abinci kin sani,tashi muje kici abinci"






A baki ya ringa bani ina amshewa,nidai satar kallonsa nake inajin wasu abubuwa game dashi,dan kwana biyun nan bana gajiya da kallonsa,duk da banayi ta yadda zaisan shi nake kallo.






Kwana biyu kin rage walwala nernah kuma kowa cewa yake kin rame,ki fada min damuwarki,kinga ni yayanki ne kuma amanarki Abbi ya bani,banaso ace na gaza wajen kulawa dake"




Qaramin bakinsa kawai na zubawa ido ta yadda yake shiryo zance.


Da can mantawa yayi da amanar yake gasa min aya a hannu?




Ki fadamin mana kinji nernarhnah"






Inason ganinsu ammi ne"na fada dan kawar da zargi.






Murmushi yayi"kinga kuwa indai mukayi waya sai tace na gaishe da auta kawai fada miki ne banayi dan nasan rigimarki"




Ya abdul da gsk?dan allah ka kiramin ita yanxu"nace ina miqewa.






Sai kina cin abinci kuma kinyi qiba sannan,har gida zan kai ki sannan muje gidansu ya aisha"




Haka ya ringa ja min rai har nayi zcy nayi tapiyata daki.




Shirin bacci nayi duk da ba bacci nakeji ba.


Wayata na janyo tare da dannawa aunty anisa kira.




Hira mukasha inda take fada min suma sun kusa tahowa dan fara shirin bikinsu mufida.




Sai da muka gaisa da yaranta tukunna mukayi sallama,kafin na cigaba da karatun novel dina.




Da sallama a bakinsa ya shigo cikin wata shadda sai gyalli yakeyi,nidai har ya qaraso idona a kansa,Domin zan iya irga lokutan dana ganshi cikin manyan kaya gashi sai zuba qamshi yake.


Wayar hannuna ya karba ya ajiye gefe.




Shine kk gudo kk barmu ko?kinga ni fita ma zanyi zanje zance ne,baki ce nayi kyau ba"yace murmushi kwance a fuskarsa.




Saida na rintse idona dan takaici kafin na qaqalo murmushi.




Kayi kyau sosai,saika dawo"




Haka ina kallo ya fita,sakin kuka nayi na tausayawa rayuwata,dan a yanzu na tabbatarwa kaina na fada tarkon sonshi,dan da gsk kishinsa nake.




Wayyo allahnah,zuciya baki min adalci ba,sbd me zakimin hk?why?why?






Kuka nasha na godewa allah kafin nayi addu'a na gyara kwanciyata,dan yau bazan kwana a part dinsa ba,ya zama dole na nisanta kaina dashi tunda kusancin da muke dashi ne duk ya jayo min hk.




Amma kuma sai me?duk yadda naso bacci ya daukeni abin yaqi yiwuwa,ga wani zafi da zcytah takeyi idan na tuno inda mijina ya tafi.




Ta wani bangaren banga laifin zcytah data kamu da son daddyn shahid ba,domin ya cancanta a soshin.


Amma kuma ta wani bangaren nasan yafi qarfina,abinda yake qara sagar min da gwiwa kuma bai wuce kalamansa ba da yasha fadamin su lokutan da suka wuce amma idan na tuno daddyn shahid din da dana yanxu ba daya bane sai naji sassauci kadan.






Haka na ringa juyi a kan gado tare da neman mafita amma ban samu ba.


πŸ’™πŸ’™RABON KWADO....πŸ’™πŸ’™πŸ’™










Na Er mutan ungogoπŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹






Ina alfahari daku Rabon kwado fans,ina gdy da fatan alkhairinku game da exam din da nayi.


Da yardar Allah zan fara subirbido muku rabon kwado.










πŸ…Ώ145-πŸ…Ώ150








Har su mubina suka gama kallo suka dawo daki kusan 11 na dare ba daddyn shahid ba alamarsa.




Gsky zance yayi dadi..






Wai ina yaya yaje ne naga har yanxu bai dawo ba?"mubina tace.






Zance ya tafi inaga acan zai kwana"na fada a qufule ina daukan iman datai bacci don mayar da ita dakinsu.






Dana dawo dukkansu ido suka zubamin,nidai kuma daukar shahida nayi na fice na barsu.






Ina komawa na nemi gado na hau tare da jan bargo.






Bacci fa bai kamaki ba sister"mufida tace.






Idan batai bacci ba fita zatayi ta nemo shi ko kuma ita tace yaje yakai daren?wlh dama nice ke khadija wlh dasai yau mutum ya gane kurensa,sbd rainin hankali da matarka zaka tafi wani zance?"






Ni mgnrma qara bata min rai takeyi,haka mubina ta cigaba da mita,jin dirar mota yasa dukansu suka nufi bakin window tare da daga labule.


Zaiga zance wlh da ummi zan hada shi"mubina tace tana sakin labulen tare da dawowa.


Yadda nakejin zcytah kamar zata fito yasa nayi saurin dafe qirjina kozan samu sauqi.




Nasani dama son maso wani shi zai kasheni tunda nasan yadda na fada tarkonshi bazai taba sona ba.


Namiji kenan!kamar ba shine dazu ya gama yabo da koda ya fatima ba amma 6month da mutuwarta har ya fara neman wata,Allah sarki wanda ya mutu ai ya mutu,nida nake rayenma watana 4 da aure akace ya sadiq yayi aure bare ya fatima da yasan bazata dawo ba.








Sallamarsa cikin dakin yasa zcytah qara gudu wajen harbawa,dan dole na kuma dafe dai dai inda nake tunanin anan zcyr take.






Mufida ce ta amsa sallamar dan mubina rufe ido tayi kamar mai bacci,ni kuwa dama har kaina yana cikin bargo duk da ba sanyi akeyi ba.




Mufida badai har sunyi bacci ba?"yace






Eh mn yaya bakaga qarfe nawa ba?"mufida tace.






Mtw wlh ni kaina bansan dare yayi haka ba,dan taba min nernah ta taso mu tafi daki"naji yace.






Inaji mufida na tashina nayi mata banza harta gaji ta qyaleni.




Barta tunda bazata tashi ba,saina dauketa dan nasan tana jina"




Cak!naji an daga ni tare da janye bargon.




Qoqarin kwace kaina na farayi,ganin haka yasa ya qara rungumeni a jikinsa ya nufi hanyar waje.




kuka na farayi a hankali har saida naji ya saukeni akan gadon.




Dagoni yayi har lkcn idona a rufe yake sai hawaye da yake zuba dan kukan bamai sauti bane.






To menene kuma na kukan bagashi na dawo ba?ki daina banason kuka kinji?"yace tare da saka hannu yana sharen hawayena.




Jin ya daina goge hawayen yasa na bude idanuwa na.




Caraf muka hada ido nayi saurin kauda kai.


Saida naji ya tashi kafin nayi addu'a na gyara kwanciya duk da na fahimci a bedroom dinshi nake ba wanda na saba kwanciya ba.




Da taimakon Allah da addu'ar danake yasa na fara jin sauqi a cikin zuciyata.Gskyr batureda yace"Struggle Never End"ni kuma qaddarata kenan dakon soyayya,na gama ta ya sadiq yanxu na fada ta wani.




Ganin dakin ya dauki duhu yasa na qanqame jikina tare da fargabar allah yasa ba irinta ranar bane,to ai yau banyi masa laifi ba.




Jin an riqoni yasa na kuma firgita tareda qwala qara.




Qara riqoni yayi bayan ya kunna Lamp dake gefen gadon inda haske ya fara kawowa kala daban daban.




Ki rage tsoro kinji nernerh?"yace yana qara shiga jikina kamar mai jin sanyi.




Nernah inason yin aure amma wata zuciyar na rayamin idan nayi haka kamar ban kyautawa fatima ba,ki bani shawara dan allah""








Shiru nayi ina jujjuya maganganunshi,wato shi baya ma daukata a matsayin mata?Eh mana ai dama ya jiga ya sanar dani a mai yiwa yaransa hidima zan zauna nice dai na zaqe gashi na janyowa kaina na fada tarkon sonshi.






Ki fada min yadda zanyi nernah,inaso ne a hada bikin dana su mubina amma bansan yadda mutane zasu dauki mgnr ba,musamman ma ummi plzz ki fadamin mafita"












Tirqashi!!




Idan kece khadija wace iriyar shawara zaki bashi?shin xaki bashi shawara yayi auren ne ko kuwa?










Khayratie er mutan ungogoπŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹










Ya Abdul kayi aurenka kawai?ya fatima ta riga ta tafi bazata dawo ba,mgnr mutane kuwa ka toshe kunnuwanka domin Allah ne halarta muku auren mace fiye da daya idan har zakuyi adalci,bare ya fatima bata raye.Ka sanarda ummi insha Allah zata amince"nace muryata a rauna ne.






Jin yayi shiru bashi da alamar mgn yasa na janyeshi a jikina na fara sauka a gadon.




Ina kuma zakije?"najiyo shi.






Ban jiyo ba illa qoqarin mayar da kwallar data taru a idona da nayi.




Zanje na kwanta ne dare yayi"nace cikin dauriya domin kadan ya rage na fasa ihu.






Kizo ki kwanta anan mana?"






Banyi mgn ba sai ma hanyar fita dana nufi da sauri jin kukan takaici ya taho.






Ya bari idan yayi aurn ya samu hakan daga matarsa,dama yace bazan iya daukar dawainiyarsu shida yaransa ba,dan hk daga yau na daina yarda ko hannuna ya taba,kamar yadda yace shi yayana ne zanzauna a matsayin qanwarsa,soyayyarsa kuwa zanyi ta dakonta har lkcn da allah zai yayemin ya bani mafita.






Haka na raya daren da kuka da addu'ar neman sassauci,saida naji zcytah wasai kafin na nemi makwanci cike da qissima abubuwa iri iri.




[09-07, 12:55 PM] Cwt-besty: πŸ’™πŸ’™πŸ’™RABON KWADO....πŸ’™πŸ’™πŸ’™










Er mutan ungogoπŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹










πŸ…Ώ191-πŸ…Ώ195






Bugun get din na shigayi ba tare da tunanin wani abu ba,hkn yasa su ummi nufo inda nake cikin hanzari.


Jin wata tsawa ta cikin gidan yasa na tsaya da bugun da nakewa get din.


Wani murdadden soja ne ya fito kakkaura mai jini a jika,siffarshi ma kanta abar tsoro ce.


Masifa yake da gurbatacciyar hausarsa.ganin yaya sun qaraso yasa na harareshi tare da murguda bakiπŸ™„πŸ˜


Yaya ne ya shiga bashi hqr tare dayi masa bayanin gurin masu gidan mukazo.


Hajia yasan da zuwanku?"itace kalmar data kuma batamin rai da sojan ya fada.


Wai yaushe mutanen nan sukai arziqin da ganinsu ma sai an nemi izini?


Kince mini ke yaronsu ne,bari na kira hajia a waya,idan yace abarku ku shigo to"sojan ya fada yana shigewa ciki.


Lallai ma mutanen nan wato Duniya sabuwa suka samu suke cin karensu babu babbaka"na fada cikin takaici.


Malama kiyi mana shiru"yaya yace ganin yanayin ummi.


Su mubina ne suka tattaro yaran suka biyomu don ganin mu a tsaye.


Leqowa sojan yayi tare da yafito mu don hk muka shiga qatuwar farfajiyar wadda ta qunshi bangarori guda shida.yanayi da tsarin gidajen duk iri daya ne kamar yadda suke a jere bibbiyu bibbiyu.
Daga gefe wajen ajiye motoci ne da kuma qaramin masallaci.


Hajia yace a shiga daku,daya dauka masu neman taimako ne sai da nace a mota kukazo,kinsan hajia bayason talaka"sojan yasa yana murmushi.


Mu duka ba wanda ya kulashi,bayansa mukabi ganin ya nufi daya daga cikin gidajen.


Knocking yayi wata matashiyar yarinya ta bude,inda yayi mata bayanin mune baqin hajia sannan tayi mana iso.


Qaton falon nabi da kallo ina qissima kudin da aka kashe masa,gsky mutanen nan sun sami duniya,kardai ace wannan rubabbiyar tsohuwarce a ciki?


Zama mukayi akan kujerun ni harda miqe qafa.


Hajia na hutawa,amma nan da 1hour zata fito"yarinyar ta fada tana komawa inda ta fito.


Shiru mukayi kowa da tunanin da yake ganin yaran kamar sun takura yasa na janyo remote control din dana gani kan centre tble na kunna t.v.


Hararata ummi tayi nayi murmushi kawai.


Wai me wannan tsohuwar take nufi ne?sai kace munxo neman wani abu,ko kuma bamu da aikinyi ne?"yaya ya fada cikin bacin rai ganin mun haura awa daya a zaune.


Ayyah babanah,ka qara hqr mana har lkcn da zata fito,idan muka abinda ya kawomu ba shikenan ba"


dama sabon shigar arziqi ai sai ya nuna kansa,bare wadanda suka samu sama ta ka"na fada ina qara bararrajewa kamar ina falon ummi😊.


Anisa na qarajin bakinki ranki zai baci"ummi tace.


Jin alamar bude qofa yasa duk hankalinmu yayi wajen.


Dariya ce ta kusa subucemin ganin baba shatu a while chair,kai da ganinta sakasan taci duniya,kamata yayi zuwa yanxu tana ta istighfari domin mutuwa ko yau ko gobe,amma sbd budurwar zcy sanye take da rantsattsen less don masifa harda kafa wani dauri a goshi.
Harara ummi ta gallamin hakan yasa na gintse dariyata ina kallon ikon allah don yan mata biyu ke turota.


Bangama shan mamaki ba saida naga sun shimfida mata wani rug sun shimfideta akai tare dayi mata matashi sa cushion,ta wani kishingida kamar wata sarauniya.


Saida ta kuma dai daita zaman glass din fuskarta kafin ta fara binmu da kallo daya bayan daya.


Gaisheta muka shiga yi,kafin ummi tayi mata bayanin mu suwaye da kuma abinda ya kawo mu.


Shuru tayi tana qara binmu da kallo kamar tanason gano wani abu,kafin daga bisani tayi murmushi.


Dama nasan wannan ranar zata zo,dama kuma wannan ranar nake jira,domin nasan dole akwai ranar da zaku nememu,kuma na godewa allah da ina raye wannan rana tazo,ranar da ahalin abubakar suke durqushe a gabana suna neman wani abu gareni nida ahalina"


Kallon kallo muka farayi danjin abinda ta fada,ita ta dauka abu mukazo nema a gurunsu?ai duk lalacewar goma tafi biyar albarka.


Mannira!mannira!Ta shiga kwala kira.wata budurwace ta fito tana wani yauqi.


Nifa shiyasa banason zuwa bangarenki hajia,kita batawa mutum suna kuma kullum sai na fada miki munirat sunanah"


Kedai kika sani 'yar nema,maza kirawon iyayenki kice inason ganinsu yanxu yanxu"


Ficewa tai batare datayi mana mgn ba,muma ko kallo bata ishemu ba.
Muna nan zaune raina in banda suya ba abinda yakeyi,sbd yadda baba shatu take zuba mulki saika rantse jinin sarauta ce.
Su mufida kallo daya zaka musu ka gano bacin ran da suke ciki musamman ma mubina,bare kuma oga kwata kwata daya hade fuska yana danne danne awaya.Ummi ma dauriya ce kawai ta lullube damuwarta.


Uncle sani ne ya fara shigowa kafin sauran suka fara zuwa daya bayan daya.Bayan gaisuwa ba wanda yake qara mgn.
Ni dariya suke bani ganin yadda suna shaidamu sai kowa ya fara cin magani da shan qamshi.


Kamar yadda kuke gani wadannanahalin danuwanku abubakar ne,mahaifiyarsu tamin bayini sunxo ne akan mgnr auren wadancan yaran guda biyu.To yanxu dai niba dolensu bace,kune dolensu,don hk idan da akwai abinda zaku iya taimaka musu dashi sai ku basu"


Gsky hajia ta bangarena babu wani abu dazan iya,ban sani ba ko sani"uncle auwal ya fada yana ciccin magani.
Har yaya zaiyi mgn ummi ta hanashi,don hk nima dole na hadiye mgnr da nayi niyyar yi.


Banda abin hjy ai kinsan yanxu bamuda wasu ajiyayyun kudi da zamu iya dauka muyi kyauta dasu,muda muke shirin saka hannun jari a qasashen waje ai muma abin a bamu taimako ne"


Murmushi baba shatu ko nake hajia shatu mai jan kai tayi,kafin ta kalli su aunty hafsatu.


Ku kuma fa iyayen amare ko akwai wata gudummawa?"


Abinda maza suka kasa ai mu mata ba'a sako mu a ciki ba,Allah dai ya bada zaman lpy,ya bada yadda za'ayi"aunty zuwaira ta fada.


To asiya kin daiji daga bakin iyayen nasu,don hk ayi gaba ko za'a dace,ko kuma a fitowa yara da haqqinsu da sunusi ya washe ya kai qasar waje"inji baba shatu.


Allah ya huci ran hajia,dama ba munxo neman wani abu bane,domin alhmdllh bamu nemi komai mun rasa ba ba,tunda har wasu suna samu daga qarqashinmu Suna ci,sannan ta sanadiyyar abinda muke dashi har wasu sunaji kamar sunfi kowa arziqi a duniya.munxo ne domin sanar dasu iyayen nasu domin fita haqqinsu,don koba komai su dangin mahaifinsu ne suna da haqqi akai"


Ke asiya,karki kuskura kizo har cikin gida kice zaki zage mu,idan ba maular ba mezai kayoku inda muke?to wlh salin alin ki tattara kan watsattsun yaranki kuyi gaba tun kafin nasa a wulaqanta ku"aunty hafsatu ta fada tana miqewa kamar zatayi dambe.


Hafsatu kenan,ai watsattsun yara sune wadanda aka ciyar dasu da haram,aka shayar dasu da haram kuma suka rayuwa cikin haram,kuma sanin kanki ne ahalin abubakar sunfi qarfin wulaqanci daga wulaqantattu wadanda suke taqama da dukiyar marayu"


uncle sani ne ya miqe yana huci kamar zai daki ummi.


Barta sani ai idan bata zagemu ba bazamusa zafin talauci ya ratsata ba"baba shatu tace.


A fusace yaya ya miqe yaja hannun ummi suka fice,don haka muma muka kwaso yaran muka fito muka barsu sunata zage zage.
Ni kuwa raina fes,don ummi ta gama min komai data fada musu wadannan maganganun.


Daqar muka samu ummi ta dawo hankalin ta,don hawan jininta saida ya tashi,satinmu daya a asibiti aka sallamo mu,uncle kuwa fada yaitayi akan zuwan namu.shine dashi da wasu daga cikin abokan abba sukai komai daya shafi mgnr aurensu mubina.


Baba shatu da ahalinta kuwa bamu qarajin duriyarsu ba,amma lkc lkc akan yi barna a company,amma zuwa yanxu ni na daina zargin su baba shatu,nafi tunanin ta wani bangare ne muka qara samu maqiya.






Cigaban lbrπŸ‘Œ
[09-07, 12:55 PM] Cwt-besty: πŸ’™πŸ’™πŸ’™RABON KWADOπŸ’™πŸ’™πŸ’™












Er mutan ungogoπŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹












πŸ…Ώ186-πŸ…Ώ190




Sosai hankulanmu suke a tashe don iya buncike anyi amma ba'a gano musabbabin zurarewar kudin ba,hakan ya bamu tabbacin na jiki jiki wanda yasan sirrin abbanmu shike aikata hakan.


Addu'ar da muka yawaita yasa asirinsu ya fara tonuwa.


Inna ladi itace shugabar masuyi mana hidima a gidannan,komai idan suna buqata ta hannunta ake basu,hatta albashi ita ake bawa tana basu.kasancewarta dattijuwa yasa muke girmamata,ba kamar ummi data dauki dukkan yarda ta bata.


Azal ce ta ciyota da kanta tazo tana kuka da neman gafara akan duk abinda ake ciki tanada masaniya,domin ita aunty hafsatu(yayar abba)ta bawa wani abu a leda tace ta tabbatar da zuba a abincin abba.washegarin da yaci abincin shine wannan ciwon ya kama abba.


Kuka nasha sosai dan ummi sam taqi amincewa na nada mata dukan da zata daina numfashi.
Da uncle ma yaji shida yaya cewa sukai zasu kai qara kotu ta haka ne za'a gano duk wani mai laifi.Amma fir ummi taqi amincewa acewarta abin kunya ne mu tsaya shari'a da yanuwan mahaifinmu,kuma koshi yana raye tasan bazai goyi da bayan hakan ba don hk mu barsu da allah ai shi ba azzalumin sarki bane.


Badan uncle yaso ba yabar mgnr,amma yasa aka kori duk wasu masu hidimar gidan don yace da hadin bakinsu komai ke faruwa.


Daqar ya yarda aka samo sabon get man,mai bawa shukoki ruwa sai kuma wadda zata ringa taimakawa ummi da abinda ba'a rasa ba,amma itama bata shigowa part din gidan tanacan part din da aka tanada domin masu aiki,kuma idanma ta kama zata shigo to iyakacinta falon qasa.


Durqushewar A.A motors yasa aka siyar da sauran Kadarorinsa domin farfado da company din.




Tunda yanuwan abba suka samu abinda sukeso suka dauke qafa daga garemu,akasin da da kullum suna tafe a hanyar gidanmu.hakan ya qara tabbatar mana da cewa komai daga garesu ne.Kamar yadda basu qara neman mu ba muma sai muka manta dasu.


Tasowar bikinsu mufida yasa ummi ta matsanta sai munje wajensu mun sanar dasu domin a yanxu bamuda wasu dangin mahaifa da suka wucesu.


badan raina yaso ba na tattaro yara muka zo domin zuwa wajen dangin mahaifinmu.


Gaba dayanmu kwanmu da kwarkwatarmu muka tafi tsohuwar unguwar da suke zaune.Munsha wahala sosai don har mun fadda tsammani zamu koma gida domin duk yadda ummi take musu kwatance kowa muka tmby sai yace baisan wadanda muke nema ba.


Wani mai kanti mukai sa'a ya gano kwatancen da muke dan kusan shekara 8 kenan rabonmu dasu.


Hajia ai idan kwana kuna tambayar auwalu da qaninsa sani bazaki sani ba,nima dan dai na dade a unguwar ne yasana gano wadanda kuke mgn akai,mgnr gsky yanxu duk ahalinsu sun tashi daga wannan unguwa.Akwai wata sabuwar unguwa da ake kira sabuwar abuja can suka koma wajen shekaru 4 da suka wuce.yanxu hakazan muku kwatancen unguwa kuna zuwa ku tmby kigan hajia shatu mai jan kai na tabbata duk wanda kuka tmby zai nuna muku"


Duk cikinmu ba wanda ya iya mgn saboda mamaki da al'ajabi ni kuma mamaki nake har yanxu baba shatu na raye.


Yaya ne ya miqa masa hannu suka qara musabaha,mudai mota muka koma muka barshi yanawa yaya kwatancen unguwar da zamu nufa.




Har muka dauki hanya ba wanda ya iya cewa komai.
Kamar yadda dattijon yayiwa yaya bayani hk muka isa unguwarmai qarancin jama'a da zirga zirgar ababan hawa.


Yayane ya fara parking don dama motarmu ce a gaba inda yake tuqamu sai ni a gefensa sai shahid,zaid,zarah da shahida a back seat.
Dayar motar kuma driver ne sai ummi,mufida,mubina da kuma iman.


Mun dade a cikin mota kafin yaya ya samu wanda zai tmby inda aka kwatanta mana.
Dawowa yayi muka qara gaban wani qaton gida wanda za'a kira da estate.


Yaya ba'a samu gidan bane?"nace ganin ya tsaya kuma baice komai ba.


Nan dai wanda natmby ya nuna min,amma ina tunanin gsky banan bane"yace yana nuna estate din.


Wangale daya daga cikin manya manyan get din estate din yasa muka maida hankali ga rantsattsiyar motardata sako kai waje.


Da hanzari yaya ya fita don gani motar na shirin wucewa,gashi na waje baya iya hango na cikin motar.


Ganin mamallakin motar ya sauke glass suna mgn da yaya yasa na fito kamar yadda naga ummi ma ta nufi wajen.


Kafin mu qarasa mai motar ya maida glass din tare da bawa motar wuta yayi gaba tare da budemu da hayaqin motar,kana gani kasan da gayya akai hakan.


Saida hayaqin ya lafa kafin muka samu qarasowa ida yaya yake a qame kamar an dasa shi.


Ba gidan bane ba koh?"muka fada a tare nida ummi.


Gidan ne,don fu'ad ne ya fita a mota yanxu"yace yanason boye damuwarsa.


Fu'ad?fu'ad fa kace"muka sake tmby kamar hadin baki.


Eh shine,kawai mu koma gida don ya sanar dani babu mai sauraronmu tunda ba'asan da zuwanmu ba"ya fada yana tpy dan komawa mota.


Eh lallai,shi fu'ad din har yaushe yayi baki da arziqin da zai fada mana haka?sbd rashin mutunci harda budemu da hayaqi,to wallah yau komin bala'i sai mun shiga gidan nan koda shugaban qasa ne a ciki"na fada na nufar get din da aka rufe baba dadewa.


Muje zuwa don jin yadda zata kaya.shin suna nasarar shiga gidan ko kuwa?idan sun shiga wace iriyar tarba zasu samu wajen masu gidan?


Er mutan ungogoπŸ’‹πŸ’‹
[09-11, 7:57 PM] Cwt-besty: πŸ’™πŸ’™πŸ’™RABON KWADO....πŸ’™πŸ’™πŸ’™










Er mutan ungogoπŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹






πŸ…Ώ196-πŸ…Ώ200




Gaba daya jikina yayi sanyi da jin lbrnsu,inda tausayinsu ya mamaye min xcy.
Sosai na jinjinawa qoqarinsu don idan bakaji lbrnsu ba bazaka taba tunanin sunada wata matsala ba.


Amma khadija bayan abinda kk fadamin dazu akan fadanku da broh babu wani abu daban"ta tmby ni.




A iya sani na babu komai aunty anisa,koshi yace nayi masa wani abu?"nace ina kallonta.


Kamar zatayi mgn kuma sai tayi shiru.


Shikenan dai kiyi bacci yanxu kinga dare yayi sosai"


Haka na kwanta inata jujjuya lbrn a zcytah,na dade banyi bacci ba kafin sarkin barayi ya sace ni.


Banyan munyi sallar asuba ma banyi wani bacci mai yawa ba sbd rashin sabo,dan hk qur'ani mai girma na shiga karantawa.


Dana gama ma na qara kwanciya amma baccin yaqi zuwa,don hk na shiga nayi wanka.
Dakinsu mufida naje sunata sharar bacci,dan haka na dauki kayana na sakatare da kafa dauri duk da banyi kwalliya a fuskata ba.


A hankali nake takawa ina qarewa falon saman kallo,kafin na fara saukowa daga stairs din.


Can saman kujera na hango ummi da littafin azkar da alama karantawa takeyi.


Qarasawa nayi na zube kan rug ina gaisheta.
Kamar ko yaushe ta asma cikin kulawa kafin tayimin nuna dana koma kan kajera,murmushi kawai nayi ba tare dana koma ba.


Hk muka kasance tsahon lkc,ganin ta gama azkar din yasa nayi mgn.


Ummi akwai wani abu daza'a taimaka dashi?"


Aa diyatah yi zamanki,akwai mai aiki zata gudanar da komai,zuwa yanxu ma nasan ta kusa kammalawa.Su wadancan kasoshin har yanxu baccin suke?"
Murmushi nayi ina qara qasada kaina.


Bude qofar falon da akai yasa muka kalli gurin a tare.


Sanye yake cikin suit ash colour,fuskarnan tashi kamar kullum,amma kana ganinsa zakasan akwai abinda ke damunsa,dan tafiya yake kamar yana tausayin qasa,akasin da da yake tafiya cikin kuzari,qasaita da tafin jarumta.
A cikin sakwanni da basu wuce 10 ba na gama karantar yanayinsa,kafin na dauke kai kamar ban damu da sanin wanda ya shigo din ba.
A dan nesa dani ya zauna tare da lankwasa qafa sannan ya shiga gaida ummi.


Fuskarta ba yabo ba fallasa ta amsa a taqaice ba tare data kalleshi ba,hakan zai tabbatar da akwai wani abu a qasa.


Nima gaidashi nayi kamar anyi mini dole,shima a taqaice ya amsa yana satar kallon ummi da alama bashida gsky.


Su shahid sun tafi school ne?"yace.


Aa kai ake jira kazo sai ka shiryasu ka kaisu"ummi ta fada still bata kalli inda yake ba.


Tsam ya miqe ya isa inda take ya zauna tare da riqo hannunta.


I'm so sorry umminah,wlh indai a kan mgnr jiya ce na janye tunda

Please Login or Register in order to submit comment