Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

da gsk na rasashi๐Ÿ˜ญ.


Kinci abinci kuwa?"
Naji yace.


Eh"


Bakici ba nasani,kuma idan kinason mu shirya ki tashi ki dauko abinci kici,idan ba haka ba kafin gobe zakiji lbrn nabar garinnan"


Dan allah karka tafi,wlh xanci"na fada ina qara sautin kuka.
Baiyi mgn ba sai tari da yake tayi tun inayi masa sannu har nayi shiru ina kuka.


Ya sadiq ka gani koh?kaga zamu cutar da kanmu sbd farin cikin wasu koh?"na fada danjin tarin ya lafa.


Dif!!ya kashe bawar ba tare da yayi mgn ba,haka naita bin number din amma bata shiga.


**-**-**-**-**-*-*


Yau ta kama Alhamis,wanda a lissafinsu abbi saura kwana biyu daurin aurenah,zuwa lkcn duk wanda ya gani saiya tausaya min,sbd na lalace kamar ba khadija yar gayu ma'abociyar san ado da kwalliya ba.
Ina zaune a tsakiyar yayyena da suketa yimin magiyar naci abinci,amma ni duk hankalina ba'a kansu yake ba,tunanin nusaiba da ya sadiq nake,dan tun ranar da mukai wayar nan banqara samunshi a waya ba,nusaiba ita kanta na kasa samunta,gashi har lkcn ban qara ganin qeyarta a gidan ba.


Khadija!khadija!!ko khadijan bata nan ne"najiyo muryar abbi na kwalan kira.
Saida gabanah ya fadi danni yanxu tsoron kiran abbi nake.
Ya ruqayya ce ta miqon hijabi tare da cewa "maza kisaka kije kiranki yake"
saka hijab din nayi na fito tsakar gidan wanda na kusa kwana 4 ban tako shi ba.
Abbi yana tsaye a qofar dakinsa naje na zube ina gaisheshi da kodaddiyar muryata.


Ki shiga ciki Abdurrahman yananan"yace yana nunan dakinsa.


Abdurrahman?waye kuma haka?
Ganin ya tsaya yana kallonah yasa na miqe na danna kaina dakin ba tare da nasan mai kiran ba.
Rass!Gabana ya fadi dan ganin mijin ya fatima a zaune kan sallaya ya tankwashe kafa yana latse latse a wayarsa.


Ba shiri na tsugunna dan jin wani jiri danayi yana qoqarin kayar dani.
Mun dauki tsahon lkc a haka inata saqa da warwara na jiyo takunshi yana qarasowa inda nake.
Zama yayi daf dani wanda yasa bugun xcy tah qaruwa da sauri.
Sai daya gama qaremin kallo danni koya aka kalleni inaji a jikina.


Dubeki dan Allah,ke a dole xaki aure mijin yayarki saboda cin amana koh?to inason ki sani,zaki aure ni kamar yadda kike buqata,amma ki sani na karbi wannan qaddararran auren nakine sbd yarana suna buqatar 'yar aiki..."


Inaso kisa a ranki ba gidan aure zakije ba gidan aiki xakije,dan nasan kinsan nafi qarfinki tun ba yau ba"


Sannan naji kamar ance wai kina zuwa jami'a koh?to inaso daga yanzu ki saka hakan a tarihin rayuwarki,domin zakina zama a gida ne kinamin gadin gida na.wannan shine saqon idan kin kiyaye kanki"


Innalillahi wa inna ilaihirraji'un!!
Wai meyake faruwa da nine?me yasa rayuwa zata juya min baya irin haka?bayan hanashi aurena da akayi burin nashi ma baza'a bari na cika masa ba?


Bansan lkcn da ya fita a dakin ba,sai muryar abbi dana jiyo yana cewa.


"me kuma kk jira har yanxu baki shiga ciki ba"


A hankali na furta"Abbi ku taimaka min na cigaba da karatu na koda zaku aura minshi dan allah"
Guri ya samu ya zauna kafin yace"khadija inaso kisan cewa abdurrahman a yanxu kamar mijinki yake,zan iya cewa yafini iko dake,kamar yadda ya buqata baya son kici gaba da xuwa mkrnt dole ki hqr da hakan.ki duba dukka yanuwanki akwai wadda take gidan miji take karatu?fasa rayuwa sukayi a haka?to ki cire wannan a ranki ki tashi ki bani waje"


A hankali na miqe na fara barin dakin,wanda a lokacin juya ta dibeni ta zubar a wajen.


Ina farkawa na ganni kwance akan gadon asibiti.
Meyasa ma aka kawoni?aida an barni a gida na mutu kawai na hutu da wannan baqin cikin.
A hankali na miqe zaune dan inajin qarfin jikina.zare allurar qarin ruwan nayi na wurgar domin bana buqatar hakan.
Tashi nayi na shiga toilet nayi fitsari tare da dauro alwala dan nasan ana bina sallah tunda yanxun naga kamar safiya ce.


Ina fitowa naga ya aisha a zaune.Riqoni tayi tanamin sannu,nidai daka na amsa na dauki hijabin dana gani na saka.


Yaya yau wace rana?"nace ina kallonta.


Yau friday"


Au ai nazata wannan karon sati nayi a asibiti ba numfashi,amma duk da haka langwabewa zantayi har abbi ya gaji ace an fasa auren,tunda ina asibiti dai ba'a dauran aure ba.


Saida na idar da sallah nayi wanka naci abinci na kwanta muna dan taba hira da ya aisha dan da alama taji dadin ganin nadan saki raina.


Da dare inajin muryarsu abbi na rufe ido haka suka gama maganganunsu suka tafi.


Washe gari nida ya aisha muka yini a asibitin dan bayan ita ba wanda ya leqo,da dare ma haka.
Ranar lahadi ina zaune na jingina da bango ina sana'ar tunani,ya aisha kuma taje gida,naji an turo qofar dakin tare da sallama.
Nusaiba ce,dan haka da gudu na tashi naje na rungumeta.


Kuka ta fara min,ni kuwa naje na zaunar da ita a kan gado ina kallonta,domin ni sha'awa take bani yadda take kukan dan ji nake dama nice na samu damar zubar da hawaye.


Ganin batada alamar tsayawa da kukan yasa na fara rarrashinta.
Daqar tayi shiru tana sauke ajiyar xuciya.


Sis ina kk shiga inata nemanki,kuma kinsan a halin danake ciku ina buqatarki a kusa dani?"nace ina qarasa goge mata hawayen fuskarta.


Kiyi hqr sis,bama nan ne sai dazu muka dawo,kuma danaje gidan ammi tace kuna asibiti"


Eh muna nan tun ranar alhamis,amma ina kukaje?"


Muna asibiti ne ya sadiq bashida lpy,wai ciwon zcy ne ya kamashi,yanata aman jini,shine uncle dinmu yace kawai a fitar dashi abroad,to jiya da dare suka tashi mukuma yau da safe muka taho"


Ciwon zcy?nusaiba ciwon zcy fa?meyasa ni bai kamani ba sai ya sadiq?Nusaiba dan allah ki kaini wajenshi naganshi"nace ina girgizata.


A yanxu sis ya sadiq ya mana nisa,yana buqatar nisanta da duk wani abu dazai daga masa hankali,kuma a matsayinki na matar wani a yanxu inaso mubar mgnr wani daban"


Matar wani?waye ya fada miki ni matar wani ce a yanxu?"


Naje gida mana ammi tace jiya da safe an daura aurenki,ko kina nufin baki sani ba??


Shiru nayi dan bani da abin cewa.
Yanxu ina gadon asibitinma baza'a hqr da wannan qaddararran auren ba?wai me nayiwa abbi da zafi haka harya tsane ni?


Amminma cewa tayi Abbin yace anjima za'a kaiki wai kya qarasa jinyar acan,shiyasa ma na taho dan muyi sallama"


Anjima za'a kaini?Lallai abin na abbi ya girmama.


Sannan ya sadiq yace na fada miki dan allah ki maida hankali akan krtnki danki cika masa burinsa,a lkcn baya iya mgn sai a paper ya samu ya rubuta min"nusaiba ta kuma cewa.


Wayyo nusaiba ina akeso na saka kaina?krtnma an hanani birinsu na mutu kawai.ni dama nasan na rasa komai tunda na rasa ya sadiq"


Kibar fadar haka khadija,dama allah yayi bazaki cika masa burin ba"


Amma nusaiba rashin adalcin....


Ya isa dan allah khadija,ba kowani mgn ake fada a irin wannan al'amarin ba,bamusan abinda allah ya boye ba"


Haka nusaiba taita tausata da dadadan kalamai har lkcn da ya aisha ta dawo,bata wani jima ba ta tafi wanda sai lkcn na samu hawaye suka zubomin.
๐Ÿ’™๐Ÿ’™RABON KWADO....๐Ÿ’™๐Ÿ’™๐Ÿ’™






Er mutan ungogo๐Ÿ’‹๐Ÿ’‹๐Ÿ’‹








๐Ÿ…ฟ51-๐Ÿ…ฟ55




Nayi nisa a tunani naji alamun tafiya.ban dago ba dan bana buqatar ganin ko waye.




Sannunki da zuwa 'yata,ya kuma kk zauna a qasa kamar wata baquwa?"


Saurin dagowa nayi dan jin muryar mace.
Kallo daya zakayi mata ka gano tsantsar kamar da sukeyi da mijin ya fatima๐Ÿ™.
Kana ganinta kaga cikakkiyar mace mai kamala,wadda ta jiqu da naira.
Katse tunanin nayi na fara gaisheta ganin tana ta sakarmin murmushi.


Lpy lou,ya jikin naki?"


Da sauqi"nace ina tunanin ina tasan banida lpy.


Ai inata son xuwa dubaki to allah bai nufa ba,ya hqrinmu na rashin fatima?"


Alhmdllh"nace idona na kayo ruwa.
Da gudu shahida tazo ta hau kaina.


Aunty wai grandy tace tare zamuje gidanmu dake,kina dafa mana abinci,ki shirya mu mu tafi scul kamar yadda momy take mana?"
Daga mata kai kawai nayi.




Amma ke bazaki tafi ba kamar yadda momy ta tafi koh?"nan ma daga mata kai nayi.
Zata kuma watson wata tmbyr matar tace da ita.


Ya isa haka,kibarta ta huta bakiga bata da lpy ba?"


Tashi tayi ta koma can gefe ita a dole taji haushi.
Sai lkcn daddyn nasu ya fito yana riqe da hannun iman sai shahid a bayansa.neman guri sukayi suka zauna inda iman tazo ta hau kaina ta zauna.


Kai bakaga auntynku ba bazaka gaida ita ba"tace tana kallon shahid dake game abinsa.


Baiyi mgn ba saima tashi da yayi ya koma inda ya fito.


Tasamu a gaba tayi taita nasiha,nidai inaji ne kawai amma hankali yanaga yadda zan fara rayuwa a gidan ya fatima a matsayin matar mijinta,da kuma yadda zan rayu da mutumin da natsana ya tsaneni.Ammi zanyi qoqari wajen ganin nayi duk abinda nasan baza'a samu matsala a wajena na.


To ummi xamu wuce dare yanayi"ya fada yana miqewa tare da duba agogon dake tsintsiyar hannunsa.


Ka daiji abinda na fada maka koh babanah?banason wani abu ya fara daga gareka dan nasanka sarai"


Insha allah ummi bari muje"yace yanayin gaba.


To 'yata Allah ya tsare hanya ya qara sauqi.Ki kula sosai kinji?su kuma yaran za'a barsu anan zuwa wani satin kafin nan kin qara warwarewa"


Wayyo allah!!yanxu mu kadai zamu tafi salonma ya kasheni a hanya?yanxu taya zan fara rayuwa daga ni sai shi a cikin gida?
Miqon ledar datayi yasa na dago tare da qaqalo murmushi.


Nagode ummi saida safe"


Har harabar gidan ta rakoni inda shi tuni ya shige mota.


Ganin a backseat nazo hakan yasa yanxuma na bude nayi zama na a ciki.


Munfi mintuna biyar a wajen bamu tafi ba,nidai bansan dalili ba.


Wlh idan baki dawo gaba ba zaki fitar min a mota sai dai ki taho da kanki"najiyo muryarsa.


Ikon allah!shi matar tasa ta mutu ma bazai saduda ba?
Budewa nayi na shiga gaban batare dana kalleshi ba,dan ko kallonsa banason yi.


Kin zata kin kai matsayin da zan zama driver dinki ne?to kisani ko a mafarki hakan bazata kasance ba,idiot kawai"


Kalmar idiot din ce kawai ta bani haushi amma sauran maganganun ko a jikina,dama ni bana kai kaina inda allah bai kaini ba.


Haka na cigaba da tunani har na fara bacci.har mukaje ban sani ba,dan mugunta maimakon ya tasheni shine ya bugamin kai da jikin motar.


A firgice na tashi dan naji zafi sosai,shi kuwa ficewarsa yayi ya barni.
Haka na fito ina sosa gurin ina binsa a baya.
Bangarensa ya shige ya barni a nan,ganin tsayuwa bazata yimin ba yasa na nufi bangaren ya fatima.


Falon yananan kamar yadda nasanshi sai dai wasu canje canje da ba'a rasa ba kamarsu labulaye da sauransu.


Kai tsaye bedroom din na shige dan sosai nake a gajiye.
Danayi shirin baccin kuma sai na kasa na shiga tunanin rayuwa.


Allah sarki ya sadiq ko yanxu a wani hali yake?Tuni idanuna suka ciko da kwalla.


Ya allah ka bawa bawan nan naka lpy,ka bashi sauki da kuma hqrn rashina.
Saukowa nayi daga bed din na nufi akwatin da naga ni dan ina tunanin itace wadda ya aisha take fada.
Wayata na shiga dubawa dan inason jin muryar ammina.
Amma abin mamaki ba waya ba dalilinta.harna hqr xan koma na kwanta sai kuma na bude aljihun akwatin.


Wata qaramar wayace wadda ake mata laqabi da keypad sabuwa dal.
Kunna wayar nayi amma ba contact ko daya,dana qara dubawa ma sai naga ba sim card dina bane wani sabone.


Allah sarki ni!!haka akeso na cigaba da rayuwa ba tareda farin ciki ba.


Number din ammi nasa da yake na hadda ce amma bata shiga ba,dole na hqr na fara dannawa ya sadiq kira duk da an sanar dani baya ma qasar.
Ba yadda banyi na tuno number din nusaiba ba amma na kasa dole na sawa zcytah hqr na koma nayi lamo kamar wata marainiya.
Ganin kwanciya bazata min ba yasa na tashi naje na dauro alwala dan kai kukana wajen ubangiji.
Sai uku saura na tashi daga sallaya dan jin barci ya fara doko sallama.


Tun daga ranar ban kuma ganin ko quda a tare dani ba,koda yaushe ni kadai kamar mayya.
Hakan yasa na qagu sati yazo dansu shahida su dawo koba komai sa runga debemin kewa kafin su tafi scul.


Tun inajin tsoron girman gidan ni kadai har na hqr na fara sabawa da zaman shiru da tunani.
๐Ÿ’™๐Ÿ’™RABON KWADO...๐Ÿ’™๐Ÿ’™








Er mutan ungogo๐Ÿ’‹๐Ÿ’‹๐Ÿ’‹




So much luv u my fans๐Ÿ’ž๐Ÿ’žAllah ya bar qauna๐Ÿ’‹๐Ÿ’‹








๐Ÿ…ฟ56-๐Ÿ…ฟ60




A daddafe nayi sati daya a gidan nan,jina nake kamar a prison,to ko a can ai ba kai kadai kk zama ba.
Yau sati na daya a gidan amma jina nake kamar nayi shekaru,to ai koba komai mutum ma rahma ne,bareni da bansaba zaman shirun ba.


Tunda safe na tashi da dokin yau su iman zasu dawo dan haka nayi wanka na shafa mai wanda rabona dashi tun kafin rasuwar ya fatima.
wata atampa na saka sabuwa,Don naga sababbin kaya a cikin wadrob nasan aikin ammina ne ko yanuwana.


Kitchen na shiga na fara dora ruwan shinkafa wanda tunda nazo tea kawai nakesha idan naji yunwa zata halaka ni,rana daya ce nasan na dafa indomie.


Shinkafa da miya nayi lafiyayyiya wadda miyar taji kaji dan ba laifi komai na amfanin gida akwai a kitchen din kai harta kayan lambu(vegetables)friege dinsu daban,kaji ma haka.


Coslow nayi sannan na hada pineapple juice.Dinning nakai na jefe sannan na zauna zaman jiran tsammani wanda yafi kama dana gawon shanu,domin har la'asar basu ba dalilinsu.


Bedroom din na koma na dauko wannan akwalar wayar wadda tafi kama da calculator,dan ganinta ma bata min rai yake tunda batada wani amfani.Ba contact bare memory shiyasa tun a ranar na kashe na jefa akwatin.sai yau dana dauko na kunna gidan radion da ya sadiq yake ko xanji wani abu game dashi.


Dakinsu shahida na shiga na gyara kafin na dibo wasu kayan nasu na kayo cikin wadrob din bedroom din ya fatima,dan idan suka dawo bazan bari suna kwana su kadai ba,koba komai nima na riqa jin motsin mutum a kusa dani.


Tsaf na gyara dakin tare da saka room freshner sannan na rufo.
Dakin oga shahid na shida dan duka dakunan a jere suke sai qaton falo a tsakiya tare da dinning area.irin dai wanda ake cewa mu hadu a falo.


Dakin kaca kaca yake da takardu ga kayansa da suke bar baje a qasa.haka nabi na tattara na gyara sannan na fito nayi alwala dan magriba tayi.


Har akayi issha babu su hakan yasa na cire raina a yau zasu dawo.
Har na fara gyangyadi akan sallaya naji an fado kaina.


Momy au aunty mun dawo"


Ai nayi fishi tun dazu inata jiranku bakuxo ba"nace ina juya baya.


To ba daddy ne yaqi zuwa da wuri ba muma mukaita jiransa"Shahida tace.


To naji ya ummin take?"


Lpy lou,tace wai mu gaida ke kuma duk abinda kk ce muyi mu ringa yi kema momynmu ce.wai haka aunty?"


Eh mn kuda baku sani ba?ba kuga da momynku tana nan ba idan kukace ayi muku abu tana cewa ga babarku can kuje gurinta?"


Eh haka ne"suka hada baki.


Yauwa,yanxu kunyi sallah?"


Aa"


To ku shiga toilet kuyi alwala sai kuxo kuci abinci"


To amma zaki kunna mana catoon koh?tunda momy ma tana kunna mana"


Eh zan kunna muku"nace ina tura qeyarsu.


Aunty ni ban iya alwalar ba"iman tace tana kallona.


To muje nayi miki"na fada tare da miqewa.
Saida sukai sallar kafin muka fito falo da taimakonsu na kunna qatuwar plazma din domin kunsan babu a house๐Ÿ˜œ.


Abinci na zubo musu na zauna ina basu a baki muna kallo.
Shahid ne ya fito a dakinsa ya wani rakube kamar na allah.


Kazo kaima kaci abinci"nace ina kallonsa.


Ni bazanci dasu ba"


To kaje kitchen ka dauko plat a zuba maka"


Haka muka zauna suna cin abinci muna hira,naji dadi sosai dan mutum rahma ne,kuma duk sainaji qunci da damuwar danake ciki kashi 50 babu ita.


A hankali ya turo qofar kafin ya qaraso cikin falon da wannan tafiyar tasa ta taqama.sallamar ma ciki ciki yayi ta inda yaran dukansu sukaje suka dane shi.


Iman ya daqa sama kafin ya ajiyeta sunata dariya.


Dama yana dariya haka?ban taba ganin ko murmushinsa ba tunda nake.zuba masa ido nayi inda muna hada ido ya watsomin wata harara.
Ba shiri nayi qasa da kaina.
inaji sunata surutansu nidai nakai plats din kitchen kafin nayi hanyar daki dan naga sun manta da rayuwa a wajen.


Ke zonan"najiyo muryarsa.


Ke?baisan sunana ba daxai kirani da ke?
Tsayawa kawai nayi ba tare dana juyo ba.


Ko ni nazo?"naji ya kuma fada.


A hankali na dawo na nemi guri na zauna.


Shahid kuje zamuyi magana da auntynku"yacewa yaran.


Tafiyarsu tasa falon yin shiru sai qarar tv,inda ya dauki remote ya rage qarar.




Ina fatan kina sane da dalilinki na zuwa gidan nan?idan ma kin manta to ki tuna kinxo gidannan ne a matsayin yar aiki.dan haka yanzu zan kafa miki dokoki kanar yadda ake kafawa duk wata mai aiki idan tazo,haka kuma idan kin saba zan hukunta ki kamar yadda ake hukunta yan aiki."


Inaso kisan cewa gobe monday yarana suna da scul,dan haka kafin 7:30 ki tabbata kin gama shirya su,kin hada breakfast dinsu sannan kinyi musu abinda zasu tafi dashi wani daban ba wanda sukai b/fast ba.ina fata kin gane abinda nake nufi?"


Banyi mgn ba kuma bani da niyyar yi dan bansan mezance masa ba.


Tashi yayi ya kashe tv tare da fita ya rufo qofar.
Nima tashi nayi naje nayi musu wanka inda muka sha tataburza da mutumun shi wlh bazan masa wanka ba,nidai qyaleshi niyi naja suiman muka tafi bedroom dimmu.wannan wayar na dauko dan da alamar yau zatayi amfani,Alarm na saita na 4:30am dan banason wata matsala ta hadoni da wannan mutumin dan naga qiris yake jira ya qaddamar mini.




Ana Tare๐Ÿค๐Ÿค๐Ÿ’™๐Ÿ’™RABON KWADO...๐Ÿ’™๐Ÿ’™






Khayraty Er mutan ungogo๐Ÿ’‹๐Ÿ’‹๐Ÿ’‹






๐Ÿ…ฟ61-๐Ÿ…ฟ65




Qarfe 4:30 na asuba alarm ya tashe ni da yake bani da nauyin bacci.


Alwala nayo na gabatar da raka'atanul fajr kafin na dauko qur'ani na fara karantawa.
Saida akai kiran assalatu kafin na kayo sallar asubahi.


Kitchen na nufa dan fara gabatar da aikace aikace na.


Doya na fara ferayewa sannan na feraye dankali bayan na dora ruwan tea akan cooker.


Soyayyan dankayi da kwai nayi a matsayin breakfast,inda nayi feten doya wanda yaji hanta a matsayin wanda xasu tafi dashi.


7:09 na kammala komai hakan yasa na koma daki na shiga tashinsu.


Da rigima da komai na samu na kallama shiryasu cikin uniform dinsu,inda na nufi dakin oga shahid dan taimaka masa ya shirya dan lkc ya tafi gashi ko breakfast basuyi ba.


Haka muka fafata dashi,ko dan yaga ina cewa yai sauri ya ringa abubuwa kamar mara laka,nidai danaga ya fito a wanka na fito na qyaleshi.


Dinning mukaje na fara hadawa su shahida b/fast din dan 7:30 din harta dan gota.


Kamar kullum da tpyrsa ta taqama da isa ya shigo falon inda sai a lkcn ma nasan akwai kofa da zaka iya shiga bangarensa ta nan falon.


Tashi sukayi sukaje suka rungumeshi,kafin ya sakarwa kowa kiss a kumatu.


Good mrng my angels"naji yace yana shafa fuskokinsu.


Shahid ne ya fito nidai na hada masa nasa abincin,inda nake saqe saqe na gaisheshi ko kuwa?


Kar naje na gaidashi ya yarfa ni,kuma sai nake ganin kamar idan ban gaida shi ba ban kyauta ba.


ina kwana"nace ba tare dana kalleshi ba.


Bai amsa ba hakan yasa nayi dana sanin biyewa dayar xcyta data saka na aikata haka,gashi ya shareni kamar baisan inayi ba.


Shahid sauri fa zakayi kaga driver yana jiranku kar kuyi late"yace yana zama akan kujerar falon.
Saida shahid din ya gama suka dauko lunch-box dinsu dan tafiya,a inda shahid din ya bude dan ganin mene a ciki.


Kai kai kai!Daddy kaga abinda tayi mana,wlh ni baxanje da wannan abin ba yan class dinmu suyi min dariya"yace yana ajiye basket din nasa a gaban daddyn nasu.


Sai lkcn ya kalleni,nidai ina tsaye da plat din da suka gama cin abinci mamaki ya cika ni.
Dan yaje da faten doya shine za'ayi masa dariya?faten da na baje basirata akanshi shine akeyi masa haka?


Kuje wajen motar ganinan,duk ku ajiye baskets din"yacewa yaran.
Aikuwa ba musu suka dire suka fice.


Wato bakiji gargadin danayi miki akan kulamin da yara ba koh?to ki sani kamar yadda na fada indai kk yi laifi zan hukuntaki kamar yadda ake hukunta masu laifi to zan aiwatar da hakan,ki jira purnishment dinki kafin dare,hakan xaisa ki ringa kiyaye duk wani abu daya dangance ni da kuma yara na"


Yana gama fada yayi ficewarsa abinsa.


Guri na samu na zauna inda wasu hawayen takaici suka zubo min.Wato duk qoqarin da nayi na hana kaina bacci nayi abinda yace badan komai ba sai dan banason matsala ta fara daga bangare na amma hakan bai samu ba.Bai yaba abinda nayi musu ba duk da dama ba dan ya yaba nayi ba,amma shine zaice wani zai hukuntani.
Banga laifi na ko kadan ba,sbd bai fada min kalar abinda zanyi ba,bansan wani irin abu suke tafiya dashi ba amma da yake ya tsaneni shine zai dora laifin akaina.


Daki na koma na kwanta ina kuka,dan bacci da gajiya ke damuna amma nasan bazan iya baccin ba.


Haka na wuni sur ni daya a daki saida naji yunwa na neman kasheni na rarrafo na dauki faten da suka bari na fara ci.


Wai wannan abincin ne za'ace baza'aje scul da shi ba?to ko shugaban qasa ya samu wannan abincin ci zaiyi bare su daba yayan kowa ba.


Bayan la'asar zaman dakin ya isheni,ina fitowa falo na ganshi a kishingide.
Wlh na tsorata sosai dan banyi tunanin da mutun a gidan bama duka.


Zo nan"najiyo muryarsa cike da isa.


Can gefe na zauna ba tare dana kalleshi ba.


Kamar yadda na fada miki dazu zan hukuntaki akan lefin da kk yi,yanxu ina so kiyi abinci kala hudu da juice kala biyu,ko wanne ya kasance dai dai cin mutum goma ne,na baki nan da awa biyu idan kk wuce haka ki tabbatar gobe xakiyi wanda ya ninka hakan."


Komai na amfani akwai a kitchen,idan kuma kina buqatar wani abu zaki iya fada in babu sai a siyo."


Tofa!wata daban,da gsk aikin nazoyi kenan?
Ta inama zan fara wannan aikin har kala 4 a cikin awa biyu?kuma ma wai dai dai cin mutum goma.


Ko a gida bantaba yin girkin da mutum goma suka ci ba,amma gashi an kawo ni inda zanyi,allah sarki ni.


Kina batawa kanki lkc ne"na jiyo muryarsa.


Daki nayi ina zuwa na fada kan gado na rushe da kuka.


Abbi why?Abbi meyasa zaka kawoni inda ba'a qaunata?Abbi meyasa zaka daina sona ka hadani aure da mugu mara tausayi?
Ya sadiq kazo gareni dan allah,ina buqatarka a kusa dani,nasan da kana kusa bazaka bari a cutar dani ba....haka na ringa kuka ina surutai,saida nayi mai isata kafin na bawa zcyta hqr na yanke shawarar zuwa nayi girkin.


Tashi nayi na nufi kitchen tare da tunanin abubuwan da zan dafa masu sauqi wadanda baza su ja lokaci ba,dan yanxu ma na kusa cinye awa daya.


Haka na raba hankali na,inda na dora coconut rice akan electric,fried rice a kan cooker,sai kuma blander din kayan miya dana jona a socket,ga blander din fruit itama tana markada min abinda zanyi juice dashi.


Juice din na fara gamawa,inda nayi lemon mangwaro,sai kuma pineapple and coconut juice.


Saida na gama coconut rice din sannan na dora macaroni armlet a electric din.
Da taimakon allah na samu na gama girkin amma kala uku nayi dan bazan iyayin na hudun ba tunda ba fadar allah bace,wannan dimma da nayi nayi qoqari dan sosai na gaji danma abincimasu sauqi nayi sannan na samu kayan aiki masu sauri.


A coolers na zuba abinci,yayin da na zuba juice din a jugs naje na jera a dinning,ni har mamaki nake yadda zaiyi da wadannan abinci masu yawa haka.


A falo na wucesu nayi ciki abina dan tun dazu ina jiyo dawowarsu dan yanxu har an idar da sallar magriba,inacan ina aikin daba godi bare na gode.


Shahida ce ta biyoni.


Aunty wai meyasa bakya zama tare damu da daddy muna hira kamar yadda momy takeyi kafin ta tafi?"


Kamo hannunta nayi muka zauna a gefen gado.


"kinga shahida banason surutu kinji koh?idan kuma kinaso mu bata shikenan"


To na daina"


Yawwa babyna,kije kuyi hira dasu ya shahid kinga na gaji wanka nakeso nayi gashi banyi sallah ba"


Dana shiga toilet haka naita gasa jikina da ruwan dumi sbd rashin sabo,dan yau na aikatu ba kadan ba.
๐Ÿ’™๐Ÿ’™RABON KWADO...๐Ÿ’™๐Ÿ’™






Khayraty Er mutan ungogo๐Ÿ’‹๐Ÿ’‹๐Ÿ’‹






๐Ÿ…ฟ61-๐Ÿ…ฟ65




Qarfe 4:30 na asuba alarm ya tashe ni da yake bani da nauyin bacci.


Alwala nayo na gabatar da raka'atanul fajr kafin na dauko qur'ani na fara karantawa.
Saida akai kiran assalatu kafin na kawo sallar asubahi.


Kitchen na nufa dan fara gabatar da aikace aikace na.


Doya na fara ferayewa sannan na feraye dankali bayan na dora ruwan tea akan cooker.


Soyayyan dankali da kwai nayi a matsayin breakfast,inda nayi faten doya wanda yaji hanta a matsayin wanda xasu tafi dashi scul.


7:09 na kammala komai hakan yasa na koma daki na shiga tashinsu.


Da rigima da komai na samu na kallama shiryasu cikin uniform dinsu,inda na nufi dakin oga shahid dan taimaka masa ya shirya dan lkc ya tafi gashi ko breakfast basuyi ba.


Haka muka fafata dashi,ko dan yaga ina cewa yai sauri ya ringa abubuwa kamar mara laka,nidai danaga ya fito a wanka na fito na qyaleshi.


Dinning mukaje na fara hadawa su shahida b/fast din dan 7:30 din harta dan gota.


Kamar kullum da tpyrsa ta taqama da isa ya shigo falon inda sai a lkcn ma

Please Login or Register in order to submit comment