Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Jummala ta koma daki in da Hawaila take, ta dakko mabirgin ta zankadede tai dakin ta rufe qofa, ji kake tim tim, tana jibgar su, ita Huwaila ba kwarin guduwa sai baki, nan take ta ko fara magana" Allah marka ki kyale mu ai iskanci ba kan mu farau ba, kuma naga iyayen yaran na gida ne, su bangis ne, kakan su na gidannan shima yana zuwa lalubar ki duk daren duniya baku ko gajiya ko daga wa juna qafa, mu ki daina dukan mu, dan naki bai fito ba namu ya fito bazaki kashe mu a banza ba, kk qara dukan mu sai na fada ma Baban mu in ya dawo kuna kebewa keda yayan shi" qam taji an qame mata bakin nata, rufe bakin ta Huwaila Marka tai bam tana waige2, tana kallon qofa, ko wani yaji? Jitai an banko qofar da mugun qarfi, wani tsoro ne ya kama ta ba ta san sanda wata muguwar tusa ta kwace mata ba, zama tai kusa da yaran suna ta toshe hanci dan azabar wari, Talle ne idon shi ya kada yai jawur akan na da, in aka ce xai iya kisa a wannan halin ba za.a musa ba, damqo wuyan Marka yai kamar zai kashe ta, ya jawo ta tsakar gida yaran su na biye, qananan na kuka manyan da suka ji kuma suka gane me ake suna mamakin abun, har qofar yayan nashi ya je ya wurga mai ita a jikin shi, daidai ya fito da tabarma a hannun shi zashi zaman qofar gida na safe da suke yi, janye jikin shi yai yana wani ja baya " Subhanallah,meye haka zaka raban matar ka a jikina, bayan kasan ba muharrama ta bace" wani gigitaccen mari Talle ya hankada mai, zai magana ya qara make shi ya tintsira, ya kasa magana ma, zaman yan bori yai a wajen ya hau kuka, kuka yake suma kuka suke, gaba daya sun kasa daina shiru, wani haushi ne ya kama Talle kukan uban me suke, kuka ai shi ya kama, miqewa yai a haukace ya bisu da duka, duk wanda ya samu ya maka, har yayan nashi, bakin shi dai kam kamar wanda aka rufe, tattare wa nai nace bari nai Abuja in sun gama dake2n na dawo naji ya masu ciki?





Allurar bacci yai mata ya tsaya akanta yana qarewa qirjin ta kallo, qiji a cike a tsaye, amma haka za a je a yanke su, ya roqe su tinda yana son ta a mata yanda ba zata mutu ba, a mata kamar za ai operation ne yanda daga baya zata ji sauqi, su ci gaba da rayuwar su, hawayen tausayin ta ne ya zubo mai for d first time in his life yaji tausayin wani da zasui aiki akan shi,hawa gadon yai ya rungumo ta ya dora kan shi a qirjin ta, wasa ya shiga yi da su, kamar zai cinye, da kyar ya hakura, ya dauke ta yai mota da ita, ya fara daukan dajin su Oga Zaks. Hankalin Alhj Kalla a tashe yake ganin rashin dawowar Saudat, ya zai yi yau? Ta ina zai fara samo wadda za sui aikin akan ta, tinda ita ta gudu taqi dawowa? Anya ma zai iya kyale ta haka? In yace zai mata wani abu.asirin su ne zai tonu, duk da yana da tabbacin ba yanda za ai dasu, dan manyan qasar sun daure masu g.... a haka dai yai ta tinani sai da Alhj Salihu ya mai waya yace shifa ya dau hanya, tambayar shi yai matar shi ta dawo ne shi? Ya tabbatar mashi da dawowar ta, miqewa yai ya ce" duk wanda yaci ladan kuturu dole ya mai aski" waya ya zaro ya kira Yar Gwal, tana wani rawar kai da jiki yau da sa'a ta tashi ta san a bata samu ba zata samu dubu dari biyar, to me ta manta? Da hanzari ta tashi ta hau shirye2n fita, qawayen ta ne suka fara tambayar ta ina zuwa da safennan, bayan qa'idar su fitar dare ne? Sanar da su tai inda zata, shewa suka dauka wasu kuma suka.tabe baki, a haka ta gama shiri.ta fita, a qofar gidan ta same shi ya hadu cikin manyan kaya mai irin nasu na zuwa gidan Oga Zaks, shigewa tai ta fara mai karuwanci da shafe2, biye mata yai dan yana buqatar hakan kan su isa, a motar suka samu nutsuwa,yace "ya kamata yau na kaiki wajen shaqatawa na musamman mui satia can ba mai takura mana ko ya neme mu" wani juyi tai da mazaunan ta a kan cinyar shi ta sakko ta zauna a gefenshi amma rabin jikin ta na nashi, tana sauke nunfashi, cike da kissa, murmushi kawai take, dan Alhjn akwai kai mutum duniyar sama, gaba daya jikin ta a mace yake, haka suka dau hanyar dajin Oga Zaks, suna isa motoci ne ba iyaka, bayan su isa je taga mata kala2,maza duk shigar su daya, mata kamar guda bakwai, wasu da gani na aure ne, wasu irin ta ne, haka ta ga suna wata irin gaisuwa, sannan suka shige ciki gaba daya kamar su ake jira, harda wadan da basu zo da matan su ba ma, wani qaton waje taga sun nufa , kan su isa taga dukkan Alhzawan nan da suka zo da mata, sun dakko wani red yadi sun nuna masu suna kalla har ita sai suka zube a qasa, ita dama Suwaiba oganniya ta dade a sume, daukar su sukai suka aje a wani gadaje da aka tanadar masu, Oga zaks ne da sauran mutanen wajen kowa ya cire kayan shi, haka suka tsaya ba kaya a jikin su, aka dakko wuqa, kowa ya kama wadda ya kawo, Alhj Salihu ne ya zo gaban Suwaiba, zuciyar shi a cunkushe, ji yake kamar ya bijire ma Dodon nasu,amma tinawa da azabar da zai shiga in yau bai wannan abun ba, kawai ya saka ma nonon Suwaiba wuqa, haka suka yanke masj Nono dukkan su suka tari jinin a wasu qorai qanana da suka rine da jini, kuka Alhj Salihu ya fashe d shi da yaja hankulan mutanen wajen, kowa daya kalle shi, ga uban ciki a gaba, ga baqi da yai yana maiqon zufa, sai dariya ta kama su, suka dinga dariya, saida Oga Zaks ya daka masu tsawa suka nutsu" Me yasa ka kuka Salihu?" Oga Zaks ne yai wannan tambayar," ina son matata Oga a san ya za ai a mata aiki a shafe wajen kar ta mutu , ka taimaka min Oga.kumin alfarmar nan oga" dariya sosai Oga Zaks yai sannan yace" karka damu i will keep my word ai , ni nace maka zamu san ya zamui matar ka baxat mutu ba, ita waccan guduwa tai ne?" Ya maida tambayar kan Kalla, " Eh Oga, da suka tafi ganin gida qin dawo wa tai ita" " ba damuwa yanzu dauke ta kui dakin duba marasa lfy da ita" da gudu Salihu ya dauke ta sukai can ya shimfide Doctors biyu ne suka hau kula da ita ya koma wajen tsafin nasu, jinin suka sha akai ta bayarwa wannan ya sha ya ba wannan, a haka suka gama suka rage dan kadan suka zuba a wani waje da naga sun qawata da ado suka zuba wa jinin nan danan ya tsotse kuwa,haka aka kammala komai sauran matan aka tattare su suka kai su wani daki baqi, ita ko Suwaiba da aka kammala bashi matat shi sukai ya saka kayan shi ya kaita mota, hanya suka dauka yana kuka hankalin shi tashe, Kalla na biye da shi a motar shi hankalin shi kwance, horn yai ta mai yanda suka saba in zasu rabu amma bai mayat mai ba, kada kai yai yaga ba ma amfanin komawa gida kawai bari ya tafi club, karkata motar shi yai ya tafi, sun isa gida ya dakko ta ya shiga daki da ita, kan gado ya aje ta, ya zuba mata ido yanda ta dashe tai fari alamar ba jini sosai a jikin ta, kwanta wa yai kusa da ita, ya rungume ta, a haka yai bacci, ba shi ya farka ba sai sha daya na safiya wanda ta sanadin motsin Suwaiba ne ya sa shi tashi, tash tai zata miqe taji wani sharp pain a qirjin ta , komawa tai ta kwanta cikin zubda kwallah, ji take kamar an yake naman wajen dan azaba, ni ko nace ba kama bane Suwai matar manyaπŸ˜‚
Baki ta bude tace.....
[11/26, 12:35 PM] Hermeebrah: πŸ’…πŸΌ 'YAN ABUJA πŸ’…πŸΌ




Ina qara bada hakuri dai dan Allah masu son Novel din nan ta PC ba zai yu nai ta sending from d begining ba, i am so sorry, kui man hakuri zuwa dan kwanaki kadan zan kammala dika na mayar Document, inshaa Allahu, Na gode sosai,Love u from qarqashin heartπŸ˜ƒ, u guys ar awsome ❀




Page 23:



Gobe ne ranar da Jabeer zai dawo, waya suke da Juwaireren shi, gaba daya ta shagwabe ta susuta mai lissafi, ji yake kamar ya dawo a daren, ko da fuskar ta ne ya kalla, ya san zai ji nishadi, kwantar mai da hankali tai akan gobe suna tare, kar ya damu, tina mai tai akan yai addu'ar bacci kafin ya kwanta, sukai adduar tare suka kashe waya, bayan cika juna da "I love u", da sukai bacci ne a bangaren Juwairiyya da Jabeer mara dadi, don tin da ya tafi hakan ne , baccin baya masu dadi ba junan su a kusa, a haka bacci barawo ya dauke ta bayan juye2 da ta sha, da sassafe ba yan tayi sallah, tayi abubuwan da suka zama na al'adar ta da safe kamar yanda kuka san Juwaireren Mama, tashi tai yau ranat gyaran lambun ta ne, taso ta bar shi tai gyaran gida tai ma Yah Jabeer din ta girke2, amma ta saka diguwar riga gajera, mai hannun vest, ta dau kayan gyara lambun ta taje, ta tattaba abubuwan da suke da buqatar gyaran, Juwairah akwai saurin aiki akwai kuma biyan buqata( ba a son mace ta kama aiki daya taita fama da an xo aga ba wani abun kirki da ta qulla bayan kuma ita a qasan ranta aikin nan take bil haqqi, gani take tana ta faman aiki amma an kushe ta, to yar uwa kin kama aiki daya kina ta yi kuma wataqila ba ma wanda ya fi zama dole ba, kin bata lokacin ki ya tafi baki qulla komai mai amfani ba, kinga in kina da miji mai mita akan komai dole zai magana, dan haka ana son mace mai zafin nama, mai saurin aiki, kuma tai aikin da kyau) tama gamawa ta wanke qafa da hannu ta shiga daki, ta hau gyaran ko ina, ta canja bedshit, ta dakko wancan ta fito da shi ta gyara palon ta, ta canja mazaunin kujerun ta, sallamar Nafee ne ya sa ta dan tsagaita da aikin ta, shigowa tai" haba matar Yayah ai sai ki kirani, da wannan tsohon cikin kk aiki irin haka, wata bakwai fa, kun shiga na takwas, ki ja mana aiki, habaa gaskiya banji dadi ba" ta fada tana turo dan bakin ta wai ita ba a kyauta mata ba, murmushi Juwairah tai ta kama kafadun ta" kar ki yi fushi da ni 'Yar qanwata, taho ki taya ni, na dauka kina taya Innarmu aiki ne, shiyasa ban kira ki ba, tayata aiki ai yafi nawa" murmushi sukai tare suka ci gaba da aikin, bayan sun gama canja fasalin wajen ne, suka debo ruwa da tsumma nan ma suka goge ko ina, kitchen ta tafi ta barma Nafee ta qarasa nan din,taje ta mai na shi kyaran sosai kamar Jabeer din zai leqa in ya fara shigowa, bayan ta kammala da nan ne ta wuce toilet, Nafee ce ta bita ta amshe wankin toilet din , bayan sun gama ne aka fara gyara tsakar gidan, in da yake anyi siminti, nan wanke wa Juwairah tai qasan kuma suka share" wai nikam me zaki dafa mai ne naga baki fara batun girki ba" His favorite u know, da kudin da ya ban jiya nai aike kasuwa an siyo man kwai, nama dankalin turawa, da cabage sai carrot da green beans kindan bak da su a lambu, sai flour ina da mai, an siyon yan kayan qamshi da maggi, dan wake zan mishi, kin san shi a duniya na kula yana son abunnan" " wai sosai ma kuwa, bakigan shi bane yana satar danwake a tukunyar Innar mu da dai kin sha dariya, Innar mu in ta kama shi sadaf2 take tafiya ta damqe hannun shi da ludayin tsamar danwaken, yai ta ihu ta qi saki" dariya sukai tayi sosai tinawa da wannan kabarin, miqewa sukai suka fara gyara dankalin, suka yanka veges harda na lambun nata, ta debi dan alayyahu kadan, da albasa mai ganye, suka gama yankawa sai ta soya dankalin nan ta dakko dafaffen naman ta da suka yanka qanana ta soya sama2 ta aje gefe, sannan ta rage man suyar ta dakko jajjagaggen kayan miyar ta, da ba timatir sosai guda biyu kawai tasa ba manya ba suma sosai, ta saka da tafarnuwa da kayan qamshi ta soya ta saka maggi da dan gishiri, sannan ta dakko wannan veges din ta zuba akai bayan ya fara soyuwa, ta juya suka tirara, sai ta juye akan wannan dankalin da daman, ta juya su, suka hade, dakko dafaffen kwanta tai shima bayan ta bare ta hada da shi ba tare da ta yanka ba, ta juya su tare,flask din ta ta dakko ta zuba wannan hadin ta rufe ta rage masu nasu, dakko flour tai naga ta dakko wani gari" Matar yayah wannan garin meye?" " to tambaya an fara ne, garin wake ne na markada da yar dawa kadan, sai alabo, na niqo su shine zan hada da flour din yafi dadi sosai" " Auuuuhooooo, to ai sai ana yi ana tambaya ko kinga laifina?" " Aa aa matambayi baya bata ai" murmushi sukai ta debo kuka, mai dan yawa yanda zai santsi, ta dakko ruwan kanwar ta, ta zuba ta hada da wani ruwan dan bata son ta cika kanwa da yawa, ta kwaba yai laushi kwabin, ba tauri sosai ba ruwa, haka ta kwaba ruwan na tafara ta fara jefawa qanana, dan yafi dad, bayan ta gama ta tsame a ruwa mai kyau ta hada mai nashi a flask, ta miqe ta barma Nafee ta qarasa ita timatir daya ta dakko nunanne, ta fada mai sugar a tsakiya bayan ta yanka, ta hau goge fuskar ta da shi, sai da ga baya kuma ta dau rabin ta saka xuma ta goge fuskar shima, nan da nan wani duhun murhu da rana ya bace fuska ta dau kyalli da kyau, bayan ta gama kuma ta dakko lallen ta, ta saka mai man kwakwa kadan ta kwaba shi, ta hau murge jikin ta duk inda hannun ta ya kai musamman fuskar ta, kafin kace me Juwairere tai kamar ba ita ba," tab lallai Yayah na shan dadi aradu, yau fa ba ranar gyaran jikin ki bane, bama ki dade da yi ba amma ji yanda kk koma kamar wata tauraruwa" " Nafee kenan, ai ita mace ana son in mijin ta yai tafiya ko na kwana daya ne ya dawo yaga ta canja kawai ko ta ina, balle wannan da kk gane we ar talking about Yah Jabeer, My love, everything" dariya sukai, Nafee nata tsokanar ta ta gama ta shiga wanka, shigar da yake matuqar so tayi ta dakko kayan ta fara sakawa, doguwar rigar material ne aka mata irin na masi ciki, an daure sama kamar bra akai mata sai hannun ya zamana a wuya aka daure shi, cikin nan ya sha mai da gyara, sai kyalli yake gwanin sha'awa, sai dogon wando da akai mai fadi sosai ta zura, ta dakko kayan gyaran gashin ta, ta tsaga daga gefe, ta kwantar da shi, ta daure in a ponytail style, qamshi kam ranar kamar an barin turare, fuskar ta daga powder sai lipstick, ta gyara girar ta, ta saka kwalli,( kwalli na da matuqar tasiri ga mace, macen da ta saka kwalli ta iya kallo ta yi a rayuwa, in baki iya ba koyi ki fara)dogon hijab ta saka, tai sallar magrib ta zauna, tai azkar din ta, ta fara karanta qur'ani, ana kiran sallar isha'i ta tashi ta fara, Sallama yai ya shigo, yana ganin tana salla ya aje kayan shi yai alwala shima ya tafi masjid, tana idarwa qara gyara jikin ta tai duk da ba abin da yai, ta qara turare, ta gama, dauke kayan da ya shigo da su tai, na ajewa a kitchen ta kai ta fito da kayan nashi,masu datti ta fitar wamda bai amfani da su ba ta mayar wajen kayan su, sai wata leda da bata taba ba ta aje a gefe,daga alamu tsaraba ne, ruwan wanka ta je ta hada mai mai dumi, ta dawo kenan zata zauna taji shi, bayan qofa taje ta maqale tana ta dariya qasa2, shigowa yai yana ta dube2 bai ganta ba, sai da ya kama qugu sannan yace" Juwaireren Mama ko ki fito ko na zauna a qasa naita kukan rashin ganin ki, in an shigo nace baki son gani na ne" kan ya rufe baki yaji ta mai wata iriyar runguma ta baya wadda tasa shi fidda sautin da bai san ta ya akai yayi shi ba,( rungume mutum ta baya akwai yanayin da mace ko miji zasui ya zama ba wata runguma da ta fita dadi, ana yin ta ne ta hanyar zuro hannu a hankali ka zagaye mutum sai ka ja shi baya cikin shauqi ka manna shi da jikin ka) juyawa yai gaba daya ya daga ta sama, suna ta dariya, kisses kam kun san ranar an yi bari da ruwan su, zaunar da ita yai a cinyar shi, yana shafa cikin ta, yana ma cikin surutu kamar wanda yake hira damutum babba, dariya kawai take yi ita kam, " sannu da zuwa hasken cikin gidana, tin da ja tafi kaga daya gidannan duhu ya mamaye shi, yau haske da ya bayyana daban ne, na gode Allah da ya ban kai a matsayin miji, Yah Jabeer ba zan iya rayuwa ba kai ba, i missed u so very much" ta qarasa tare da qanqame shi tana hawaye, dagota yai yana jin wani sabon qaunar ta na ratsa shi, dan yasan she meant every word, " Hushhh Husshhhh my princess, ki daina kuka, Yah Jabeer na Juwaireren Mama ne ita kadai, bana fatan na wayi gari baki kusa dani, u ar my happiness, i cant do without u, u ar everything that i ever wanted in my life, so don't be scared of loosing me, nine ya kamata naji wannan tsoron, amma ba zan damu ba dan nasan zuciyar ki, da ruhin ki , da gangar jikin ki nawa ne" wata runguma ta qara mashi da ta saka shi jin dadi sosai, daga shi tai ta ja hannun shi zuwa wanka ta taya shi yai wankan yai brush suka fito ta shirya shi bayan sun gama ne kan shimfidar da suke cin abinci ta jawo hannun shi ta zaunar da shi, shikk binta kawai yake kamar raqumi da akala, dan waken ta fara zubawa a gefe, wanda har wani kyalli yake dan santsi sannan ta zuba mai wannann hadin da tai na dankali, zobon da ta dafa da abarba, da cittta kaninfari, kai da kayan qamshi dai da suka dace dika, ta saka harda cocumber, ta sa sugar, ci yake yana lumshe ido kawai, yana wani gurnanin magana amma ba a ganewa me yake fada, daukan zobon da aka saka a randar sanyi yai dan basu da fridge yai ya kurba, saurin bude idon shi yai sannaj ya mayar ya kulle, " Yah menene, yayi daci ne jo wani bu?" Ta fada tana zaro ido waje dan a tinanin ta ko bai mai bane, " matso kiji me yai" yana dan yatsina fuska, ita kuma sai ta danji zuciyar ta ba dadi, saboda gani take ta bata xobon garin iyayin mai hade2, dan ba ta san dama ana saka cocumber ba qirqira tai, matsawa tai kanta a qasa, " sai kin rufe ido zaki iya shan wannan abun, matso sosai na baki da kaina kiji ya yai" matsawa ta sake yi, ta rufe idon, jitai ya kama lips din ta yana masu wani salon da ya sa ta magana a qasan maqoshi, saida ya dade kan ya sake ta, ta kasa bude ido, dan wasu taurari ke mata yawo a kai" bude idon mana Princess, ni ba mai kudi bane bare na maki kyautar wannan kayan dadin da kk ban yau, amma na san i will make u feel something special, with every part of me" daukr ta yai sukai daki, zan bisu aka bugon qofa,nace ba sai an karya ma Hammana hanci na ba, zan tafi malamaiπŸ™„πŸ˜™πŸ˜™πŸ˜™πŸ˜™
[11/26, 12:35 PM] Hermeebrah: πŸ’…πŸΌ ' YAN ABUJA πŸ’…πŸΌ







BY HAERMEEBRAERH






Page 24:






" Adda Saudat dan Allah ki ban dubu daya mana ina son in dan ja jari ne ko ba yawa, xaman haka baya min dadi,ke ma kuma ya kamata kafin kudin hannun ki su qare ki kama wata sana'ar saboda kin saba yanzu da kudi, randa kk da buqatar su kk rasa ba qaramin damuwa zaki shiga ba" tinani Saudat take mai zurfi, can ta nisa tace" gaskiya kin ce wani abu kema, zan baki dubu biyar ki ja jarin, ni kuma zan fara kasuwanci ta waya da naga qawaye na da nai a whatsapp da facebook sunayi, ana samu in ka riqe amanar mutane, sai kaga ka samu riba mai yawa kana daga zaune" " yauwa Adda, sannan ina son nuna maki kinga Mama Bilki mace ce mai kirki, tana matuqar son mu, sai dai tabbas tana kishi da Goggo, wanda wannan dole ne a zaman kishiyoyi dama,mu sai mu kau da kai akan wannan, tinda iyayen mu ne, ba ruwan mu da hurumin su ta wannan bangaren, ya zama wajibi mu masu biyayya dikkan su, su a matsayin iyayen mu, itq a matsayin matar Abban mu" shiru Saudat tai domin maganar qanwar ta ta yau tana shigar ta, amma akwai nau'i na girman kai, da kishi a zuciyar ta, " hmmmm zan duba na gani" ta miqe ta dakko mata kudin ta bata, akan idon Goggo kuwa, " habaaaa Salma ai innice ke yanda na canja uwa, yan uwan ma canja su zan, auhoooo ba zaki iya canja yan uwa ba saboda kin same su su masu arziqi ne ko? Zaki roqa za a baki ko" " ni fa Gogga ba haka bane, ya kamata ki bude idon ki ki gane inda gaskiya ta dosa, ki daina rufe idon ki akan abinda bai kamata ba" " rufen baki sallamammiya kawai, an yi asiri da tuggu kala2 an rabani dake, to kije nima na huta da dawainiya, da dan wani da zanyi" juyawa tai tabar wajen Salma kuwa cikin qunan rai da baqin cikin halayya ta uwar ta ra shige dakin Mama Bilki, wadda taji komai, fadawa kan cinyar ta tai tana kukan takaicin hali irin na uwar tasu, shafa kanta kawai Mama Bilki take, bata furta mata komai ba," Mama ni fa ba kwadayi ne ya sa na tambayi Adda Saudat kudi ba, na tambaye ta ne naga ko tirare bani da shi, ga shi yanzu sai da Alimun ko lemon tsami nake amfani a madadin tirare, ba dan komai ba sai babu da take neman ta min yawa,amma in ina sana'a kudin zasu taimakan wajen kula da abinda ke cikina, shine Goggo take fadan maganganu marasa dadi akaina" " hakuri zaki Salma uwa ba abin wasa bane, dole mui mata biyayya in ba inda za a sabawa Allah bane, dan haka ki hakuri tin da kin samu jarin yanzu me zaki na yi na siyarwa?" " Mama Bilki ni da ina son na fara saida Meatpie ne, naga kina da

Please Login or Register in order to submit comment