Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Rai na kwantar dakaina Akan qirjin mubash in Ina dukan qirjin NASA a hankali Ina Kar yatafi ya6ud'e idanunsa na yafemai!


Wallahi tallahi masu karatu harga Allah mutuwan mubash ya rikitani Kuma yashigeni sosai da sosai in maqiyinkama ya mutu ya kakeji bare mubash Wanda yakasance miji agareni adaa dukda zaluntata dayayi na gwammaci _Saki Akan _auran wahala_ !

Mutuwarsa ta ratsani Kuma taqaramun imani sabida mutuwar tasa ta tabbatarmun da duk fariyan bil'adama da wannan ran ne yake tinqaho da fariya kwantil kwanta inta fita daga sassan ruhin mutum shikenan fa! Shikenan fa wlh komai NASA yaqare iliminsa dukiyarsa mulkinsa qimarsa fa! Komai NASA taqare wlh saidai fa amai komai fa amai wanka a sallaceshi a haqa gabari abinnesa kowa ya Kama gabansa abarka dakakai sai halinka da sallolinka fa! Shikenanfa 'ya'yan ka matayenka iyayenka abokanka Yan uwanka dukiyarka motocinka komaifa bazasu zo su zauna dakaiba iyakarka suma rakiya gidan gaskiyarka iyaka asaka motarka akawoka aciki yanzunkamma da talakan da Mai kud'in duk cikin akora kura fa akesa gawan nasu akawofa!

Kaico duniya da haka Kuma zakaga muta dasa buruka kala kala a duniyan Nan dafa anciremana ran Nan shikenn fa tamu ta qare shikenan fa wlh lokaci qanqani zaa manta dakai! Kai jamaa wlh murage wasu abubuwan damuke aduniyan Nan Dan mutuwa Bata sanarwa Bata Kuma fashin d'aukan kowayene kuwa a duniyan Nan tunda Wanda Ubangiji ma yafisoduk duniya nabiyullah mutuwar tazo ta tafi dashi uban wayene bazai tafiba? Wayene nace bazai mutu ba? Wlh Babu kowa komai da kowa zai mutu wlh mukoma ga Allah!


D'agoni da habeebty tayine yasani kallanta itama kobaa fad'amunba tana cikin wani yanayi na tausayi fad'awa nai jikinta nasoma Rusa wani sabon kukan Wanda ta kyaleni inayi batareda ta lallasheniba Dan shine kurum zai kawomun sassauci a yanzun Babu abinda nafi buqata sama dashi in ayanzun! Kai Allah jiqan mubash dai kurum masu karatu inaji Ina gani aka dau mubash akamai wanka akamai sutura aka Tara mutane aka sallaceshi aka kaisa gidan gaskiyarsa!


Ohni Aymanah shikenan fa mubash ya mutu ya tafi bazaa sake yayinsa ba Kuma Kai jama'a yanzun duk abinda mubash keyi adaaa akacemai haka rayuwarsa zai qare ai bazai ma sakema Wanda Yama Mai wannan maganar Koda kallon kirkiba!

Hmm masu karatu haka rayuwannan take fa yau Kaine gobe ba kaiba waiyioo! Masu karatu wlh muji tsoron Allah!

Mubash Allah dai yajiqanka ya kyautata makauncinka ya Kuma yafema laifuffukanka!


Haka naruqa jinyar mutuwar mubash a zuciyata sainajima dama wlh bankai qararsaba na amsa sakina cikin ruwan sauqi kurum Kai wlh duk nice sanadin mutuwarsa! 😭

Yar uwa na yawan nusata Akan nadaina cewa nice silan mutuwar mubash kawai haka Allah yatsara mutuwarsa zata kasance!


Sosai suke kwantarmun da hankali itada mijinta harnasoma sakin jiki Amman akowacce sallata Ina saka mubash a aduaa Allah cigaba damai gafara!


Masu karatu kwanaki fa sai tafiya yake sakanni da mintuna sai shud'ewa take ana maraici dare zai tsala safiyama tayi haaka rayuwa taita cigaba da tafiya da dad'i ba dad'i yanzunkam namance mubash saidai inamasa aduaa ba fashi hankalina yanzun duk yayi gida gun dangina kurum nakeson tsintar kaina Danko duk dad'in gidan uban wani gidan ubanka yafi kodako ace Kashi kukeci agidanku Kam!


Ayaude ansa ranar tafiyar mu nigeria Nan da 2wks kai masu karatu zanso kuga irin farin cikin danake ciki wlh Dan ko sadda habeebty tasanar Dani rumgumeta nayi Ina ihun murnarta harda raawata wlh yooo badoleba bayan shekaru aru aru har 6 zan sake ganin sany'in idanina su Marwa mamanmu mamy yapendo yaa Salim su anty ameena da Rabin Raina Yaah Hydar wacce kaliyar murnace bazanba ko makka aka biyamun iyakata murnarnan Kai masu karatu tsayawa labartamaku tsananin dad'in danake ciki Kam yanzun 6ata tym ne kawai kudai nabarku ku qiyasta! 🤗



Tun ranarda sakin mubash yahau kaima Amma fa tashiga gyarani gyara kuwa irin ta amare acewarta Dana koma Nigeria sai aure niko sai wani dad'i nakeji jikina harya Kuma murjewa sai yalqi da sheqi yakeyi ko giftawa nai sai nabar tsarabar kamshin jikina Dan qamshin danakeyi na dabanne acikin qamshi Kam! Kai Babu abinda zan iya sakama Amma dashi sai fatan gamawa da duniya lfy kurum Dan ko uwatace abinda zatamun Keenan wlh!



Zuwanmu Nigeria sai kankama takeyi fa 💃🏻Niko dad'i kaman ya kasheni tsaraba Kam saidai inban fitaba jidosu kurum nakeyi musamman Yaah Hydar kaikace nama rigada nazama matarsa ma 🙄ko ince Yama yarda ya amsa soyayyata ma ! Oho ni ina ruwana nidai jido tsaraba kurum nake kaman bansan ciwon kud'iba!


Su Yar uwa har mamakin iriyan San danake ma Yan uwana suke Dan Babu Wanda banma tsaraba ba kaf dinsu!


Ayau take jajibarin sallata fa masu karatu😂💃🏻ko ince jajibarin zuwana Nigeria aradu😂ai daka ganni zaka ga ainihin Aymanah Mubin tafarkon lbr Dan tsokana da barkwancina duk dawo dasu nai su habeebty mamaki suke waidama Ina magana har haka😂Niko nace tab ai inaji nafi aku marigayi mubash ne ya ladaftar da bakin😂!

Zaune nake ana mun gyaran Kai had'i da kunshi Mai kyau nida habeebty kaikace amarya 😉Niko yinakeyi da biyu Dan nabirge Yaah Hydar eheee🏃🏽‍♀Dan yanzun bazai ganni bai kyasaba Dan Aymanar yanzun tafi Aymanar daaa kyau da diri masu kyau kam😂!


Mungama gyararmu yayi kyau daganan muka nufa kasuwa mukasoma wasu siyayyan!



Nigeria Kam Yaah Hydar ya rigada yasan zuwan Aymanah Dan har yasoma tanadi da shirye shirye na musamman ! Yapendo har tambayarsa take kwana2 taga yasanja ne yadawo so cool da yawan faraa abinda baasansa dashi daba Daria yake Mata yace zatasan abinda kesasa faraa Nan bada jimawa ba!



Kowa fa adanginsu Aymanah nagani maqil agidan yapendo su yaa Fahad da Salim su anty ameena zubaida Kai duk 'ya'yan gidan namu da jikoki duk suna gidan su marmy da mamanmu da kakarmu kowa yayi jugum jugum a falo!

Yapendo ce ta Soma gajia tacire tagumin datayi sannan tace
"Salim Kuma kiransa Mana kozai shiga"

Kuma Kiran Yaah Hydar Salim yayi Amman amsar d'ace itace lanbansa a kashe!

Alama yayma Yapendo alaman haryanzun akashe!


"Toh shi yaron Nan Wai Mai yake nufine yatasa hankalin kowa yace Azo Abuja kowa yabar aikinsa gashi zuby dake lgs ma tazo mutane dake nesa duk yasa sun hallara Amman ya watsar damu tun jia ya kashe wayoyinsa Wai Mai Aliyu ya maidamune Wai!


Yapendo ta qarake maganar cikeda Jin haushi daddy ne yace Tai haquri tundadai akaga Hydar yayi hakan yanada babban daliline shiyasa Amman inba haka ba bazai kirasu abanzaba ai sudai qara bashi zuwa gbe!


Nandai aka cigaba da tattaunawa da mamakin Kiran da Hydar yasa amasu!


⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀

Ahayye Mata muqame qam sabuwar rawa muqame qam qam Aymanah a nigeria😂kuzokuga zumud'i Mana hohohooooo Aymanah jitake kaman Tai tsuntsu ta dire a gombe⛹🏻‍♀😂gata ga marmy ga mamanmu ga marwatyn ta hooo waiyoooo! Dad'i tun ajirgi take ta leqe itadai taqosa sukowa nigeria aiko ana sanarwa sun iso Nigeria harda ihun murnarta habeebty da Dr Saad sai Daria suke Mata tafiyan ya kasance tarda Aymanah ne da habeebty da Amma harda iftital Dan tace saitaje hakanan mijinta yakawota akataho da ita!


Koda suka iso airport sun Taras ana jiransu duk azaton Aymanah driver insu Dr Saad d'inne na Nigeria yazo dg maiduguri har abj Dan daukansu a airport! Aymanah sai rawar Kai nakeyi Kai kace achan birki nafaso zaman tsangwama nakeyi yoo wlh duk dad'in wani qasar qasarka ta haihuwa tafi dad'i zadai kata marmarin son zuwa wasu qasashen Amman dakaje kadade zakaji kaqosa kadawo taka qasar musamman mu Yan Nigeria 😂⛹🏻‍♀


Damuka shiga motama kasa 6oye murnata nai na rungume habeebty Ina fad'in:


"Waiyooo habeebty na yau zanga my Yaah Hydar da marwatyn da mamyna da mamanmu😢"

Nan wani guntun hawaye yayi zirya a idanuna! Habeebty cikin murmusawa ta sa hannunta tashare hawayen nawa takuma rungomoni a jikinta tana shafa kaina tana fad'in:

"Kwarai kuwa Masoyiya yau zakiga *swanty hydar* dinki da su Marwa harma kikwana dasu in Sha Allah!

Taqarasa maganar cikin garaji Dan bataso tafiyataba wlh matar na qaunata harcikin zuciyarta da gangan jikinta shisa bataso rabuwanmu ba Amman namata alqawari zan ruqa zuwa gaisheta akai akai murmusawa kurum take tace tunda ba dawowa zanyi gaba dayaba ai ba anfani!


Nandai motar Tai tsit Shima Dr Saad qarfin Hali kurum yake Dan baiso komawata Nigeria yanzunba ayadda muka saban Nan!


Nandai motar tacigaba da tafiya har cikin layin maitama Aiko nace muna Isa hotel zance masu muje gidansu Yaah Hydar dansuma maitama suke Kuma zan Gane gidan!


6angaran su yapendo kuwa yau tun 10am Yaah Hydar ya diro cikin gidan aiki yasha fad'a gun yapendo Wai yabarsu a shany'e kaman wani sa'o'insa yau kwana2 Keenan ya kashe waya ko uban mai zai gayamasu hakan ohon Masa shidai haquri yaruqa Basu yace su Adana tambayoyinsu Kuma zai sanardasu dalilin zuwan dayasa suyin!

Basugama tsinkewa da lamarinba Saida sukaga masu abinci niqi niqi ana shigo da abinci sanfari sanfari kaman wa'inda zasuyi tarbar shugaban qasa da ahalinsa!


Shide yace su Adana tambayoyinsu! Amman kowa fal mamakin wannan Abu marmy ce takasa haquri Dan gaba dayansun suna zaune afalone rantakwaf familyn Aymanah abin so ma sha allah Kam! Abinka da jinin larabawa! Ko Ina suka shiga haskawa kurum sukeyi!


Marmy ta kalla Hydar daketa faman latsa waya Yana wani qasaitaccen murmushi Wanda rabon dasuga yanayin irinsa wlh sun mance! Kowa kallo yamayar Kan Hydar in Wanda yaci kwalliya cikin tsadaddar sheda yasha dinki da aiki sunmasa kyau sosai wlh Dan koni Saida na kyasa😂malika ma ta kyasa teemah marafa dasu hauwee da Nana Khadija da my nabee da su ummu afrah Kai har maman khairat ma Saida ta kyasa😂tace indoodo badun badun baban khairat ba danaa..... Saurin kulle Mata baki nai nace Kar angon Aymanah ya jiyomu Mana maman khairat ya hanamu ganin Aymanah da yadda zasu kwashe😂😂😂tace toh indoodo jaaa muje kicigaba da bamu lbr nace yanzun kuwa nandai suka ban hankulansu nikam nacigabada zayyano lbr😂😂😂!


Hydar yayi kyau wlh ba wasaba dama gashi kekkyawansa d'an balarabansa kayan tamasa kyau sai tashin qamshi yakeyi kaman angon dazaakaimai amaryarsa😂!


Marmy ce tace:

"Nikam babana Wai aure zakayine?"


Kowa saiya maida idanunsa Kan mamy shiko gogan naku Kuma gyara zama yayi Yana wani kalan murmusawa sannan ya kalli marmy yace!


"marmyn mu ai kaman ma hakanne Amman wannan ranar daban take ko auran iyakar murnar haka" 😄


Yaah ameena ce tace "Yaah Hydar plsss now ka gayamana man!


Yaaa zubaida ma tace;

" Pls Yaah Hydar naaaah"


6angaran mu kuwa wani kalan kyalle Mai qamshi habeebty tasa ta rufemun idanu dashi Wai zatamun surprise Niko duk naqosa naga surprise in Dan sai shillawa motar mu take Kan titi Chan dai naji motar ta tsaya tana horn alaman an iso ana jira a bud'e gate mutsu mutsun son cire abinda aka d'auran idona dashi nake Amman habeebty da iftital sunqi barina Wai ai yanzun zan cire karnadamu!

D'agowa Yaah Hydar yayi zai Basu amsa sai ya jiyo horn a gate alamun abinda yake jira sun iso zumbur sukaga ya miqe harda had'awa da gudu gudunsa sukam kallon al'ajabi kurum suka bi Hydar dashi Dan abin NASA yadaina Basu mamaki saidai al'ajabi Kam Saida yazo daidai qofan fita yajuyo yace:

"Dan Allah Kar Wanda yabini amsan tambayanku zai amsu yanzun Nan! "

Diga haka yayi saurin ficewa a falan saman dasauri da sauri yake sakkowa daga matakalan benen burinsa kurum yagansa gun Aymani d'insa!

Bud'ewa Mai gadi yayi Daman yarigada yasan da zuwanmu Aiko mukai parking Dr Saad ne yafito yatari Yaah Hydar da jikinsa ke karkarwa riqesa Dr Saad yayi Dan Yaah Hydar har yayi hany'an wajen motar Dan kawai yaganni Niko idona a rufe bansan wainar daake toyawaba!

"Calm down my man! Aymanah zata fito yanzun but yadda muka tsara sai kabari komai ya wakana hakan mna my guy"

Dr Saad ya ida maganar cikin Daria Yaah Hydar yace"oh kaikam wlh Saad so nake kurum naganni kusada my Aymani wlh"

Bai idasa rufe bakiba muka sany'a qafafun mu muka fito acikin motar haka kurum naji gabana ya fad'i aduaa nashiga nanatawa a zuciyata a hankali nace:

"Yar uwa dan Allah kiciren wannan abin"

Daidai saitin kunnena ta matso tana fad'in:

" Karki damu yanzun Nan "

Kamani tayi ta qarasar Dani daidai saitin yaaah Hydar inda yake tsaye ya saki baki da hanci Yana qarema Aymanah kallo daga sama har qasa Niko qamshin turarensane yabigi hancina jinai kurum turaren ya kwantamun a Rai a hankali nasoma Kiran habeebty ciren kyallan Nan plss tafiya nasomayi Ina lalubanta gijib naji na bigi mutum da sauri nayi baya shiko yayi azaman taroni na fad'a a faffad'an qirjinsa wani ni'emtaccen qamshin jikinsane ya manne hancina lakwas nakwantar dakaina akan qirjin NASA Ina Mai shaqan daddad'an qamshinsa batareda nasan wayeba!

Ahankali naji hannayensa abayan Kaina alamun Yana naiman bakin qullin Dan ya kwancemun aiko Nan ya kma yashiga kwancemun a hankali har yagama cirewa tsuri yayimun da idanunsa yana kallona Dan ban bud'e idanunba a hankali nashiga bud'e manyan idanuna nasaukesu Akan kekkyawar fuskan Yaah Hydar d'ina zubur kman wacce aka mitsila namiqe Ina kallonsa fal mamaki fuskata bakina na karkarwa nake fad'in......

"Yaaah ..... Yaaa.. Hy......

Ai ban Gama idasa Kiran sunan NASA ba kurum na fad'a jikinsa na rungume shi qam gudun Wai karya gudu yadda yasaba mun gazau a birki nafaso hakan yasa na qamqame abuna shiko mutuwar tsaye yayi ganin Ina naiman mutar Mai da jiki gasu habeebty da Dr saad a tsaye yasashi zuwa daidai kunnena yace............ "Ay.......... ✍🏼




A hayye chas masu karatu😂⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀finally finally Aymanah ta had'u da Yaah Hydar d'inta Shima ya had'u da Aymanar sa har ta qanqame abunta gudun karyamata gizo koyazata wakana tsakanin wa'innan masoya? 😂⛹🏻‍♀Saidai kawai kunbiyoni a next page in Sha allah !



*Real pure moment of life writers*

😭 *AURAN WAHALA KOH SAKI*?! 📝🙆🏻😭

By Ayshkhair☺
Page 50

Aymanah"!

Chak natsaya da numfashina Jin sunana abakin yaah Hydar! Ai jinai duk duniya babu sunan dayakai sunana dad'i inhar zaa ruqa fad'i sunan yadda yaah Hydar ke Kira! Yooo too nikam ban ta6a jinsa yakirani da sunana ba Saidai yacemun *kee*!

Wlh sunan baqaramin dad'i yay Mai abaki ba!


Miqar dakaina nayi Ina kallansa da idanuna Gaza cigaba da kallan idanunsa nayi sakamakon wani kalan kallo dayakemun Dana Gaza fassara Mai kallan ke nufi!

Habeebty ce ta matso daf inda muke tana Daria tace:

"Mushiga ciki ko?"

Sai anan tunanina yasoma dawowa kallan yaah Hydar nayi nakuma kallan Yar uwa love Dan tabbatar da abinda nake gani! Jinayi yaah Hydar yajany'o hannuna Niko nabisa kaman sokuwa muna binsu Dr Saad abaya!

Nidai tunani fal Raina! Wai yaakayi su Dr Saad suka San Nan gidan? Yama akayi suka san Ni anan gidan en uwanane aciki waikodai mafarki nakeyine?

Hakan yasani mintsilan Kaina waiko zan tashi a baccin danakeyi Amman sai nagani fa zahirine ba mafarkiba?!



Shigowan mu falan yapendo na qasa yasake tabbatar mun dacewa vafa mafarki nakeyiba!

Stairs d'in dazai sadamu da falan samanta muka hau har muka Isa daf da show mirror d'in falan Wanda anan qofar dazai shigar dakai falan yake!

Bin mirror d'in nayi da kallo en uwanane biljik zaune a falan kowa yay tagumi nikam Ina kallansu Dan tawaje mirror d'in transparent ne tacikene tint mutum dake ciki bazai ruqa ganin mutumin dake wajeba Amman mutumin dake waje zai ruqa ganin mutumin dake ciki!

A hankali yaah Hydar yasakemun hannuna sannan ya waiga ya k'alla su Amma dake tsaye yace:

"Bari nashiga Ina zuwa"


Da Tam"suka amsamai shikuma yasa Kai yashiga!

Jinake kaman nayi gudu nashiga cikin falan Amman ganin yamun alaman najirasa yasani tsayawa!

Habeebty tazo inda nake ta Kama hannuna kallanta nay idanuna raurau da kwalla SA hannunta tayi tana sharemunsu tana mun "shiiiii" 🤫hakan ko yasani yin shuru inamata dariya daidai Nan yaah Hydar ya fito yazo daidai inda muke habeebty ta sakeni tana kallan yaah Hydar Wanda Nima shi nake kallo!

Kamo hannuna kurum yayi batareda yacemun uffanba hakan yasa su Dr Saad binmu a baya tsayawa yayi cak daidai qofar shiga ya k'alla Amma yace Mata bismillah ba musu taqaraso ta tura qofar bakinta d'aukeda sallama kowa a falan ya xuba Mata idanu had'i da amsa sallaman Dan zaquwa suka waye! Dan Hydar cemusu yay sunyi babban baqi hakan yasasu son ganin baqin dahar yashafi ilahirin kowa ganin baquwar fuska yasasu Kuma 6arewa a al'amarin basukaiga wani tunaniba iftital, fahimna(habeebty),Dr Saad, yaah hydar shigowa cikin falan duk suka ma kansu mazauni Banda yaah hydar dake tsaye bakin qofan! Gaisuwa ce tasoma shiga tsakanin en falan kowa dai sai mamakin baqin suke kowa ya zaqu yaji qarin bayani wajen yaah hydar murmusawa yayi sannan yace:

"Umma(yapendo)dadaji, daddy, Abba (mahaifin Hydar),iftihal,marmy, maman mu, imtinan Fahad, Salim, Ameena, Marwan
Farid, salima, Aminu , Zubaida, Marwa,!"

Duk yakira sunayensu ajere ayadda suka zauna yakebin kowa da idanu sannan yakira sunayensu!


Numfashi ya saukar sannan yacigaba da fad'in:

"Bayan shekaru masu yawa dasuka wuce farincikin ko wannenku yakau ko wannenku zaman duniyan kawai yake batareda Jin dad'inta ba ayaukam zanmaido maku da fitilar haskenku ayau farincikinku zai dawo ayau komai naku zaidawo normal in Sha Allah !"


" Wai Kai bazaka fiddamu cikin wannan mystery d'inbane Hydar!"

Fad'in yapendo daddy ne ya amshe da fad'in:

" Munajinka Hydar"

Murmusawa yakuma yi sannan ya k'alla kowa a falan wa'inda duk suka maida hankulansu kansa Kai kace d'aukan lectures sukeyi!😂lol


Maida idanunsa yayi Kan qofar falan sannan yace "ki shigo"


Nikam 'yar Aymanar KU da na zaqu na shigo har wani d'an rawa nasaki na scn d'aya waiyooo yau bayan shekaru 6 zan Kuma sany'a family Ina a idanuna Kai Allah nagodema!

A hankali na sa hannuna natura qofar falan Kaina a durqushe kowa dake cikin falan idanunsa duk Akaina jira kurum suke nad'aga Kaina Dan inada tabbacin ko sallamata a zuciya kurum suka amsa a hankali naji yaah hydar yace mun!

"D'ago ki kallesu"

A hankali nad'ago Kaina na saukesu Akan Marwa wacce ita nake fuskanta ko kad'an Marwa Bata ganeniba Dan dama da wuya taganeni Dan nasanja sosai wheather in Nigeria dachan ba d'aya bane! Dan haka saina maida idanuna Kan yaah zubaida itama takalleni d'auke Kaina nay na komar Kan marmy wacce ta tsureni da idanu tanason gasgata idanunta mamanmu ma quri tamun da Ido!


Yapendo ma da daddyna kallona kurum suke ganin kaman Basu ganeniba yasani kawai rugawa na fad'a jikin daddyna Ina kuka ziiiiir shiko mamaki hakan yabasa hakanan kowama hankulansu yakoma Kaina dake jikin daddyna Ina kuka sukam mamakin abinnan suke saidanai kuka na ma'ishi sannan daddy ya d'agoni Yana fad'in

"Kobaa fad'aminba takukanki da abinda kikai a yanzun kurum sun tabbatar min ke d'iyatace ked'in _Aymanah_ ce!

Ai kaman had'in baki en gidanmu suka miqe a firgice harsuna had'a vaki wurin fad'in

...Ayman.aaaa.hhhh


Da sauri na miqe akan qafan mahaifina naje na rungume mamanmu da marmyna wa'inda ke tsaye sororo Aiko sautin kukana ya tabbatar masu dacewa eh lallai nid'ince dai 'yar su data 6acemasu silan AURAN wahala _Aymanah_
Hummmm masu karatu tsayawa fad'amaku shock in da murnar da en gidanmu sukai da dawowata saimu shekara bangamaba ku ayyana kurum!

Nan danan kowa yacigaba da murnar ganina akasani a tsakiya kowa sai santin yadda nadawo yake yayyina kaman su cinyeni Marwa Kam hannunta na saqale cikin nawa taqi sakina gani take tamkar amafarkine abin! Iyayena sunma su Dr Saad godia harda hawayensu muna zaune yapendo na cigaba da kwararo masu godia kamn haka:

"Haqiqa kud'in mutanen kirkine nagartattun bayin Allah daace ana samun mutane masu taimako kamarku da tuni duniyanan ta d'aukaka Allah saka maku da alkairi yadda kuka dawo Mana da farincikin mu Kuma Allah ya baku gidan aljanna ya had'a fuskokinku da annabi muhd mungode mungode mungode! "😪

Nan yapendo ta share hayawayenta Daddyna ma yay godia marmy da mamanmu ma suka masu godia dukda bawai anbasu asalin lbrn abinda yafaru bane kawai dai Hydar yace dasu sune suka riqeni tsawon shekarun Nan!

Kowa dai zuciyoyinsu fal tmbaya kowa nason sanin ydda na rabu da mubash Amman dadaji tace abari ayi salla aci abinci mu huta sannan sai abada lbrn abinda yafaru Dani a baya!

Hakan ko akayi Saida mukayi salla mukaci abinci mukai wanka nikam bacci ma na hau yi sai gab da magrib nafarka nay salla!

Ina zaune Akan abin sallata Ina cigaba da godia ga mahaliccin sammai daqassai daya tsayayta Raina har izuwa wannan ranar Dana sake saka iyayena a idanuna!

Fad'uwa ruf daakai abayana yad'an sani firgita Aman Jin dariya yasani saurin juyo dakaina wata 'yar kekkyawar yariny'a ce wacce bazata wuce 3yes ba Sany'e cikin Riga da wando anmata parking gashinta cikin kalaba guda biyu yarinya kobaa fad'amunba na hango kamanninta da Marwa Amman mamaki abin yaban shin Marwa tayi aurene? Yaah hydar in ta aura? Rasa Wanda zaiban wannan amsar tambayar nayi Nan danan naji hawaye nasauka a kumatuna Amman sai wannan yarinyar tasany'a hannayenta biyu tagogemun su dasauri na kalleta nace:

"Princess ya sunanki?"

Cikin d'oki dajin dad'in nakirata princess tacemun cikin hausan gwarinta da bai Gama Kama bakintaba"cunana l2l Aymanah! Amman uncle hydar nakirana l2l ayni"🥳

Ta ida maganar cikeda murna Niko Gaza tun
nani nayi tsayawa chak nayi Ina qarema yarinyan kallo itako sai murmushi takeyi Chan tacemun:

"Uncle Hydar yace mun yau secnd mommahna tazo shine ya nuna mun inda yake inje ingedaki" 😟

Ta ida maganar Cike da d'oki niko a Raina cewa nai " secnd mommah? Keenan hasashena ya tabbata yaah Hydar ya aura Marwa Keenan ? Aybansan sadda nasoma furta innalillahi wa'inna ilaihir rajiun da sauri ba itako l2l ayni kallona kurum tashigayi tana mamakin abinda nake fad'a haka itako ganin haka saita miqe tsam ajikina da saurinta batareda na hankalta da tashin nata ba ji kawai nai tasoma kwala Kiran sunan mamanta "mommah! Mommah"

Karo sukai da Marwa dake shirin shugowa d'akin Dan kirana riqe Ayni Marwa tayi sannan tace:

"Ha'a baby mi Mai yafaru? Ina 2 mommah in?"

Cikin hakin gudun data d'anyi tasoma Kama hannun mamanta tana janta had'ida fad'in

"Mommah 2moma ay tana ta kuka a d'aki"

Da sauri Marwa tace " kuka?! Kuka fa?!

Jaan hannun Ayni tayi kurum suka shugo d'akin Niko inanan zaune dirshen a inda Ayni tabarni fuskana wanke da hawaye inko Marwa dagaske ta aura yaah Hydar harda baby aurena bazai ta6a yiwuwa dashi ba jinai duk d'okin dawowata Nigeria nadaina jinai dama ban dawoba jinake kaman nai tsuntsuwa nakoma birki nafaso akandai na zauna na iske wannan lbrn Yaya zanyi? Ina zankai son yaah hydar?

Bankaiga samo amsan tambayar tawaba naji anta6ani bansan da shigowanta ba hakan yasani saurin d'agowa Ina qaqulo murmushin dole nace:

"Marwaty yaushe Kika shigo?

Tsayawa Tai 🤔 chak tana nazarina kafun taja numfashi ta k'alla Ayni sannan tace "l2l aynin uncle inta jeki falo gunsu hanan mommah nazuwa kinji?! "

Gyd'akai kurum yarinyan Tay tawuce abinta Niko mamaki nakuma yi toh maisa take Kiran ubanta da uncle? Ay if ba uncle take kiransaba ba yadda zaayi ace Marwa tace Mata Yar gatan uncle inta Saidai tace Yar gatan babanta ko?!

Nanma bankaiga bama Kaina amsa ba naji Marwa nafad'in:

"Keko kukan Mai kike?


Kallanta nai nace " Marwaty Ashe kinyi aure har da baby kikasa Mata takorata ba dole nay kukaba? "

Na tsinci Kaina da Mata wannan qaryan murmusawa tayi tace"wlh Bari yanzun 4yrs Keenan ai tun vayan 6atanki da shekara 2 nay aure acewar su yapendo AURAN kawai shine zai taimakamun wajen rage damuwa da rashinki akusa Dani shiyasa nay aure baby na d'aya Mai sunanki Saidai muna kiranta l2l Ayni inda yaah Hydar dakansa yasa Mana wannan nickname in saikuma yabita l2l aymana ya6ace!


Murmushin kuka nay nace "Allah sarki my Marwa yanzun kunyi aure da yaah Hydar Keenan?! "


Daria tay sannan tace " rabani da AURAN wanchan kekam"


Kallanta nay a fili batareda tunanin zuci ba nace"kaman yaah? 🙄"

Murmushi Tay tace"Dan yafi qarfina!"
."yaakai yafi qarfinki?"
"Dan ya dad'e da mallakema wata zuciyarsa Kuma hasalima Ni bana Mai qaunar aure sai qaunar en uwantaka?!

sai a karonnan na zaro idanu a xuciyana nace wa yaah hydar ya mallakama zuciyansa Kuma tundadai bai aura Marwa ba Kam tasan tabbas da gaskiyanta ya mallakama watakanshi Kuma tabbas tasan yaa aureta yanzun da sauri nace"yaah Hydar yayi aurene? Kuma wa ya mallakama zuciyarsa Wai?"


Marwa tayi mamakin maganganuna Amman sai tayi tunanin qilan Dan najima ban tareda sune!
Murmushi Naga tayi sannan ta kalla agogo taga ankusa Kiran sallan isha'i Kuma zaman bazai kasance ba sai anyi sallan isha.

Kallona tayi ta sauke numfashi sannan tace:

"Miqe kibiyoni kiga Abu!"

Aiko miqewa nayi kaman wata sokuwa nabi bayanta Koda muka fito haraban falan ba kowa hakan yasany'ani tunanin sunje salla fita mukai gaba d'aya a part in yapendo Naga mun shiga part d'in yaah Hydar dam dam naji gabana yafad'i kardai ace matar yaah Hydar Marwa tazo nunamin nandanan na Soma had'a zufa! Riqo hannuna Marwa tayi tana fad'in:

"Mu shiga kiga ikon Allah ,Dan na tabbatar yaah Hydar na masallaci yanzun!

Aiko muka shiga muka iske bayanan, Nan muka chusa kanmu cikin falan ganin Babu kowa wayam a

Please Login or Register in order to submit comment