Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ya bushe a tsaye mamaki yake wai ase dama General Aliyu ya iya fillanci ji yadda ya juye kamar cikin su yake rayuwa shi kam sai murmushi yake dan tabbas Aliyu ya burgeshi ase akwai masu adana yarensu dan irin wannan ranar.

Suko Aliyu zuwa yanzu d'an fullo har ya masoshi tare da rik'o hannushi ya miqa mai sanda cikin fillanci yace.
"Ko zakayi kiwo?"
Ba kin shi kawai ya d'an motsa alamar murmushi sannan yace .
"Yanzu dai tabbaya muke sai wani jiqon in na kuma zuwa sai muyi kiwon ko".

Ido ya tsurawa fuskar Aliyu tare da cewa.
" kai ko bakayi fillanci ba wlh zatinka ke muna kai asalin ba fulatanine gaba da baya,
dan haka ba matsala menene tabbayar?".

Ajiyar zuciya ya d'an sauqe tare da yamutsa fuska yace .
"Rigar Rumoh nake nema".

Cikin tsoron ya zare ido tare da ja baya gani da nunashi yana fad'in.
" kodai kune mutannen birnin nan da kuke zuwa kuna korar mutanen rigar Rumoh! kuna kashe su! kuna kama musu yan matan su! kuna tafiya dasu birnin! sannan Ku sace musu shanayensu! da raqumansu! kuna zalum tarsu?".

Sani ne ya buga mai tsawa cikin fad'a yace.
"Shi wannan mai gaskiya me baya aiki sai na gaskiya shi ba mugu bane shi mai taimakon wanda aka zalum tame".

Cikin tsoron yace "ya zanyi na yarda?".

Qara matsoshi yayi tare da cewa.
" Shin kana jin General Aliyu Muhammad Umar Rumoh?
shin kasan shine shuga ban kare haqqin makiyaya dake cikin fad'in wannan qasa tamu da suke cikin dazuzzuka da tsaunuka? shin ko kasan shine soja na forko d'aya rasa cikin dajin Sambisa ya kuwa ci nasara?".

Shiru yayi tare dayin murmushi ya matso kusa da Aliyu a hankali yace.

"BANDIRAWO ka makaran kana can kana baiwa wasu sashuka na qasarmu ranka dan ka karesu yayinda masu b'arnar sukazo tushenka suka tarwatsa mutanen ciki suka koresu suna kashe na kashewa suka qona na qonawa".

Cikin tafasan zuciya Aliyu ya rumtse idonshi tare da cewa.
" Muje ka kaimu Rigar Rumoh na gani".

Shiru yayi tare da siyayar da hawaye ya kamo hannun Aliyu cikin takaici yace.
*Bandirawo* a inda muke tsayennan cikin asalin rigar Rumoh ce ai an dad'e da watsa rigar Rumoh ta zama wurin kiwonmu yau kimanin shakaru 4 kenan da y'an ta adda suka hana rigar zaman lafiya sabida suka watsasu,
Kaga wadan can rigogin dake kusama
kullum cikin baraza na ake musu kan dole subar nan ".

Jikin jijiyar bishiyan da suke qasanta Aliyu ya zauna tare da dafe kanshi har zuwa d'an wani likaci sannan kuma ya miqe tare da cewa Sani.
" Shi kenan na rasa ma dafa na rasa ma dosa mu tafi Sani zan qare rayuwa ta ba farin ciki".

Cikin sanyi da tausaya mai Sani ya miqe tare da cewa"oga kaqa yamma tayi kuma ba zamu gane hanyar ba mu roqi Gainako ya rakamu".

Matsosu gainako yayi ganin suna tafiya dan Aliyu ya muna baya buqata.
da sauri yasha gaban sa cikin sanyi da jin son shi yace.
"Bandirawo kalli kan dutsen can da wancan qoraman".
Ido ya tsurawa dutsen da saman qoraman sai wani irin farin hayawi ke tashi tuni wurin ya fara rufewa da hayaqin sai duhu ya fara qaruwa".

Maganar Gainako ta kuma katseshi cikin fillanci dai har yanzu yace.

" kaga wannan yanayin shi muke kira da *Labbare* yanayin ne da yake sauqa da zaran yamma tayi dashi muke kwana sai kuma gari ya waye yake fara tafiya da zaran labbare ya sauqa ko dabbobinmu basu fiye gani sosaiba kuma sanyine ke ratsa ko ina sannan tanan baku da hanya fita sai ta bayan dutsen inko nan zakubi dole sai kun kwana a nan kafin ku samu fita sabida yanzu duk ta inda zakubi zaki hadu da hayaqin labbare da kuma makiyaya sun taso kiwo".

Ido Sani ya dan kuma warewa ganin a take wurin ya fara wani irin yanayin duhu da sanyi mai tsananin gaske.

Shi kam Aliyu duk bai ganiba don baijin komai
Amman gani tako ina dabobine ke faso dajin na fita yasa dole yabi hanyar zagayen yayin da Gainako ke binsu a baya tare da sakin wani irin ihu irin na makiyaye da dabobnsu,
aiko sai ga dabobin sun biyishi a baya.
Cikin d'aga sauti yace.
"BANDIRAWO Ku biyoni zan nuna muku hanya".
Jin haka yasa suka rinqa bin shi a baya da motar su.

Tafiya mai dan nisa sukayi
Sai gasu sun fito ta bayan wata rigar Fulani mai matuqar kyau da tsari rigace mai zagaye da ni'imomi da korayen tsirrei ta bayan rigar shukoki ne masu matuqar kyau daga gaban rigar kuma wata koramace mai ruwan garai-garai ke gudana sai dutsen dake gaban qoramar gaba d'aya wurin sai ya banda wani kalan qamshi da ni'imah.

Gainako tsayuwa yayi tare da ajiye sand'ar kiwonsa a wani fili mai farin yashi dake gaban qoramar sannan ya juya gunsu dai-dai lkcin wani farin dottijo ya fito cikin wani gida daga dukkan alamu gidane sai dai yanayin gidane mai zagaye da katanqar manyan duwatsu,
kai tsaye gunsu dottijon ya nufo cikin sanyi da tsura musu ido tare da murmushi
cikin sanyi yace.
(" Surbajo waru d'o")
"D'an saurayi zo nan"
Cikin sanyi suka matsoshi Sani ne ya gaida shi shiko Aliyu kawai bin shi da ido yake .
Cikin sanyi ya juya tare da cewa su biyo shi.
Shi kam Aliyu bin shi kawai yake cike da mamaki inane nan kuma Gainako ya kawosu.
Suna shiga tsakiyar gidan
dottijon yace
"Badd'i waru an e Inna waziri"
Badd'i kizo keda Inna waziri kuzo da madara da ruwa munyi baqi".
dai-dai lkcin wata Yar budurwa mai kimanin shekaru 16 ta fito daga cikin wata bukka riqe da gwaryya a hannuta kanta a qasa tafiya take cikin kula da qoryar karta subuce ta fad'o ta fashe,
tazo dai-dai kan Aliyu da yake sunkuye yana qoqarin kwance but din qafafunshi qoryar tai qasa......

*Wasa farin girki masu karu yanzu muka fara shiga cikin labarin muje zuwa*

By
Garkuwar Fulani
[8/18, 6:26 PM] πŸ’žIt's @lh@jiπŸ’ž: πŸ“πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡
*BANDIRAWO* page 5⃣
Na
*Aysha Ali Garkuwa*
πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡

Pure moment of life writers


*dedicated 2 Ummu amhumy tare da Billy A A & baiwar Allah amnoor*


Ya d'an kalleta a fakaice ganin yadda take tatsar cikin iyawa da qorewa idonta a qasa kamar wacce ta lumshe su yayinda ta kauda kanta gefe kamar mai gudun kar ta shiqi qamshi nono kanshi ya kawar tare da matsowa gefen Bappa cikin yanayin shi na tsuke fuska ya dan shafa kanshi tare da cewa.
"Bappa yanzu nake son zamu wuce dan tafiyar dake gaban mu tana da nisa."

Matsoshi Bappan yayi tare da miqa mai madarar da ya tatso yanzu sai tururi take yace.
"Gashi kasha maganin sanyi."

Kai ya d'an juya a hankali yace.
"kai Bappa da sanyin safiyar nan mutun ya kama d'ura nono a cikinsa."

Murmushi yayi tare da miqa mai har bakinshi ganin shirin bashi yake a baki, yasa hannu ya karb'a tare da d'an sha,
lokaci d'aya ya d'anji sanyi ya sake sa,
sannan ya miqawa Sani sauran shima ya sha,

Haka sukai ta d'an zagawa cikin garken bayan d'an wani lokaci Bappan ya miqe tare da cewa.
"Bodd'i zomu je cikin rafi da aiki a ciki."
Sannan ya kalli Aliyu cikin kula yace.
" (Surbajo war en yaha) Saurayi zomuje."
Shi kam Aliyu ido ya zubawa Sani ganin azarb'ab'in shi tuni shi har yayi gaba ganin haka yasa ya bi bayan su ta gefen dutsen da suka ratsa
A hankali yarinyar da ake kira da Badd'i ta bi bayan shi suna tafe har suka isa cikin lambun.


A hankali General ya lumshe ido tare da hard'e hanna yenshi a qirjin shi sannan ya rinqa d'an zagawa cikin lambun yana mai mamaki ganin irin ni'imomin da Allah yayiwa ma zauna wannan wurin komai mai sanyi Allah ya basu ba abinda babu a cikin lambun na y'ay'an itatuwa hatta tupa da inabi akwai su kad'an a ciki bar pia kam ayaba lemu goiba abarba kakana maggoro dibino kashu,
gefe d'aya kuma rekene iya ganin mutun.

yana cikin shaqar qamshin da wurin ke fiddawa yaji Bappa na cewa .

"Bodd'i kicire wanda bai qarisa nunan ba sabida su Surbajo zasu tafi dashi kinga kar ya logob'e a hanya da zafin mota."

Gunta ya juyo d'an shi yarinyar Sam mamaki take bashi ita bata mgn sai iya barna da jiqa mutane da nono.

Itako bata ma san yanayi ba dan ko inda yake bata dubawa aikinta take cikin sanyinta banana take yanka manya-manya sai kuma ta koma gefen pia tai ta sinko manya sannan ta juya gun Inabi da tupa suma ta had'a saida ta cika kondon kabar guda biyu manya da fruits sannan tazo ta ratsa gefen shi cikin sanyi ta matso Bappa a hankali take magana shi dai ba jin me take fad'iba,
Amman dai ya lura cikin shogoba take magana abinda shiko ya tsana a rayuwar sa ko dan bai tashi da hakan bane.

Kai ya kawar ganin yadda Bappa ke mata magana cikin kulawa harda kama hannu ta yana hura mata iska ko tofi yake mata ne ma oho musu .

Daga nan kuma ita ta fara fita ta nufi gida shiko Bappa ya kira Sani dake ta cin banana kamar biri yace .
"Sani d'auki wannan kondon mu tafi" shiko ya d'auki d'ayan sannan ya kalli Aliyu yace kai kuma d'auki nonunan ayaban nan mu tafi gida."

Toh kawai yace sannan ya d'auka suka kama hanya.

Bayan sun fito ne yaga kab ba shanayen sai y'an qananan da aka bari dan bazasu iya nisan kiwo ba wurin yayi shal sai korayen tsirrei dake zagaye dasu.

Kai tsaye cikin gida suka shiga Bappa na gaba suna baya har qarqashin bishiyar ced'iya dake tsakar gidan,

Inna na ganin su ta shiga d'aki tare da d'auki taburma ta zo ta shimfi d'a musu sannan ta zauna kan kujerar tsuguno dake gefen wurin, Bappa ne zauna tare da kallon Aliyu da ke zaune gefenshi cikin murmushi yace.

" Inna Waziri ga jikanki mai irin halin Sayyadi naki!"

A hankali ta juyo ta tsura mai ido cikin sanyi tace .
"Surbajo me sunan ka?."

Kanshi a qasa yace.
"Aliyu "

Ajiyar zuciya ta sauqe tare da yin murmushi tace .

*"Aliyu Haiydar* babu rego ko gafalelle Haiydar Jan zaki gadanga kusar yaqi ."

Jin kala manta yasa ya d'ago kanshi ya kalleta lokaci d'aya kuma suka had'a ido da ita sai kuma yayi mamakin ganin hawaye na bin fuskar ta .

Sai kuma yaji abun bai mai dad'i ba sai ya rinqa juya mata kai a hankali tare da cewa.
"Kiyi haquri "

Duk da baisan damuwar taba yaji yana tausaya mata itako sanyi taji da ban haquri shi.
Bappa kam sai murmushi yake tare da binsu da ido a filiko yace.

"Inna Waziri baki kawowa jikokin naki abinci ba gashi sunce yanzu zasu tafi."

Miqewa tayi tare da shiga kitchen ta fiffito musu da abin kari ta jera musu kan taburmar shiko Bappa ya bud'e musa sannan ya biqa musu ruwa a qoryar suka wonke Hanna yensu,
tare suka ci abinncin da Bappa yana mai kallon su cikin qauna.

Bayan sun gama sukaje sukayi wonka suka shirya tsab Sani yasa musu kayansu a mota ga kondunan fruits har 3 ga qoren gon zabbi har 2 ga jara kunan man shanu guda 3 tare da jarakunan nono 2 sannan ya had'asu da qoryan zuma yar asali har guda biyu.
sannan suka shiga cikin gida sukawa Inna sai wata rana har zasu fita suka tsaya cak jin muryar wata tsohuwa cikin matsifa tace.

"Kai Bappa wato har zakayi baqi har su gama zaman su,
ni bazaka ce suzo su gaida ni ba,
Ku kuma baqin muna furci ko Baku San darajan manya ba!
ke kuma muna fuka harda kukan gulma toh wlh ki shirya yaune zakiyi kuka mai dalili Yau zaki mai mata kukan da kikayi shekaru 40 da suka wuce!
Ku kuwa baqi yau zaku san kun shigo inda ba'a fita dan kun tari kan bala'i da kukazo nan garin!
ke kuma Bodd'i ko? Yau kyawun naki zai zama ganimar wasu gara dai!."

Cikin mamaki Aliyu da Sani suka juya suna kallon Bappa da inna wacce tuni take zubda qollah murya na rawa take cewa.
"Dan Allah Lari karki cutarmin da Bodd'i,
Lari kibar baqin nan karki sasu cikin mugun furuci !"

Ido suka tsurawa Bappa cikin tuhuma da neman qarin bayani,
shiko Bappa hannun su ya kamo har zuwa bakin motarsu
cikin sanyi yace.
"Aliyu kar ku tsaya neman qarin bayani ba lokaci ku tafi kawai kar masifan bakin Lari ya shafeku ."

Cikin jin haushi ganin gaba d'aya yadda suka rud'e da kalaman matar ya kalli Bappa yace.
"Bappa wacce ita? kuma me had'inku da ita? me kuma zata yi muku?!"

Hannushi ya kuma ja cikin murmushi qarfin hali yace.
"Aliyu kubar wannan yanki Ku hamzarta kar lokaci ya kure muku."

Ganin bazai basu amsa ba yasa suka juya zasu shiga ,
Sosai Aliyu yai mamaki ganin irin kaya da Bappa ya had'a musu ,
Matsoshi yayi cikin sanyi yace.
"Bappa wannan kaya ai sunyi yawa".

kai ya gyada mai tare da cewa .
" a a Ali bayyi yawaba kai dai kuje sai wata rana."

"Toh mun gode" yace tare da juyawa har zai shiga mota sai kuma ya juyo da sauri cikin mamaki jin hayaniyar shanaye da raquma da suke ta shigowa cikin rigar a guje ma kiyayan na binsu a baya tako wacce kusurwa shigowa suke.

Ganin wannan Gainako da ya kawosu rugar ya nufi Bappa a guje yasa shima ya dawo gaban Bappa .
Shi ko Bappa ido kawai ya rumtse tare da cewa.
"Gainako yau kuma rigarmu zasu shigo ko ? yau ma Bodd'i suke son d'aukewa ko?."

Sai hawaye shar a idonshi shiko Gainako sai haki yakeyi cikin d'auki war numshi da haki yace.

"Bappa sunce in muna son kanmu da lafiyar mu a kai musu Bodd'i!
inko muka bari suka shigo wlh zasu kashemu su qona rigarmu kamar yadda sukayiwa rigar Rumoh."

Kafin yayi magana sai ga mutanen rigar duk sun hallara qofar gidan a gaban su wasu dottijai guda 3 suka kalli Bappa cikin tausaya wa sukace.
"Bappa ka samu Ku fita ta qofar baya kaida Bodd'i dan tabbas ita suke hari."

Cikin tsoro wani matashin da ya iso yanzu yace.
"Wlh suna nan a qofar bayan ma sunce nanda azahar a fito musu da ita da kuma dabbobinmu."

Shi kam Aliyu so yake sumai bayani suko sun k'asa sai b'ari suke.

Bappa ko jin haka yasa ya matso jikin Aliyu hannushi ya riqe cikin rawan murya da neman
alfarma yace.
"Aliyu taima konka nake nema zaka taima ka min?."

Cikin kaushin murya yace .
"Bappa ka gaya min meke faruwa?,
ai taima ko shine aikina kodako zan rasa raina sabida nai alqawatin taima ko kafin na fara wannan aiki nawa Bappa aini raina da lafiyata kan taimakon qasata yake ka gaya min suwaye ke son kasheku?."

Kai ya rinqa juyawa cikin sanyi ya koma cikin gida ,
Jim kad'an ya fito riqe da qura'ani mai girma cikin sauri ya miqa mai tare da cewa.
"Aliyu kayi alqawari tsaka ninka da Allah zaka taimaka min zaka kuma riqe amana?."

Ranshi cike da jarum ta yace.
"Nayi alqawari zan taima ka maka kuma zan riqe amana bazan kuma k'asa taima ka maba."

Cikin jin dad'i yayi ajiyar zuciya sannan ya kalli mutanen wurin tare da riqe hannun Sani.
" yace Sani Kaine shaidan Aliyu a garinku in kun koma."
Ya kuma juya ya kalli taron mutanen wurin cikin d'aga murya yace.
"Ku kuwa kune shaida na da alqawarin Aliyu."

Kusan a tare su kace
"Ehh".

Murmushi qarfin hali yayi sannan yace.
" Aliyu na baka auren Amina Bodd'i bisa alqawarin da kayi min!
Kuma yanzu za'a d'aura auren!
yanzu kuma zaku tafi da ita!"

Shi kam Aliyu ido ya zaro woje tare da bud'e baki zayyi magana .

Da Sauri
Sani yace.
"Alqawari kayi oga kuma tsaka ninka da ubangiji kai wannan alqawarin."

Yana rufe baki ya juya ya zaro kud'i masu yawa a cikin moto sannan ya d'auki kondon dibino d'aya cikin sauri ya dawo gaban Aliyu daya murtuqe fuska kamar zayyi ruwan jini.

Kud'in ya miqawa Bappa tare da cewa.
"Ga sadakin ta dubu 50 sannan ga dibino kawai yanzu a d'aura Aure,
shi oga namiji ne ya halatta ya karbawa kanshi Aure." .....

Gaddara ta rigayi fata General Aliyu yanaji yana ganin wata gaddarar rayuwa ta auka mai Wanda dole girman alqawari da bakinshi ya karbawa kanshi Auren Amina.

Ana gama daurin Aureb tare da shaidun mutanen rigar Bappa ya shiga cikin gida,
cikin sanyi da tausayawa kanshi da matarshi da Bodd'i ya kalli Inna ba tare da wani baya niba ya kamo hannun Bodd'i tare cewa Inna.
"Kiyi haquri wannan shine mafita kuma wannan itace sabuwar gaddararmu."

Itako Bodd'i sai binshi tai yana riqe da hannuta.

Gaban Aliyu ya tsaya da ita tare da miqa mishi hannuta cikin sanyi yace.
"Aliyu ga matar ka!
Bodd'i kekuma kibi mijin ki!"

Ita kam bata fahimci komai ba a zancen nasu sai dai ta fahimci tafiya zaiyi da ita shiyasa sai hawaye ke bin fuskar ta.

Shi kuwa kamar makaho Bappa ya jashi har cikin mata Sannan Sani ya shiga suka tafi .

Suna fita cikin rugar ta gefen dutsen Membila sai ga motocinsu da suka bari cikin Membila cikin mamaki Aliyu ya kalli captain Sani da neman qarin bayani duk da dai ya gane Sanin ne ya kira su dan suzo su bawa mutanen rugar kariya.
hakan ko yace mai .
"Oga nina kirasu."

Kai ya gyad'a sannan yace .
"Toh motoci 4 su isa wanda sojoji kusan 28 a cikin sannan yace .
mota d'ayar kuma ta juyo su koma tare.

Haka kuwa Akyi matoci 4 suka nufi cikin rugar,
suko su Aliyu sunka nufi Hanyar Gembu
domain zuwa Yola..

A cikin motar kuwa Bodd'i ta.....

By
Garkuwar Fulani
[8/18, 6:26 PM] πŸ’žIt's @lh@jiπŸ’ž: πŸ“πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡
*BANDIRAWO* page 6⃣
Na
*Aysha Ali Garkuwa*
πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡

Pure moment of life writers


*Wannan shafi nakune ku kad'ai Sisters In Islam Mmn jhadijah tare da Y'ar mutan wudil sa'a tafi manyan kaya nis@ online writers & Hurairayabo and Feedoh*



Dungu lewa tai wuri d'aya tana mai wani irin kuka mai sanyi da tausayi dan,
gani take shike nan an rabata da tushenta gatan ta ji take kamar an rabata da farin cikin ta,
a ranta take tuna meyasa Bappa baiyi tunanin komai ba ya had'ata da wannan mutumin mai fuskar mugaye,
cikin jin zafin zazzabin da yake shirin rufeta ta d'an bud'e idonta tana mai kallon tsaunu kan da tsirren da suke ketawa yayin da suke bawa rugar tasu baya a take ta saki wani kuka mai cin rai tare da qamqame jikin ta,
ta takure can gefe jikin motar.

Shi kuwa Aliyu ido kawai ya rumtse cikin wani irin zafi da ranshi ke mishi ,
tunani yake shi da yazo neman mafita da samun sauqi sai gashi wani baqin shafi ya shiga cikin littafin qaddarar rayuwar sa,
shin ina zai Ajiye wannan yarinyar da wani matsayi zai nunata ga Mahaifin shi? da yayan mahaifin nashi ?
shin da wace fuska zai nunata ga sauran abokan aikin shi ?,
kai ya kuma juyawa da qara rumtse idon shi tuno Mama da yayi ko me zatace kan wannan batun ! wanne sherri kuma zata bishi dashi !,
shi a wanne yanayin yazo duniya da ya kasance ba mai ji bantan lamuran shi .

Haka yai ta tubka da warwara,
yayin da shiko Sani driving kawai yake,
zuciya yarsa cike da farin ciki ko ba komai yasan insha Allah nan bada jimawa ba Ogan shi zai samu sauyi a rayuwar sa a haka suke tafe kowa da abinda ke ransa, Bodd'i ko tayi kuka har muryarta ta dashe fuska ta kumbura.

A haka har suka bar jihar Taraba suka fara nausawa cikin jihar Adamawa Yola tafiya suke cikin sanyin safiya yayinda Sani ya samu hanya ba cunko son ababen hawa ya rinqa tsula gudu kamar masu firewa yayin da. motar su Garbe ke biye dasu a baya.

10:25 Am Suka isa dai-dai Gurore inda hanyar ta kasu 3 d'aya hanyar da zata sadaka da cikin birnin Adamawa d'ayar kuma wacce zata fiddaka Adamawa zuwa su Gombe Bauchi Jigawa Kano Kaduna Abuja Katsina Sokkoto da dai sauran sashoshin dake gefen,
d'aya hanyar kuma wacce ta kanta suka bullo itace hanyar tafiya Taraba kuma itace ke sada mutun da qasashen kudancin Nigeria kama su Calaba Onitsha Binuye da dai sauran su.

Suna zuwa dai-dai wurin Sani ya juyo cikin neman izini yace.
"Oga cikin Yola zamuyi ne ?"

Ba tare daya bud'e ido ba ya bud'e baki cikin bada umurni yace.
"Miqewa zakayi kawai muyi tafiyar mota dan bazan tsaya jiran ✈ bare ma wannan bororiyar bata da komai bare muyi tafiyar da jirgin."

Toh yace tare da juya hancin motar suka kama hanyar Gombe,
Allah sarki,
Badd'i bata taba zaton rayuwar ta zata juya mata haka ba yau gashi tabar rugarta tabar jihar ta gashi har tana qetare sauran jihohin da suke maqobtaka da jihar su, zuwa yanzu tabar jin ko yanayin sanyin jihar ta bare qamshin furannin rugarsu,
kuka ne tayi shi har qarfin ta ya qare gashi dama ba abinda taci.


Tafiya ma bud'in ilimi Mahmud Yau yai nisa,
yauko Amina ce tai nisa inda tabar sunan Bodd'i a rugarsu ta d'auko sunanta. Amina daga Gombe ko taji wani sabon suna a bakin Sani .

1:00 pm suna cikin birnin Gombawa diban fari ba'a kwana damuba a tashi.

Kai tsaye Shagalin ku Restaurant suka wuce,.Suna isa bayan Sani yayi parking kafin ya fitoh mah su Garba sun fito daga tasu motar a guje suka bud'ewa General Aliyu mota tare da sara mai kab suka qame har saida ya fito,
Sannan suka bishi a baya har ciki yayin da ma aikatan wurin suka fara yi musu hidima cikin karra mawa suka isar da Aliyu can cikin wurin na musamman su kuwa suka koma baya gun sauran mutane gaba d'aya aka shirya musu abinci da nasha suka fara ci domain sauri suke Yau suke son zarcewa Kaduna.

Shi kuwa General zama yayi cikin nitsuwa sannan ya lumshe idonsa tare da shaqan qamshin wurin wanda ya had'e da sanyin A,C a hankali ya rinqa sauqe ajiyar zuciya har zuwa wani d'an lokaci sannan ya bud'e idon shi cikin furza numfashi ya d'an juya kenan ya haggo Captain Sani ta cikin glass din wurin wanda yake kib da area park daga duk kan alamu magana yakeyi amman bai jin abinda yake fad'in ganin haka yasa ya zaro phone enshi ya kirashi ,
bugu d'aya ya d'aga cikin tsuke fuska yace .
"Kai Sani me ka tsaya yi ka dai san akwai sauran tafiya a gaban mu kai sauri ka shigo kuci abinci muyi sallah sai mu tafi."

Cikin kula yace.
" Oga Meenal taqi ta fito tazo taci abinci kuma sai kuka takeyi."


Baki ya tab'e cikin tsawa yace.
"Toh sai me cikin ka ko cikin ta ? ai in taji yunwa zama taci wani bai saniba kar taci mana kai me naka a ciki,
kawai dai inma baza taci abinci ba toh ta fito tayi sallah tun kafin su Garba su fito su ganta aikin banza kawai."

Ido ta tsurawa Sani cikin zubda qollah dan kab taji abinda yake fad'in ga uban tsawan d'aya buga wanda ya firgitata,
cikin zubda qollah ta zuro qafafun ta cikin dishewar murya tace.

"Bandirawo a ina zan samu wurin sallan?."

Gefen wurin ya nufa da ita sannan ya kaita gun masalacin dake wurin Wanda ga fomfunan da keta zubda ruwa a nan tai al'walah sannan tai sallah duk Captain Sani na tsaye yana mata gadi tana idar da sallah ta komai cikin mota,
shiko ya shiga ciki ya d'an ci abinci a gaggauce sannan ya musu Othern abinci yaje ya aje cikin mota sannan suna fitowa sukayi sallah 1:35 pm dai-dai suka bar garin Gombe.

Kafin 2 ma sun isa Darazau Dara birnin bauchi daga nan suka harba jigawa dutsen kafin 6 sai gasu a Kano ta sabo tumbin giwa .

A nan suka tsaya suka ci abinci sukayi Sallan maggari ba sannan suka jira har zuwa isha bayan sunyi ishan ne suka fara shirin tafiya bayan sun dudduba lafiyar motocin nasu sannan suka kama hanyar Kaduna.

Allah Sarki ita kam Meenal gani take tunda take a rayuwar ta bata taba irin wannan tafiya mai nisan ba tun a Yola ta fara tsinkewa da cewa shike nan an rabata da iyaye ta bare yanzu da taga bayan kanon ma gaba zasu qara kawai sai ta ringa tsiyayar da qollah tare da jan wani irin numfashi ta duqqule wurin d'aya.


A ganin su Captain Sani wanda ya taso Taraba 2 Kaduna in yazo Kano ai ya iso gida.

Dan haka yanzu tafiyar suke a tsanake ,
9:00 pm Suna cikin birnin Kaduna kai tsaye agguwar Sarki suka nufa cikin tafiyar shaidawa mutanen gari General Aliyu na gari.

Jiniyar su ce ta

Please Login or Register in order to submit comment