Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

releasing video tarayyana da wata da I know nothing about!”?

Knocking kofan akayi kallon Abee Mustafa yayi yace “gasunan” sanan yajuya yace “bude musu kofa Hamza” juyawa Hamza yayi ahankali yabude kofan Haruna da Police nan mai suna Abdul ne suka shigo sai Gwaggo data rike hannun Lujain gam dake lullube suka shigo tana hura hanci sai Baba dasu Baffa da Yayan Lujain sai Mama wuri harun yanuna musu kan dogon setin kujerun office din zazzamansukayi Gwaggo ta zaunar da Lujain da sheshekan kukanta kawai ketashi acikin office din itakuma Gwaggo tabi kowa na office din da kallo tace “nifa ba zama takawoni ba waye mutum dayaja sunan diyata yabaci aduniya ina mai kampanin?” Ahankali Abee da kanshi ke kasa yadago kanshi gently yazubama Gwaggo idanunshi da hakanan kawai taji magana ya makale abakinta.
💫 SAKON SO 💫


M SHAKUR ✍🏻


Abu daya zan fadamuku gareku masucin hakki na, da masu daukan book dina suna sawa a site dinsu, damasu sawa a YouTube, da dukma wata ko wani mai amfani da book dina yana kudi without consulting me wlh wlh ban yafeba kuma bazaku taba ganin cigaba ba dan hakkin wani kukeci, kome zakuyi da rubutu na contact me first! 07012181461



Jama’a I am back! Wannan littafin nawa zaku sameshi a all my social media platforms 💃 idan kuna kuna bina a Instagram ko Tiktok su akodayaushe zai kasance sun wuce yan WhatsApp da Episode biyu💃💃

Ku danna link dinnan dan following dina a Instagram;
https://www.instagram.com/p/CnmsOO8I0XL/?igshid=MDJmNzVkMjY=


Ku danna wannan link din dan following dina a TIKTOK;

https://vm.tiktok.com/ZMYekGsQV/
DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JINKAI



EPISODE 1️⃣
~Masjid Ibn Taymiyah~
Aka rubuta ajikin babban masallacin dake cike makil da jama’a kowa yaci manyan kaya manyan shaddoji da kanagani kasan daurin aure ake shirinyi, wani matashin saurayine ke sanye da manyan kaya dakuma babban Riga na shadda datasha aiki yana tsaye daga ta wajen masallacin yana kallon agogon hannunshi da alamu lokaci yake dubawa chan kuma yadago kanshi yana leken kan titin da masallacin ke kai, tabashi akayi daga baya dayasa dasauri ya waigo wani matashin saurayine yatabashi shima yana sanye da manyan kaya yasha hula kube, cikeda damuwa yace “he’s 20minutes late Arif kazo mutafi koda na’ibin limamum masallacin nanne ya karba maka Auren, duk an taru mutum daya ake jira haba mana is not cool” girgizamai kai wanda aka kirada Arif yayi yace “I know he will come let’s just give him some time, Uncle Hamma is just…..” dasauri abokin yace “sociopath” wani mugun kallo Arif yamai zaiyi magana daidai wata Babban jeep na parking abangaren masallacin dayadan sami space na parking, wani kalan walwala ne ya bayyana akan fuskan Arif baisan lokacin dayabar abokin nashi yafice daga cikin premises na masallacin dasauri ba dudda jama’a na kwalamai kira ta ko’ina suna ango ango baibi takansu ba yay wajen motan dayake nan bamaka ganin kowa na ciki sabida tinted glass ne duka kuma arufe, ahankali yasa hannunshi batare daya jiraba yabude gaban motan bangaren mazaunin direba tareda tsugunnawa har kasa cikeda girmamawa batare dayama kalli fuskan mutumin dake cikin motanba yace “barka da zuwa Uncle Imran” wani magidancin mutum ne zaune cikin motan da akalla zaiyi 48/49yrs yana sanye dawani soft milk yadi daya haska bakar fatanshi dake bala’in sheki tsabagen hutu.


Yanada cikan gashin gemu sosai gasunan baki sidik masu tsayi kadan dawasu sirarren saje dakenan a kwance suma lublub, ga cikan gashin gira dakuma suman kai dudda lafiyayyan hulan minister na kanshi hakan bazaisa kagane cewa yanada cikan sumaba, yanada wasu kalan kananun yet manyan idanu idan ya zubamaka su idanba ka natsu ka kalleshi ba zaka dauka idanun nashi a lumshe suke amman abude suke ras kwayan idanun farare fat, hancinshi dogone sosai kuma siriri sai lips dinshi dakenan jazur, kallo daya yama Arif dake tsugunne kanshi akasa babu wani murmushi ko fara’a akan fuskanshi sannan kuma babu wani bacinrai ko wani yanayi akan fuskanshi saima fuskanshi dake nan adake dake lullube dawani kalan warm rahama akai, kaman baiso yay magana yace “Arif” wani kalan murmushi Arif din yasaki cike da mugun girmamawa yace “na’am Uncle Imran” tareda dago kanshi yadan kalleshi saikuma yasake sauke kan nashi kasa dasauri baitaba ganin mutumin dake tattare dawani kalan mugun kwarjini dakuma haiba irin na Uncle Imran ba, duk yanda kakai ga bushewar idanunka baka iya kallon tsabaragen idanun Uncle Imran kamai, Ahankali kaman baiso yay magana cikeda wannan natsuwan yace “get up kayanka will get dirty” tashi Arif yayi babu gardama still kanshi na kasa hakan yasa anatse ya sauko daga cikin motan yafito ya tsaya kusada Arif duk tsayin Arif akafadar Uncle Imran yake dan Uncle Imran giant ne sosai, dudda babba ne shi ya manyanta amman jikinshi da gabobinshi gabaki daya atsaye suke tsaf kana ganinshi kaga wanda yake gyara jikinshi ta hanyar cin lafiyayen abinci dakuma excercise, yana sanye da babban riga dake kyalli da wandonshi daya tsayamai a daidai idanun sahu, kafanshi na sanye da ankle sock dake cikin wani givency covershoe dake sheki sosai, juyawa yayi yadauko wani bakin glasses dan idanunshi basason haske sosai yasaka sannan yakalli Arif dakanshi ke kasa yace “muje ko”? Gyadamaikai Arif yayi yace “to bismillan mu Uncle” yay maganan suna jerawa tunda yake baitabajin mutum dake kamshin turare kwatankwacin irin turaren Uncle Imran ba, turaren Uncle Imran nada bala’in dadi gasu da sanyaya rai, tun kafin su karasa cikin masallacin mawaka da maroka kemai wake wanda ko kadan bayaso hakan yasa baice musu komiba koyabasu kudi ba yawuce suka shiga masallacin nan da nan abokin Arif yace “waliyin Arif ya iso” karasawa sukayi cikin aka zazzauna nan da nan aka daura aure tsakanin Arif da Salma akan sadaki 500k wanda Uncle Imran yabiya mishi akai addu’a ana gamawa ko sec daya tal bai karaba yamike yajuya Arif yatashi dasauri yabishi abaya, abokin Arif yataba wani abokinsu da duk sukabi Arif da Uncle Imran din dasuka fice daga masallacin da kallo yace “dan Allah jibi Arif saikace yaga God” dayan abokin mai suna Muhammad yace “to ai kusan hakane wannan Uncle din nashi shiyamai komi aduniya tundaga primary school konine abinda yafi hakama zanmai wlh Aliyu tunda mahaifinshi ya gudu yabarsu bai kuladasu ba” tabe baki wanda aka kirada Aliyun yayi yace “bakasan waye mutumin nan ba idan kasan irin kalan bakin girmankan dayake dashi saikai mamaki bakaga yanda babu wanda yagaida a masallacin nan ba sai uban dingile wando shi adole ustazu da ijiye gemu” wani kallo Muhammad kema Aliyu yace “waikai Ali me mutumin nan yamaka ne danni wlh banga aibunshi ko daya ba”? Mugun kallo Arif yama Muhammad yace “bazaka gane bane waini mutumin nan zai hana aiki sabida wai inashan taba yay rejecting application dina a company shi, shi wayasan kalan abubuwan dayayi lokacin dayake matashi yana soja kafin yay retire”? Kalan kallon da Muhammad kemai yasa yace “me to ai gaskiya nafadi ni to even tell you the truth gwara dabai daukeni ba dan ance mahaukaci ne tuburan tuburan saidai in alluran sojojinshi basu tashi ba wlh bakaga saisa har yanzu babu wacce ta yarda ta aureshi ba sai tsufa yake agidan tsohuwarshi” wani mugun harara Muhammad yamai yace “kainedai kaga tsufan dan ni bangani ba wlh ko mahaifin Arif daya girma yafishi tsufa, haushin shi kawai kakeji sabida yahanaka aiki dayayi, kuma aure dabaiyiba shine baiyi niyya ba tunda akazo har gida aka kashemai mata da yara biyu” dasauri kaman jira Aliyu yake yace “kasan shekara nawa yanzu da mutuwansu? This is the 13th year amman har yanzu bai kara aure ba, wlh basabida mutuwan matanshi bane ba, matsalan haukanshi yasa babu wacce ta yarda ta aureshi” zai cigaba da magana ganin Arif na tahowa wajensu yasa yay shiru yamike tsaye yana kakkabe rigan jikinshi.
EPISODE 1️⃣1️⃣




Jama’a I am back! Wannan littafin nawa zaku sameshi a all my social media platforms 💃 idan kuma kuna bina a Instagram ko Tiktok su akodayaushe zai kasance sun wuce yan WhatsApp da page biyu💃💃

Ku danna link dinnan dan following dina a Instagram;
https://www.instagram.com/p/CnmsOO8I0XL/?igshid=MDJmNzVkMjY=


Ku danna wannan link din dan following dina a TIKTOK;

https://vm.tiktok.com/ZMYekGsQV/
DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JINKAI



Hannunta Baba yakama cikeda damuwan dazaka iya gani kwance kan fuskanshi yace “Gwaggo dan Allah ki zauna kiyi shiru maza suyi magana, haba mana Gwaggo” Abdulhadi shima cikeda damuwan yace “dan Allah Gwaggo, dan Allah” cikeda bacinrai Gwaggo tace “aini banmasan kamilin mutun bane haka ba babba kuma, nadauka irin yaran nanne dake tashen balaga masu kudi da rawan kai amman wannan kalleshi nutsaste kamili dashi” hannunta da Baba keja alamun ta zauna yasa ta zauna kan kujeran tace “nayi shiru yanzu amman wlh idan baku karbanma jikata hakkinta ba wlh zan bude bakina ehe” ta zauna tana goge kwalla, dan murmushi Musty yayi yataho wajensu anatse yace “dudda nasan kowa hankalinsa atashi yake gaisuwan musulinci wajibi ne dan haka Assalamu Alaykum” atare dukansu su Baba suka amsa, Musty yace “nasan meke tafe daku amman dan Allah alfarma nake nema inaso kafin ku yanke hukunci kokuyi wani abu zan muku bayanin komi dakuma asalin nuna muku video CCTV camera dake nan akowani lungu da saku na company mu” gyadamishi kai su Baba sukayi alamun tom, yace “ni sunana Mustapha nine babban abokin Imran gashichan aboki nane tun muna yara yan kanana” yanuna Abee daya maida kanshi kasa dukansu suka kalli Abee, Musty yace “ga kannenshi chan Hamza da Ibrahim wayan nan kuma abokanenshi ne, Imrana nada yara hudu, biyu sun rasu tareda matarshi da akazo har gida aka kashe” ahankali su Baffa sukace “Allah musu rahama” Musty yace “sai biyu yanzu keraye, namijin nada shekaru 22, macen 21, nasan kuna mamaki maisa nake fadamuku haka inaso kusan waye Imran ne, bawai sabida Abokina bane, tunda nake bantaba ganin mutum mai kiyaye dokokin Allah kaman Imran ba tun yana kankanin shi mutum ne kamili nutsastse mai amana, abinda kuma yafaru tsakaninshi da yarku was nothing daya wuce kaddara kokuma nace samin akasi akayi wannan shine kawai abinda zance bari na kunna muku CCTV camera footage na ranan dasukazo makarantan kugani Ibrahim zokasa” zuwa Ibraheem yayi gaban babban tV dake office din yamakala flash dinshi saiga video yafara daga inda sukazo makarantan tundaga waje har zuwa ciki da lokacin datace zatai fitsari anajin maganan dudda bada kyau yake fitaba aka nuna inda ta tsaya tana juye juye dan bata gane bayin ba saitabi corridor tahau gudu tana ciro su waya da chocholate har zuwa inda ta bangaje Abee Musty yace “inaso kusaka idanunku akan wan nan mutumin” bayan ta wuce tai kwana aka nuno Abee yayi hanyar office nashi ya murda akulle sai kuma yay hanyar bayi saiga mutumin yafito, saikuma aka shiga lokacin da Lujain tashiga bayin da gudu daganan babu komi kuma sabida babu camera a bayi, saiga Abee shima yazo yashiga, Gwaggo ta gyara zama idanunta kaman zasu fito su sauka kasa, saiga mutumin yazo ya soka waya yana video jin muryan mutane yatafi yabar wajen kusan 2min da shiganshi saiga Lujain tabude kofa ta tsaya sai gashi anyo ball da jakanta da wayan ta tsugunna ta dauka ta goya ta gyara riganta tana waige waige tawuce dahar yanda mutanen nan suka mata kwatace saiga Ibrooo yazo har bayin yashiga rikeda key sannan aka nuna musu duka video Lujain a factory da yanda tai Plate har lokacin databar company su sannan ya katse.



Anatse Musty yace “abu na farko danakeso kugane kuduba lokutan da abin yafaru idan fasikanci ko wani abu sukayi dan wanan lokacin yayi yagama? Sanan akanme yana mai kampanin nan gabaki daya bawai shida wani ba bazai kaita office nashi ba inda akwai daki, bayi dakomi aciki sai nan bayin kowa bayin ma’aikatanshi Iyye? Koma bayin kowa ne zai iya sa security idan wani abu zaiyi yace kar wanda yazo banda haka kuma bayin maza ne ita meya kaita bayin maza dudda nasan yaran makaranta babu abinda waya baya sasu suyi tunda harta bugeshi batama tsaya ta kalleshi ba balle bada hakuri, abu na karshe video dakuke gani idan kunada wayanda sukasan computer zasu iya gayamuku cewa anyi editing dinshi da yanda kofan ke jijjiga da muryan karan datakeyi duka kari ne, saikuma shi wanan mutum dakukaga yay video yaturama abokina messege kan yanaso abashi miliyan dari da kampanin nan koyayi releasing video shi yana tarayya da wata shi yasan baiyi abu hakaba yay blocking kaman yanda kukaji abin nan kwatsam haka muma muka jishi kwatsam, dan Allah dudda dai babu abinda kaddarace bayasawa amman babu amfanin cewa wannan keda laifi ko wanchan keda laifi, munsan sunan diyarku yabaci haka shima nashi yabaci amman dan Allah kuyakuri, dan Allah abu baiyi dadi ba ko kadan” binsu Baba Gwaggo tayi da idanu daya bayan daya kowa jikinshi yay sanyi dan babu karya amaganan su bawai wanan ba dukansu sun kalli Abee baiyi kama da wanda zai aikata hakaba dan zai iya haifan Lujain dinma kuma itama tafadi abinda yakaita bayin tun kafinma suji bakin na mutanen nan, tsaf abinda tafadi shi suka gani a video, babu atom of lie aciki, kumama idan akace za’ayi blame yarsu ce taje bayin maza ita takai kafanta, this is just a common mistake da kowa can make ganin yanda sukai shiru babu wanda ya furta abu yasa cikin kumfan baki Gwaggo tace “ohhh barakuce komi ba”? Dasauri Baba yace “Gwaggo dan Allah kiyi shiru kitashi mutafi gida kawai”. ”mtswwwwww” Gwaggo taja wani mugun tsaki ta mike tsaye batai wata wata ba ta jaye gyalenta data lullube Lujain dashi idanunta sunyi jajir fuskanta yay jaaaa sabida kuka jikinta dabare da jirwajen drinks fuskanta har kyallin dankon drinks yake tana kuka sosai tana wani kalan ajiyan zuciya tarike jikin kayanta gam da hannayen ta data dunkule kowa yabita da kallo adakin banda Abee da kanshi ke kasa, duk wani mai imani da zuciya yakalli Lujain saiyaji jikinshi yay sanyi, Gwaggo na rike da gyalen ta taka zuwa gaban table din da Abee ke zaune cikin ihu tace “kawani sauke kai kasa kaman sabon ango kalli jikana nace, dago kanta ta kalleta” ahankali Abee yadaga kanshi yadan kalli Gwaggo sannan gently yakalli direction din datake nunamai gabanshi na faduwa sauke idanunshi dasukai jaa yayi kan Lujain dake kuka sosai idanunta akasa yay shiru danji yayi zuciyanshi tai wani iri, komawa Gwaggo tayi wajen Baba ganin yana kallon Lujain din datace ta fizge paper da aka bama Lujain amakaranta tadawo ta ijiye gaban Abee tace “kaga yanda akama jikata wanka da lemu tundaga ka har kafa banda haka makarantan suka bamu takarda waisun koreta sabida fasika ce mugun iri zata bata musu sauran dalibai” fashewa Gwaggo tayi da kuka sosai daidai nan ta durkushe awajen ahankali Abee yasauke kanshi ganin yanda tsohuwar da akalla zata girmi Hajiyanshi da yan shekaru na kuka sosai agabanshi, Baba da Abdulhadi ne sukazo wajen da saurinsu zasu dagata tace “wlh kuka tabani zan daga muku nono awajen nan ku kayaleni kawai” tai maganan tana tashi takalli Abee da kanshi ke kasa sannan takalli Musty tace “kaga yarinyar nan dakake gani haka marainiya ce uwarta na nakuda kanta haifeta ta mutu agurguje akai operation aka cirota sabida wai tasha ruwan cikin wanda yamutu yarinyan nan dakuke gani saida tai kusan shekaru biyu acikin kwalban asibiti ni ke biyan komi ubanta wannan din nan dakuka gani” tanuna Baba dashima yasauke kanshi kasa tace “shi baida kudin biyan kudin kwalba duba sha biyar duk ranan duniya acirota daga kwalban wai mutafi gida, likita kuma yace ana cirota baifi tai awa ashirin da hudu ba zata mutu, mijina babansu mai kudin kauye ne daya mutu inada gado kap na saida gidaje na manya manya a binni guda hudu da shanaye na kauye haka na biya dubu sha biyar biyar na shekara biyu cur kafin acirota, nine komi na diyar nan tundaga zama a asibiti, abincinta, kayan sawanta da rainonta da komi ma, koda aka bani ita haka muka dawo gida yau lafiya gobe ciwo ko shigowa bayayi yadubata dan yanada wasu yaran lafiyayyu marasa ciwo, nikuma na nunamai zan iyama jikata mai ciwo gata tamafisu jin dadin duniya, saida yarinyar nan takai shekaru bakwai aduniya tafara makaranta” Gwaggo tashare idanu dan hawayen sinki tsayawa tace “bakuga yanzu tana shatara a SS2 ba bayan su Samira suna shekaru sha shidda sun zana jarabawan kare sakadire, amman ita har yanzu bata gamaba sabida ciwo, ni nasan wahalan danayi akan jikata nasan gumi rashin bacci rashin sukuni danasha akanta, har yau har gobe tunda tazo duniya bantaba baccin dare bantashi ba saita tadani, yau awayi gari sunanta yabaci kuce nai shiru koda akace zata mutu ban hakura akanta ba yanzu ne da lafiyanta kalau zan hakura nai shiru akanta wlh wlh Billahillazi La’ilaha Illahuwa bazata yuba ko laifinta ne ko laifinshi ne nidai nasan bakuyi fasikanci ba dan bangani alamu a jikinta ranan ina tareda ita data dawo daga makarantan ai kaima bakai kama da Babba mai lalata yaraba dan haka idan kunason zaman lpy abu dayan zan gayamaka shine ka auri jikata! Ka auri dan baran iya da raina da lafiya na inaji ina gani sunan jikata yabaci ba, tun yanzu a makarantan su kadai an mata wanka haka da koro uwa wacce aka kamata dumu dumu tana zina, ahanamini yarinya fita titi gudun kar adinga nunata wlh baran yarda ba, hanya dayace shine ka auri jikata!”



Jama’a I am back! Wannan littafin nawa zaku sameshi a all my social media platforms 💃 idan kuma kuna bina a Instagram ko Tiktok su akodayaushe zai kasance sun wuce yan WhatsApp da page biyu💃💃

Ku danna link dinnan dan following dina a Instagram;
https://www.instagram.com/p/CnmsOO8I0XL/?igshid=MDJmNzVkMjY=


Ku danna wannan link din dan following dina a TIKTOK;

https://vm.tiktok.com/ZMYekGsQV/
DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JINKAI
Jama’a I am back! Wannan littafin nawa zaku sameshi a all my social media platforms 💃 idan kuma kuna bina a Instagram ko Tiktok su akodayaushe zai kasance sun wuce yan WhatsApp da page biyu💃💃

Ku danna link dinnan dan following dina a Instagram;
https://www.instagram.com/p/CnmsOO8I0XL/?igshid=MDJmNzVkMjY=


Ku danna wannan link din dan following dina a TIKTOK;

https://vm.tiktok.com/ZMYekGsQV/
DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JINKAI


EPISODE 1️⃣2️⃣



Kowa na dakin hatta Lujain din dake kuka sosai dashi kanshi Abee saida yadago kanshi yakalli Gwaggo jin abinda tafadi, cikin tsantsan nuna seriousness Gwaggo tace “eh haka nafadi, nace saika auri jikata! Duk abinda babba ya hango karami bazai hango ba, wannan video dakuka nunamin kokun watsashi aduniya mutane ba yarda zasuyi ba bazai wankemin jikata ba, hanya daya zai wanke jikata tastas shine ace kaidin mijinta ne da aure tsakaninku, daga masu gulma dashi usulin algugumi dan wutan jahannama daya yada video dana tabbata baku ganshi ba haryau saisuji kunya kaga ko banza yay aikin banza, shi bazai sami miliyan darin ba shibai samu kampanin ba” hannunta Baba yakama zaiyi magana Gwaggo ta fizge hannunta idanunta sunyi jajir tace “wlh wlh duk wanda yace saija dani cikinku saina tsine mishi albarka ubanme zaka gayamin lokacin dazata mutu ma baka tsaya mata ba yaune da aka kirata da fasika zaka tsaya mata? Nine komin Lujain, nine uwarta, nine ubanta, nine kakanta, kamin shiru kawai, wlh wlh saiya aureta akan wani dalili zaija sunan diyata ya baci kuma bazaiyi komi ya wanketa ba, wlh saiya aureta inba hakaba wlh wlh sai hukuma tarabamu, marainiyan yarinya na eh ku jibeta fa abin tausayi ubanta bai damu da ita ba sabida yaga batada mahaifiya, inda yau mahaifiyarta na raye Kunsan kalan tashin hankalin dazata shiga kuwa? Bayan kunsan rayuwa yakoma yanzu iskanci ado ne wajen namiji mace ce rayuwanta zai baci har abada, yanzu awannan video banda bayanshi anga fuskanshi eh? Yar yarinyar nan dai akaga fuskanta har akaga tana gyara riga, idanba aurenta yayi ba koya wanketa wazai auri Lujain iyye? Kufadamin wani namiji ne zai aureta? Wasu iyayene zasu bar dansu ya auri yarinyan da video fasikancinta ke yawo a yanar gizo? Shi yanzu bashi kwana biyu anmanta dashi itako fa? Namiji mutane barasu iya taranka ma itako Yar yarinya mace halama saidai tadaina fita danta fita tareta za’ayi amata duka a titi, yakukeso tayi? Matar ubanta kuma dama ba sonta takeba kaga gwara ka aureta naga kanada hankali kanada yara dasunma girmeta zaka rikemin ita amana koyau na mutu banda nadama dama kullum tunanina wazan aura mata da hankalina zai natsu dashi ashe kai Allah zai kawo mata amman ta wannan kaddaran” Gwaggo tafashe da kuka muryanta kawai akeji a duka office din ganin yanda take kuka kuma su Baba sun kasa mata magana gudun karta tsine musu yasa ahankali Mustafa yaje inda take tsugunnawa yayi yakamota kaman yakamo mahaifiyarshi hannu yasamata a fuska yana goge hawayen datake yace “dan Allah Gwaggo kiyakuri kidena kukan nan dan Allah sabida ni” ahankali tahadiye kukan tana kallonshi cikeda lallashi yace “Gwaggo kinga nan office neko wannan matsalan kuma matsala ce daya kamata atattauna agida kibamu address din gidanku anjima da daddare namiki alkawari dukanmu shima harda iyayenshi zamuzo sai ayi magana da kyau Gwaggo kinji Gwaggo amman yanzu kutafi, itama ku kaita gida tacire kayan nan kar wani abun yasameta maganganun nan da ake agabanta bai dace ba, kuma babu kyau yanda kike kuka agabanta, kece karfinta, kobaki hakura kitafi dan kowaba kiyi dan ita naga yanda kike sonta” juyawa Gwaggo tayi takalli Lujain dake kuka sosai har lokacin taji barata iya musuba tace “gidan mu na nan kwanan tipa a Gwarimpa idan kun shigo gida na biyar mai gate mai ruwan goro” anatse Musty yace “zamuzo anjima da daddare” tashi tayi tadauki gyalenta dake kasa taje wajen Lujain ta lullubeta dashi ta kama hannunta tadagata tace “muje Allah natare dake, nima ina tareda ke” su Baffa duk suka tashi, Musty yace “kaisu ta back door bata gaba ba sabida reporters” binsu su Ibro da Hamza sukayi dan kaisu sannan ahankali Musty yazauna tareda sauke wani ajiyan zuciya yana kallon Abee, Harun yace “wlh wlh idan aka kamo yaron nan I will make sure yay rotting at the worse Nigeria prison” Abdul yace “the guy is evil” daidai nan wayan Musty yashiga ringing ganin Hajiya ne yasa yakalli Abee da kanshi ke kasa yace “tashi muje gida Hajiya is calling” batare daya kalleshi ba yana kokarin fara typing yace “ban tashi daga aiki ba sai 4, and this is just 12:54” shiru Musty yayi yana kallonshi Allah kadai yasan yanda yake hurting right now amman bazai taba nunawa ba, ganin bakinciki Abee zai cusamai yasa yajuya yakalli su Harun yace “kumuje” saikuma yajuya afusace yadauki wayan Abee dake kan table yace “shima ka kwace idan ka isa” yawuce yafita fuuu daidai Hajiya na kara kira dauka yayi kafinma tayi magana yace “Hajiya gani nan zuwa komi yazo dasauki kada kidamu kanki hawan jininki yatashi” katse wayan yayi suna fita suka shiga mota sai gidansu Abdallah da Kausar sun dawo daga makaranta dudda sunada lectures ganin videos dake trending na babansu, Zainab data tafi daga ita har mijinta sun dawo, kofar gidansu yacika kaman anyi mutuwa dayan anguwa babu wanda baya sonshi a anguwan dukansu sun karyata guards na estate dinsu sun hana ko reporter daya ya shiga saida su Musty suka fara gaisawa da mutanen waje sukace shairi akamai sannan suka shiga ciki bayan babban Liman na anguwan wanda yake matsayin ubansu yabisu zuwa cikin gida duk suka zazzauna a falo idanun kausar yay jajir taci kuka harta gaji na Abdallah ma haka amman shi baiyi kuka ba.



Hajiya kafin suyi magana tace “ina yake”? Musty yace “ai kinsan Imran da taurin kai yace aiki yake sai 4 yake tashi daga aiki munbarshi achan danko jawoshi zamuyi da karfi bazai tahoba amman Ibro da Hamza na chan tareda shi karki damu” tagumi Hajiya tayi Anty Binta ta bubbuga mata baya yace “dan Allah Hajiya kada kidamu kanki” anatse Hajiya tace “Meya faru Musty”? Ahankali yabasu labarin daga farko har karshe tsaf da yanda iyayen yarinyar sukazo da abinda sukayi kowa yay tsit adakin na kusan minti biyar sannan Hajiya tai breaking shiru takalli Liman tace “Liman kaine kake matsayin mahaifin yaron nan yakake ganin za’ayi”? Ahankali Liman yace “shi aure rufin asiri ne kuma sutura ne ga mumini, gabaki dayan mu nan munsan Imran bazai taba iya aikata wannan abuba abinda nakeso kuduba anan shine ayar dake tattare da abin nan inhar Allah ya shiryamai wannan kaddaran

Please Login or Register in order to submit comment