Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ya shigo dakin ya sameta dasu Ammi ya zauna gefenta ya kalleta cikin tausayawa yace ya qafar ta fara sakewa ko ? ta kalleshi cikin yanayi anya kuwa kana tausayamin ta tura baki ta murxa ido alamar zata fara sabon nata cikin kukun ta kalli Ammi tace Ayyah Ammi Dan Allah ki sashi ya kaini a cire cikin ta kamo hannun Umma tace Umma kuyi mishi mgn ya kaini a cire cikin kar ya kasheni ko ya maidani gurguwa Ammi ta kalleta cikin tausayawa tace kiyi haquri fati ai in an cire cikin kema zaki cutu gashi baiyi qwariba kuma ma ai komai da lokacinsa ta daqo ta kalli Ammin ta fada jikinshi tace toh Ammi kice ya kaini gun bappana ta fada cikin kuka tace Ammi tun da nazo garinanfa sau daya naga bappana randa yazo daurin aurensu Nazir inna takam ban sake ganintaba kusan shekara 5 ban gantaba Hammana ka kaini Dan Allah kar Na mutu ban sake ganintaba
Cikin kulawa Ammi da Umma sukace zakije Fati zai kaiki kinji ko kontar da hankalinki suka fita suka barsu
a parlor Ammi da Umma suka yiwa maimartaba bayanin komai cikin mmk yace Amman dai Hassan halinshi sai Allah ace kana zaune da yarinya ka hanata ganin iyayenta kai kuma kamar Dan yaye kullum sai kazo gun naka iyayen a take ya bada damar su shirya gobe jumma suje da kanshi ya shiga dakin ya samesu tana kwance a gefe shiko ya riqe kai da hannu bibbiyu ya kallesu da kyau yace Fateema ki dina kuku Hassan ka shirya gobe zaka kaita garinsu aiko cikin jin dadi ta rinqa godiya wani farin ciki ya rufeta Abban Na fita ta Dan ja qafar da qarfi ta matso gunsa tace Hamma tashi ka tayani shiri wancan babbar jakar zaka miqomin insa ka yana ya kalleta da kyau ganin yadda lokaci daya ta koma cikin farin ciki shima sai yaji sanyi a ransa ya jawota ya rinqa tsokanarta.
Garin Ardo yabani gari mai dadi gari mai tarin albarkatu d ni,imomi garin Fulani da ma noma garin dake qushe cikin qoramai da itatuwa masu dumbin tarihi a garin buba yero tun da suka iso kwadan ta hanqo tsaunukan dake yiwa garinsu katanga da babban titinnan da zai kaika dadin kowa isakar wurin mai sanyi ta fara ratsa jikinta ta lumshe idanta ta rinqa ajiyar zuciya tana shaqar qamshi. Furannin tsurran wurin ta maida kanta ta jingina da kujarar motar dai dai lokacin Hassan ya Dan karya kona ya dauki yar siririyar hanyarnan da zata sadasu da wuro yabani a daidai lokacin ta bude idanta ta zubawa lambu kam dake zagaye dadu ido cikin mmkin gani wani irin canji da wurin ya samu hanyace lafiyeyyiya ke kwance daga gefe kuma anyi burtali Na zamani gun da dabbbobi zasu bi can Dan gefe kuma qoraman ne aka sarrafasu cikin hikima akai kwami kwami inda dabbobin zasu sha ruwa ga can wani faffadan fili kuma da aka zagayeshi da woya mai raga raga inda dabbobin suke rayuwa ga wasu abubuwa kuma Na tatsar nono cikin sauqi
kai saiwa lissafin yadda garin yabani ya zama babban aikine ita dai ido kawai ta ware har suka isa farfajiyar qofar gidansu abin mmk a nan yake cikin mmk ta kalli Hassan dake ta murmushi ganita cikin farin ciki ga wani ya nayi da yake tunawa Na zamansa a nan gun tsawon wani lokacin da ya shude abin ya rinqa dawomar kamar a film duk ran jumma,a Hassan a garin yabani yake sallan jumma,a anan yake cin abinci Amman duk zuwan da yake bai tabajin shauqiba sai yau da yazo da Habibatinshi tace Yaya ko dai mundanyi batan hanyane ya kalleta cikin ido da shauqi ya shafa cikinta da ya fito ras a jikinta yace Fateema kin taba ganin inda da ya manta gidan ma haifinshi tace a a yace toh ke dai biyoni ya bude qofa ta fito ya zagaya ya bude mata gefenta tana sako qafa bappanta Na fitowa daga wani wuri da yafi kama da asibiti mai kyau Na zamani ganin Hassan ya nufoshi da fara,a yace a a Dan Bappa kana hanya kenan yau baka iso da wuriba duk bai lura da Fateema dake ta dingisowa ba ta samu ta qarisa gunsu Bappa yaci gaba da cewa muje ka karya nasan ba abinda kaci ya juya kenan ya hanqo Fateema cikin yanayin haiba da ribar aure a jikinta gonin Sha,awa da tausayi cikin mmk da tsantsar farin ciki ya iso gareta yace mamana Allah sarki mamana ya Sa hannu ya karbi jakarta cikin qaunar yarsa yace Alhamdulillah mamana yau innarki zata samu farin ciki yau zataji saukin kewarki dake damunta Fateema kam sai hawaye take zubdawa har suka isa cikin gida da farin cikin ya dauko abin zama ya shinfida musu a qarqashin bishiyar manqoro da dabine dake tsakar gidan yana mai kiran inna ta fito daga cikin kitchen tana riqe da aqoshi da sabon faifayi rufe dashi aiko ganin yarta guda daya tilo yau kam inna farin cikinta yaqi boyuwa da sauri ta iso gun ta tallabo Fateema ta zauna ta kalleta cikin tsatsar qauna tace mamana kenake gani ba mafarkiba tai dry ta fada jikinta cikin jin dadi tace inna kema kinyi kewata Amman shine kika qi zuwa ki ganni har tsawon lokacin nan bakijin lbr Na Bappa yai dry yace ai mukam kullum muna jin lbrinki kullum jumma,a sai mai gidanki yazo garin nan anan mike sallan jumma,a tare kinga yadda ya gyara mana rugarmu gashi har asibiti da masallacin jumma,a ya gina mana Hassan yai dry yace Bappa kenan Na gina ko ka gina tunda kaqi barina nai da kudina kawai saida kasa naka inna tace ai ka kyautamin Dan Bappa yau ka kawomin mamana Bappa da kansa ya rinka kawo musu abinci Dan dama sun San Hassan zai zo komai an dafa mai abin da yakeso inna kam Tamkar zata hafiye yarta takeji
Haqiqa Fateema tayi mmkin sabo irin Na Bappa da Hassan sun zama uba da daa sat komai Na duniya sai sun shawarci juna duk yanzu Hassan ba jin kai din sai alkunya da qauna Bappa yace innar Fateema tashi mubasu gu su karya ta miqe suka tf Fateema ta rinqa bubbude kwanukan abinci ba abinda babu a kwashi cike yake da zabbi Inna tamusu irin gashi sunan Na mutan daban Fulani ga daya kwanon kuma tuqeqqiyar shinka fashe da miyar danyar kubewa tasha man shanu ga naman rago mai zaqi da taushi ya daddage a ciki sai qoriyar damemmen nono da fura Dan asali gangariya sai daya koriyar kuma madaran shanunne tafashshe sai daya koryan kuma fruits ne cike sai kwanon Sha da yake cike da run sanyi da yake fitowa ta cikin dutsen lammunsu daga dai kwariyar kuma kunun nonon shanune da garin danyar shinkafa fari tas Hassan da kanshi ya samusu tare sukaci tai mmkin mijinta sosai yadda ya zage yake cin abincin Ya dauki damemmen nonon da ludeyin duma mai kyau yasha zane ya rinqa Sha yana lumshe ido ta kalleshi tace dama kana cin abinci cikin son ran kane yace kamar Yaya tace toh gani nai sai mama tana saka dole ya danyi dry yace ai abinci Ammi Na da ummana da innata bana haufi a kai sukai dry
dama kullum in yazo sai sunje lambu tare da Bappa su kuma yi tatsar nono tare haka yauwa suka shirya tafiya aiko itama tace zata Bappa zai hanata yace ai bazaki iya tafiyarba Hassan yace abarta zasuje da mota haka sukaje yai ta daukarsu pictures cikin lambun sai garfe 1 suka dawo sukai shiri suka tf masallaci itako da innarta sukai ta hirar yaushe gamo biyar dai dai suna ta hiratsu ya kalleta yace Fateema ki shirya mu tafi ko kinga yamma tayi ai a take sai hawaye tace Dan Allah Hammana ka barni ni sai Na huta yai shiru yana kallonta Bappa yace a a mamana tashi kibi mijinki kinji ko kinsan bana son taurin kai kibi umurnin mijinki Hassan ya kalleta yace aima yanxu bazaki kuma dadewa baki zoba inkin aihu dai zan kawoki kuma innama zataje ita dai sai hawaya badon tasoba suka tursasata ta bishi Bappa yasa su gaini suka dauko jarakunan man shanu da qworen qwon zabbi da Na nono sai zabbin aka loda musu a mota ya hada mata mgnin qafar ya bata tana kuka suka tafi haka ta rinqa rusa mai kuka a mota yai ta lallashi taki har suka isa cikin gombe kai tsaye sahara hotel ya wuce da ita daukarta cidak yayi ya shige da ita har kan gado
Ta rinqa tureshi ya yajawota ya Dan matseta tai qara ya shafa cikinta ya lonqobar da kai cikin shogoba kamar yaro yace ayyah Habibati yau kadai a taimakamin tunda yau baby Na ta sakar miki qafa a tai maka a dagawa Abbanta qafa shima ya Dan samu nitsuwa da Sa,ida ya kara jawota jikinshi ya fara kiss inta ta rinqa tureshi cikin shogoba da fushi tace ni dai ka barni Na gaji ya Dan kwanto jikinta yace plzz my Habibati wlh ina cikin matsi ki taimaka min Na tuba tace toh ni da qaton cikinnan ya zanmaka ya danyi dry yace ni dai bani ixini kawai ni zansan yadda zanyi Na samu abina ya jawota ya jinginar da ita jikin gado cikin hikima ya samu gamsu ya rinqa sabbatu sai qarfe 11 suka isa gida aka shigar musu da tsarabarsu su Ammi da Umma sukai ta gdy ya bawa Abba ma saqonsa shima yaita gdy
Yanzu dai ciki ya kai aihuwa ko yau ko gobe kuma qafa ta sake tada tsiyarta ba dama..
```Sai dai Fatan. Allahu rabbi ya sauki dukkan yan uwa musulmai lfy ya bawa kowa gajerar naquda```
By garkuwan fulani
[4/12, 1:52 PM] Garkuwa Ali Aysha: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
Y'ar Fulani part 51 Na Aysha Ali Garkuwa
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
Yau dai ta samu qafar da Dan sauqi har ta fito babban parlor ana Dan taba hira da ita Zubaida Na zaune daga gefenta duk mgnar da suke akan shirye shiryen auren zubai danne da Na Amir tun dazu Hassan ya shigo bayan gaisawa da sukayi bai sake cewa komai ba sai dai ya qurawa matarsa ido in ta kalleshi ya danyi murmushi ya murza manyan idanunshi da sukayi ja suka qanaqce sai ya Dan kwanta jikin kujera ya shafa kwanceccen sajenshi ya Dan leshi lips
inshi sarai ta gane damuwarsa sai dai tayi kamar bata ganeba can ya danyi miqa da 😵 Hussain ya kalleshi cikin wasa yace kai doctor naga dai ba aikin dare kaiba jiya da zaka xo kai ta mana 😵 ya dan harareshi yace to sarkin Sa ido can dai dabara ta fado mai ya dauki phone enshi ya tura mata message kamar haka (ayyah Habibati ban sanki da hakaba bafa plzz ki tausa yawa Hammanki wlh Na kasa daurewa Na kasa sarrafa kaina ki ji tausayin mijinki kar nashiga wani hali ) ta karanta ta kalleshi ta share ya sake tura mata wani sai taqi karan tawama can dai sai ya miqe yace toh nikam sai da safe Dan ina da aikin safe ya kalleta ya danyi dry mugunta yace Fateema kizo muje ki bani pakalana Dan ina da buqatarsa yanxu aikinshi zanje nai ya qarisa mgn yana tsareta da ido tace ni kuma bata qarisaba ya katseta taso sauri nake Umma tace jeki bashi sai ki kwanta ki huta haka ta tashi da qyar take takawa tana shiga dakin
Ya jawota jikinshi ya mannamata kiss a lips enta ta Dan tureshi ta zauna bakin gado ya maso a hankali ya kai bakinshi cikin kunnenta ya rinqa huramata iska yana Dan mgn cikin rarrashi ayyah Habibati kiyi haquri wlh Na kasa sarrafa kai nane ki tausa yamin wata 2 fa ai nayi haquri a haka dai yaita mata zaqin baki har ya sameta ya kauda buqatarsa shi ya taimaka mata tai wonka ya shiryata sab sannan ya fita mama ta shigo Dan tunda cikin ya tsufa ta dawo gunta.. sun danyi hira da mama har mama tai bacci itama ta kwanta
Tana Sa kanta kan pillow taji wani irin Abu ya tsikari ququnta da qafafunta ta Dan cije baki ta kwanta ajima kadan taji abin ya sake tsikarinta sai kuma taji ya Dan lafa har taji wani irin bacci mai dadi inko in ya tsikareta a firgice zata farka haka tai ta fama har zuwa 4:Am sai lkcin kuma ta rinqa jin wani irin fitsari da baya qarewa taje yanxu tana fitowa zata sakeji anyi kiran Assalatu ta shiga Dan tai fitsarin ta kuma yi alwala sai taga Dan jini kadan a jikinta a take taji wani irin sarawa da ququnta da cinyarta keyi ga wani irin amai da ya taho mata cikin bacci mama taji kakarinta da sauri ta shiga toilet en ta taddata a ronqofe sai amai take da qyar tasamu ya Dan lfa mama tai sallah itako tana zaune tana ta faman jin azaba sai zufa keta keto mata tako ina mama Na idarwa ganin ta cikin yanayin naquda gadan gadan yasa ta fita da sauri taje ta sheidawa su Umma aiko a take suka nufi hospital Amir ke jansu sai mama da Umma tana tsakiyatsu Ammi kuma ta kira Hassan da su nazir ta sheida musu
A asibitin tun tuni doctors ke ta zirya a kanta ga naquda kama kama Amman aihuwa ta faskara ga aman da yaqi tsayawa ciwon qugu da qafafu kuma abin yaci tura Hassan kam al,amarin ya zarta tunaninsa
Yanxu qarfe 4:pm Amman har yanxu bata aihuba
Dr Halima ta fito cikin yanayin tausayi tace a gsky dr Hassan sai anyiwa dr Fateema c,s, Dan yanxu kam ga aihuwa tazo ita kuma qarfinta ya qare bata iya nishi gashi cikin ya fara haurawa Saman qirjinta Sa hannunka kawai muke so cikin rudani ya rinqa girgiza kanshi yana cewa a a insha Allahu baza a mata c,s, ba zata aihu da kanta gaba daya ya fita haiyacinsa ya rame lkci daya ya kasa koda shan ruwane idanshi yayi zuru zuru Dan firgita da tsoron halin da Habibatinshi zata kasance Umma ta kalleshi tace haba Hassan ai ko ba komai ma tausaya mata qarfinta ya qare kasa hannu a ceci rayuwarta insha Allahu ba abin da zai sameta Hussain ya karbi takaddar yada hannu yace dr Halima muje muyi aikinmu suka juya suka tf gaba daya sun gama shirin yimata aikin saura su fara kawai Hassan ya shiga tana ganinshi ta kamo hannunshi cikin murza kai tace Hammana kaga abin da nake gayamaka ko cikinan zai kasheni bazan iya haifarshiba. da sauri ya rufe bakinta yace daina fadin haka insha Allahu zaki aihu lfy ba abinda zai sameki inaji ajikina ba abinda zai rabamu ta qara matse hannunshi tace Hamma a kiramin bappana xai bata amsa Dr Halima ta katsesu da cewan ya gyara za amata allurar da zai kashe zafi za,afara aikin ya qara sunkuyowa kanta daidai lkcin taji wani irin azabar da bata taba jiba sai amai ba qaqqautawa duk ta fita haiyacinta gaba daya doctors en sukayi kanta cikin azaba taji wani irin nishi ta rinqa nishi ta qanqame Hassan ta mai wani irin riko su gaba daya basu lura da nishin da takeba sai jin kukan baby sukayi
Gaba daya suka xuba mata ido cikin mmk shi kuma Hassan tuni ya koma qasanta ya dauko baby ya macece fara tas bata da wani girma ya yanke cibiya ya miqawa Dr Halima ta fara gyara yar bayan baifi minti 15 sai ko amai kam ya dawo sabo fil yi take tana nishi sai ga wani Dan ta maida kanta kan pillow tana maida numfashi gaba daya suka dauki hamdala Hussain shine ya fita ya yiwa su Umma albishir kan kace kobo zuriyar saraki sun cika da farin ciki Amir ya kira Ammi ya gaya mata sai Alhamdulillah take ta fadi tai alwala tai nfl ta godewa rabbi mai kyau ta da qari a can banqaren kuma har yaxu mahaifa taqi samuwa duk sunyi iya yinsu abin yaci tura Hassan kam gaba daya hankalinshi ya tashi Sam ko yaran bai samu damar ganinsuba duk ta fara birki cewa Dan sai wani sabon ciwo ya taso dr Halima ta maso Dan tayi dabarunsu Na likitoci ta fidda mahaifar tana dan tabata ta dago da sauri tace dr yarima harfa yanxu akwai wani babyn a cikinta sabon naquda take. gaba daya sun cika da mmk saiko ga naguda kam gadan gadan amai sabo ya taso yi take ba qaqqautawa ga baby ta kawo kai ita kuma uwa qarfi ya qare sai ta fara nishi sai tace Hamma nagaji bazan iyaba ya koma ta kanta ya rinqa shafa kanta dr Halima kuma Na shirn karbar baby cikin qarfafa mata guiwa suke cewa kiyi nishi ki daure sai ta danyi sai kuma ta maida kai tace bazan iyaba can ta Dan qara nishin har kan baby ya fito gaba daya sai kuma idanunta sukayi luuu ta maida kai cikin gajiya tace Hamma Ku ciremin xai kasheni ya Dan kalleta cikin kidima a ransa yace dole sai Na yimiki abinda baba so yasa Dan babbar yatsarsa ya danna bayan kunneta sai ga wata atishawa mai qarfi baby da mahaifar duk tare suka fado dr Halima tace Alhamudulallah komai yayi normal Hassan yace a a Halima ai ita a sume take bani ruwa da sauri ya fesa mata ruwan ta farfado cikin nitsuwa cikin sauki aka gyara yaran da mahaifiyarsu aka kaisu inda zasu huta Hassan kam yaga gata da soyeyya agun yan uwansu farin cikin su bai misaltuwa gaba daya ma,aikatan asibitin sukaita tururuwar mishi barka a Daren sarki dasu waziri suka xo Ammi ma ta zo duk yan uwa sunyi hamdala ita kam maijego bacci gajiya kawai take da yan tagwayenta bata san abinda akeba
Jinjinata a gareki qaunari sadidan a raina Anty Hafsat matar sherif.
By garkuwan Fulani
[4/12, 1:52 PM] Garkuwa Ali Aysha: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
Y'ar Fulani part 52 Na Aysha Ali Garkuwa
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
D'akin cike yake da y'an uwa da abokan arziqi da sukazo musu murnar samun qaruwa da ganin yan 3 Hassan dake zaune a gefenta runqume da ya macen daya dan kuma Umma Na riqe dashi sai daya da suka liqawa Fateema tana tirjewa ita a barta ta huta sai kusan karfe 10 aka dan watse saura Hassan ya bawa Amir key en motarsa yace yaje ya dauko mai wata yar roba mai cike da dabino mai kyau yaje ya dauko Hassan ya karba ya miqaqa Fateema yana klonta da qauna mai zurfi yace karbi tauna duk ki basu ruwan a bakinsu ta zura mai ido tace ni fa bacci nakeji kai ka basu mana....Umma tace a a Fateema karbi ki bawa yayanki hakan yana da fa,ida sosai kece uwa anfi bukatar ki basu domin bakin uwa kuma bayarwan yana da amfani Dan da izin Allah da zai kasance mai jin mgnar uwa hakazali ka likitocin zamani sunyi ittifaqi duk abinci da Dan Adam keci sai yabi jini yabi jijiya kafin yaje ga qoqolwa Amman shi dabino kai tsaya qoqolwa yake tafiya kuma yanasa yara kaifin basira haqiqa da yawa iyaye suna sakaci da bama jarirensu ruwan dabino da zasu tauna da bakinsu.
Hassan yace gsky ne Umma ya miqamata ta karba ta tauna zata bawa Dan da yake hannuta din yace a a da babbar za,a fara haka kuma akayi duk ta basu Umma ta kalleta tace Fateema ki basu mama su fara tsotso Dan zai taimaka wurin jawo ruwa ta dago da sauri da zare 😳 tace tab Umma ni dai inajin tsoro Hassan yace babbar mgn me kike sonyi kenan tace a basu madara nifa bazan iya basu ba sunyi yawa
Abu kamar wasa taqi basu nono har aka sallamesu suka koma gida nanma anyi taqi fir innartama tazo Bappa ma yazo yaga yan jikokinshi inna kam tananan an hanata kowa ance ta haqura tai ko kwana 5 inyaso ta koma tunda ba kowa a gida.****
Yau kwanasu 3 Amman har yanxu basu samu nonon mahaifiyarsuba sai suita kuka sai dai a basu ruwan dumi in innarta tai kanta da fada sai su Umma su hanata a cewasu zata basu in nonunan suka isheta da nauyi da kukan yaran
Qarfe 4 dai dai su Hussaini da Nazir da Hassan en suka shigo dakin su samu Umma nata faman rarrashin yara suna ta tsala kuka inna nata fada ita ko tana zaune tai luf a kan gado ta Dan tura bakinta Hussaini ya karbi daya Dan Nazir ma ya karbi dayan shi kuma Hassan ya dauki ya macen sukai ta Dan jijjigasu Amman Sam sunqi shiru Hassan ya kalleta a raunane cikin lallashi yace Dan Allah kiyi haquri ki shayarda yayanki ki gafa yadda suke buqatar mamansu yunwa Na damunsu ta Dan kalleshi tace nifa wlh Hamma tsoro nakeji jiyama da inna tasa Na Dan samata a baki ita da ta fiye rakin wlh ta jamin da qarfi zafi kamar zanyi 😭 inna tace ai kema da haka aka shayarda ke ta fita tana ta fada
maxan kam sun danyi bacci Amman ita macen sai kuka take Hassan ya tashi ya nufi dakin Amminshi ya shiga da slm tana zaune kan sallaya tana riqe da carbi yazo kusa da ita ya zauna runqume da babyn ya gaida Ammi ta kalleshi a nitse tace lfy kuwa meke damunta ya kalleta a raunane yace Ammi mamansu taqi ta basu nono yunwa sukeji Dan Allah Ammi muje ki mata mgn ya qarisa mgn cikin damuwa fuska a raunane ta danyi dry tace kai yaran zamani kai Sam baka jin kunyar yaran toh ai ita Fateema kunyace ke qara sata hakan ya kalli Ammi ya lonqobar da kai yace gsky Ammi bazan yardaba zata cutarmi da yara da kunyarta ta Fulani da mutanen daa ni dai muje ki mata mgn
Ammi tai Dan murmushi tace toh ni meruwana badai Ku kunci abincin ba ya kalleta cikin sauri Dan yau dai Ammi ta nuna shi a matsayin danta mafi soyuwa har tana indai shi yaci ba matsala tanaiwa yayansa wasa yai dry cikin jin dadi yace muje dai Ammina suka futo a tare suna dry a parlor sukaci karo dasu Hassan Hussain ya kwashe da dry yace tab su Ammi manya yau hira ake da Dan fari harda dry Ammi tai sauri harararsa sukuma duk sukai dry
A dakin Ammi tai ta lallaba Fateema har ta yarda tace toh zan basu Amman kadan kadan zasu Sha cikin sauri Hassan yace eh mun yarda sai kuma ta noqe Ammi tace jeki wanke bakin nonon nanma ta noqe cikin fulakun Ammi ta gane kunyarta takeji sai ta fita ta ja musu qofar
Aiko da sauri ya matso gunta ya zuge zip din dake manne a gaban rigarta su 2 ko wanne yana kan saitin nono da kanshi yasa hannunshi ya fito da nonon ya dan kalleta cikin rarrashi yace qyara ki bata bakin nononma a wonke yake ba matsala ta qarbi yar ta Dan talla bota ta Dan sunkuyo ta miqa mata nono itako baby sai neman nonon take tanata raruma ta kasa bata ta kama Dan nonon sunan das dasu ba alamun kwanciya ta kalleshi fuska a shogobe tace Hamma kaga taki karba ko ni zan maida abina ya kalleta ido cikin ido da tsantasr qauna yace kiyi haquri bari Na koya miki ya Dan kara matsota yasa hannunshi ya kamo nono ya samata a baki aiko ta cabke ta fara zuqa dama nono ya ciko tab itako tai dan zillo tana yarfa hannu tace Hamma zafi zata ciremin bakin nono ya Dan hadata da baby ya runqumosu yace sorry my Habibati tinda dai Abbanta bai cire bakin a baya ba toh itama bazata cireba ya fada cikin wasa da zoleya ta rufe idanta Dan kunya haka yasa ta tabasu duka cikin hikima ya kuma yiwa yayansa huduba kuma a ranan sarki ya shedawa Hassan da dukkan yan uwa cewa ran suna za,a nada wa Hassan sarautarsa...........
Taro yayi taro ran sunan kuma ran nadin sarautar yara sunci sunan Abba da Bappa sai Ammi ya macen Aysha Ammin kenan sai Aliyu Hydar sai Bappa abubakar Abii duk yan uwa da abokan arziqi sun xo su Adda Mina mutan daura harda su maitamacy ikon rabbi ga kanawan dabo duk sunzo ga hajiyar SA Fiji itama tazo mutanen garin yabani ma sun zo yara sun sha kyautar

Please Login or Register in order to submit comment