Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

gida zasu koma birni kano sunbar gidan gado kaf gidan tsoron habi suke saboda masifarta bame taba mata danta musammanma jeddah Yar gaban goshinta duka yayanta biyu kacal tahaifa a duniya sai Bari da taitayi daga Jeddah sai kaninta mansur mahaifiyarta macece jarababbiya mara godiyar Allah tun suna adamawa irin matan Nan ne masu bin malamai shiyasa ta mallake mijinta malam jauro bashida wani katabus sai abunda tasashi ganin Allah ya Bata ya me kyau data fara girma saita fara tunanin ita zata zame mata kadara( kunjifa fans ka haifi diya tazama kadara Allah ya kiyayemu)shiyasa tafara koya mata kissa da kisisina tuntana Yar sagaryarta tasaba zuwa shagunan maza suna latseta suna Bata kudi tana kaiwa uwarta kwanci tashi ba wuya taxama budurwa tasamu tagama secondary School dakyar daga Nan tafara yawonta na bin maza dama maza akwai San kyawawa to Jeddah tananfa Allah yay halitta kyaune da ita kamar aljana shiyasa take Jan zarenta San ranta shiyasa take kwasar samari tana hutawa da samari har makwadaiciyar uwartama ta samu abun da takeso ranta kal suci me kyau su sha me kyau suyi wadaka da kudinsu abun yanaywa malam jauro kuna yana cimasa tuwo a kwarya abun yana masifar Bata masa rai Amma anshanyeshi beda bakin magana baya iya cewa komai sai ido duk kokarin dayake akan iyalansa araine yake gun habi wannan rayuwa da yarsa keyi shine bakin cikin yasa masa hawan jini








Kwanci tashi ba wuya har sun shekara biyu da candy Jeddah tayi fice a kafatanin unguwarsu wajen tantiranci ga jarabar mahaifiyarsu malam jauro yayi yayi taida saurayi yay mata aure sunki itada uwarta gashi beda iko dasu ga mansur yazama tataccen Dan iska sai yay wata biyo bezo gidanba wannan bakin cikin shiyay sanadin da jininsa ya Kai dari biyu da hamsin sai da suka barshi ya galabaita sannan habi ta kaishi asibiti saboda su yayan basa Nan sun tafi gantalinsuAna zuwa asibiti kwanansa uku yace ga garin kunan yabar musu duniyar kowa yasha sha aninsa dama jeddah bata gidama kwananta tara saida ta dawo washegari habi mahaifiyarsu tanata rabzar kukan munafinci ta wayance kinga ikon Allah Ashe ko maganin baze shaba mutane suka zuba musu ido jin tana zance way magani bayan kowa yasan daga inda jeddah take saboda mutunci da karamcin malam jauro maxajensu suka barsu suzo mata zaman makoki ba abunda ta bada Wanda za adafa na sadaka sai makota keta dawainiya Amma ba godi bare mun gode wata tace ina tajene taje karbo masa maganine a garinsu adamawa shiya turata Ashe ba rabon su gana itako matar ko shekaran jiya taga wuce warsu a mota adai dai Yan lemo sai Jeddah itama tafara kuka gsky duk iskancinta mutuwar mahaifi ba wasaba tayi kuka harta gaji sai bayan sadakar bakwai Nan Kuma suka balle ba uwa ba ya ko takaba habi Bata tsaya yiba mezataywa takaba ay ita Allah ne ya temaketa ya rabata da kaya yayinda dama mansur yazama fitaccen Dan iskane gagararre higher killers gashi Dan fashi kwace shaye shaye ba abunda bayayi na mugun abu nanfa duniya tabude musu sabuwa idon Jeddah ya kara budewa ta dada goge da bayan bariki akafara bin malamai kawai dai Bata shan komai









Tare sukai makaranta da afra secondary school tun suna makaranta basaji seat dinsu daya halinsu daya kawai ita dai afra ahannun matar uba take uwarta ta mutu shikuma mahaifinta bashida cikakkiyar lafiya baya fita ko ina yayyenta duk anmusu aure shiyasa lalacewar tata tay yawa b Koda suka gama makaranta kansu a hade yake sukaci gaba da tata duniyancinsu kowa yasan sirrin kowa Amma Jeddah tafi afra fitina suna yawonsu club club amma ita afra Bata kwana a waje karkarinta takai sha daya zuwa sha biyu na dare tana gida sbd tana shakkar babanta sosai dan idan tay dare sawa yake a Kira masa yayyenta suzo sunada mata na jaki to Kuma shi baya iya mikewa ba lafiya komai sai anmasa itake masa komai Dan ita matar tasa saitaga dama shiyasa takara samun damar yawonta bame samata ido Dan itama matar ubanta tanada kwadayi dataga tafara wanka zata fara lissafi asiyon kaza a tahon da kaza haka zatayta lissafi itako afra ko ajikinta tunda tasan tana rufa mata asiri babanta besan bin maza takeba yadauka kawai yawon gidan kawayene (kaji shashanci muje zuwa)






A razane suka juya wazasu gani baban rama ne da mado saurayin aduke Wanda za ay musu aure bana sunasan junansu so me tsanani anan mado ya durkushe yafara sharar kwalla duk dauriya irinta mazan ARNAN DAJI hakan besa ya daureba abun yay masa ciwo baban rama ya duka garin Yaya haka tafaru rama tafara kuka tafara magana muna zaune nida aduke mungacin farfesun kwadin datay mana mun ajiyewa tenkwai nata saita rigani wanko hannu bayan ta dawo saina fita Nima saina zaga bayan gida ina fitowa nadinga jin magana sama sama sai nadanyo sanda na labe sainaji yana cewa ina rama bazaki gayan inda takeba saina kasheki badu ya temakeka bansan inda rama tayiba Ni Bata gidannan Sam bazaki fada ba toko zanmiki abunda zanmata amadadinta nayarda kayimun komeye Raina fansane ga Yan uwana meye amfanin rayuwata inaganin Yan uwana cikin wani hali tana kuka take furta masa haka Nan ina labe ina kallo yafara cire kayansa ya juya baya saina fito Ashe aduke taga tahowata tace na koma naki na tsaya saida tahada hannayenta biyu tana rokona sannan na koma dakinka na buya saidayasha yay mankas sannan ya farwa aduke tana ihu yana zabga mata mari ahaka ya farkata farkawa ta rashin mutunci ya yagalgalata bakaramin ta adi yay mataba banjin akwai maganin dazewa aduke aiki harta gyaru takarasa cikin kuka idon mado jage jage da hawaye way waye waye sukai shiru saida baban rama ya daka musu wata mahaukaciyar tsawa ba magana ake mukuba waye da wannan danyen aiki me kikai masa ke rama daya biyoki har gida cikin rishin kuka ban masa komaiba yadade yana neman mu kadaice nakiya saboda shize auri kawata aminiyata bazan iya cin amanartaba yasha tareni a jeji ina guduwa shine ya biyoni har gida a yau besamanba sai yasamu aduke shiru na minti biyar ya gifta adakin inbanda tashin kukan tenkwai da rama da aduke bakajin komai baban rama yay gyaran murya tabbas hayaki baze hakaba tayayama bayan shine da ze aureku rama bayanan yana daure a kurkuku saboda shine cikon mutum na biyar daza a yanka nasan kowaye ya aikata wannan lefin kurufamin asiri kurike alkawarin dakuka daukarmun karku gayawa kowa abunda yasameni karku bari kowa yaji cewar aduke wadda dakyar maganar tata take fita munmuki alkawari bameji fitar maganarma zata iya sawa a hallakamu cewar baban rama way waye kugaymun nifa banganeba cewar mado zan gayama kowaye Amma saikayi alkawarin bawanda zeji wannan batu mubarshi anan iya mu biyar dinnan Ni Kuma zanje dawa na nemowa aduke magani yanzu Inasan aduke har Raina bazan taba Bari wani yajiba Amma aransa ya kudurce sai ya dau fansa ja e ne dan gidan sarki kaho Yay mata wannan aikin kasan aikinsane a razane ya dago abokina ja e yaci Amanata na rantse da gemun kakana saina dau fansa yasa Kai ya fice sunata kwala masa Kira be juyoba sai suka kara rushewa da kuka.






Tofa muje zuwa nice taku maikaunarku akoda yaushe.







*FEEDYN BASH*
[9/11, 22:29] +234 810 679 5647: *?ARNAN DAJI?*


*NA*


*FAREEDA ABDULLAHI*




*_?KAINUWA WRITERS?? ASSOCIATION_*??
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```


https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation






45-50


_*GODIYA DA JINJINA AGAREKI ANTY FAUXY YAR AMANA, AMANA TAKAIMIKI GASKIYA SAMUN MACE KAMARKI AKWAI WUYA MACE BA HASSADA BA KYASHI ALLAH YA KARA DAUKAKI DA DUKKAN YAN KAINUWA WRITERS*_




*JINJINA AGAREKI MARYAM DANDAWAKI SANNU DA KOKARI ALLAH YAKARA DAUKAKI YAKAWO KASUWA ME ALBARKA NAGODE MAKU*????????????




A fusace suka juyo suga wacece wannan? cike da farin ciki ja'e yace "itace ku cimmata ku kamon ita yanzun nan".
Tariga ta fita hayyacinta kawai gani tai sun yiyo kanta gadan-gadan nan tafara gudu, gudu takeyi suna binta abaya haka suka dingayi har suka fara shigowa gari, nan suka dakata ita Kuma ta bazama cikin gari da gudu tamkar zararriya, bata zame ko inaba sai gida, tana shiga taga haryanzu tenkwai na nan da gudu ta fad'a kanta jiki na rawa bakinta sai karkarwa yake ta rirri'keta taboye abayanta "lafiyanki aduke menene? "
Sai kallo ba magana nanfa tafara girgizata amma ina bata hayyacinta bata magana, ganin haka yasa takamata suka fice daga gidan suka tafi nasu gidan suna shiga lamunde tace
"To sarakan yawo daga ina kuke? kunsan munada mara lafiya gashi harya fara motsawa Amma ya kasa tashi saboda ciwon kansa ya dai bud'e ido yai yun'kurin tashi ya koma"
cike da farin ciki take gaya musu taga duk sun mata shiru ba wanda ya kulata, tenkwai taja hannun aduke takaita dakinsu tazaunar ta fita ta d'ebo mata ruwa a tulu me sanyi tabata takarba tasha ba tace komai ba sai had'iyar zuciya take kamar zata had'iye zuciyarta, daukanta tenkwai tayi ta kwantar da ita batace komai ba sai binta da idol kawai take tamkar zararriya ganin komai take tamkar a mafarki, "wai ankashe babanta ancinyeshi anwa aduke fyade tana chan batasan halin datake cikiba" gaba d'aya kwakwalwarta ta dena aiki ta tsaya chak ta sandare kawai akwance, ganin haka tenkwai ta koma waje taleka d'akin majinyacinta da tunda tasa Kai Bata 'kara waiwayarsaba sai yanzu taganshi yana baccinsa hankali kwance ta tsura masa ido tana hango tsantsar kyansa da nagartarsa sabanin wancen Dan iskan ja'en daba wata nagarta atare dashi sai zallar iskanci ace shizata aura tazauna har karshen rayuwarta gwara ta mutu data aure shi tana fatan wannan bawa ya kawo wani haske a wannan garin nasu.






Yadauke idonsa daga kanta cike da takaicin yadda tazama tamkar gunki gaban wanda bemasan tanayiba shigashi yana tsananin kaunarta Amma Bata saniba gata kyakykyawa me diri mtsww yaja tsaki sai da jeddah takare masa kallo ta tabbatar da yay mata ? Nan takada kai takama hanyar fita daga hall din taja hankalin maza dayawa saboda kyanta Amma batasu takeba tafuce waje tanemi waje tazauna tana jiran taga fitowarsa ayko kafin atashi taga ya fito da sauri shida wani abokinsa sun durfafo inda take Nan takara suma azaune saida sukazo gab da ita taga yabude motarsa da hanzari ta tashi ta isa gabansa Tace "sannufa" yay mata banza kamar badashi takeba, abokinsane yayi karfin halin cemata "sannu y'anmata ya kike? Ta washe baki tare da qara yauqi ta amsa da "lafiya lau" Nan suka hau zuba dama shine Wanda ya ganta tun a ciki ta tafi dashi shiko be auraba tunda yaga kamar Yar hannunce yad'ana Amma zefi san ya aureta, dataga wankin hula na shirin kaita dare saitace "abokinka baya maganane" yadan kalleshi a sace yaga yadda ya had'a rai ransa inyayi dubu ya baci sun barshi a cikin mota kamar bawansu, bayasan wargi Sam besan wanna shegen kwashe kwashen na faruk ya jiyo ya kalleta have "haka yake bikiga ya bude mota ya shigeba" "gsky yay mun" ya kalleta "Ni Kuma kinmun yaza ayi? " tai far da ido "naima kamar Yaya? " wani murmushi ya sakar mata irin nasu na 'yan duniya sannan yace "kinmun a matsayin matar aure"
Dariyar ita ma Tayi sannan tace "kaban dariya wallahi ni gaskiya abokinka nake so shi yai mun shizan aura" ya'ke yayi don maganarta ta sosa masa rai amma ya dake yace "to ni a wane matsayin zaa ajiyeni?" "Abokina" ta fada da sauri sannan ta qara da "matsayinka kenan Kuma abokin mijina" Ya kalleta rai bace yace "To wannan da kike gani ansa masa rana Kuma bayasan babbar mace sannan baya kula mata".

Ta dago ta kalleshi tace "wanne temako zakay mun yasoni ya kulani?"
"Gaskiya babu" Ya bata amsa kai tsaye "zan dai baki card dinsa da number din wayarsa, Amma Ni mezaki ban?" Ya qarashe zancen da kashe ido irin na yan bariki,
"hmmm me kake so ajikina kafada da kanka zan baka shi? " cike da murna yace "kinyi alkawari? " bata amsaba ya dora da "kawai so nake ki mallakamun kanki"
Murmushi ta sakar masa na manyan bariki tace "dan dai wannan karka damu ka kwantar da hankalinka.
"zanbaki complementary card dinshi, yadda zaki same shi a office da Kuma number din wayanshi shikenan ko? "
cike da farinciki tace "shikenan ngde gaskiya"
"to muje murage muki hanya".






Tana tsaye taga kamar ya motsa da hanzari ta karasa kusa dashi tace "sannu kafarka? " saitaga ya bude idonsa Nan tacika da farinciki da gudu tafito waje cikin zumudi take kiran lamunde tana "Ya farka ya bude idonshi" lamunde ma cikin farin cikin tabiyota suka koma suka kamashi suka zaunar dashi sai binsu yake da ido ba umm ba ummun yakasa cewa komai kansa yakeji yay masa nauyi ya daure tam ya Kai hannu ya taba sai yaji a kulle yake ashe, yay shiru ya kasa magana Nan lamunde ta dakko masa maganinsa tabashi yasha shidai bece komaiba kawai binsu yake da ido, bai sansuba betaba ganin halitta irinsuba to Amma wayema shi meyake anan? beda amsar tambayarshi sannu suke ta doka masa yanata kallonsu kamar gumaka chan lamunde tace "begama hutawa be dawo hayyacinsaba mu kyaleshi ya sarara zuwa jimawa muje" suna fita Dan naci ta fakaici idon lamunde ta koma tasashi agaba tanata kallonsa tana murmushi.






Tunaninta daya yaza ay tayi rayuwa dashi dama haka yake idanuwansama kawai abun kallone shine zetafi da ita inda yake ya aureta ko kuwa waye shima batasaniba tambayar dataketaywa kanta kenan tabbas inasan shi zan rayu dashi bazan taba gajiya da kallonsaba.







Ja ene tsaye yake ta bala'I "kuka Bari ta kubce muku tafiku gudune ko Yaya wannan yarinyar itace zata tonan asiri wajen tenkwai tabbas idan tasamu wannan labarin bazata aurenba Ni Kuma itace rayuwata ita nakeso"
cike da bacin rai damusa yace "haba sarki me jiran gado duk tarin kyawawan matanka Amma kace lallai sai wannan mummunar? "
A fusace yasa wuka ya tsarge wuyansa sai jini ya Fadi Tim kasa matacce "duk Wanda ze aibaya tenkwai hukuncinsa kenan kodako kahone kyau bashine maceba diri shine mace Dan haka ita nakeji tamun soyyarta har cikin bargona take" can yay wani tunani sannan yace "tabbas dole aduke ta bakunci lahira a yau din nan da ita da rama bazan barsu surayuba saboda idan suna raye tenkwai zata dinga tunawa da abunda ya faru Amma idan na kashesu nasan zata kara tsoronna takara yarda dani ta Mika kanta gareni kawai Koda ba a daura aurenba"
"bashari"ya Kira yaransa "yau tsakar dare tunda duhu ya fara zamuje mu kashe aduke suka sannan muje har gida mu cinye rama Dan zatai maiko" (yafara tandar baki ya tsohon maye Koda yake meye maraba yadama mayen ne) suka hau murna,ya wurgowa musu harara "kufara shiri so nake akashe aduke abar gawarta amma ita nasanja shawara ba yauba saboda gobene bikin cin jarirai Dan haka a barta sai ankwana biyu adai kashe aduke yau" Nan suka hau ihu suna murna.






Mahaifiyar ja'e ko abun duniya ya isheta tabbas sunada bukatar sanjin rayuwa jikinta nabata wannan bakon shize kawo musu sanji tayaya take wani tunani yazo mata ze zama daya daga cikin bayin bangarenta su goma ne Amma akwai wani tabbas kamarsu guda da wanchan sai dai shi be cika haskeba Amma ay akwai dabara akwai abunda suke sawa me rinar da fata shizatasa masa ta sallami wanchan ya gudu Amma sai ya warke.






Take tasa aka kirawo mata darzan yana zuwa ya zube "angaisheda uwar tausayi uwa agun yariman masarautar kuguru"
"magana nakeso miyi dakai kasaurareni sosai idan ka kuskure hukuncin kisane akanka inaso nanda Dan wani lokaci zan umarceka dakabar garin nan zansaka a hanya kafita kabar garin nan ka koma beguwa tunda su naji anacewa suna dai bautar gunki Amma basa cin mutum Kuma suna karbar bako yafi kusa da garin Nan idan Kuma zaka iya ka karawa gabama to ka kara" nan yace "ranki ya dade inada mata da d'a"
"kabarsu kaje idan komai ya nutsa kadawo garesu" cike da murna yay godiya Amma kasan ransa yana jimanta yadda ze rabu da matar sa da d'ansa "karka kuskura ka nuna musu zaka bar wannan gari nasan yadda zanyi dasu kawai".






Dare na tsalawa suka dauki hanya suka shiga gidansu aduke suka sadada dakin suna shiga sukaga mutum a kwance kawai suka Burma mata wuka tasaki ihu suka kara mata suka daddatsata cikin Daren Nan ga gari da duhu suka sa kai suka fito suna fitowa suka hau sowa da murna saura daya burin ubangidansu ya cika ya mallaki abar sansa duka da anmasa alkawarin aurenta amma yafiso ta amince masa yayi wannan alkawarin saita soshi baze taba sa mata karfiba kamar yadda yakeyi soyake tabashi hadin Kai yaji Dadi ya morewa wannan jikin nata me masifar laushi cike da farin ciki yashiga turakarsa ya kwanta.

Ahankali take takawa saboda ba isashshiyar lafiya tana shiga taji tana taka abu tana dubawa taga jini mezatay tasaki wata kara anan tafadi tasume.





(tofa muje zuwa akara hakuri dai fans ??????????bana samun damar typing me yawa abubuwan sunmun yawa kuyi hakurin biyoni kudai yanzu labarin yasoma)






*feedyn bash*
[9/11, 22:29] +234 810 679 5647: *?ARNAN DAJI?*


*NA*


*FAREEDA ABDULLAHI*




*_?KAINUWA WRITERS?? ASSOCIATION_*??
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```


https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation








GAISUWA DA JINJINA AGAREKU MASOYANA INAJIN DADIN YADDA KUKE COMMENT DINKU AKAN ARNAN DAJI NAGODE SOSAI





40-45






Cikin kuka tafara tambayarsa meyasa kuka shigo tare baban rama yace nazo zan shigo naganshi a zaure yacemun yaje gida wajen aduke akasanar dashi cewar tana Nan shine Ni Kuma naga ay shima Danane duk daya kuke shine nace mu shigo tare bansan wannan tashin hankalin zamu tarar ba dabazan Bari yashigoba kodan karyaga wannan danyen aiki yanzu Bari na hanzarta natafi daji nemawa aduke magani ku kula sosai da ita ku kula dakanku Kuma maza kuyi mata wanka ku gasa mata jikinta ya fice da hanzari ya nufi daji gabansa nata faduwa yadai dakene kawai kafin kace meye wannan rama ta Dora ruwa nan d Nan ta tafasa tenkwai ta kinkimeta takaita bayi rama ta wanke ta tsaf Dan bawani kuzari a jikin ta suka kamata suka wuce da ita gida dake kakarta ba wani gani take sosaiba batasan meya faruba suka ajiyeta sukace ta kula d kanta kafin babansu ya dawo daga dajin itadai kawai kallonsu take ita tasan metakeji Amma bataji zata rayu bazata samu rayuwa me inganciba saboda iska tana shigarta har cikinta saboda su basu da sittira sai fatar nn dasuke Dan kare gabansu da ita da mamansu ko manyan ganyaye suyi ado dasu baban rama natafe yana tunanin wannan zalinci a cikin daji kawai yaga an xagayeshi suwa ze gani ja e ne da yaransa rai bace baban rama y chakumi wuyansa la ananne badu ya tsinema mara mutunci gafallalle kacutar damu ka cutar da zukatanmu meyasa baka nemi yardartaba kasa mata karfi bayan kasan dokace sawa matanmu karfi saina dau fansa akanka macuci cike da bacin rai ya fara magana nizaka tonawa asiri ka turon tenkwai taga abunda nake aikatawa nasan Kai zaka shigo kaganni kaje ka kiratako kasan ba abunda nakeso irin ta a rayuwata ko kaho da uwata banasansu haka Dole zaka karbi hukunci hukunci me tsanani daga gareni bazan barkaba kaima kasani duk Wanda yaga sirrina saina kashe shi bazan kashe tenkwai ba Dan ita tawace amma zan kasheka zan kashe rama zan kashe aduke dukansu sai kun bakunci lahira hhhhhhh suka kwashe da dariya cike da tsoro yake kallonsu bani nakira tenkwai ba nashigo natarar suna gidan ita tasanar Dani Kai ka aikata wannan aikin amma nama alkawari bazan gayawa kowaba zan rufe wannan maganar namaka alkawari nabika nabi badu nayarda bazaka karasa rama a idonka ba bazan Bari ta fadi wannan labarin ba nama alkawari banida kowa sai ita bata da kowa saini katemakemu ja e yasheke da dariya kasan Koda wannan maganar tafita bawani abu bane saboda bame jadani a wannan gari ninake milkin wannan gari nida kaho nasan cewa jama ar wannan gari basa so asawa mace karfi Ni Kuma komai da karfi nake yinsa da karfi zan keta duk wadda naso nakuma kasheta kaima yanzu zan kasheka hhhhhhh









Haka rayuwar gidansu jeddah takasance kowa abunda yakeso yakeyi saboda uwa ba kwaba uba ya mutu a wannan lokacinne za ay bikin wata makociyarsu me suna ummi tare suka taso da jeddah makaranta daya sukai Amma kowa da halinsa shiyasa basa shiri sosai sai dai idan an hadu a hanya hy hy nan Jeddah najin labarin irin mijindazata aura sukai ruwa d tsaki a harkar bikin ita da afra tunda ansan juna saboda mijin me kudine na gaske tayi musu gaba daya ankon dinner din Dana bikin ita da aminiyarta afra sai da tasan yadda tayi suka shigewa amarya har rabon cards da ita akai takoma babbar kawar amarya ita d kawarta afra tsabar shishshigi anfara kamu washe gari dinner mijin d abokansa sun saki kudi shiyasa suke wadaka gashi sun hadu da Jeddah me bala in wayo idon cin nera wadda tasan lakanin karbar kudi a hannun namiji aranar dinner ta gaji da kyau Dan takusan fin amarya kyau Dan dai amarya amaryace kodako ta buzuzuce tanayin kyau ranar bikinta sunyi dinner dinsu meena event center dake longe road guri yayi guri anci ansha Nan aka Kira aminiyar amarya tabada tarihinta aka Kira jeddah Nan ta taso dakyar kamar Yar governor tana fita akahau shewa da tafi Nan camera tafara aikinta daukanta ake kmr baza a denaba gashi b turanci da hausa ta gabatar da jawabin ta koma Nan aka Kira aminin ango nn akafara zuga kirari yaro d kudi abokin tafiyar manya me kudi uban matsiyata Dan gidan kudi gadon kudi Nan y fito yana zuwa Nan fa kowacce yarinya taraina kanta wa kuke tsammani suhail Ibrahim gadon kudi kenan nanfa yafara larabci tamkar balarabe camera kamar zatay magana mata suka yanyabeshi mazako sai manni suke masa Ana gamawa aka saki kida Nan da nan ya balle rafar dollars yadinga zuba kudi tamkar besan ciwonsuba tamkar ya samu bolarsu nanfa mawaka suka samu nayi yi suke ba kakkautawa amarya da ango sun fito guri ya kara rinchabewa anata watsi da nera






Jeddah kuwa mutuwar zaune tay tunda taga wannan matashin meji da kudi ta mutu a zaune dama gata mayyar kudi Amma shi wannan soyayyace me cike da sha awa takamata lokaci guda nan ta mutu a zaune duk rawar kan Nan nata Babu ita hankalinta be kara tashiba sai yadda taga yana zuba dollars a tsakiyar fili dakyar taja kafarta ta koma filin tasan yadda tay ta nanuka kusa dashi kawai kallonsa take bemasan tanay ba chan abokinsa ya lura da ita yadda tazama kamar gunki shi Kuma tunda yaganta tay masa ta tafi

Please Login or Register in order to submit comment