Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ido said yayimin Murmushi,nikuwa kallonsa kawai nake,wai fah yanace danna shiryune na ke bada haddar,baisan carbinsa nake tsoro ba,dan duk sanda ya dakeni dashi kwana nake ina jin azaba,kaman ana kwaramin wuta,shiyasa nake binsa kawai a rabu lafiyah.
Tunanin na katse lokacin dana ji ankira sunana,SAMEEMAH UMAR,tashi nayi zuwa wajen karatun na fara.
Da karfi nake cikin kwarewa,saboda burina shine su sallameni a wajen nima naje naga me akeyi a cikin garin.
Kabbara naji yah dauka lokacin dana gama wajen da aka bani,da ni watace dadi zanji amma maimakon haka saima gani nake bata lokacin su sukeyi.
Da haka aka gama walimar da kuma karatun kowa yah kama gabansa,da niyyar gobe za'a ji wanda yayi na daya a bashi kyautukansa da kuma sallamarsa zuwa gidansu.
Bamu muka dawoba sai tab ana kiran magriba,bayan munci abinci mun yi komaine,na kira,sunan su khairah ina gyara zama akan katifa ta,dukkan su nutsuwa sukayi,dan sunsan hankalinsu nake bukata a lokacin,
"Yawwa inaso na gargadeku,idan aka tambayeku ni wacece naji wata tayi zancen abinda nake aikatawa,har kukasa aka ce bazan tafiba hmmmmmm,basai na fadaba kawai"
Khairah ce ta cuna baki kafin tace,
"Toh dama ko kin hanamu ai shaidar karyah zamu bayar a kanki dan ki tafi muma mu huta"
Hairah ce tayi saurin gwabe bakinta tareda yimata kallon ta shiga hankalinta,
Nikuwa tunda naji abinda tace nasan banida matsala tanan bangaren sai kuma a ji da gobe kuma.
Da sassafe na tashi yau saboda zumudi mai zai faru,cikin sauri muka shiryah domin zuwa jin sakamako.
Bayan anyi taro kowa yayi shiru yana sauraran mai gabatarwa can naji sunana yana amsa kuwwa kaman a cikin mafarki,dagaske fah ni aka kira wai na lashe gasar karatun qur'ani da kuma litattafan addini,tab lallai sunyi kuskure,tsinke tunanin nayi na tashi ina tafiyha cikin nutsuwa har naje gaban mu'allim,Murmushi yayi min tareda mikamin kyautata yana cewa,
"Hakika nay I miki murna sameemah ke yarinyace mai hazaka da kuma dagewa,allah yah albarkaci rayuwarki sannan ina muki albishir da cewa a yau an sallameki daga gidan horo na yara zakije wajen danginki ki cigaba da rayuwa kaman ko wane da mai yanci"
Banyi murnar karatun ba da kuma addu'a abinda na sani shine fita waje domin neman shaheedah shine kawai a raina,amma a fuskata murmushi kawai nayi tareda nuna masa na ji dadi sosai.
Haka taro yah Kare kowa yah karbi kyautukansa mukuma nida sauran guda ukun da aka sallamemu kaya masu kyau suka bamu ba uniform dinmu ba.
Tun kafin na shigo dakinmu su nanny sun hada min kayana uniform kuma sun dauke abinsu,su hairah nagani a,zaune ko kallon inda nake basuyiba,nima ban kallesuba,lokacin danazo fitane nace musu sai wataran,su ma toh suka bini dashi, na kama hanyata nayi hanyar waje inda za'a daukeni a mota.
Bayan mungama sallama da kowa muka dauki hanyar tafiya,sauran mazane suna ta murna zasu je gida. Daya daga cikinsu aka sauke sai shima dayan da akayi tafiya mai nisa dashi aka saukeshi.
Ni kuwa tafiya muke tun suna hakuri har suka gaji sukayi magana ganin nayi shiru bana da alamar nuna musu hanyar gidanmu,
"Keh sameemah a ina zamu saukeki ne?"
"A gidan dayake farkon hanyar dazaku shiga"
Toh kawai sukace,a bakin wani gida mai baki get suka saukeni,kayana na dauka na shige cikin gidan kaina tsaye ina daga musu hannu,saida naga wucewarsu da wasu mintina kafin nafito daga cikin gidan ina lellekawa ko wani yah ganni a cikin gidan,saidai cikin sa'a babu wanda yaganni harna fito na tari taxi.
A cikin taxi dinne na rokeshi yabani aran wayarsa, da farko bai niyyar baniba amma dana marairaicemasa akan gidanmu zan kira sai yah bani.
Number wayar shaheedah na saka,cikin sa'a kuwa sai ta dauka,da farko tayi Mamakin ganina saidai ban barta ta cikani da surutuba na tambayeta address din gidansu,tana fadamin in fadawa driver da haka har muka isa kofar gidansu kafin nabashi kudinsa ina yimasa Godiya.
Da murna ta rungumeni tana tsalle kaman zata cinyeni,cikin gidan muka shiga gashi mai kyau saboda babanta yana da kudi sosai.
Mahaifiyar tace ta tarbeni cikin mutunci da ta fadamata ni kawarta ce ta makaranta.
Satina daya a gidan su shaheedah komai yana tafiyah normal amma kuma matsalar daya shine yayanta yah takuramin waishi sona yakeyi ,saidai abinka da dan iska ina ganinsa nasan jirgi daya ne mudashi amma da alama ita shaheedah bata fahimci hakan ba,kuma duk matsalar daga wajen mamarsu ne domin itah ce take sangartasu batareda sanin mahaifinsu ba.
Yau ma a zaune muke a falo nida shaheedah mamarsu batanan ta tafi shopping,sai shaheedah ta shiga wanka nikuma ina zaune da waya a hannuna,banzata na kawai naji hannu yana bin cinyata ina daga ido naga yah shaheed ne,abinne yaban mamaki ganin abinnasa har ya kai haka. Matsawa nayi gefe batareda nace komaiba,shima sake matsowa yayi yana wani bina da mayen kallo,fuskarsa ya matso domin yah sumbaceni bansan lokacin dana zuba masa wani gigitaccen mari ba akan fuskarsa,wanda yayi dadai da shigowar mahaifiyar su ta dawo daga kasuwa.
Zubar da kayan siyayyar tayi tana bina da kallon mamaki,dan a duniya babu abinda takeso yah yayannata guda biyu ,shiyasa ta tsani jinin abinda zai tabasu ko miyeshi.
Lokacin da aka kai shaheedah gidan horo ma itace tayi kutun kutun aka dauko mata yar ta.
Matsowa tayi inda nake har sannan idonta bai dauke a kaina ba,ganin haka ne yasa shaheed yayi saurin cewa,
"Ummeeh dama ban fadamikiba wai fa dan kawai ina yimata wa'azine saboda itace take hurewa shaheedah kunne lokacin da suna gidan horo"
"Gidan horo kuma,amma naga shaheedah tacemin kawarta ce daga makaranta"
"Karyane it's ce shugabar tantirai a gidan"
Kallon su kawai nake batareda nace komai ba,dan ko mamaki banyiba tunda hakan ba bakon abu bane a wajena.
Bayan sun gama zancen sune ummeeh ta kalleni tareda cewa na bar mata gidanta ,daga kai kawai nayi alamar naji,juyawa nayi domin komawa dakin shaheedah domin tattaro kayana,kicibis mukayi ta idah a bakin kofa da alama taji duk abinda mukace,bance mata komai ba sai rabewa danayi na wuce dakin ina tattara kayana.
Rike hannuna tayi tana jijjiga kai alamar karna tafi,dafa kafadarta nayi ina cewa,
"Ahah shaheedah dole na tafi amma ba rabuwar kenan ba,nima tunda akayi haka yanzu nafison nayi zaman kaina ba nawani ba"
"Amma sameemah.........."
"Karkice komai dan kinsan ba sauraronki zanyi ba"
"Shikenan amma zan baki number BINLAD,saiki nemeshi nasan zai baki inada zaki zauna dan suna neman irinki,nima ina zuwa cikin satinnan dan akwai wani patrol da zasu je"
"Shikenan hakan yayi ni bari na tafi saikin shigo,kuma sannan ki fadawa yayanki kar ya bari na hadu dashi a hanya ko kadan,ke kinsan mai zai faru dan haka ki sanar dashi"
"Zan fadamasa ogah seemah"
Bansami kowa a farlon ba da alama ummeeh da shige dakinta shikuma gogan yah fita,shaheedah ce ke biye a bayana fuskarta tayi narai narai da alama bata son tafiyahta,saidai ni kuma a nawa bangaren tunda naga abinda yah faru naji banason zama a karkashin wani ba iyah gidannasu ba ma,address din wajen na karba da kuma numaber wayarsa kafin na tari taxi.
Bayan na shiga ne na juya naga shaheedah tana matse Kwallah,hakika nima banso mu rabuba saboda ita kadaice kawa mace dana tava yi a rayuwata,amma ni nafita juriyah badai mutum yaga raunina ba kama,ta inda muka banbanta da itah kenan,duk da ta iyah tsiyah amma tanada rauni gakuma shagwaba.ni kuwa wa yaga dutsi.

*+______________________+*
*ABIN YABO BOOKSHOP*
  Kasuwar  Rimi  Kano
Tel:📞 *07038339244*

❤❤SADY-SAKHNACEH❤❤

Kar ku manta da

#comment
#share
#like
#follow.

____** *GIDAN GANDU* **____
❤❤By sadi-sakhana❤❤


Wattpad username:SAKHNA03


❤18❤

Tafiyah mukeyi a cikin birnin har muka shiga wajen da babu gidaje sosai sai jeji,ga kuma garin yayi duhu sosai da alama cikin kowanne lokaci ruwa zai iyah kwacewa.
Driver ne yakalleni ganin muna ta shiga cikin jeji har munzo inda babu wani gida amma bance mun iso ba,
"Gaskiya kiyi hakuri amma daganan zan ajiyeki duniyah babu yarda karnaje ke mai cutarwa ce ki cutar dani,kiyi hakuri bazan sake yin gaba ba gashi kuma hadiri ya hadu inason komawa wajen iyalai na ni.............."
"Yah is a haka zaka iyah saukeni,banason dogon zance"
Bayyi musu ba kuwa yah fara fitomin da kayana daga cikin motarsa saida yagama kafin na bashi kudinsa yayi gaba.
Samun wani wajen kiran waya nayi na zauna saboda wayata babu charge.
Tun daga nesa nake ganin hasken fitilar har yah fara isowa inda nake,ban matsa daga inda nake ba bare na tashi saidai kallon mai tahowa danake duk da bansan wayeba.
Lokacin da suka iso wajena ne nakula ashe mazane guda uku sun saka rain coat bakake,zagayeni sukayi da bindiga kafin daya,daga cikinsu yasa,
"Ke wacece,sannan kuma waya aikoki"
"Bai shafeka da sanin ni wacece ba,saboda ba matsalarka bace"
Kallon na raina musu hankali suka faramin saboda jin amsar dana basu,
"Dolene ki amsa tambaya a wajen ogah binlad,ku daureta yanzunnan,sannan ku rufemata ido,sai iyayenta sun kawo kudi tukun"
Tashi nayi daga zaunen danake ina kallon su,kayana na dauka na rike kafin nace,
"Wanene wanda zan hau mashin din nasa,yazo mu tafi kar dare yayi ga kuma ruwan sai karuwa yakeyi"
Nafada ina kallon hadarin a sama,ko ban kalli fuskokinsu ba amma yanda nayi magana nasan sunyi Mamakin action dinane,hakan a jinina yake bawa mutane mamaki da halina.
Dukkansu tada mashin dinsu sukayi,ni kuwa saida naje gaban ogannasu mai barazanar kafin na dale mashin dinsa ina gyara zaman jakata.
Kara nausawa cikin dajin muka kara yi,munyi tafiyah mai nisa kafin muka iso wani gida da aka yi katangarsa da karfe,masu tsaron bakin wajenne suka bude mana,dukkansu kowa yana rike da manyan bindiga a rataye,kana ganin su kaga manyan yan iska.
A bakin wani babban d'aki muka tsaya,wanda yafi dukkan dakunan wajen girma,shiga sukayi nima nabi Bayan su.
Wani farin balarabene a zaune yasha askin tankwal sai uban gemu kaman zayyi magana,bakar jallabiyace a jikinsa ga idonsa yasha kwalli,a takaice dai jan wuyane kawai.
Sallama yamin na amsa kafin yace,
"Sunana Binlad"
"Nasani basai ka fadaminba"
Yayi Mamakin yanda nayi masa magana babu tsoro amma kuma sai yah basar,
"Baki fadamin sunanki ba"
"Kaima baka tambaya ba"
"Miye sunanki karamar yarinya"
"Sunana sameemah "
"Yayi barkanki da zuwa"
"Toh"
Daga nan na katse maganar tamu ta hanyar zuyawa ina kallon wajen,shima bai sake cewa komai ba sai kareni da kallo kawai dayake wanda inajin yanayin kallonsa a jikina,maganar sa na jiyo yana cewa,
Akwai dokoki a wajennan sannan kuma saboda ke macece akwai matsayin dazaki tsaya bakomai zamu sakaki ba kar shirinmu yah wargaje",
juyowa nayi Nima ina kallonsa kafin nace,
"Ka barni a tsaye haka ake taryar sabon member ,toh ina jin bacci kuma sannan nagaji dayawa,inayaso koma mai za'a cemin sai gobe kuma"
Daga haka na kalli wanda mukazo tare ina tambayar sa inda zan zauna,binlad ne yayi masa alamar ya kaini kawai inayso sai goben.
Da safe kuwa wata tsohuwa ta shigo hannunta dauke da tea da kuma gurasa,karba nayi na ajiye kafin naje gyara jikina tukunna,saida na shiryah na karyah tukun naji dan aike na shaidamin kiran Ogah,wani dan gyale nasaka, a kaina bayan dogon wandon dayake jikina da kuma riga iyah gwiwa.
Ya u ma kaman jiya yana zaune saidai yasaka rawani,samun kujera nayi na zauna tun baice na zaunaba,
"Ke Baki iyah gaisuwa bane"
"Na iyah amma banayi,kayi hakuri"
"Keee,..........."
"Kana Bata lokacin ka,bayan na fada maka ra'ayina,muwuce wannan shafin kawai,kafadamin menene abinda zanyi kawai"
Buga bencin dake gabansa yayi idonsa yayi jaa,da alama furucina yah bata masa rai,
"Tabbas ke baki sanniba kina bukatar a horar dake,inaso yanzunnan,samad kuyi mata bulala hamsin da dorina"
Matsowa sukayi da niyyar kama hannayena ciki harda wata mata jikinta a murde,dakatar dasu nayi kafin na wuce inda mai bulalar yake,kwanciyah nayi akan table din hankalina kwance.
Saida naji yah irga hamsin tukunna na tashi daga wajen na dawo na zauna akan kujerar danake zaune dazu,
"Yanzu shugaba zaka iyah cigaba da bayaninka tunda hankalinka ya kwanta ka horani din"
Bude baki yayi yana kallona,duk da yana kokarin boyewa amma alamun tsoro ya bayyana a fuskarsa,komawa yayi yah zauna tareda cewa,
"Zaki fara koyon sand'a ko wuce waje batareda wani yah gankiba,sannan nagaba kuma harbi da bindiga saikuma koyon fada"
"Saikuma me?"
"Banson musu ki koyi wannan din tukunna"
"Shikenan and gama ogah"
Tun daga ranar na fara koyon harbi da kuma fada babi dare babu rana,nikadaice mai koyon saboda babu sabon shiga a lokacin shiyasa masu horon ni kadai suke yiwa.
Cikin sati daya na kware wajen harbin bindiga da kuma fada,hatta wanda suke koyamindin sai sunyi dagaske su yi abinda zan aiwatar,labarine ya isa kunnen ogah binlad na himmata da kuma rashin tsoro.
Saboda yanayin nasarar dana taka a cikin wata daya sunana yah fito a cikin wanda zasu je fashi,da farko su Samad sunyi bakin ciki ganin yanda nake taka matakin da saida sukayi shekaru kafin su taka,nikuwa harka ta nake ni kadai ,saidai idan aikine yasamu muke zuwa in group,shima wani lokacin Samad ya jagoranci shirin wani lokacin kuma ni,kuma duk aikin dana jagoranta ba a samun cikas,saboda koda harbi ake nice na ke tarewa saina zo gida kafin na cireshi,idan wani yayimana cikas kuwa cizo kawai nake masa kafin bayan sati daya mutanen mafarkina sun zuk'e jininsa,dan dama abinda suke so kenan,su kuma ko yaushe cikin karamin karfin jiki sukeyi idan nakai musu jinin da suke so.
Bayan kwana biyu shiru banji labarin shaheedah ba duk da tacemin zatazo wajennamu,abinne yabani mamaki hakan yasa na shiga cikin gari da b'adda kama,mai gadinsu na tambaya a gefen gidansu nan yake shaida min kanin babanta yah tafi da itah gidansu wai zayyi aurenta a can,da farko nayi bakin cikin bamu sake haduwa ba,,amma nayi mata murna domin hakan shiyafi dacewa da itah,sama da rayuwar damuke,dan irin wannan rayuwar nikadai yakamata da dungayi tunda hakane kaddarata.
Komawa nayi jikina da sanyi jin bata gidansu ta tafi inda rayuwarta zata inganta,tun kafin na isa na watsar da tunanin ta dan yanzu banason saka wani abu a raina har ya dameni.
Maida himma nayi akan aikinmu ba dare ba rana,dan yanzu nice nake kulada da kowanne shiga da fita,saboda ogah Binlad shida Samad sun tafi kasar Brazil,binciken wani sirri,yanayin yanda abun yake tafiyha har yafi in ogah yananan,saboda sun fi tsorona fiye dashi yamzu,dan kowa yasan halina idan yah aikata abinda banceba.
Ina cikin bincikene na gano wani aiki a gidan sarkin malamai,saboda yanada kudi sosai,sannan duk wani kudi a gidansa yake tarawa.
Shirye shirye muke ba kama hannun yaro,kullum muna cikin binciken yanda zamu aiwatar da shirin.
Tun da yamma,na zabi wanda zasu bini da kuma wanda zasu kulada gida kafin mudawo,babu wanda yayi magana bare musun abinda nace,bindigoginmu muka cika da bullet,duhu yana farawa muka shiga motocinmu sai cikin gari,a bayan gidan muka tsaya muna ganin shige da ficen gidan,wasu motocine suka,fara shigowa zasu kai wajen bakwai,har wajen karfe sha daya amma babu motar da ta fito hakan yasa na bada umarnin mushiga kawai.
Wani daga cikin yaranne yace,
"Amma ogah seemah akwai fah mutane a ciki"
"Nasani ai ko makahuwa ce ni,ubanme mutanen zasuyi mana,idan tsoro kake ka zauna acikin mota,banza lusari kawai,idan kuma suka fito da kudin suka tafi fah,mu mai zamu samu"
"Afuwa Ranki ya Dade"
"Dallah yimin shiru,ku mazaje maza a kafta"
Cikin sanda muka fara dosar gudan,har muka shiga babu wanda yah kulada mu,cikin gidan babu kowa sai haske daya gauraye gidan,ina biye suna bina a baya har muka haura stairs din benin,acan wani daki karshen corridor muka jiyo maganar mutane,da alama suna cikin dakin kenan.
Alama nayiwa na baya su tsaya kafin nayiwa nagefena su biyoni,a bakin kofar muka tsaya sai kuma muka banka kofar da sauri.
Falone mai girman gaske an jereshi da kujeru,manyan malamaine a zaune amma shigarmu kowanne ya tashi ya tsaya yana kikkifta ido,jerin malam na bi da kallo inda idona yasauka akan mu'allim,"dank'ari" nace a raina.
Daga bindigar nayi sama kafin nace wa yaran,
"Maza Ku bincikemin sako da lungu na dakinnan,karku bar ko ina"
"Angama ranki yah dade"
Zagawa nayi ina kallon malaman wajen,tsawa na daka musu cikin sauri suka zube a kasa suna karkarwa,tafiyah nake saida nazo saitin mu'allim kafin na tsaya,sunansa na kira inda yah dago da mamaki da alama yasan muryar,dadai lokacin yarana suka dawo da cewar basuga komai ba,.
Cire hular fuskata nayi ina kallon mu'allim din da shima kallona yake da Mamakin.
"Kayi mamaki koh,nicedai sameemah,wannan itace hanyar danake kai ba wacce kake kokarin dorani ba,inayine saboda tsoronka badan ina so ba,tunda kai ka sanni inaso ka fadawa shugabanku yabani kudi na tafi bana bukatar taba kowa a nan wajen,idan kuma ba hakaba,karkayi tunanin,zaka iyah kallon wannan sameemar"
Tun kafin mu'allim yayi magana na nuna masa yayi shiru saboda ina kallon sanda shugaban yah mikawa yarona kudin ta gefen idona.
Tsayawa nayi a gabansa,bayan ya mika kudin nace,
"Mu zamu tafi saika musu bayanin irin kodar yaran daka siyar kafin ka samu wannan kudin,saboda su sanjaka da wuri kafin lokaci yah kuremusu,muma kuma su daina zargin mun sace kudin marayu kamar yanda ka fadamusu"
Ina gama fadamasa na tunkuda keyarsa da karshen bindigata zuwa gaban sauran malaman nayi gaba.
Sai wajen karfe biyun dare 2:00am,muka koma sansanin mu.
Ogah binlad nasamu a kan kujerarsa a zaune har sannan bai kwanta ba yana jiran isowa ta,kallona yayi da alamar tuhuma na fitar aikin danayi bayanan.
Nima banyi masa magana ba sai mika masa jakar kudin danayi,karba yayi yana zugewa dan ganin menene a ciki,
Dagowa yayi da alamar neman karin bayani,nima shiru nayi banyi magana ba ,dannaga alamar da miskilanci yadawo,
"Baki fadamin wane aiki kukayi aka samu wannan kudin ba"
"Toh ogah kaima baka tambayeni ba ai"
"Hmm kina nan da rashin mutuncinki toh yanzu na tambaya"
Labarin inda muka samu kudin na bashi tun daga farko har karshe,jijjiga kai yayi tareda mikamin alamar jinjina da hannunsa,
"Yayi kyau gobe akwai maganar dazamuyi daku,akwai wanda za'a zaba zasu je Brazil wani aiki,amma sai gobe tukunna,kowa tafiyah yayi ya kwanta,kafin muji mai ogah yake tafe dashi bayan tafiyar tasu.
*+______________________+*
*ABIN YABO BOOKSHOP*
  Kasuwar  Rimi  Kano
Tel:📞 *07038339244*


❤❤SADY-SAKHNACEH❤❤

Kar ku manta da

#comment
#share
#like
#follow.

____** *GIDAN GANDU* **____
❤❤By sadi-sakhana❤❤


Wattpad username:SAKHNA03


❤19❤

Tunda safe ogah Binlad yah taramu domin yanda lavarin yake cinsa kaman arai.
Faraway yayi da cewa,
"Yawwa kaman yanda kukaji nace akwai wani abu,nasan kunga munyi tafiyha nida Samad zuwa kasar Brazil mun hadu da wasu yan uwanmu na can,suke fadamin akwai training daza a yiwa sojojin kasashe na horon hacking,kwarewar harbi da kuma sneaking,(sanda),.
Za'ayi program na tsawon shekara uku,duk wanda yayi nasarar gama wannan horo yah fito da mataki mai kyau toh ba karamin aiki zayyiba,a yanzu haka maganar dananke mun gama yin information na badda kama ga yaranmu guda uku;Na farko Samad ta biyu sameemah sannan kuma da hakeem,saboda shi yayi karatu dama a kan na'ura,sukuma sauran kowa yasan jarumtarsu da kuma boye sirri.
Jin kaman ya gama bayaninsa ne kuma gashi banji gamshashshan bayani ba yasa ni cewa,
"Amma ogah munji abinda kace,saidai munaso kayi mana bayanin a wane irin yanayi zamuje wajenne?"
"Kinyi tambaya mai kyau,ke zakije a matsayin RAUDAH ABDULSALAM,mahaifiyar kice yar najeria babanki kuma dan palastine,zamu baki password akan raudah dakuma fuskar dazaki na sakawa saboda kar a ganeki.
Kai kuma Samad zakaje a matsayin SULAIMAN BIN HUD,sai hakeem kuma a matsayin ABDULHAKEEM BIN MALEEK,na gama bayani kowa za'a bashi information akan sabon sunansa,dakuma training da ogahna zai muku kafin yasaka ku cikin sojoji ta barauniyar hanya,saboda kar a samu matsala ko kadan.
Da farko abinne mukaji shi banbarakwai ,wai zuwa kasar Brazil kuma zama na shekara uku,har mun juya zamu tafi ogah Binlad yakirani,juyowa nayi da alamar ina jinsa,
"Da farko inaso karkiyi wata yarinta a can,tunda har yanzu bakiyi shekara sha bakwai ba,girmanne kawai da kuma zallan kwarewa a harkar teranci,toh kikula sosai karsu gano ke karamace"
Abin mamaki yabani jin yadda ogah Binlad yazageni hankalinsa kuma kwance,nima karkakce kaina nayi kafin nace,
"Toh in hakane shi tsohon yaje mana tunda yana tsoron kar yara suyi shirme idan yah turasu,sannan kuma.........."
Katseni yayi ta hanyar cewa,
"Bana bukatar jin komai,tunda kinji mai na ce kuje allah yah kaimu wani watan"
Tun daga lokacin muka dukufah yin training din yanda zamu boye kamanninmu a cikin ainihin sojoji,ta hanyar sanin abubuwan daya shafesu,lokacin da results wanda zasu tafi yazo kowa mamaki yayi ,domin a cikin wanda zasu tafi candin,a cikin mu dari kowa yah taho daga sansaninsu an zabeshi da kuma wasu sojojin daga wani waje a cikin kasar,dukkan mu iyah mutum goma suka dauka wanda zasu tafi kasar Brazil,abin mamaki babu sunan Samad a ciki.
Bakin cikine kwance a kan fuskarsa ganin zamu tafi nida hakeem banda shi,da farko nayi niyyar hakura nima,amma yanda naga yana bakincikin hakanne yasa nace zanje,dan naga ya zaiyi,kuma *zama waje daya ma ai hatsarine inji kifi*,gwanda muje muga mai duniyah take ciki a dayah bangaren.
Shiri aka gama mana tsabb muka kama hanya cikin taron sojojin palastine,bisa kasada irin tamu na rayuwa.
Lokacin da muka dira a kasar wani iri naji saboda tsawon shekarata shida nafi sabawa da kasar palastine,a air Port suka saukemu mota tazo daukarmu zuwa masauki.
Tun daga washa gari muka fara aiki ba dare ba rana,wanda cikim saka abu a rai da kuma kwazo banyi wata shida ba saida ya zamo ko ina sunan RAUDAH ne yake zagawa har na fara mantawa da Sunana sameemah in ba Hakeem yakirani muna mu kadai ba.
Sukuwa sojojin palastine har murna suke saboda a cikin tawagarsu nake,shikanasa ogahn duk abinda ban saniba shiyake nunamin domin burinsa na fito da tauraro wanda zai daga kasarsa.
Lokacin da muka shiga shekara ta biyu aiki yah fara tsananta,domin har wajen kaiwa a hari ake turamu,ni ina a cikin rukunin yan hacking amma wani lokacin idan naga yannamu zasu kasa yi,bansan lokacin danake shiga cikin filin ba,da haka ta nan ma nafara koyon aikin sojoji na shiga filin yaki,dan idan na bisu mukanyi sati biyu har wata bamu dawo sansaniba.
Wani lokacin wasu su mutu,wasu kuma su dawo a wahale,mune yan basu taimako da kuma cigaba idan wasu sun gaza.
Tunda nake binsu fili ban taba dawo wa da ciwo ko dayah ba,domin a wajen yake warkewa da kansa cikin yan mintuna,duk da babu wanda ya taba yimin magana nasan kowa na mamaki,saidai suka barshi a matsayin kwarewa ta ce kawai.
Bayan mun shiga shekara ta uku sannan kam na kware a ta bangarori da dama ciki harda abubuwan da ban taba tunanni zan gansu ba ,irin tuka egwuwa,da kuma harba bombs.
Kowa hankalinsa ya tafi yanda zaici gasar karshe saboda yakoma kasarsa cikin abin alfahari da yabo.
A cikin wata na takwas kafin shekarar ta kare muka fara shirye shiryen tafiyah wajen gasa tah karshe,wanda zamu shiga cikon wani bakin dajine mai cike da arna duk wanda yah fito da rai cikin kwana goma toh sune wanda za'a bawa tutar yabo.
Mukuma masu hacking wani mission aka bamu wanda zamuyi bayan wata daya,akan wasu gogaggun barayin hacking a kasar Canada,duk wanda yayi nasara shima shine da tutar yabo.
Shiga nayi cikin yan zuwa daji muka tafi,ko ba komai zan kashe kwarkwatar ido,aikuwa naga abin mamaki,nan akayi ta artabu aka kashe mutane da dama,mu wanda muka fito babu fi mu dari ba,dan ma na taimaki wasu da yawa.
A wajen hacking kuwa kwana muke a gaban computer sai bacci ya kama mu muyi,idan mun farka mu cigaba,mun fi sati muna abu dayah kafin wani yaro a cikin mu yagano lagonsu,muka afakamusu.
Idan aka sakawa abu rana toh sai yazo,yau mune a tsaye a fili da kayan sojoji muna kiran karbar sakamako,tun waccen satin aka fara sallamar wanda sukayi nasara,dayake mune Batch C,muna kasar Brazil,yayinda Batch A suke America,sai Batch B a Canada.
Nice na karbi numaber yabo ta uku,bayan wasu guda biyu a kasashe daban daban sun karba.
Daga kyautar nayi a hannuna,ta silver sai sheki take,anyi alamar soja mace a jiki da kuma sunana wato RAUDAH, yayinda a daya bangaren kunnuwa na suke jiyomin karar sauti tafi rafff rafff da kuma harbin bindiga,kuma duk ni akeyiwa.
Kowa murna yakeyi acikinmu zai koma gida da irin nasarar daya samo,wanda suka mutu kuma saidai muce Allah ya jikansu da rahama.
Shugaban tawagar palastine ne ya taramu murna a cikinsa kamar ba gobe,bakinsa yaki rufuwa saboda murnanar nazo tah uku,a cikin kasashe da dama,magana yah faracikin harshen turanci maimakon larabci,wanda yasan kowa yah iyah saboda zamanmu cikinsu.
Kowa zuwa yayi yah kwanta da niyyar gobe za'a fara shirye shiryen komawa gida jibi kuma mu tafi,
Wani duhu nake gani saidai duk da bana gani sosai nasan gidanmune na Nigeria,wutace take cin cikin gidan amma kowa yah ki kaiwa taimako,gani na nayi a tsaye a gefen gidan mutanen cikin gidan suna ta ihuu amma babu wanda ya kulada ni,wani mutum ne naga yazo wucewa na ja rigarsa,tsayawa yayi yana kallona kafin nace,
"Bawa allah baka ganin suna neman taimakonka ne?"
"Nagani amma ke da kike yar gidanma aikin barshi ina kuma yani,ke mai zai hana kidawo ki taimakesu hannunka a baya rubewa kayanke ka zefar,saidai kayi masa magani koda kuwa maganin akwai wahala har ka samu yah warke........kidawo gida,saboda wanda yabar gida ,gida ya barshi.

****
Da sauri na tashi daga kan katifata jikina

Please Login or Register in order to submit comment